You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta hada ta saka a fridge.

Sai da ta gyara kicin din sannan ta tafi ta kwanta, ba ta jima da kwanciyar ba, barci ya yi awon gaba da ita.

Bude ido ta yi ta gan shi tsaye a kanta alamun shi ya tashe ta, mi'ka ta yi ta sake juyawa don ta ci gaba da yin barcin.

"Ki tashi ki yi sallah biyu fa ta wuce".

Kan dole ta tashi don kuwa ba karamin jin dadin barcin ta yi ba, har ta idar yana kishingide a gefen gadon, ya kalle ta ya ce

"Kin yi abincin, ko kuwa ke ce abincin?"

"Don Allah ka barni na ji da abin da ya dame ni, ina dai rufe ni ka yi, ba ka tunanin faruwar gobara ko wani abu na ibtila'i, ina kulle ba?".

Cike da rashin damuwa ya ce "Na fi ki tattalin lafiyar ki, na riga da na yi riga-kafin komai. Ba ki amsa mini tambayar da na yi ba?"

Shiru ta yi ta kyale shi, ganin haka ya mike ya na cire rigar shaddar jikinsa, ya cire wandon, ya yi saura daga shi sai Boxer da singileti.

Inda take zaune ya nufa ya mikar da ita yana fadin "Taso".

Kwacewa ta yi ta fita falo a guje, tana fadin, "Wallahi ba za ka tsofar da ni ba, ga abincin can a kicin".

Yana dariya ya biyo ta ya zauna a kujera ya ce "Zubo mana"

"Ni na koshi".

"To ni zubo mini".

Ta fita tana kunkuni ai tun farko shi ne ya'ke zubo musu abinci, sai yau zai ce ita za ta zubo.

Haka ta shiryo masa abincin har da zobo, dadi ya kama shi sosai, ya dinga cin abincin hannu baka hannu kwarya, tabbacin tunda ya fita bai sa komai a cikinsa ba.

Yana kallon yadda ta zauna a falo ya san ta ki shiga daki ne don kar ya mata wani abu, abin da ba ta sani ba a falon ma ba abin da zai fasa.

"Sa'adah! Don Allah mu shirya haka nan, wallahi na gaji da fushinki, ki yi hakuri kin ji na janye wallahi ke kamila ce, mai kirki ce".

Ko kallon sa ba ta yi ba, bare ta amsa masa.

"Kin ga siyar mini da fushin to".

Ta zumbura baki sosai, ta sake yin shiru.

"Ki shirya gobe na kai ki, ki yini a wurin Inna, idan za mu dawo sai mu tsaya a Sahad store mu sayo iron din da ki ka ce na sayo miki"

Nan ma shiru ta yi.

"Kin ji"

"Ni wallahi albarka".


"Tom shike nan satin sama makaranta za ta tura mu Jami'ar Jos Seminar, ki shirya mu je, ki gaida Anti Sumayya".

Murmushi ta yi ta sunkuyar da kanta.

Shi ma murmushin ya yi tare da tambayar "Kin sayar?"

Kai ta daga tare da cewa "E amma fa har da fitar goben".

"Na sani ai, tunda mun shirya, mu je ki taya ni barci, kin san jiya ban yi wani cikakken barci ba, kuma na yi fitar sassafe."

Sai da ya fita ya kewayo sannan ya kwanta, ta bi shi tana masa tausa har ya yi barcin.

Shike nan rikici ya kare.

Ranar da suka tafi Jos ba su isa ba sai yamma likis, don haka a Hotel suka sauka, duk da Sa'adah so ta yi ta sauka a gidan Sumayya.

Washegari da safe da zai fita wurin aikin da ya kawo shi ya ce ta shirya ya raka ta, da yamma zai zo su dawo, nan da nan Sa'adah ta canja fuska, tana fadin "Ni dai ka bar ni na dinga kwana a can tunda dai kwana uku kawai za mu kara yi".

Kai tsaye ya ce "Ba zan miki karya ba, ba zan iya ba, zan dinga kai ki da safe, idan yamma ta yi, zuwa Maghrib zan dinga zuwa muna dawowa".

"Ni gaskiya kwana nake so na yi"

Ido ya zuba mata sosai, ba tare da ya ce mata uffan ba, ta sunkuyar da kai kasa, saboda yadda ta ke jin kallon na ratsata.

"Yini za ki yi"
Ya sake maimatawa a gajarce.

Bata rai ta yi sosai amma ba ta ajiye kayanta da ta dauka ba.

Ya kalle ta ya ga ta yi kicin-kicin da fuska, ga kuma kaya a hannun ta, shi ma ya daure tasa fiye da yadda ta yi.

"Ni ko kwana daya ka barni na yi".

Ransa a bace ya ce "Ke ki yi duka kwanakin ma, mu hadu a tasha ranar tafiya, idan kuma kwanakin ma sun miki kadan, ki yi ta zama har sai kin gaji".

Ajiye kayan ta yi, sannan ta bi shi suka tafi. Kowa sai kunci yake yi da dan uwansa.

Shatar taxi ya dauka suka nufi unguwar su Sumayya, ba mai cewa kowa uffan.

Da murna Sumayya ta karbe su, cikin kankanin lokaci aka cika gabansu da abin karyawa, a gurguje ya ci abincin ya tafi, ciki-ciki Sa'adah ta ce "Sai ka dawo" Ba tare da ta raka shi hanya ba.


"A hakan kike so ki mallaki mijin?" Sumayya ta tambayi Sa'adah.

"Tunda kuka zo fuskarki a daure, sai da ya tashi, kika ware, tun yanzu za ki koya masa bagarar da lamarinki? Tun yana tsoron ganin fushinki, har ya daina?"

"Da bakinsa ya ce mini zai zo Jos, na shirya zai kawo ni na gaishe ki, kuma yanzu ya ce ba a nan zan sauka ba, sai dai na dinga zuwa yini, akan mai zai hana ni kwana?"

"Akan ya damu da lamarinki mana, ke yanzu ba ki ga alherin da ya miki ba, idan kuwa haka za ki dinga masa zai daina kokarin kyautata miki. Me ya kai ki yin musu, har da fushi akan abin da ya zartar?"

Haka ta dinga mata nasiha cikin rarrashi, har Sa'adah ta ji ba ta kyauta ba.

A ranar Sumayya ta fahimci Iyah na da ciki, amma ganin ba ta san tana da shi ba, yasa ita ma ba ta mata maganar ba, kuma lafiyar ta kalau, ba wani tsirin abinci ko laulayi, kawai dai yawan kwanciya take yi.

Da kanta ta masa waya, da ta ga an yi Magariba bai zo ba, tana tambayar yaushe zai zo.

"Kin fasa kwanan ne?"

"Yinin da na yi, ba tare da kai ba, a daddafe na yi, sai yanzu na gane, ko kace na kwanan ma ashe ba zan iya ba."

Da'di ya kama shi ya ce "Har na dawo masaukinmu amma bari na zo".

Sosai suka huta, zuwan su Jos sai ya zama tamkar Honey Moon a gurinsu. Son juna ya karu a zukatansu.

Wani irin so da zazzafan kishin MK, ya cika zuciyar Sa'adah, zuwa yanzu ta tabbatar ya iya soyayya, irin wadda ma ba ta yi zaton akwai irin ta ba.



Alkalamin *SURAYYA DAHIRU*
✍🏼✍🏼.
[6/7, 11:54] Aminan Ibrahim: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*





55-56




Kwanan su uku da dawowa, jikin Sa'adah ya rikice da wani irin zazzabi da amai.

Ganin kullum ciwon gaba ya ke yi ba baya ba, yasa ya kaita asibiti, test aka ba su, tunda kan Taifod, malaria, da ciki (P.T).

Sakamakon na fitowa komai Negative, illa na cikin da ya kasance positive.

Maganin tsayar da amai da karin jini aka ba ta. Sai Panadol, tare da fadin sai a hankali za ta sami lafiya tunda jikinta na samun sauyin yanayi.

Sosai MK ya ji dadi, sai fadin Alhamdulillah yake yi har suka dawo gida.

Sannu kuwa har gajiya da amsawa take yi, motsi kadan zaicce sannu, tamkar mai nakuda.

Kwana biyu ta warware ta shiga harkokinta ba wata matsalar komai, lafiyayyen ciki ta samu komai ci take yi, ko sau nawa MK zai neme ta ba ta gajiya, wani lokacin ma ita take yin dalilin da za su hadun.

Mamakin yadda ta zama expert a wannan harkar take yi ba gajiya, har Allah-Allah take yi idan ya fita ya dawo, ko kuma dare ya yi.
Ta san mabukaciyace ita, amma ko kusa ba kamar yanzu ba. Tunda ta sami ciki, ba ta sake hadiyar Viagra, bare ta ce ko shi ne yake sababa mata yawan son sex.

Daga dukkan alama cikin ne ya zo mata da wannan salon, wadda take fatan kar ya zame mata dabi'a ta dindin, MK da'din hakan yake ji ba kadan ba, kullum a cikin fadin "Madalla da Babyn nan yake."

Cike da zumudi suke goyon cikin, wani irin kyau Sa'adah ta yi, fatarta ta sake yin laushi, ta goge ta yi tas, MK baya gajiya da kallon ta musamman yadda kirjinta ya cika dam, kugunta ya bude sosai.

Shi kansa MK ya murje farinsa ya karu sosai, kallon su kawai za a yi a san suna cikin kwanciyar hankali, da mutunta juna.

*BAYAN WATA SHIDA*

Zaune take a tsakar gida tana waya da Inna, "Inna har yau ba za ki zo kiga inda nake ba?".

Daga can bangaren ta amsa da cewa " To Baffanku ne ya hana ni, wai mai zan zo na yi miki".

"Cikin shagwaba ta ce "Na san da kin karfafa Inna da tuni kin zo, haka na sha jinya har na warke ba ki zo ba, da Anty Sumayya ce a garin nan take rashin lafiya da kin je kin ganta, amma ai ni ma Baffa ya zo ya ganni." Ta fada a sanyaye.

Dariya ta yi tana cewa "Iyah ashe dai har yanzu da saura, na dauka kin yi hankali sosai, musamman da na ga kina zaune lafiya da mijinki kuma kin tsare kanki ba kya yawo".

"To Inna yanzu na kai wata biyar ban zo gidan nan ba, tunda na ji fa'danku, ba na yawo na tsare kafata, ba sai ki dinga zagayowa kina gani na ba".

"E gaskiyar ki, to ki kwantar da hankalinki, ina tafe tunda ga Baffanku ma yana jin ki da kunnensa".

Da haka suka yi sallama ta kashe wayar, da kyar ta samu ta tashi saboda yadda cikin ya mata nauyi sosai tamkar ba cikin fari ba. Watansa bakwai, amma sai a yi zaton a watan nan za ta haihu, duk da cewar watansu takwas da aure.

A fili ta ce "Gara ki zo ki gan ni, ki ga yadda na zama".

Washegari kuwa bayan azahar sai ga Inna da yar rakiyarta Zainab Ma'aji.

Mamaki ya yi matu'kar kama Inna ko kadan ba ta san cikin har ya tsufa haka ba, ta san dai tana zargin ko da cikin tunda rabon da ta sa Iyah a idonta an kai wata biyar koma ya zarce hakan.

Ta zauna tana mamakin yadda ta aune ta zama babbar mace komai nata ya bude, da kyar take zama da tashi.

Kallon Zainab Inna ta yi ta ce 'Ashe kin kusa zama uwa amma ba labari?"

Dariya sosai Zainab ta yi tare da fadin "Inna Ina zan iya hirar haihuwarmu ta fari".

Yayin da Sa'adah ta sunkuyar da kai kasa alamun kunya.

Zainab ce ta shiga kicin ta hado ruwa da lemo ta kawowa Inna, ta sake komawa ta dauko tiren da ta gani an shirya kayan abinci a kai.

Hira suka yi, cikin walwala har Inna ta fahimci sauyin da Iyah ta yi, ta fara yin hankali.

Sai da suka zo tafiya, ta fashe da kuka, kamar wata sokuwa.

Cike da tarin kauna Inna ta sata a jikinta, tana fadin "Kukan na menene kuma Iyah? so kike ki tayar mini da hankali bayan cike nake da murnar ganin ki cikin nutsuwa da walwala, ko wani abin na damun ki ne?"

Cikin kukan ta ce "Ni so nake ki dinga zuwa".

Cikin rarrashi ta ce "Wani satin zan dawo, ai yanzu kam dole Baffanku ya bari na dinga zuwa akai akai".

Da haka ta lallaba ta suka rabu lafiya, ta raka su har gate bayan Inna ta shiga dakunan ta gani tare da sanya albarka.

Suna tafe Inna ta ce da Zainab "Ina murna Iyah ta yi hankali ashe dai da saura, indai ba so take na zama uwar zamani ba, ina ni ina zarya a gidanta?"

Dariya sosai Zainab ta dinga yi tana fadin "Mene ne a ciki Inna? Kin san Baffa ne ya hana mijinta barin ta zuwa gida, ke ba sai ki dinga zuwa ba".

"Ba ku da hankali"

Har gida Zainab ta raka Inna sannan ta tafi gidansu.

Allah- Allah Inna take yi Baffa ya dawo ta ba shi labarin Iyarsa ta kusa zama uwa.


Tunda su Inna suka tafi, ta debo kayansu da ya wanke jiya, ta zauna ta fara guga.

Ta kammala nasa tsab ta-ci karfin nata, ya dawo.

Ta fara kokarin tashi ta karbe shi, ya tsaya daga inda yake ya bude murya ya ce "Yi zamanki ki ji da kanki".

Ta koma ta zauna tare da cewa "Sannu da dawowa"

Bai amsa ba ya shiga kicin ya ajie ledar hannunsa, ya zubo abinci a plate, tare da cokula biyu.

Gefe kuma ya wanko guiba ya zubo a bowl.

Yana zama tun kafin ya yi magana ta sa hannu ta dauki gwaibar ta fara ci.

Ya kalleta ya ce
"Sau nawa zan ce miki ki daina gugar nan idan na sami dama zan yi?"

"To ina zaune haka ai bai fi motsa jiki ba, ni fa har wankin ma zan iya mana, kawai dai na bari ne saboda ka ce ba ka so.

Ya zuba musu abincin, yana fadin mun yi Ba'ki ne yau, ko kuma wani abin za mu yi da daddare?"

Tana murmushi ta ce "Yau babbar bakuwa muka yi baka nan"

Ya zuba mata ido cike da neman karin bayani.

"Inna yau dai Allah ya nufa ta zo"

Da sauri ya ce shine baki fada mini za ta zo ba?"

"Ni ma fa ban sani ba kawai ganin su na yi ita da Zainab".

"Ba ni labarin yadda ta kaya, kin saka hijabi kin boye cikin?"

Tana dariya ta ce "Ban saka ba, amma dai na ji kunya ba kadan ba, ita fa ba ta san ya girma haka ba".

Shi ma cikin dariyar ya ce "To me kika ba su da za su tafi?"

"Ban basu komai ba".

Ya rage fara'a ya ce "Kai Iyah don rowa?"

"To ai na ga farkon zuwa na na kai mata atamfa da sabulai, zuwan da na yi na karshe ma ka ba da kayayyaki na kai mata, yanzu ni kuma ba kudi ne da ni ba".

"Kudin da yake cikin durowa a dakina fa?" Ya tambayeta yana kallon ta.

"Uncle ai ban fada maka zan taba ba, sannan kuma cewa ka yi na sayayyar kayan Baby ne".

"Daga yau ban miki iyaka da komai nawa ba, akan su Hajiya da Inna, komai kika ba su ba zance don me ba?".

"Tom shike nan na gode zan gyara".

"Ina ta cin abinci baki sa hannu ba?".

"Ci abinka ni kunu zan sha, dazu Zainab ta taya ni muka yi".

"Kwana biyun nan ban san me yasa ba na son shinkafa ba".

Sai da ya kammala cin abincin ya tashi ya zubo mata kunun a katon mug, sannan ya jona gugar ya ci gaba da yi.

Suna zaune aka fara kiran Magariba, daidai lokacin kuma ya kammala musu gugar gabadaya.

Ya yi alwallah ya nufi Masallaci, ita ma ta tashi da kyar ta yi alwalar.

Kafin ya dawo ta shirya kayan su cikin durowa, ta tattare falon, ta kunna turaren tsinke na Touch Me.

Haka kwanaki suke ta shudewa har watan haihuwa ya kama, komai na Sa'adah ya sake canjawa, fuskarta, ta yi wani iri, hanci ya bude sosai, baki ya zama kato tamkar ba Sa'adah yar kwalisa ba.🤣

Ita da kanta ba ta son ganin fuskarta a madubi, MK idan ya kalle ta dariya take bashi, amma ba ya iya dariyar a gabanta, tun kwanaki da ya kalle ta ya fashe da dariya, ita kuma ta saka masa kuka mai tayar da hankali, da kyar ya shawo kanta, shike nan bai kara ba, sai idan ya fita ko ya shiga dakinsa ya yi mai isarsa.

Ranar Alhamis da yamma ya isa gidansu, bayan sun gaisa da Hajiya Babba, ya tambaye ta yadda za a yi akan sayayyar kayan haihuwa.

Ta kalle shi da kulawa ta ce "Haihuwar ta matso ne?"

Ya ki tankawa.

Ta yi murmushi ta ce yanzu fa an daina wannan ala'adar, a yi sayayya amma wai sai ranar suna da a ba da kaya, kawai ku je ku sayo kayanku, ku ajiye Allah ya raba su lafiya".

A zuciyarsa kawai ya amsa, ya mata sallama ya yi dakin uwarsa!ya mata bayanin yadda suka yi da Hajiya Babba.

Ta ce "Shike nan a yi yadda ta ce din, ko ka hada su da Samira ta raka ta, tunda ku ba ku san mai aka fi bukata ba".

A gidan ya ci abinci kasancewar daga makaranta ya zarto, sannan ya musu sallama ya tafi.

Haka kuwa aka yi tare da Samira suka je kasuwar kayan jarirai ta asibitin Nassarawa suka zabo kayayyaki daidai misali, wadda za a fi bu'katar su.

Ganin kayayyakin nan ya karawa Sa'adah kaguwar ta haihu, da MK ya dawo ya ga yawan kayan da kyaunsu, shi ma ya ji dadi tare da yabawa Samira.

Dadi ya kama shi ganin da ya yi Sa'adah tana ta murnar kayan. Ya ce mai ya rage ba a saya ba?"

"Uncle komai an siya kawai rigunan ne unisex, sai anyi haihuwar za a sayi na mace ko na namiji, sai durowar Baby kawai".

"Tom shike nan su ma zan saya muku, ke ina naki kayan?"

Ta fara daddaga kayan gun tana neman ledar da kayan suke ciki, shi ne ya hangota ta fada tsakanin kujeru, da kyar ya janyo ta.

Ya bude yana ganin inner wears ne, sai pads, saboda ya tura Lagos Anty Hafsatu ta siyo mata lace da shadda.

Ya daga bireziyar da ta masa kyau sosai, har zai mayar, sai ya yi niyyar tsokanar ta, ya ce
"Anya wannan za ta miki kuwa?"

"Za ta mini mana ba ka ga an kara size din akan wadda na saba sawa ba?"

"To abin ne na ga kamar ba za ta rufe su ba".

"Kuma haka zan ta zama, ai Inna ta ce zan huce".

Ya guntse dariyarsa ya fita yana fadin, yanzu zafi ne da ke?"

Sai da ya dawo ya zauna ya ce, "Ki fito da kayan da zan kai miki dinkin".

Shiru ta yi masa tana ala'adarta ta zumbura baki.

Ya maze ya ce, "Da ke fa nake magana kin san na sha fada miki ba na son na miki magana ki yi kamar ba ki ji ba.

Ga mamakinsa sai ya ga hawaye na zuba a idonta, kafin ya tambayi ba'asi ya ji tana cewa, "Da alama idan na yi kiba daina sona za ka yi, kullum sai ka mini dariya, ina kallon ka kawai sharewa nake yi, don ma kai ka mayar da ni hakan din".

Ta kare tana kifa kai a hannun kujerar da ta ke zaune, tana masa kukan iyashege.

Maimakon ya ji ya damu sai kawai dariyar ta zo masa sosai, ya dinga kyakyatawa.

Lamarin da ya harzuka ta, ta tashi ta koma daki tana kuka sosai.

Sai ya yi shiru da ya hasaso yadda hanci da bakinta suka zama sai ya sake fashewa da dariyar, ya jima kafin ya samu dariyar ta tsaya masa.
Ya shiga mayar da kayan cikin ledoji ya kai su dayan dakin da ba kasafai suke amfani da shi ba, ya bude wardrobe ya zuba su ya rufe.

Dakin ya bi ta, ya samu tana ta goge fuskarta da tissue, kusa da ita ya zauna ya rungumo ta ta gefe, so take ta fizge amma ta kasa, ya fara magana a hankali.

"Me ya sa kike da saurin kuka ne Iyah? So kike Babyn mu ya zama mai kukan banza? Me yasa ba ki san wasa ba, ko buhu kika zama wallahi ba abin da zai ragu a son da nake miki, ba sha'awar ki nake yi ba, ba jikin ki nake so ba, ke nake so. Tsufa ko tawayar halittar ki ba za su canja soyayyar da nake miki ba, ki ri'ke wannan".

Sai ta lafe sosai a jikinsa tana sha'kar kamshinsa, ta sa hannu ta balle links din dake gaban rigar ta zura hannu tana shafo kirjinsa.

Cikin lokaci kalilan suka birkice, Sa'adah, ba karamin kidima MK take ba, nauyin cikinta baya tasiri a wannan fagen. Sosai kalamansa suka sata farinciki, shi yasa ita ma take mayar masa da tarin soyayyar da take masa a aikace ba ka jin komai sai numfarfashin MK.
Soasai suka sha shagalinsu, katon cikin su ba ya hana su komai, sai dai Mk ya san yadda yake yi ba tare da ya takura ta ba.

Yana tsaye gaban madubi, yana daura Agogon hannunsa, ita ma ta fito daga wanka daure da tawul, a bakin gado ta zauna tana ta numfarfashi, shi ya taimaka mata da shafa mai, pant da siket kawai tasa ta zura doguwar riga marar nauyi.

Ya dauke tawul din ya shanya a kofar bandakin. Ya dauke bireziyar da ba ta saka ba ya mayar inda take ajiye su.

Dake ya saba da tsokanarta ya kalle ta yace, "Iyah na lura idan kina koke-kokenki inviting dina kike yi ashe, daga yau na fahimta. I will be noted".

Hararar sa ta yi tare da cewa "Ka daina ce min Iyah, ba na so".

"Ni kuma ina so".

Duk wani abin da za a bukata lokacin haihuwa MK ya tanadar mata, hatta dinkunan da za ta saka ya karbo, ba abin da suke jira illa zuwam ranar haihuwa.

Ranar Talata da ta yi daidai da hudu ga watan Mayu 4/5, tun Asuba take faman murkususu, tun tana daurewa har ta gaza, a sukwane ya samo Adaidaita Sahu suka nufi asibitin Murtala, waya ya yi wa Hajiya Babba, ita ma a gaggauce ta bi su, sai da ta isa, sannan ya koma gida don dauko akwatin da suka shirya kayan zuwa asibiti, da kuma tabarma.

Karfe 1:45pm na rana Sa'adah ta haifo sankacecen yaro namiji mai cike da koshin lafiya, kukan da yake canyarawa ne ya tabbatar ma Hajiya Babba, Sa'adah ta sauka.

Ana zuwa albishir da karban kayan jariri, MK na isowa, ya tarar da labari mai dadi.

A Daren ranar aka sallame su, bayan an tabbatar da lafiyar uwa da jaririnta.



```Alkalamin Surayya Dee```
✍🏼


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.






57-58


Kafin wayewar garin labarin haihuwa ya isa kunnen Yan uwa da abokan arziki.

Umman fanshekara da ta kasance kanwa ga Baffa, Ya'yan Baffani su ke(cousins)! za ta zauna da Sa'adah kasanitacecewar mijin ta ya kwana biyu da rasuwa, kuma ba ita kadai bace tana da abokiyar zama.

Sosai Mk yake hidima da mai jego, komai akace ana bu'kata da rawar jiki zai kawo, har wadda ma ba a nema ba.

Umma sai yaba kirkin Mk da iyayensa ta ke yi, kullum suka zauna da Sa'adah sai tace "kin yi Sa'a Iyah, kin hadu da miji da ya gaji arziki d mutunci a wurin iyayensa, shi kam bai shure kyawawan dabi'un gidansu ba".

Murmushi kawai Sa'adah ta ke yi tana gasgata maganar Umma.

Ranar suna yaro ya ci sunan mahaifin Mukhtar, wato Muhd Kabir tun a ranar kuma Samira ta lankaya masa Jawad.

A zuciyar Sa'adah ba Jawad ta so ba, amma saboda kara ga kanwar Mk sai bata canja ba.

Sosai aka yi shagalin sunan Jawad abinci mai kyau aka yi a gidan su Mk, aka ciko manyan kuloli aka zo da su, jollof din shinkafa, bandashen Gurasa, da Alale. ga kuma dangin kayan sha irin su zobo, ginger, da kunun Aya masu dadi da sanyi. mai daukan hoto da video duk motsin Sa'adah sai dai ta ga hasken camera, tun safe kafin a cika suka sha hotuna da Mk cikin kwalliya ta burgewa.

Da azahar sai ga Halima da Safina sun zo kwatsam,sama sama suka gaisa da Zainab Ma'aji ta gabatar musu da abinci da kuma abin sha, yayin da Sa'adah keta rawar jiki akan su, suna ta yatsina, hatta abincin ma ko hannu ba su saka ba bare su ci.

Cike da murmushi Sa'adah tace "idon ku kenan, sai yau kuka tuna da Ni, ashe ma kunsan inda na ke! nema na ne baku

Please Login or Register in order to submit comment