You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Downloaded From https://tknovels.com.ng [5/11, 17:15] ~fatieshak🌹: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺


https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/


*Bismillahir Rahmanir Rahim*
*Ina farawa da sunan Allah, ina neman tsari da rubuta 'Barna! Ina rokon na yi rubutun da za'a 'karu , ayi amfani da shi.Tsira da aminci ga shugaba Annabi(S.A.W.).*

*GARGADI*
_A kiyayi taba min labari na ta kowacce siga, Hakkin mallakar tawa ce ni ka'dai, Dole sai da izinina kafin a karanta shi a kowacce irin kafar sadarwa, wadda ya shiga hakkin mallaka kuma ubangiji ya isar mini._

*JAN KUNNE*
*Gaba'daya Wannan labarin kirkirarsa aka yi(Fiction)!haka sunaye da garuruwan da ke ciki bana kowa bane, na zabe sune kawai dan 'kawata labarin, dan haka duk wadda yaci karo da abin da ya yi kamacanceceniya da rayuwar sa bada shi ake ba, arashi ne kawai*

*JINJINA*
_GA MARUBUCIYA_
*FADILA LAMIDO*
*SUGARI BA KI YI FARIN BANZA BA*.


*SADAUKARWA*
_Tun daga farkon labarin har zuwa karshen sa gaba'daya sadaukawa ne ga shugaban kungiyar_ *LAFAZEE WRITERS*
*SADIQ ABUBAKAR*.



1-2




Harabar makarantar kwana ta Gwamnatin Tarayya da ke garin Kiyawa (FGC Kiyawa), cike take mak'il da motoci da jama'a kama daga iyayen yara, da su kansu daliban rukuni-rukuni, gungu-gungu, cike da walwala sai ciye-ciye ake yi kasancewar yau ake ziyarar dalibai (visiting day).

Daga can gefen lambun makarantar, wata matashiyar uwa ce da a 'kalla ba za ta wuce shekaru talatin da biyu ba. Zaune take kan lallausar darduma wacce da alamu da ita ta zo, gefenta kulolin abinci ne da kuma ledoji masu dauke da tambarin *Sahad Store.*

Zaune take tana baza ido ta ga ta ina tilon dan'ta zai bullo, ba ta ankara ba ta ji an rungume ta tare da ambaton "Mamiii!"

Cike da dariya ta dago kai.

"Jawad wai ba ka san ka girma ba ne? ba don a zaune nake ba ai da ka kayar da ni."

Ya sake komawa ya kwanta a jikinta tare da cewa,

"Nayi kewarki Mami! Ina Inna?".

"Ta ce, a gaishe ka, shekaranjiya ta tafi Gamawa biki"

"Ki ce ba ta yi mini girebar ba kenan?" Ya fada cikin turo baki irin na sakalan yara.

"Wace ita? Ai ranar Laraba yini ta yi tana hidimar girebarka, bata samu sukuni ba sai da ta kammala."

Sai a lokacin ya saki fuskar yana cewa,

"Allah Sarki Innata!" Ya tashi a jikinta ya ci gaba da cewa,

"Ina yini?"

Ta amsa tana bin sa da kallon mamakin irin girman da ya 'kara cikin lokaci 'kalilan da ba ta gan shi ba, tana mamakin inda ya sami girman jiki tun da dai daga ita har mahaifinsa ba wani girma ne da su na a zo a gani ba, hasalima in ba ka sani ba cewa za ka yi 'kaninta ne.

"Kai Mami sai kin gano munina!".

Ya fada yana rufe idonsa da hannuwansa. Ta yi murmushi,

"Girmanka ne yake ba ni mamaki Jawad ka kerewa tsawona fa!"

"To, Mami aike tsayinki kadan ne, ni kuma irin tsayin Babana na yi."

"A'a, kai kam sai ka fi shi tsayi duka-duka fa watan jiya ka yi sha uku amma ka zan'kale haka!"

Cikin shagwaba ya fara fadin "Haba mana Mami ki daina fada, kar ajiyo. I am 15 fa!"

Ta kwashe da dariya tare da cewa
"Mantawa na yi ashe ka fi ni sanin ranar haihuwarka?".

Daidai lokacin ya zuge Jakarta ya dauko tsaleliyar wayarta ya mik'a mata, ''Bude mini na kira malam na ji ko ya dawo."
Ba ta ce uffan ba, ta karba ta bude masa kamar yadda ya bukata. Lambobi ya shiga daddanawa har ya jera lambar da ke adane a 'kwa'kwalwarsa a cikin wayar ya danna kira ya kara a kunne, tamkar da ma jiran kiran ya shiga ake yi, ya ji an dauka ba tare da ba ta lokaci ba, sallama ya yi tare da fadin,

"Malam!"

Daga cikin wayar aka amsa da,
"Jawad kana lafiya? Ka gan ni nan ina kan hanyar zuwa wurinka."

Cike da murna yace. "Ka dawo daga Bauchin ke nan?"

"A'a ban dawo ba yanzu dai nake kan hanyar dawowa na iso Babaldu zan biyo ta Dutse na iso Kiyawa."

Dadi ya kama Jawad, ya shiga masa addu'ar isowa lafiya, tare da cewa, "Ina wajen da muka zauna a waccan ziyarar."

Ya kashe wayar yana cewa "Oh! Allah ya so ni, jiya fa da na yi masa waya ha'kuri ya ba ni akan ba zai sami zuwa ba sai satin sama, saboda yana Bauchi, ko don bai ji na amsa masa na ha'kura ba ne, shi yasa ya bar komai ya taho?"

Ita dai ba ta sa masa baki ba har ya kammala maganarsa.
tana nazarin lokaci a agogon hannunta daya nuna 'karfe biyu har da mintuna talatin da biyar. "Ko ina ne Babaldu kuma? Ko har zai iya isowa kafin hukumar makaranta ta rufe shigowa?"

Tabe baki ta yi tana ji a ranta to ina ma ruwanta? Amma wani sashi na zuciyarta na fada mata saboda Jawad ne, ina mama ba wadda ya zo mini? Ya katse mata tunani,

"Baban Khalifa ne ba lafiya yana asibiti ka ga ai bai kamata na yi maganar mu taho tare da wani cikinsu ba."

"Me ya same shi?" Ya tambaye ta cike da nuna damuwa.

"Malaria yake ta yi har ta kada shi."

"Muma Mami ita ake ta yi anan, Allah ya sauwa'ke ya bashi lafiya, to yanzun a tasha kika sauka?"

Ta girgiza kai tana cewa, "Shatar mota muka dauko ni da iyalan gidan Ma'aji. Ka ci abincin sai mu je ku gaisa, suna can gefen mata."

Bayan La'asar ba da jimawa ba, ya iso cikin makarantar sanye yake cikin tsadadden yadi fari 'kal! 'Kafar shi dauke da takalmi cover ba'ki, kansa cike da gashi, ya dora hular zanna-bukar wadda ba ta rufe gashin ba, 'kamshin turaren Versace ke tashi a jikinsa.
A hankali yake tafiya cikin nutsuwa, matsakaicin jiki ne dashi, amma dogo ne yanayinsa daya da tauraron wasan kwaikwaiyon nan Yakubu Muhd, ba yadda za ka yi ka kalle shi ka ce shi ya haifi Jawad, sai dan tsananin kamar da Jawad ke yi da shi.

Tun kafin ya'karaso Jawad ya hango shi, don haka ya kwasa da gudu ya nufe shi.
Ga mamakin Sa'adah, sai ta ga ya 'daga Jawad cak ya yi juyi da shi tamkar yadda yake masa yana yaro.

Ya dire shi, ya ru'ko shi ta gefen shi suka doso ta, wadda duk ilahirin mutanen dake wajen sai da suka bi su da ido suna sha'awar Jawad da Babansa.

Kujera ya samo masa ya zauna daga gefe, amma ba wani tazara da inda Sa'ada ke zaune, ta juya musu baya. Hira suke cike da doki.
"Amma anya Jawad kana karatu kuwa? Ina *C.A* Result dinka?" Ya zura hannu a aljihun wandon shi ya zaro takarda ya mika masa ya karba ya bude yana dubawa, fara'arsa na 'kara fadada, ya ninke ya kalli dan nasa ya ce, "That is my boy weldone! Ka ci gaba da dagewa."

"Ni da zan zama direban jirgin sama, ai dole sai na yi karatu Malam, ko ka manta?"

"Murmushi kawai Malam din ya yi yana satar kallon gefen da Sa'adah ke zaune kamar ko yaushe ta ci kwalliya ta burgewa cikin tsadadden leshi doguwar riga(bubu), hannayen ta sun ci jan lalle da zobunan Dubai Gold, 'kamshinta na dindin na turaran Escada sentiment, turare na mussaman mai sau'kar da nutsuwa ga duk wadda yake shakar shi, sai kai wa hancinsa ziyara yake yi.
Ta sake zamowa yar yarinya, ta fi kama da 'yan shekaru ashirin da biyar ba wadda ta ba wa talatin baya ba.
Jawad ya mi'ke yana cewa, "Malam Ina zuwa.''

Kai kawai ya kada masa, kai tsaye uwarsa ya nufa, gabanta ya tsugunna ya ru'ko dukkan hannayenta,

"Mami ki zo ku gaisa da Malam mana"

Kai ta girgiza masa alamun ba za ta ba.

"Haba Mami gaisuwa kawai?"

Kan ta sake girgizawa a karo na biyu, tana ci gaba da latsa wayarta a cikin manhajar WhatsApp inda abokan tafiyarta suka ce mata ya kamata su ta fi haka nan, kar su yi dare. dan haka ta fara tattare warmers din da ta zo da su, tare da mi'ka masa ledojin siyayyar da ta kawo masa, tana sake jaddada masa ya kula da karatu ya kuma kula da ibada, muryarsa na rawa alamun zai yi kuka ya ce mata, "Ba fa ki gai da Malam ba".

A dan tunzure ta ce "Dole ne?"
Ganin kwalla a idonsa sai jikinta ya yi sanyi ta dauki handbag din ta tare da basket mai dauke da kulolin ta ce "mu je to."

Karbar basket din ya yi suka nufi Malam din da tazarar su bai fi taku biyar ba, don haka a kan kunnen shi duk yake jin tattaunawarsu.

Ba ta isa daf da shi kamar yadda Jawad ya yi ba, ta tsaya daga dan nesa ta ce, "Ina yini?"
ji ya yi kamar ba zai amsa ba tunda a wulakance ta yi gaisuwar, Irin gaisuwar je ka na yi ka, amma ganin Jawad ya zuba musu ido, sai ya amsa har ya na tambayar Inna, wanda ta ji shi, amma sai ta yi kamar ba da ita yake ba. Hannu ta mikawa Jawad akan ya ba ta basket din, no'ke kafada ya yi tare da cewa!

"Mami, Malam fa Kano zai wuce, don Allah ki bari ku wuce tare."

Wani malolon ba'kin ciki ya sa ke turnuketa, bayan ya tilasta ta, ta gaishe shi, ya kuma sake baro wata magana.

Ba ta ce masa komai ba ta fincike basket din tana cewa,
"Na gode ba sai ka kara gani na zo ba bare ka yi mini wannan iya shegen!"

Ta juya ta fara tafiyarta mai cike da nutsuwa, da sauri Jawad ya bi bayanta, yana cewa, "Haba mana Mami kar mu yi haka da ke!"

Kawai sai ta saki basket din hannunta da jakarta ta riko shi ta ringa zuba masa rankwashi tare da dundu, a sukwane Uban ya taso ya karbe shi yana jin takaicin ta na sake kama shi, wai a makaranta ma cikin jama'a ba za ta fasa halinta ba? Sa'arsa daya ma, wajen ba mutane kusan duk an watse sai tsirarru.

Ta sunkuya ta debi kayanta ta tafi tana huci, ganin haka Jawad ya fincike daga hannunsa ya bi ta yana fadin,"Ina zuwa Malam!"

Da gudu ya cim mata ta baya ya rungeme ta yana fadin,

"Am sorry Mami, very sorry!"

"Ai ni kuma ba ruwana da kai Jawad, tun da dai kai ba ka jin magana, na hana ka wannan manyancen naka, na hana ka shiga abin da bai shafe ka ba, amma ka 'ki, to ka je ka yi ta yi."

Ya marairaice yana ba ta ha'kuri har dai ya samu ta ha'kura ya ga murmushinta.

Malam yana zaune yana kallon su har suka ba ce ma ganinsa, a ransa yana mugun tausaya wa Jawad, tun da shi burinsa a ce Mamansa na tare da su, wadda faruwar hakan sai ikon Allah.

Yana zaune, ya dawo ya tarar da shi yana ta tunani, "Ni ma ai zuwa zan yi na tafi. Mu je mota ka kwaso kayanka."

Daidai lokacin wayarsa ta dauki ruri, yana dubawa yaga matarsa ce Farida ya amsa, tambayar Jawad ta yi, wayar ya mi'ka ma yaron tare da cewa, "Karbi!"

Ba wani karsashi ya karbi wayar har ita ma ta ji babu dadi tana tambayar shi ko lafiya ya ce mata, "Lafiya lau!" Bana son Malam ya tafi ya tafi nee, sannan baku zo ba ke da Hajiyan Bichi".
ta shiga bashi hakuri cike da murna ganin ya fara dawo mata tamkar farkon zamansu.

Suna tafe yana masa nasiha tare da nuna masa ba ayina uwa ba a yin musu da ita, dole a bi ta yadda take so, sannan ya daina shiga matsalar da ba tashi ba, hawaye yake gogewa tare da cewa,

"Ni dai Malam ka dawo da ita gidanmu ni ma in dinga ganin Mamana a gidanmu, kamar yadda nake ganin na friends dina, kowa Mamansa da Babansa tare suke zuwa masa amma banda ni!"

Ya 'karasa cikin kuka sosai, janyo shi jikinsa ya yi yana dan bubbuga bayansa alamun rarrashi yana cewa
"Ina ce ni ma tare da Antinka nake zuwa maka?"

"Amma ai ba da Mamana kuke zuwa ba!"

"To ka kwantar da hankalinka, ka dinga mana adddu'a sai ka ga very soon ta dawo har ma ka zama Yaya Jawad kana so?"

Ya daga kansa tare da sa hannu yana goge hawayen da ya'ki tsayawa.

"To in dai kana son haka, ka daina damuwa ka kuma daina yiwa Mami maganar bare ta dake ka, kawai addu'a za ka na yi, ni kuma ka dinga tuna mini, wataran sai dai ka dawo hutu ka ganta a gidanmu."

"Malam da gaske?" ya tambaya cike da zumudi.

"E Mana indai ka daina kuka, ka daina damuwa, ka daina damunta, kana addu'a to ina tabbatar maka ba abin da ya fi addu'a juya lamura!"

Murmushi ya shiga yi yana goge hawaye da handkerchief din hannunsa yana 'fadin,
"Ai ko Malam ban san murnar da zan yi ba,, kuma har da kai zan 'dauka a jirgin nawa".

Dariya Mk ya yi tare da cewa "Ai kuwa dai nima naji dadi tunda albakacin Mami zan shiga jirgin Jawad"
Kunya ta kama yaron yace "Ai dan ita bata taba shiga bane"

Ya sake cewa, "Malam ka gai da Hajiya, kuma ina zuba idon zuwanta, tunda ba ta zo yau ba, ina bin ta bashi!"






Alkalamin
Surayya Dahiru ✍️
[5/11, 17:15] ~fatieshak🌹: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺






https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/





*Tukuici ga*
*FADILA LAMIDO*
*BINTA UMAR ABBALE*
*ZAINAB MAZAWAJE*

*Nagode da Shawarwarinku da 'karfafa guiwa, Allah Ya saka muku da alheri, Ya 'kara daukaka.*


*GODIYA GA MAKARANTA*
*Na gode da yadda kuka 'karbin wannan labarin, ha'kika jiya na ga ruwan masoya, ban yi zaton a 'kankanin lokaci littafin zai 'karade duniyar karatu haka ba, na gode muku sosai, in sha Allah ba za ku yi NADAMAR bibiyar wannan labarin ba!Heart U all*


3-4




A sanyaye ya fito wa da Jawad kayayyakin provisions din da ya kawo mishi, tamkar wanda zai yi rabin shekara bai je gida ba, yana sake jaddada mishi ya daina damuwa ya kuma ci gaba da karatunshi.

Ya shiga mota Jawad na 'daga mishi hannu har ya fice, bai yi nisa sosai ba don kuwa bai gama barin garin Kiyawa ba, ya hango su Sa'adah da wasu matan a waje, gefe kuma an bude motar bakanike sai tabe-tabe yake, ga dukkan alamu motar ce ta lalace musu, kamar ya wuce sai kuma ya kasa.

Don haka sai ya tsaya a gabansu, bai fito ba, sai ya lalubo lambar da Jawad ya kira shi da ita dazu, ya san tabbas layinta ne duk kuwa da ba ainihin layin ta ba ne daya santa da shi.

Ya danna alamar kira, yana hango ta tana ta kici-kici da jakarta wurin lalubo wayar, amma abin mamaki ya ga ta fito da wayar amma ba ta dauka ba har ta katse, mamaki ya kama shi wai yaushe Sa'adah ta ko yi jarumta akan lamarinsa ne?
Ya yi jim yana tunanin rabon da Sa'adah ta shiga harkarsa, ba shakka ba lokaci ne Mai tsayi, ba ta sake neman shi ba, ba ta sake duba dukkan lamarin sa ba, ta yi fatali da shi da dukkan soyayyarshi, abin da ya dade yana mamakinsa. bai daddaraba, ya sake 'kira tana gab da tsinkewa ta daga ba ta yi magana ba, amma dai ta kara a kunnen ta, sanin halinta da ya yi na ba za ta fara magana ba, yasa shi cewa,

"Ke na gani a titi a na muku gyaran mota?".

Cikin rashin nuna damuwa ta ce "A a ba ni ba ce."

Bai yi mamakin amsarta ba ya ce. "Amma ba ke ce nake hangowa a tsaye kina amsa wayar nan daidai jikin Alheri bread🍞 ba?"

Shiru ta masa sai ji ya yi ta ma ka'tse wayar gaba'daya.

Shiru ya yi ranshi na suya ya na sake jaddada halayyarta a jininta ne ba za ta sauya ba.

Har ya ta da motar da niyyar barin wajen ta je ta 'karata, sai kuma ya tuna uwar Jawad ce tilon 'dansa, ya tabbatar da tare yake da Jawad din, ba zai yarda su tafi su bar Maminshi a bayan gari jejin Allah ba, ga yamma ta yi likis sosai, sanyin da ake 'dan busawa ya sake taimaka wa garin ya yi dan duhu, don haka sai ya fito bayan ya kulle motar ya nufe su.

Yana zuwa ya ga har da Zainab Ma'aji da wasu mata biyu da bai gane su ba.

Ita ko Zainab tana ganin shi ta saki fuska."Lah! Uncle kai ne ashe."

Ta gaishe shi irin gaisuwar da dalibi ke yi idan ya ga malamin da ya koyar da shi a baya. Shi ma ya amsa da jin dadin girmama shi da Zainab ke yi tun fil azal.

Hannu ya mi'ka ya dauki yaronta Walid ya masa wasa sannan ya ce, "Motar taku lalacewa ta yi ne?".

"E wallahi ga mu nan dai ana ta faman gyara".

"To ku zo mana mu wuce tun da ba tabbacin za ta gyaru yanzu".

Kallo ta kai ga Sa'adah da ta koma baya ta yi kamar ba ta gan shi ba, ta kuma cika ta yi fam kamar kububuwa.

Zainab ta ce "To uncle bari na yi wa abokan tafiyar tamu magana."

"Okay"
Kawai ya ce, yana ci gaba da wasa da Walid dake ta bingila mishi dariya tamkar ya san shi.

Bayani Zainab ta musu kamar yadda ya bu'kata, dukkan su sun amince, su bi shi, amma ban da Sa'ada. Don haka Zainab da 'yan uwanta su ma suka janye tun da dai ai sun san saboda ita ya tsaya har ya nemi ya taimake su, to kuwa ta ya ya za su ce za su bi shi alhalin ita ta yi rantsuwar gara ta kwana a nan da ta shiga motarsa!

A matu'kar kunyace Zainab take ba shi ha'kuri tare da ba shi uzirin direban ba zai ji dadi ba, ya san sarai Sa'ada ce ta'ki amincewa, amma sai ya ce ai zan sallame shi ku zo mu tafi kawai.

Nan ma sai ta sake dora wa 'yan uwanta laifi akan yayarsu tace ba zasu sab'awa direban al'kawari ba. Ya jinjina hankali da Zainab ke da shi, duk da ya san 'kawar ta ce ta'ki amincewa, amma ba ta fadi hakan ba, sai kariya take ta bayarwa, ina ma tun farko Sa'ada ita ta ri'ka a matsayin 'kawa, ba bara gurbi irin su Halima da Safina ba?

Wanda 'kawacenta da su bai amfane ta da komi ba sai muguwar asara da nadama, tunda sun mata ingiza mai kantu ta yarda har ta tsinke igiyar aurenta, a yanzu kuma sun bar ta sun koma suna zunden ta.

Don haka sai yace "To shi kenan ba damuwa ya matsa ga bakaniken dake ta iyakar kokarin shi don ya ga motar ta tashi.

magana suke yi da direba, cikin ikon Allah ba a wani dauki lokaci sosai ba motar ta gyaru, amma har an yi sallar Maghriba, dan haka malam da direban suka yi jam'i suka yi sallarsu, yayin da matan suka shiga wani kewaye su ka yi ta su.

Bai yarda ya tafi ba sai da ya ga tashin su sannan ya taka ya isa inda motarsa take shi ma ya bi su a baya.

A cikin motar kuwa yayyen Zainab sai caccakar Sa'ada suke da rashin kirkinta, "A haka kike son komawa gidan nasa? Ba kya girmama shi, a gaban kowa za ki iya keta shi?"

Cikin turo baki ta ce "Ni fa Anty da ne na yi haukan banza na son sai ya mayar da ni, yanzu kuwa ko ni da shi muka rage ba na sonsa ba zan koma ba"

Cikin fushi ita ma Anty Asiya wadda ita Zainab ke bi, kuma da ita duk a ka yi gwagwarmayar su Sa'adah, ta ce, "Ai shima ba son naki yake ba, shashasha da ba ta san me ya kamata ba."

Dattijon dake jan motar ya ce, "Um'um fa! Ba'a shiga lamarin mace da namiji, ai koni da yau na fara ganin su na hango soyayyarta mai yawa a idonsa da gangar jikinsa, ita ma kuma duk wannan kumburin da take yi da fiffi'ka duk soyayyar ce, da alama dai kishi ne ke dawainiya da ita a kansa, dan na ga fishi take mai tsanani da shi!"

Dukkan motar a kasa dariya a na cewa Baba ashe duk ka gano su?

Yace , "Haba yara mu da muka ga jiya muka yau, ku duba fa duk iya shegen da ta yi akan ba za ku bi shi ba, bai fa iya tafiya ba har sai da ya ga tashinmu, wannan kadai ya isa kowa yasa lunzami a bakinshi akan lamarinsu, suna da yara ne?"

Zainab ce ta ce "Yaro ne daya har ya fara girma, shi suka jewa visiting"

Ya ce, "Ai shike nan magana ta 'kare, ko kowa bai musu sulhu ba, yaron zai zama tsanin afuwa a tsakaninsu, mu yi musu addu'ar fatan alheri, amma soyayya akwai ta"

Aka sake sa dariya ban da Sa'ada da ta yi kicin-kicin da fuska.

Tsohon ya sake cewa, "Ina cewa da za mu zo ita ce a gaban motar nan haka da za mu dawo,har muka zo inda motar ta lalace ita ce a gaban?amma ina ganinsu da za ta shiga gaba ya galla mata harara sai kawai naga ta shige baya."

Gabadaya aka sake dariya har da Sa'ada wadda ita ta karfin halin wannan bawan Allah ne, ita ba ta ga harara ba, ta san kuma tabbas bai yi 'karya ba, kaifin idon Malam ne yasa ta kasa shiga gaban motar wani akan idonsa, sai ta bige da cewa "Lallai Baba ba komi na gode" da haka ta sace ta daina fishi.

Shi ko Malam yana tafe yana ayyana abubuwa masu girma game da lamarin ta, komai nata burgeshi yake, bai ta ba ganin halittar da ke daukan hankalinsa irin surar ta ba, kawai wasu daga cikin halayyarta ke 'dimauta tunaninshi su hana shi zaman lafiya amma duk sanda zai dora idonshi a kanta sai ya ji bai ganin komai da kowa sai ita.

Har yau har gobe yana son ta, amma ta riga ta shayar da shi bakin cikin da zaman aure zai yi wuya tare da su. Har suka iso Kano tunaninta yake idan ya tuna *happy moments* dinsu yayi murmushi, idan ya tuna *though times* dinsu sai ya ja tsaki ko ya furta ya *Salam* ko *SubhanAllah.*

Ba su rabu ba sai da suka zo Gandu ya yi wa direbansu fitila ya wuce, a nan ma sai da Baba ya tsokaneta da cewa

"To Sa'adatu wannan fitilar fa da ya yi bata kowa bace, taki ce!"

Suka hada baki wurin fadin, "Ai kuwa dai Baba!" suna kuma dariya.


```Alkalamin
SURAYYA DAHIRU``` ✍🏼✍🏼


🌺 *HALIN YAU*! 🌺





```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

`

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/

*SADAUKARWA GABA'DAYA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*




5-6



Har 'kofar gidan yayarta Sumayya suka kaita dake kan titin Kwankwaso Gandun Albasa, sannan suka juya,
Baba direba, nata jaddada mata ta daina saurin fushi mabudin fitina ne, ta yi godiya, tana cewa su Zainab sai nan da kwana uku za ta dawo unguwar tasu lokacin innarta ta dawo daga tafiyar da ta yi.

Da sallamarta ta isa cikin katafaren falon Sumayya, ba kowa sai TV da take ta babatu hadi da dan dirin AC da ke tashi a hankali, ga 'kamshin *Air Freshner* dake tashi sannu a hankali, take ta ji duk gajiyar da ta kwaso ta taso mata gabadaya.

Dan haka sai kawai ta zube a Kan doguwar kujera ta yi kwanciyar ta ba ta jima da kwanciyar ba, barci mai nauyi ya yi gaba da ita.

Sumayya fitowa tayi daga bangaren maigidan, da a yammacin yau aka sallamosu daga asibiti, ta ganta tana ta barci. Murmushi ta yi tare da cewa, "Oh a 'yar wannan tafiyar ne kika gaji har haka?" Ta gyara mata rigarta da ta 'dage, ta shige kicin don hada tea.

Hayaniyar

Please Login or Register in order to submit comment