You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta shigo gidan a sukwane, tunda ta ga motarsa a waje ta shigo a hanzarce, zuciya na 'bari, ba ta yi zaton zai dawo ba, wacce irin 'kaddara tasa ta bar kayan nan da waya a fili?

Kai tsaye 'dakinsa ta shiga dan ganin wanne kallo zai mata?

Har 'bandaki baya nan, bugun zuciyar ta ya karu, cikin shahada ta nufi ta nufi falon , bata ganshi ba, fargabar ta ta 'karu ta tabbatar ya ga wayar nan.

'Karfin hali ta lalubo ta dora a fuskarta duk kuwa da zuciya da gangar jikinta sun 'ki karban wannan 'karfin halin.

Da sallama a bakinta ta shiga dakin, yanayin da ta iske shi, sai da ya ka'da mata 'ya'yan hanji.
Bai 'dago ya kalleta ba, amma ya amsa sallamarta da murya marar amo.

Ta aro jarumtar 'boye kaduwar da take ciki, ta matsa kusa da shi tana cewa "Ba ka jin dadi ne, da kace sai yamma za ka dawo, a Ina ka baro Jawad?"

Ya dago yana kallon ta, yana jin wata irin tsanar ta na neman Samun muhalli a zuciyar sa.

Bai amsa mata ba, ya zuba mata ido yana jin tamkar ya tashi ya yi ta dukanta. marar gaskiya akace ko a ruwa gumi ya ke yi, ta dinga jin 'barin jiki irin na fargaba, ta yi sukuri tamkar ace 'kyat ta fece da gudu.


Ya mi'ke ya isa inda take tsaye yace " A Ina kika samo wadannan kayayyaki masu daraja?"

Cikin rawar murya tace "Anty Sumayya ta aiko mana, dama na fito da su idan ka dawo, ka gani"

Ya zuba mata ido yana kallon yadda ta ke shirya zancen da babu azanci a cikinsa, ledar kayan ta nuna daga Egypt kayan suke, sannan a cikin kwalin wayar akwai risit din siyan wayar a ciki mai dauke da sunanta a takaice( S.B). Kwanan watan ya nuna ta kai wattanni biyu a hannun ta.

Ya ce "Sumayya yaushe ta je Egypt ban sani ba? Ta hannun wa sa'kon ya same ki?"

Ta muzanta kwarai da gaske, ta kasa bude baki ta yi magana.

Ya dauko wayar yana cewa "Wannan wayar da ta lashe manyan ku'da'de Sumayya ta aiko miki? Ko kuma saurayin ki, ki ka fa'dawa mijinki ya gaza?"

Ya mi'ka mata ya ce "Bu'de mini! tashin hankalin ta ya ninku, Baki na rawa ta ce "kar ka yi aiki da zato, wayar Halima ce ba tawa ba".

Idonsa ya canja zuwa jah, jijiyoyin kansa suka bayyana ru'du ru'du, makoshinsa ya bushe, zuciyarsa ta cushe da tsananin bacin rai, hankalin sa ya kai 'kololuwa wurin tashi.

"A zafafe sosai ya ce " wacce maganar zan kama, wayar Halimace ko Sumayya ce ta kawo miki?
ki bude min wayar nan tun kafin na tozarta ki, domin sai na dauke ki munje gaban Halima, Ina rantse miki da ubangiji agaban Baffa za'a yi komai".

Ta fara kuka tana cewa "Ajiya ta kawo mini itama ba tata bace, dan Allah ka yi hakuri, gaskiya na fada maka".

Karon farko da hakurinsa ya kwace ya dauke ta wani irin mari mai katse ji da gani na wucin gadi! ya ce "Da aurena Sa'adatu, da aurena akan ki? Idan wayar Halima ce to wannan Agogon da kayan na uwar waye?"

Tsananin zafin marin yasa habo ya goce mata, duk da hakan bata damu ba, asalima kukan tsayawa ya yi cak duk da hakan furucinsa ya fi firgita ta sama da marin

A gigice ta ce " gaskiya na fada maka, ka yarda da Ni"

Ta riga ta kudiri aniyar komai zai mata ba zata bude ba, domin a jiya ma sun yi chart da Khalil, duk da ba wani dirty abubuwa suka tattauna ba, amma akwai maganganun da ba zata so Mk ya gani ba, mussaman hotunan sa da ya turo mata, ita kuma ta tura masa na Jawad.

Hankalin Mk ya kai ma'kura wurin tashi ya matsa kusa da ita sosai yace "ki bude min wayar nan idan ba so kike ki wulakanta kanki ba".
ta karba, amma ilahirin jikinta rawa yake yi na tsananin tsoro da firgici.

Fiye da mintina goma tana ri'ke da waya amma ta 'ki budeta, lamarin da ya sanya Mk ya ce ta fita suje gidan su Halima, ya tasa ta a gaba har tsakar gida, anan ta coge akan ita ba zata je gidansu wata Halima ba.

Ya nuna ta da yatsa ya ce "Billahillazi sai kin je, daukota zamu yi, muje gaban Baffa shine al'kalin wannan jahilcin na ki".

Ta rasa inda zata tsoma ranta, ta tabbatar Halima kai tsaye za ta ce ba wayarta bace tunda ba ta 'ki ta kashe auren Mk ba dama.

Ya koma 'daki dauko mukallin mota, tashin hankali yasa ya kasa ganin inda ya ajiye, yana cikin dube dube kawai sai jin 'karar fashewar abu ya ji da karfin gaske.

Ya fito da sauri, ya ga wayar ta rotsa, ta fashe sosai, ta wargaje yadda ba zata tashi ko ta moru ba.

Bai san sadda ya isa gareta ba, ya sha'keta sosai, sai da ya lura tana dab da sumewa ya wancakalar da ita, ya hau dukanta da hannuwansa.

Ganin yana dukan amma ba abin da yake ji na sauki sai ma 'karin tafasar zuciya, ya kyaleta ya zauna a kasa dabas ya dinga ambaton innalillahi wa ilaihir raji'un, hawaye bakin ciki na tsere akan fuskar sa.

Ta dago da 'kyar ta ga yadda ya ke zubar d hawayea! a fili bai damu da aga yana kukan ba, duk wata dauriyarsa sa ta kwace a YAU.

Hankalin ta ya sake ri'banya tashi, ta dinga kuka tana fadin " Ka yafe mini, wallahi ba wayata bace".

A tunzure ya antayo ashar irin wadda bata taba jinta ba, ya maka mata, tare da cewa "Idan ki ka kuma bude baki da nufin yi min, magana ko bani ha'kuri Billahillazi sai na miki abin da baza ki manta ba".

Wayarsa ya ciro aljihu, da kyar ya iya lalubo sunan Fahad Auwal!
Dalibinsa ne tun a FGC yana cikin samarin Sa'a duk da dai bata ta'ba kulashi ba, sannan yanzu ma dalibinsa ne a B.U.K.

Da girmamawa ya gaida Mk.

Cikin rashin sukuni Mk yace "Fahad cikin class mate din ku na FGC akwai mai karatu a Egypt kuwa?"

Dan Jim Fahad ya yi sannan yace"Khalil Ibrahim ne kawai a Egypt".

Ko godiya Mk bai tsaya yi ba, ya katse wayar.

A fili ya ce "ban da tabbas, amma idan har yanzu kuna tare na tabbatar kun tabbata wakilan manyan shedanu a doron 'kasa".

Ta 'kara karfin kukanta ta ce "Mala.. ya katseta ta hanyar jifanta da takalminsa da hagu. Tare da cewa "ki mini shiru, dama ai na fada miki ba zan sake yi miki uzziri akan shedanun yaron nan da baisan kimar da darajar aure ba".

Ya jima yana ambaton addu'ar we yayewar ba'kin ciki, *"YA HAYYU, YA QAYYUM BI RAHMATIKA ASTAGIS*.

Ya 'dan sami nutsuwa ka'dan ya kalleta ya ce " kin yi wankan ko ba ki yi ba?"

Da'di ya kamata mussaman da ta tuna da asuba ya gama mitar hakurinsa ya 'kare, wannan karon period dinta takes too long. ta yi dariya ta ce bai 'karu ba kawai matsuwar da ka yi ne, amma dai nasan ba tantama I will be ready today.

Tunaninta nemanta zai yi tunda dabi'arsa ce ya kusanceta a lokacin da ya ga shaidan zai dagula zaman lafiyar su.

Da hanzari ta ce "Na yi".

Ya zuba mata ido sosai yana so ya ji ko akwai sauran gurbi a zuciyarsa da zai sake yi mata uzziri, sai ya ji babu saura, yana jin idan bai rabu da ita ba, tabbas ba'kin cikinta ne zai zama ajalinsa.

Dan haka muryar sa cike da rauni, hawaye na zirarowa ya ce "*Na sake ki, saki daya Sa'adatu*! Na ba ki dama ki zama yantacciyar da ki ke fata".

Ta 'kwala uban ihu mai gigitarwa.




30/04.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._*

_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_

*Godiya ga makaranta*
*Ina matu'kar Jin dadin yabawar ku kan rubutuna, Hakika da kune Halin Yau ya je inda ban yi zaton zai je ba. na gode muku dukkan makaranta littafin HALIN YAU da fatan ana lura da sakon da nake nufin isarwa, ana watsi da shiriritar da yake ciiki, Ubangiji ya bamu damina Mai albarka*.

*Bari na sada zumunta da ku masoyan Sa'adah*
*Hajiya Rabi Sani*
*Aisha(cisse)*
*Tababa ta Malam*
*Asma'u Umar Ingawa*
*Samira Annuri*.
*Khadija Sadiq*
*Safara'u Niger*.
*Zainab Abdallahi*
*Aishatu maina*
*Khadija Bishir(Dijengala enterprises)*.
*Masoyan da yawa mu tara a shafin gaba*.

* SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



78.




Kuka ta ke yi tamkar ranta zai fita, ta rarrafa ta ri'ke kafarsa ta dama.
Cewa ta ke yi " Kar ka mini haka Malam, laifina bai kai ka 'dau wannan hukuncin ba, dan Allah ina sonka, ina son zama da kai".

A hanzarce ya fincike kafarsa, ya nunata da yatsa amma ya kasa bude baki ya mata magana saboda yadda yake jin wani irin sanyi na ratsa shi duk kuwa da yanayin garin a daure yake da zafi, saboda hadarin da ya hadu amma ruwa bai sauko ba.

Da 'kyar ya mike, ya shiga dakinta, ya dauko mukallin motar wadda yana tsakar dakin a yashe, rashin nutsuwa ya hana shi ya gani.

Ya fito, ya tsaya yana kallon yadda take kuka mai tsananin ciwo, irin kukan nan da ba ya sa a ji sau'kin tashin hankalin da aka tsinci kai a ciki.

A hankali ya ce "Tashi muje na kai ki gida".

"Dan Allah Malam ka yi hakuri Ni bazan tafi ba".

Fuskar nan a daure tamkar hadari ya ce " Ba za'bi na baki ba, ki tashi na kai ki cikin mutunci, tun ba ki tafi dutse a hannun riga ba".

Hawaye face face a fuskarta, Ta ce "iddah zan yi a dakina kamar yadda shari'a ta tanadar, ka girmama shari'a.

A kufule ya ce "wallahi ba anan gidan ba, ki je, ki yi a gidanku duk wata zan aiko miki abin da zai ishe ki! Na 'ki na girmama shari'ar, ke iyakokin ubangiji nawa ki ka take saboda son zuciyar ki, yanzu ne ki kasan ka'idojin shari'ar?"

Ta yi 'kasa da kanta dan kaucewa kallon tsanar da yake mata.

"Tashi muje" ya fada a kausashe.

Ta 'ki koda motsin kirki, sai shesshekar kukanta kawai, wadda ta ke yinsa har cikin 'bargonta.

A hasale sosai ya ce " Sa'adatu taurin kai a yau ba zai amfane ki da komai ba, bazan dauke ki da karfi ba, amma ki sani idan har ba ki tashi na mayar da ke cikin mutunci kamar yadda aka bani ke cikin mutunci ba, komai zai iya faruwa a tsakanin mu, na tsani na bude ido na ganki".

Nan ma ko uffan ba ta ce ba, sannan kuma ta 'ki tashin.

Ai kuwa ya ce "shikenan! Komai ya faru ki kuka da kanki, ya shiga 'dakinsa, mintina biyu ya sake fitowa ya dubeta tana kuka tamkar Baffah da Innah sun mutu rana 'daya, amma ko tausayi ba ta bashi ba.

A kausashe ya ce "Zan fita yanzu! kuma wurin Baffan zani na fada masa yau na mayar da ke 'yantacciya, amma ki sani Billahillazi idan har na fita ni ka'dai na haramtawa kaina ke, idan haka ta faru, shari'ar ta ce ba dalilin ki zauna kimin idda a gida ko?".

Tamkar tab'ab'biya ya ga ta mike ta fita waje a guje, ya bi bayanta dan ya lura tamkar ta zauce ne.

Ba ta tsaya a harabar gate din su ba, waje ta fita kai tsaye, ta yi kicibus da wani tsoho sosai, zai wuce, a gabansa ta zube cikin fitar hayyaci tace "ka taimake ni Baba"!

Dai dai lokacin Mk ya fito ya tarar da su a hakan.
Da sauri ta dinga cewa "ga shi nan Baba, bashi ha'kuri saki na ya yi, fa'da masa Allah ba ya son saki, yana kuma tare da masu hakuri"

Kallonta kawai za ka yi ka gane sakin nan ya susuta ta, ya gigita ta sosai.

Tausayinta ya cika zuciyar dattijon, ya kalli Mk ya ga shima a gigicen yake kwarai da gaske.

Duk da hakan sai yace "zo kusa da ni 'dana, Mk bai 'ki ba, hakan nan ya matsa kusa da shi ya tsugunna, a tausashe yace "ka yi hakuri ka ji! da gaske Allah na tare da masu ha'kuri, ba a biye sha'anin mata, yanzun nan za su rufe ido su yi abin da za su shekara suna nadama".

Mk dai baice masa komai ba, bai ji kuma zai janye sakin nan ba, tabbas sai ta je ta banbance tsakanin zaman gidan miji da rayuwar da take hari wannene 'yanci?

A hankali tsohon ya kuma fa'din "na tabbatar ko iya haka ka barta ta gane bakin Rijiya ba wurin wasan makaho bane".

Murya ba sauti Mk ya ce "Baba kar ka sa na yi abin da zan zalunci kaina, ina ro'kon ka, ka yi ha'kuri, al'kawari 'daya zan maka, matu'kar zuciyata ta huce da lamarin yarinyar nan, to kana cikin wadda zata ci darajar su na yafe mata, amma a yanzu idan ka tirsasani na mayar da ita, auren namu zai iya lalacewa gaba'daya, ka yi ha'kuri ka fahimce Ni".

Kafin Dattijon ya yi magana Sa'adah ta zabura ta sake kwasa a guje ta shige gidan.

Tausayinta ya cika zuciyar wannan tsohon, ya riko Mk sosai ya ce " Na fahimce ka 'dana, ba kuma zan maka dole ba, mai 'daki shi yasan inda yake masa yoyo! Amma ina son ka ri'ke a ranka cewar yarinyar nan tana sonka sannan uwar ya'yan ka ce, dan haka kar ka yi amfani da zato wurin hukunta ta, ka boye laifin ta, Allah ya muku albarka gaba'daya, ya kuma huci zuciyarka".

Da ga haka ya saki Mk ya juya, ya tafi, ga mamakin Mk sai ya ga cikin sakwanni mutumin nan har ya yi tafiyar da ya bacewa ganin sa, ya dinga wasiwasi anya kuwa wannan mutum ne? a tsufansa ba zai iya irin wannan sauri haka tamkar walkiya ba, ya shiga gida yana ayyana ko dai aljanine cikin aljanun Sa'adah.😂

A bakin motar ya tarar da ita, tana tsaye hawaye ya ki tsaya mata.

Ya bude gate din, sannan ya karasa ya bude motar suka shiga, sai da ya rufe gidan sannan suka tafi.

Ta by pass hanyar 'Dorayi ya bi dan haka hanyar ba yawan motoci, sun zo daidai Wailari ya ga ta fara wata irin jijjiga tana cewa "Laifina bai kai wannan hukuncin ba, kar kasheni da raina, Baffa ba zai bar Ni na zauna masa a gida ba, ina ka ke son na tafi?" Sai kawai ya ga ta sume.

Kan dole ya gangara gefen titi ya bude ruwan roba na Highland da ke gaban motar mai dan sanyi, daga gidan Mahmoud ya taho da shi, ya watsa mata, ajiyar zuciya ta saki tare da rushewa da kuka sosai har muryar ta fara dashewa, fadi take yi "Ka ji tausayina mu koma gidanmu, Jawad zai yi kukan rashi na, komai ka ce na yi bazan kuskure ba, na yarda ka 'Kara aure, ka sake 'karawa, ka sake 'karawa, ya fi mini sau'ki da na rasa ka".

Idan ya ce jikinsa bai yi sanyi ba, ya yi 'karya, idan yace maganganun ta basu yi yunkurin karya masa zuciya ba ya yi munafunci.

Ya zuba mata ido yana kallon yadda tashin hankalin awa daya rak ya susuta ta, yaci gaba da kallonta yana so ya samu dalili gamsasshe da zai mata afuwa, amma da zuciyarsa ta hararo masa cewa "Hai'ntarsa take yi shiyasa ta 'ki bari ya ga ta'addacin da ta ke yi da aurensa akanta, sai ya ji zuciyar sa tana zafi tamkar ana gasa burodi.

Ya zuba mata ido ya ce"Sa'adatu kowanne bawa da irin kaddararsa, Allah ya sani na iya bakin kokarina na mu zauna lafiya, kuma shine shaida akan son da nake miki, matu'kar gaskiya zan fada miki, zuciyata ba za ta nutsu da ke a yanzu ba!
Al'kawarin da zan miki daya ne, ba wadda zai ji mai ya ha'damu, Ina tabbatar miki zan dauki laifin a idon kowa, kema kuma kar ki fa'dawa kowa ko da Baffa ne kuwa".

Ya yanko tissue yana goge'kwallar da ta cika masa idanuwa.

Ta zama very speach less, bugun zuciyar ta ya karu, wani irin zazzabi mai zafi ya fara kokarin kai mata caffa. ta koma ta kwanta a jikin kujerar tana jin duk wani tashin hankalin duniya yau ita aka ha'dawa shi.

Tsawon lokaci suna haka, shiru ya ratsa, sai fama suke da radadi a zukatan su.

Cikin 'karfin hali ya tayar da motar ya hau titi, karon farko da Sa'adah ta yi fatan inama su yi hatsarin da zai zama ajalinta, ta huta da azabar ciwon da ke damun zuciyar ta.

Bai tsaya ba, sai a kofar gidan su, gabanta ya yanke ya fadi, ta tuno maganganun Baffa a ranar da zai kaita dakin aurenta.

Ta kalle shi ta ce "Baffa korata zai yi, kar ka barni anan, mu tafi gidanmu Malam, na yi al'kawarin ba zan sake ri'ke kowacce irin waya ba".
Ta ru'ko hannunsa ta sake fa'din " Na amince ka yi amarya ka tafi da ita karatun da za ka tafi, Ni ka barni zan jiraka, fatana kar ka barni".

Magana ta ke yi ba kuka, sai tsananin bacin rai da tashin hankali.

Ya kalleta sosai "a karon farko da ya ganta cikin NADAMAR gaskiya, sai dai nadama marar amfani ta ke yi domin ta riga ta yi a 'kurarren lokaci.

Baice komai ba, ya bude motar ya fita, haka ta bude itama ta fita sanin akan titi suke, a zaure ya tsaya ya ciro wayarsa ya 'Kira layin Baffah, ya sanar masa ya zo yana zaure.

Cikin rashin sa'a ya ce "dazun nan na tafi Gogel, sai jibi kuwa zan dawo, ko akwai matsala ne?"

Kai tsaye Mk ya ce "akwai Baffa Amma zan zo na sameka anan din"

"Ba sai ka zo ba Mutari, in sha Allah zan juyo a yau ba sai gobe ba".

Ya yi godiya, sannan suka kashe wayar.

Sa'adah na rakube a jigin bango, ta matso ta tsugunna guiwa biyu ta ce " Rashin samun sa alamun ubangiji bai son rabuwarmu ne, Dan Nabiyur Rahamati ka dauke ni mu koma gida".

Ya kalleta sosai ya furzar da iskar bacin rai ya ce "wa ya siya miki Wannan Agogon da kuma waya?"

Hawaye ya balle mata, ta rasa mai za ta ce.

Ganin ta yi shiru ya sa shi cewa tashi ki shiga gidan zan je shago na jira dawowarsa.

Ya fita da sauri, ya yin da ita kuma ta durkushe a 'kasa tana kuka sosai.

Ta jima tana kukan da 'kyar ta tashi ta shiga gidan ta tarar da mahaifiyarta tana zaune tana Jin radio.

Tana layi ta 'karasa kan tabarma sabon kuka na kaico iri iri na sake ku'buce mata.

Tambayar duniya ba wadda Inna bata mata ba amma ta 'ki tankawa, lamarin da ya dagula hankalin ta.

Kan dole ta 'kira wayar Baffah ta sanar da shi ga Iyah ta zo tana ta kuka, kuma ta ce mijinta ne ya kawota da kansa.

Ya amsa mata da gashi nan ya juyo.

Ta ajiye wayar cikin sanyin jiki ta kalli yadda ta ke kuka jikinta har 'bari yake yi, ga wata irin rama ta yi, har ba'ki ta ga ta sake yi mata sosai.

A hankali ta;ce "kin tasa ni a gaba kina irin wannan kukan mai tayar da hankali, amma kin 'ki bu'de baki ki fa'da min mai ya same ki, ba Kya jin tsoron ciwo ya kada ni, kinsan fargaba da zullumin da nake ciki?"

****
Mk na zaune a shago, amma jinsa yake tamkar a cikin rijiya saboda tsananin yadda ya takura ga wani irin matsanancin kishi ya matse kofofin numfashinsa, ya sababa masa azabben ciwon kai mai tsananin. Yawun bakinsa ya kafe sai daci yake ji har makoshinsa! ya ciro wayarsa ya kira Mahmoud ya sanar da shi, yana cikin matsala ya zo gidan Hajiyan Bichi ya same shi.

Ya fito kai tsaye ya tari mai acaba(A lokacin ba a hana ba) ya kai shi gidansu, dan bashi da sukunin da zai iya tu'ki, domin al'amarin na nisa damuwar sa na 'kara girmama, wani abu ne mai tsananin ciwo ya tokare a 'kahon zuciyarsa mai azabtarwa.

Yana isa kai tsaye can cikin dakin Hajiya ya shige ya wuce ta a falo tana yanka kankana.

Mamaki ya kamata, ba zata iya tuna yaushe rabon da ya shigo ya ganta a falo amma ya zarce uwar daki ba.

Ta yi jim, tana sauraronsa ganin fitowarsa, amma abin mamaki mintina fiye da goma sun shude bai fito ba, dan haka sai ta mike ta bi bayansa dan jin ba'asin wannan sabuwar dabi'a.

Yanayin da ta tarar da shi ya tabbatar mata akwai matsala, da azama ta isa gareshi tana cewa lafiyar ka kuwa?

A hankali ya ce"kaina tamkar zai fashe Hajiya"

Da jimami ta ce "Ai da Abbas ko Akil ka kira wani ya raka ka asibiti, a kwanta da ciwo ne ba a sha magani ba?"
Dai dai lokacin Mahmoud ya iso suka gaisa da Hajiya da ta fito falo tana masa iso.

"Shiga! yau zuwa ya yi ya mini sake sake a gado da sunan ciwon kai".

Mahmoud na dariya ya mike yana cewa " Hajiya ai gara ya kwanta ya more da zarar kunga mun yi aure shikenan sai ku dora mana dukkan girma alhalin matu'kar kuna raye mu yara ne 'kananu".

Ya shige cikin dakin.

Kallon Aminin nasa ya yi ya tabbatar yana cikin tashin hankali babba. Yasan karfin zuciyar Mk duk abin da ya bayyana a jikinsa tabbas ya yi tsamari ne.

Da gaggawa ya shiga ya zauna a gefen gadon, ya na fadin "me ya ke faruwa ne?"

Cikin rawar murya Mk ya dinga yunkurin magana amma ya kasa yi, ga mamakin Mahmoud sai ganin kwalla na gangarowa ta gefen idon Mk.

Take hankalin Mahmoud ya yi tashin gauron zabi, murya kasa kasa cike da tsantsar aminci da kulawa, ya ru'ko hannuwansa ya ce "Yi hakuri Mukhtar! Fada mini damuwarka in sha Allah I will stand for you".

Da rawar murya Mk ya dinga ambaton Sa'adah, Sa'adah".

A hanzarce Mahmoud ya ce" me ya same ta, me ta yi?"

Da 'kyar ya bude baki ya ce "mun rabu, na saketa Mahmoud"! ya karasa da murya mai cike da tashin hankali.

Wani irin zabura Mahmoud ya yi ya mike yana cewa"How comes, akan me? subhanllah!"

Shiru ya ratsa dakin! kowa tunani, na katantanwa da shi.

A kasan makoshi Mk ya ce " ka
fa'dawa Hajiya, tashin hankali na yadda zan fa'da mata, da yadda za ta karbi lamarin".

Mahmoud ya zuba masa ido, yana kallon irin yadda Aminin nasa ke zu'ko numfashi da 'kyar tamkar mai fama da cutar asma.

A hankali ya koma ya zauna yana jin tashin hankali shima na ziyaryartar sa.

Tausayin Mk ya ratsa shi ya sake ru'ko hannuwansa a karo na biyu ya sassauta murya ya ce," Ina fatan sakin sunna ka yi, ina fatan mu gyara wannan matsalar kafin su Hajiya su ji, yanzu ina ita Sa'adah ta ke?"

Cike da rashin kuzari ainun ya ce "Na kaita gidansu, saki daya na yi mata, abin da nake so ka fahimta, da abin zai gyaru da ko kai ba zan raba 'bacin ran da kai ba".

A hankali Mahmoud ya muskuta ya ce "Kar ka yi haka, ka yi hakuri mana, da wanne irin ido za ka kalli dattijon arziki irin Baffah?"

Wannan karon Mk ne ya tamke hannun Mahmoud ya zarce da cewa "shine babban tashin hankali na, fiye ma da yadda nake jin fargabar da Hajiya za ta shiga, amma

Please Login or Register in order to submit comment