You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya musu jagora har dakin da Mk yake kwance.

A zaune suka taradda shi, Farida tana tsaye a gabansa hanunta na dama ri'ke da hannunsa, yayin da hannun na hagu ri'ke da kwandon zuba abinci, alamun tafiya zata yi.

Zuciyar Sa'a ta buga da tsananin gaske, ta zabura, zata koma da baya, Zainab da Abbas kawai suka lura da hakan, Dan haka cikin hikima Zaynab ta ru'ko hannun ta da karfin gaske, kan dole suka karasa shiga sosai.

Zainab suka gaisa da Farida ta tambayi mai jiki, sannan ta gaida Mk da ya yi mutuwar zaune, saboda yadda ya ji wani abu da bai san menene ba ya dirar masa, gashi dama fama yake da rashin karfin jiki.





Surayya Dee
โœ๏ธโœ๏ธ.


๐ŸŒบ *HALIN YAU*! ๐ŸŒบ

*NA*

*SURAYYA DAHIRU*.


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ยฎ_* โœ๏ธ
โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ษ—amfare da bin ฦ™a'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
____________(โœช)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*



*GAISUWAR GIRMA GA*
*HAJ SALIHA A.A. ZARIA.*
*MARUBUCIYAR BEGE*
*ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA MAI ALBARKA*.

104-106.


Farida na ri'ke da hannun Mk, ta kalli Sa'a da murmushi ta ce "Maraba da Gogel, karaso kusa mana".

Takaici a zuciyar Sa'adah tamkar ta rushe da kuka, ta ki sakar masa hannu dan ta nuna mata itace matarsa. Sannan dan ta tabbatar mata ita bakuwa ce yanzu a wurin Mk, shine take mata iso a gabansa?

Ta daure ta hadiye damuwarta ta yi kamar bata ga hannuwansu a sarke ba, ta cewa Farida "Sannun ki".

Daga inda take tsaye ta kalli Mk ta ce "ya ya jikin?"

Daga haka ta tsuke bakinta, tana karanta duk addu'ar da ta zo bakinta, tabbas Mk ne ya wula'kanta ta saboda ya nunawa Farida ita ba wata tsiyar ba ce. Shiyasa ya ki zame hannunsa da yake cikin nata.
Amma ai ya yi da yar halak.

A hankali Mk yake kallonta ta kasan ido, yana nazartar yadda take kokawa da fishin da ya ke yun'kuro mata.

Cikin hikima ya zare hannunsa a hannun Farida, gumi sai yanko masa yake yi.

Da sauri Farida ta 'kara karfin A.C da gudun fanka, saboda zufar da taga na karyo masa wadda kawai ta fargaba ce. A ransa ya dinga nazarin anya zai iya jarumtar ri'ke mata biyu kuwa? Saboda yadda ya dinga zullimin kasancewarsa a gabansu a lokaci 'daya.

Mk na wanna tsinkayen ya ga Farida ta ajiye kwandon hannunta tabbacin ta fasa tafiyar kenan.
Wato duk ha'kurin mace ta iya shu'umanci indai akan kishi ne?
Yau ya gasgata hakan domin ko kaffara ba zai yi ba, idan ya yi rantsuwar saboda Sa'adah ta 'ki tafiyar.

Dan haka ya yi kicin kicin da fuska, ita kuma sai kokarin yi masa fifta take yi.

Yayin da Sa'adah da Zainab suke ganin ikon ubangiji na yadda Farida ta kankane komai, Zainab da Mk ne suke mamakinta. Yayin da Iyah ta san dama Farida zata yi abin da ya fi haka.

Abbas ne ya leko daga bakin kofar ya ce "Farida ina ta faman jiran ki, so nake na yi maza na kai ki na dawo, kafin su tafi kar abar shi ba kowa, Hajiya ta tafi tun dazu, zan biya na dauko su Anty Amina Kuma".

Ai kuwa ta ce "je ka dauko su kawai, idan Akil ko Ahamad sun zo, sai je su dauko mini motata, ko kuma na fita na hau adaidaita sahu".

Abbas ya yi sakare yana mamakinta a ransa tare da cewa "Ah adole ita ba zata basu damar ganawa ba, duk da dai bata nuna bacin rai ko damuwa ba.

Sai a lokacin Mk ya ce" amma kin san ban son Ahamad yana hawa motar ki saboda ba ya tuki da nutsuwa, Akil kuma yana shago sai dare ya fara jah yake zuwa".

Ta marairaice ta ce "Ba damuwa sai na hau adaidaita sahu".

"A a bana so kin sani, bana so".
Ya sake sassautawa "ya ce ki je ya kai ki, ana idar da Sallar isha ki rufe gidan, sannan ki taimake ni ki sha maganin ki please".
Ya fa'da cikin sigar rarrashi da kulawa.

Amma ta yi mirisisi ta ki tafiya, lamarin da ya sake dagula lissafin Sa'adah, wai yau a gabanta wata macen take nunawa ta fita son Mk, ta fita kusa da shi.
A gabanta shima ya ke nunawa wata macen tattali da kulawa? Wannan shine duniya rawar yanmata.
Shirun da Farida ta yi ya tabbatarwa da Mk bata amince bane, ya kalleta a tausashe ya ce "Ban son ki wuce lokacin shan maganin ki ne, gobe idan zaki taho, ki taho da shi, sai ki yi ta zamanki, amma yanzu taimake ni ki je ki kular mini da lafiyar ki".

Nan ma ta yi shiru, Mk ya ce "shikenan ai, tunda so kike mu kwanta gaba'daya".

Dakin ya yi shiru na mintina uku, Zainab na mamakin irin wannan al'amarin, ta kasa cewa komai duk da bakinta cike
yake da tarin maganganu, da suke bu'katar fashin ba'ki.

Irin kallon da Farida take yiwa Mk da idanuwanta masu maiko ya sa
nan da nan zuciyar Sa'a ta hauro, ta kalli Abbas dake bakin kofa yana tsayawur jiran Farida, amma ganin Sa'adah yasa ta fasa tafiyar dan kar ta samu damar 'dagawa mijinta hankali ๐Ÿ˜€

Ta ce "Uncle Abbas"

"Na'am Anty Sa'adahtu".

"Tafiya zan yi, kuma akwai sakon da zan fa'da masa, zo ka ri'ke mini shi zuwa waje na mintina kadan".

Da sauri Abbas ya shigo yana cewa "daga nan ma na zagaya da shi, dazun nan likita ya gama ce mini kwanciyar ta yi yawa, ya dinga yin atisaye ko a cikin dakin nan ne".

Ya isa jikin gadon ya mikawa Mk hannun, ya dago shi.

Ya sunkuya ya janyo masa takalma a a kasan gadon ya saka sannan ya mikar da shi, suka fita a hankali.

Zainab ta dinga jin wani irin farin-cikin iyakar da Sa'a ta nunawa Farida.

Sun Jima da fita sannan Sa'adah ta dauki handbag dinta zata bisu, Farida ta ce "Gogel ko zaki fitar masa da kujera, jikin nasa ba kwari har yanzu".

Da sauri Sa'adah ta saki murfin kofar, ta dawo ta zuba mata ido, sai kuma ta sassauta fishinta tace "Da a ce Sa'adatu Kika kira ni da shi, da ko kula ki ba zan yi ba, sai dai na ce miki to, ko da ba zan yi abinda kika ce din ba, sai dan na nuna miki am matured now. Amma tunda Kika 'Kira ni da Gogel zan tabbatar miki har yanzu waccan Gogel din ce dai da kika sani, Billahillazi ki fita a idona, kada ki sake yun'kurin shiga tsakani na da shi, ko ki nuna mini ga yadda zan yi masa, if not kin dai sani. Ba zai zamewa Iyah Basiru komai ba wajen nuna miki har yanzu ina cikin shekarun da ba a mini kan kara ban yi na ice ba".

Daga haka ta juya tana cewa "Zainab zo muje, idan na gama sai mu wuce ba sai na dawo nan ba".

Suka fita bayan Zainab ta cewa Farida Allah ya Kara lafiya.

Sun zo inda su Mk suke zaune, Zainab ta yi masa addu'ar samun lafiya mai dorewa ta yi gaba, haka Abbas ma ya mike suka basu wuri.

Sa'a ta zauna tamkar gaske magana zata yi masa, amma ban da cika tana batsewa ba abin da take yi.

Ta tabbatar Farida na hango su ta windo, shiyasa ma da ta zata zauna sai ta juya baya ta yadda ba zata ga fuskarta, ba haka ma Mk bayansa zata hango.

Banda son ta nunawa Farida dan taki tafiya ba shine dalilin da zata hanata magana da shi ba, da bata tsaya kula Mk ba, tunda agabanta yake nunawa Farida soyayya har ya na lallaba ta.

Dukkansu kowa fishi yake da dan'uwansa, domin ganin ta da ya yi da Khalil ba karamin kidima shi yake yi ba, dan haka, ya danne zuciyar sa ya ki mata magana.
Amma dai a kasan ransa sun bashi dariya ita da Farida kwarai da gaske.

Mintina ashirin na cika ta tashi ga mamakin Mk ya ga ta mi'ke tana murmushi ta fito da wayarta ta Kira Zainab tana fa'din idan Abbas na kusa ki ce masa ya zo mun gama".

Aikuwa sai da Abbas ya zo, ta tafi bata ce da shi uffan ba, sai Abbas ta yiwa sallamah da fatan samun lafiya ga marar lafiya. Mk ya bita da ido yana ganin yadda take tafiya, sai ayyanawa yake yi ko sai yaushe zata daina rikicin gan-gan?

Ban da karfin halin Sa'a ya zata zo ta tarar da mace da mijinta, sannan ta ce sai ya fito waje sun yi magana alhalin ba maganar zata yi ba, kawai son rikici ne da son nunawa Farida karfin da take da shi a zuciyar sa.

A mota Zainab ta ce "Tabdi yau na ga kishi, ashe haka abin yake?"

Sa'a da dama kiris take jira sai kawai ta fashe da kuka.

Jikin Zainab ya yi sanyi sai kuma ta ce "Menene abin kukan kuma? Duk irin jarumtar da Kika yi".

Ta kasa magana illah kukan da ya ki yankewa, tana ta hararo hannun Mk a cikin na wata a gabanta kuma, tabbas har ta mutu ba zata daina kokawa ba.

Da kyar Zainab ta shawo kanta, "kin samu labarin auren Halima next week?"

Murya a dakushe ta ce " a a"

Zainab ta ce "to ai ke ce kinki shiga cikin group din mu na old girls a WhatsApp".

A sanyaye sosai ta ce "Bar ni kin ji, inace ga abin da biyewa 'kawayen ya janyo mini, kina kallon yadda wai magana da Malam ya zama sai an mini iyaka. Ta rushe da kukan da ya sanyaya jikin Zainab, itama idonta ya ciko ta kasa ce mata komai, tana tuki tana taya Sa'adah kuka.

Da kyar Zainab ta shanye kukan ta ce "Ai Halima tana cikin bala'i ke har Safinan ma, domin dai saurayin Halima ya ki aurenta ne adalilin wastewarsu suke yi. Dake akwai alaka tsakanin su da gidan iyayen saurayin shine aka masta masa amma ko kadan babu kwanciyar hankali a tare da ita.

"Ita Kuma Safina har yau dai bata karbi result dinta ba, kiga dai a bayansu da shekaru masu yawa kika shiga makarantar amma kin kammala kin barta".
Aure kuwa shiru kake ji sai dai ana nan ana addu'a. Komai lokaci ne. Amma su kam hakkin kashe aure ne ya saka suka kasa samun nasu auren".

Cikin kuka sosai Sa'a ta ce "Tabbas su Halima sun yi wa rayuwa ta illah, Amma kuma ai da gudunmawata, yarda na yi da su, sannan nima ina da tawa matsalar, bayan wadda suka cusa min, kawai iza mini wutar suke yi, Amma ni na hura abata.
Dan haka na yafe musu, amma bana fatan mua'amala ta sake hadamu, rabona da su tun ina gidan Malam, in sha Allah kuma rabuwarmu kenan domin tarayya da su halaka ce, na rufe babinsu har abada, dan haka kema daina yi mini maganar su".

Zainab ta dinga lallashin Sa'adah da maganganu masu taushi, tana nuna mata, ta yawaita addu'ar sau'kin kishi, itama zata taya ta, sannan yadda ta yi maganar a fita mata da shi waje suyi magana a gadarance, amma ya tashi duk da baya jin da'di ya isa ta gane har gobe ita ke jan ragamar zuciyar sa, sai dai dole ya yiwa Farida adalci domin matarsa ce, dole kuma zai sota.

Zainab ta nisa ta ce "Dan Allah Sa'adah ki 'dore da kyawawan dabi'un ki, kar ki bari kishi ya mayar da ke 'yar gidan jiya, kin san dai yanzu ba ke ka'dai bace, kuma Wallahi duk son da namiji yake yiwa mace indai ta cika kishi da korafi, fita fit take yi a zuciyarsa.
Ke ce uwargida tunda baki yi wani auren ba, dole ki 'dauki hakuri mai yawa. Ki koyi hakuri da juriya, duk yadda kike da mutum kar kiyi zancen abokiyar zamanki da ita mussaman dangin miji, domin duk ranar da abu ya ha'do ku da su, sai sun zayyane mata komai, a hada da sharri ma, daga nan girman ki ya zube a idonta, itama kuma ta sami damar da zata dinga fa'din munanan dabi'un ki".

"Na gode miki Zainab! Na sani ke din mai sona ce ubangiji ya sanya mu cikin masu zumunci dominsa".

Sa'a ta fa'di hakan a sanyaye.

Zainab ta ce "gida zan ajiye ki, ko gidan Anty Sumayya?".

A tunzure ta ce "gidan ubana zaki ajiye Ni, ai Ni da gidanta sai ta neme Ni".

Zainab ta yi shiru! ta san tana tofawa baza su rabu cikin da'din rai ba.
Wasu daga cikin halayyar Sa'a a jinita ne ilimi ko shekaru ba zai sa ta sauya ba, rikici na cikin abin da ba zata daina ba.

A Daren ranar Baba Isa ya dawo asibitin ya fa'dawa Mk ranar juma'ah mai zuwa za'a mayar da aurensa da Sa'adatu, amma ta nemi abarta ta kintsa kafin ayi maganar tariya tunda titsiye ubanta ya yi mata, ba dan tana so ba.
Ya ce " Na kuma yi mata wannan laminin, dan haka ba zata tare ba, sai ta shirya, wannan umarni na ne".

Baban ya nisa ya ce "Soyayya da sanin darajar Dan Adam ne kawai ya sanya Malam Basiru zai sake baka aure a Karo na biyu! Ka sani da ni da mahaifinka ra'ayin mu daya, shawarar mu daya, hakanan neman kudinmu daya, abin da Zan fa'da maka yau, na tabbatar da yana raye a gabansa zan fa'da maka domin ka sani idan ina waje baya ta'ba nuna shine ubanku yana dora ni akan komai nasa matu'kar anan Kano ne, da bashi da dan'uwan jini.
To ka saurare ni da kyau ni na karba maka amanar yarinyar nan, idan har ka bari ta wulakanta ina rantse maka da Allah ni ka wulakanta, na kuma tabbatar idan har ka wulakanta ni, zaka wulakanta Kabiru, hakkin abotarmu ba zai bari ka ga haske ba, ko bayan ba raina, ina maka wasiyya akan yarinyar Malam Basiru domin ni dai banga mai arziki a wannan zamanin irinsa ba, Ubangiji ya bashi wadatar zuciya, ya bashi alheri mai yawa, wadannan kuma sune kololuwar arziki".

Da tsananin farin ciki Mk ya ce "Na ji Baba, in sha Allah ba zan sake kunyata ku ba, komai zata yi zan yi ta ha'kuri, zan kara hakuri akan ha'kuri. Ya sauko ya durkushe a gaban dattijon ya ru'ko hannun sa ya ce " Baba ina maka shaida baka watsar da iyalin amininka ba, har yau din nan da tsufa ya cimma maka sosai, baka huta da yi mana hidima ba. Ina yi maka fatan samun aljannar da Annabi ya yi bishara ga masu kyautatawa iyalan wadda suka rasu".

Jin wannan albishir din ya sake 'karfafawa Mk jiki, domin zuciyarsa ta yi haske. Washagari da safe aka sallame shi.
Ya isa gida bisa rakiyar Dr 'Karfi, tarba na mussaman ya samu daga Farida.

'Karfi bai jima sosai ba ya tafi. Mk ya dinga biyewa Farida na yadda take ina ka saka da shi.

Ya fito wanka ya tarar da ta ajiye masa kaya a bakin gado, gajeran wando ne tiri kwata kalar ruwan 'kasa, sai farar riga ti.shet ya fesa body spray ya sanya kayan da ta riga ta feshe su da turaransa na Versace.

Tawul din da ya dauro, ya dauka ya rataye shi a bandakin, yana fitowa ita kuma ta shigo dauke da tiren kayan abinci.

Yana zaune bakin gado yana kallon yadda ta yi masa shimfida, ta fara zuba masa abincin da ya kasance dankalin turawa da miyar albasa sai gashashiyar kaza, gefe yankakkiyar kankana ce jawur da ita, an lullubeta da ledar rufe abinci.

Sama sama ya ci abincin, ya mayar da hankalinsa wurin shan kankana, ya kalleta ya ce "zanga ranar da zaki daina bani lemo da safe".

Ta mike da sauri tana cewa"wallahi na dafa maka shayin ga su cups nan flask din na manta".
Cikin kankanin lokaci ta kawo masa, da kanta ta zuba masa, tunda ba ma'abocin shan shayi da madara bane.

Bayan ya kammala ta 'ballo masa magungunansa ya sha.

Ya mike ya ce " Bari na sauka na dan kewaya, bana jin ciwo a tare da ni, amma sam jikina babu karfi".

Ta ce "hakan ma babu laifi, ko na dauko maka lucozade it will help".

Ya kalleta ya ce "Bari na kewayo dai, so nake mu yamutsa shimfidar can."
Ya yi nuni da gado.

Kunya ta kamata ta yi murmushi, ba tare da ta sake cewa komai ba.
Ya juya ya fita.

Hakan kuwa aka yi, domin bai wani jima ba ya dawo, hakanan duk yadda yake jin rashin kuzari, sai da ya zartar da kudirinsa. Duk yadda take ro'kon ya bari ya warware sosai, amma bai ji ba.

Sai fa'di yake "kewar ki na yi sosai, har addu'a nake na samu sauki na dawo gida, ba dan komaai ba, sai dan na kasance tare da ke".

Da'di ya matu'kar kamata, ta tabbatar tana da matsuguni a zuciyar mijinta. duk dai abin da Sa'adah ta yi mata a asibiti, yasa ta gane har gobe tana da karfi a zuciyarsa.

Yini guda bai fita ko ina ba, da aka yi azahar ya ci abinci, ya sha magani barci ya yi sosai.

Dan haka bai fita ba, sai a washagari, ya fita zuwa gidan Hajiya, fa'da da Jan kunnen da ta yi masa akan ya ri'ke Sa'a da girma ba ka'dan bane.

Fa'di take "ubanta mutum ne har da rabi, ka ji tsoron ubangiji ka ri'ke ta da Amana, na sha fa'da maka ba hankalin ku daya ba".
Ya amsa da zai kiyaye.

Daganan ya leka shagonsa, ya kuma gaida Baffah.

Baffah ya ce "wannan karon ma sadaki kawai zaka bata"

Da sauri ya ce "A a Baffah bar ni kawai na yi mata komai, gatan zai mini yawa, yanzu Ina da halin yin dukkan abin da ake yi, na gode sosai da karamci, Ina fatan kar Allah ya sa na sake kunyata ka Baffah".

"A a ni ba ka kunyata ni, bare ka nemi tsari da sake maimaitawa, ba komai tsakanin mu sai karramawa, domin tunda kaki fa'dar abin da ya hadaku, kuma kowa ya gane itace mai laifin, sai na gane kai din jarumine, adaline, mai kuma kaunata ne, Koda ha'kurin ka ya kwace amma ai hankalinka bai kwace ba, domin baka tozarta mini Iyah ta hanyar fa'din aibunta ba, dan haka Ni baka mini komai ba, sai alheri."

Ya zarce da cewa "a farko da zan baka ita, sai da na jaddada maka kar ka bari ta kangare maka, duk kuma wadda ka ga tana mu'amala da su, hankalinka bai kwanta da su ba, ka shata musu layi, Ina jin dai baka dauki wannan shawarar ba shiyasa kuka tsinci kanku a halin da kuke ciki, ba fa zan rufe ka ba, kaima kana bari soyayyarta na rinjayar ka a gurare da dama, a farkon rikicin banyi magana bane saboda yadda ka boye komai ka sata itama ta rufe komai"

Mk da ya san Baffah gaskiya ya fa'da sai ya sunkuyar da kansa kasa, ya kasa cewa komai.

Tsawon lokaci kafin Baffa ya sake cewa "Na horeka da yin adalci a gidanka, ka yi iyakacin bakin kokarinka, ka yi adalci, sai kuma ka barwa Allah ya taya ka. Domin a yanzu ma ina sake fa'da maka duk abin da bai maka a tare da Iyah ba, tun kafin ku yi nisa ka taka burgi akansa, su mata da ka gansu idan ba a kula da tarbiyar su ba, nan da nan zasu halaka kansu su halaka mazansu".

Jikin Mk ya yi sanyi, domin kuwa a kullum dabi'un Baffah na fahimtar da shi bai gama saninsa ba, har yau din nan bai ci karo da mutumin da ya fi mahaifin Sa'a karamci da fadar gaskiya ba, ko da kuwa gaskiyar akan kansa ne.

Mk da ya rasa mai zai ce sai kawai ya sunkuyar da kansa kasa ya ce "Madallah da zuciya irin taka, dama ka sha fa'da mini ba Sa'a ce ta hada mu ba, ba kuma zata zama dalilin rabuwarmu ba, tabbas na gasgata hakan".

Mk ya zarce da fa'din
" Alherinka yawa ne da shi Baffah! A duk lokacin da nake gabanka sai nake jina tamkar ina cikin shekaru irin na Jawad. Saboda zuciyata tana samun nutsuwa, domin tana tare da wadda yake girmamata, yake ganin kimarta. Kai ka'dai ne baka ga laifina akan kaddarar rabuwarmu ba, Kai ka'dai ne ka yi mini shaidar fin 'karfina al'amarin ya yi, haka kai ka'dai ne a duk tsayin wannan tafiyar bai juya mini baya. Haka nan yanzu kowa jan kunne yake mini akan na rike Sa'adah komai zata mini na yi hakuri, kar na ce komai.
Kai ka'dai ka ce na yiwa 'daya matar tawa adalci, kai ka'dai ne ka ce kar na yi hakuri da Sa'adah a inda zata kuskure ko ta sab'awa ka'ida.
A yau na sake ganewa kai din ba uban Sa'adah bane nawa ne"

Ya yi shiru saboda yadda yake jin rauni na shigar sa, ko mutane nawa ne irin Baffaha a Yau?

Ya tuna kwanakin baya yadda ya zaunar da shi yana fa'da masa tsananin son da yake yiwa Iyah! Amma a yau ya ture wannan soyayyar ya fa'di gaskiya, ayiwa Farida adalci, kar kuma ya bawa Sa'a damar da zata halaka, ta halaka shi.

Ya dago idansa da suka ka'da ya ce "Baffah kwanakin baya ka ce mini baka ta'ba mallakar abin da kake so kamar Iyah ba".

"Eh"
Baffah ya amsa a taikace .

Mk ya ce "Nima yau zan fa'da maka ban ta'ba son wata mace a duniya kamarta ba. Zan yi iyakacin kokarina na dauki shawararka na kar na bari ta halaka mu, Amma fa'da mini maganin rikicinta Baffah! Ita din sarka ce mai rikicin gan-gan".

Dariya ya yi ya ce "ai ba zata daina ba, Amma ina tabbatar maka zata rage da yawa daga cikin rikicin nata mussaman na dogon buri da kawaye yan karya domin ka shayar da ita mamaki. Abin da na san ba zata daina ba, shagwaba, saurin kuka, da kishi. Wannan kuma kaine zaka kiyaye motsuwar kishin, shagwaba da kuka kuwa idan ta yi ai sai ka rarrashi abarka".

Kunya ta kama Mk ya kasa cewa komai

Sosai ya yi godiya sannan ya mike yana cewa "Makaranta zan tafi".
Da sigar tsokana Baffa ya ce "Ba zaka leka ku yi tozali ba?"

Kunya ya ta sake kama Mk ya ce "Ai mun yi fa'da Baffah, ba zan nemeta ba, sai ta neme Ni".

Dariya sosai ya yi tare da cewa "Anya kuwa ka yi gaskiya Mutari? Amma dai ba ruwana".

Ko wayar Sa'adah bai nema ba, bare ya je gidan wurinta, ya wuce makaaranta.

Sa'adah ganin kwanaki biyu da sallamo Mk amma bai nemeta ba, ya sake hauhawar fishinta, yayin da shima fishin yake yi da ita mai tsanani, kawai ya samu salama ne na tabbacin zata dawo hannunsa, amma ganinta da ya yi da Khalil ba 'karamin haushin ta ya ji ba, kullum da aikinta yake kwana, yake tashi tunda shine sanadin da yasa take mua'amala da ahalin Khalil.

Kwanaki uku ya rage daurin aurensu amma babu fahimta a tsakanin su lamarin da yake ciwa Sa'a tuwo a kwarya, wani sashi na zuciyarta ya ce saboda yana da wata matar ne, wani sashen kuma ya kore wannan tunanin tare da tuno mata, tana budurwa ma haka ya dinga Wannan wula'kancin har ta yi zaton soyayyar ne bai iya ba.

A daren Mk na zaune a falon sama yayin da Farida ta yi filo da cinyarsa, yana wasa da dogon gashinta tamkar mai yin kitso, sai fama yake da bugun zuciya adalilin yana son fa'da mata, juma'a mai zuwa daurin aurensa da Sa'adatu.

Sau uku yana yun'kurin fa'da sai ya kasa, da 'kyar ya yi kundubalar cewa " My ferial tashi ki zauna magana zamu yi da nake bu'katar nutsuwar ki'.

Ta tashi da sauri kuwa, ta zauna sosai tana fuskantar sa.

Cikin karfin hali ya ce " Ranar juma'ah mai zuwa idan muna cikin rayayyu, za'a mayar da aurenmu da Sa'adah".

Wani irin tashin hankali ya ziyarci Farida, irin wadda bata ta'ba hasashen zata ji shiga ba, ta dinga yun'kurin bude baki ta yi magana amma hakan ya gagari Kundila.

Ta dinga karanto addu'a, amma duk da hakan sai da hawaye ya goce mata, wani irin tukuki

Please Login or Register in order to submit comment