You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da yanci, Ina kuma ga kin shiga babbar makaranta, ki zauna ki yi rainon Jawad kawai, tunda nace ki cire loop din nan, amma sun zuga ki, kar ki bari ki tara yara mu tsufar da ke, to ki zauna ki tabbata da kuruciya".

Kuka take yi, tana bashi ha'kuri, yace "na gama maganata, zabi na gareki, dan kuwa wallahi ba za kije ki koyo mini karatun raini da rashin da'a ba, a haka kina iya zagina,nan gaba kuma sai dai na ji mari."

Kuka take yi tun daga kasan zuciyar ta, a duk tsayin rayuwarta a duniya a ranar ta fara sanin Ashe kuka ma kala kala ne, duk wadda tayi a baya na nisha'di da shagwaba ne, na yau ne take yin na zunzuruntun bacin rai.

Ya kalleta yace "Ba abin damuwa bane Wannan fa, domin na riga da na baki damar ki, dan hakama nake ta dan jah baya, dan mu dan saba da rashin tarayyarmu, Ina tabbatar miki idan kin zabi makaranta akan aure! Wallahi zan dauki nauyin karatunki, kuma zan wanke ki a gun su Baffa, zan dauki laifin rabuwarmu Ni ka'dai."

Murya na rawa tsabar kuka tace, "Dan girman Allah yaushe na zage ka?"

"Kina nufin na miki sharri ba ki zage ni ba?"

Ta sake ru'ko hannuwansa da kyau tana harhado kalmomi tace " Ni bance haka ba Malam! amma dan Allah ka yi hakuri, na canja Wallahi, ba zan sake ba"

"A ranar da kika zage ni dama na tabbatar miki u will pay for it! zaki yi karatu da yardata ka'dai, idan na gamsu kin canja din da gaske, idan na tabbatar ba mahalukin da zai canja ni a zuciyar ki".

Ya zare hannuwansa daga nata ya mike, itama ta mike ta tsugunna ta ru'ko kafafuwansa, tana fadin "Malam bazan iya barinka ba, dan Allah, ba dan halina ba, ka janye wannan kudirin ina son karatun amma da yardar ka nake so".

Yace "idan kuwa kina son karatu da izinina, wallahi ba bana ba, to be frank Sa'adatu! ban san time din ba, har sai na gamsu ba third party a tsakanin mu, sai na gamsu na wuce zagi da diban albarka ta kowacce fuska daga gareki".

Ta sake shi! sanin halinsa idan ya rantse shikenan ya gama magana, ta ha'kura tana jin bakin ciki tamkar ta mutu! ta huta. Kuka ba irin wadda ba tayi ba, Mk da kansa mamakin kansa ya ringa ji, bai taba zaton zai iya mata haka ba, sai dai wata'kila yadda take gasa masa duk maganar da ta zo bakinta yasa ya iya jarumta haka.

Sa'adah tana ji, tana gani, ya hanata makaranta, duk ta zama wani iri, zaman nasu dai gashi nan, ta koma shiru, ba walwala sosai, kullum cikin kunci take amma bakinta dif, sai kuma yanayin data koma ya dame shi, fata yake su koma kamar da, rayuwar farin ciki, amma abin na neman cin tura, a zahiri dai suna zaune lafiya amma kuma babu nisha'di a cikin zaman.

Saboda su Halima da suke fadin "dama ai sun san pooling dinta yake yi, ba wata makarantar da zai barta, duk dan'iskan namiji zai yi iya yinsa ya kulle matarsa a gida saboda sun San Annabi baya tuntuben harshe, duk abin da ka yi da matar wani, sai anyi da taka.


Wattanni kusan biyu zamansu ba armashi, bata masa komai na laifi, amma kuma ta dadare ranta, suna cikin haka, aka fara babban zabe na kasa, kowa yasan Malaman jami'oi ne baturen zabe, Dan haka wata guda aka dauka ana yiwa su Mk horo na mussaman kan yadda zasu kare muradan yan kasa, kar su yarda ayi amfani da su, ayi wa dimokaradiya kafar ungulu, Malaman addini suka dinga musu wa'azi na suji tsoron Allah su yi gaskiya a cikin aikin da za su yi, karshe suka rufe bayanin da cewa duk wadda aka bashi kudi dan ya yi magudi, to ya karbe kudin ya adana, sannan ya yi adalci, ma'ana ya fadi sakamako na gaskiya.

A yanzu da suke shiga shekaru biyar da aure shi da kansa ya tabbatar tsoron ta yake yi, idan akwai abin da ya tsana to ta share shi, ko ta tsiri fushi, ko ya fita sai ya dawo, yasan yadda ya yi ya shawo kanta, yayin da ita kuma take jin kanta a sama komai take so sai ta same shi, SUMAYYA kanta mamakin yadda Sa'adah ta dawo take yi, kullum cikin tsadaddun sutura take , hatta salooon din da Sa'adah take zuwa one in town ne, kullum suka yi waya sai ta mata nasiha ta saukaka buri, ta rage dorawa mijinta hidimar da bai kai ya yi ba.
Itakuwa sai tace da ba zai iya ba, ai da bai yi ba, ya hanani karatu ai kuwa dole yamin yadda nake so, tunda idan ban ci ba ma, na waje ne zasu ci, har Sumayya ta gaji ta zuba mata ido tana mata addu'a.

Rannan da yamma Zainab Ma'aji ta ziyarce ta, kasancewar ana daukan lokaci kafin su hadu a dalilin Zainab din tana karatu ne a Jami'ar jahar kaduna(K.a s.u). ba kowanne hutun ma take zuwa Kano ba, sai take barin hoste ta tafi gidan kanwar mahaifiyarta ta yi hutunta indai ba mai tsayi bane.

Mamamki ta tsaya yi ganin yadda Sa'adah ta koma, ta goge sosai, fatarta ta yi fresh tabbacin tana samun tsadadden mai, tasan Sa'adah Yar gaye ce, amma ko kusa ba kamar yanzu ba, da ta ke samun dukkan wants dinta.

Sauyi sosai ta gani tunda ga jikinta, da abubawan more rayuwa na gidan, da cima ta mussaman, ga wata irin ginshira da ta gani a tare da ita.

A sanyaye Zainab tace "Kin zama wata Hajiya ko big madam zance? lallai Uncle a gaishe shi, ina Jawad? hatta maganar Sa'adah ta canja sai anfitar mata da wani salo na daban. lamarin da Zainab ta dinga dariya tana fadin ko za ki yiwa kowa wannan iyashegen ban da ni.

Suka yi dariya gaba daya sannan suka shiga hira, a gidan Mk ya tarar da ita, ta gaishe shi da girmamawa, shikuma ya dinga mata barka da zuwa cikin karamci, a dan dawowarsa da ya yi , Zainab ta fahimci abubuwa biyu, Uncle Mk ya gama lalacewa akan soyayyar kawarta, yayin da ita kuma Sa'adah take amfani da hakan take yin duk abin da take so.

Zainab ta tsinci kanta da adduar ALLAH yasa su Halima ba su jefa ta cikin HALIN YAU na bin malaman tsubbbu, domin ta tabbatar tun shekarun baya da Halima bata gama sanin kanta ba, take zuwa gidan malamai, ko aiken uwarta ko na kanta.

Har ta bar gidan tana jinjina wa Mk tana fatan Allah ya bata miji mai kwatankwacin halayyar sa.

Manyan kudade Mk ya samu a zaben da aka gudanar, saboda karamar hukumar da aka kai shi, itace mafi yawan jama'a, ganin gwamnati mai ci zata sha kaye, sai ta hargitsa zaben wannan yankin, tare da kiran Mk har gidan gwamnati a sirrince, aka tura makudan kudade a asusunsa akan ya canja alkulluman zaben, ya karbe kudin kamar yadda aka sanar da su.
bai canja alkulluman ba, amma sai sakamakon ya zama inconclusive, ma'ana bai kammala ba.

Kwana biyu yana jin farin ciki, yana ayyana indai kayan 'kawa sune muradin Sa'adah zai mata su, zai kashe mata ko nawa ne dan zamansu ya dawo tamkar shekaru biyun farko na aurensu.


Ba zato, ta ganshi da deep freezer, hankalinsa ya kwanta da ya ga Sa'adah ta yi murna, rabon da ya ga murmushinta sosai irin haka tun kafin su fara yar tsama.

Tare suka fita, suka yi siyayya mai uban yawa da tsada, hatta Sa'adah da kanta sai da ta girgiza da irin manyan laces da atamfofi super, da kuma shadda getzner da Mk ya dinga dibar mata. matu'kar tace abu ya mata kyau zaice ta dauka.
Barin takalma kirar itali da dogayen riguna rantsatsu, hatta turaren Escada da yasan tana so amma baya iya siyansa saboda tsadarsa, a wannan lokaci guda biyu ya siya mata, bayan kayan kwalliya na garari, suka zarce bakin asibitin Nasarawa, suka yiwa Jawad siyayyar hadaddun kaya masu yawa, hatta dan gidan Mahmoud da ya kasance jariri(Dady) sai da suka masa siyayya sosai.

A hanyar su ta komawa ya bata labarin inda ya samo kudi, ya kara da cewa
"Ina son na kewaye mana filinmu, a kuma fara ginin zuwa inda zai samu, a hankali kuma sai na dinga yi, har na kallama".

Ya kalleta ya ga farin cikin ta ya kasa boyewa yace "ki nutsu ki fada mini irin tsarin da kike so a miki a ginin, nasan dai kina son garden?"

Da azama tace "Da swimming pool, sannan upstairs nake so, irin wadda kafar benen zata kasance a tafken falo, a mini dining area, sannan kicin ya zama a cikin falon yake a fili, Ina fatan ka gane irin wadda nake nufi?"

Cike da shauki yace "Na gane duk da bai gama zuwa mana ba, nasan kema a finan finan ketare kike ganin kicin din, ba damuwa za'a miki irinsa Ummu Jawad my dear".

Ta rufe ido tana jin duk wani kunci na zuciyarta ya wanke mata tas. Shikuma yana ta barin jiki wirin sake sata walwala.

Tafiya ya shirya musu zuwa Abuja, duk a kokarinsa na son dawo da amincin dake tsakanin su.

Gidan Mahmoud da yake Goron Dutse, aka kai Jawad saboda makaranta, kuma yafi kusa.

Ranar Alhamis suka tafi, sun Isa lafiya, karfe uku suna madaidaicin Hotel din da ya kama musu daki.

Sallah suka yi, sai cin abinci ya biyo baya, wadda a hanya suka tsaya ya siyo, sai da suka koshi, suka yi wanka dan warware gajiya, sannan suka dora da sallar la'asar.

Barcine ya gwada musu fin karfi, Mk ne yafara yi, Sa'adah ta zuba masa ido tana kallon kyakkawar fuskarsa, da yadda yake sauke numfashi a hankali cikin nutsuwa, wani irin shauki na mamayarta, tana jin sonsa na bin duk wata kafa ta jikinta. A haka itama barci ya wuce da ita ba zato.

Sai daf da maghrib suka farka, suna mamakin lokacin da suka shafe suna barci.

A gurguje, Mk ya dora alwallah ya fita neman massalaci, ai kuwa cikin sa'a bai yi tafiya mai yawa ba, ya samu.

Kafin ya dawo Sa'adah ta ninke shimfidar gadon, ta dauko bedsheet din da ta zo da shi ta shimfida, ta sake dauko burner ta jona ta zuba turaren wuta, nan da nan daki ya dauki daddadan kamshi.

Ganin lokaci ya tafi bai dawo ba ta gane sai ya sallaci isha lafin ya shigo.

Ya dawo ya sameta cikin kwalliya sosai, ga sanyi ac da kamshin turarenta da kuma na turaren wuta ya cakude, dakin ya zama na mussaman.

Da sauri ya yi wurgi da ledojin hannunsa wadda gasasshiyar kazace, sai kuma ruwa da yogurt masu sanyi. ya isa kusa da ita yasa hannun ya rungumeta tsantsan yana ta shin shinarta, ita kuma ta lafe a jikinsa tana jinta in a new world.

Sun jima a hakan, kafin ya saketa, ya zauna a kasan kafet, idonsa ya kada, leda ta bude ta dauko plate da ta juye musu kazar, suna ci ta gabatar masa da shayi a dan karamin flask ga kuma cup da spoon a ciki, ya kalleta da murmushi yace "shiri kika yi haka?" Murmushi ta yi kawai.

Suna kammalawa Sa'adah ta yo brush, ta hadawa Mk ruwan wanka. Kafin ya fito ta shirya cikin sabbin nighties masu daukan hankali. Ya fito daure da faffadan tawul, ya tarar da jallabiya da gajeran wando akan gado, ga kuma body spray dinsa na Malizia.

Turaren kawai ya fesa ya dauke kayan ya dorasu kan side drower.

Ya zauna sanyi dakin na ratsa shi, yana ayyana suna komawa zai sanya musu Ac.

Tana tsaye tace "ba zaka sanya kayan ba?" Ido ya kanne tare da fadin "Ban bukatar su a yanzu".

Kunya ta kamata, ta waske da fadin "Mai ba zaka shafa ba shima?"

Maimakon ya amsa mata sai ware ya dukkan hannuwansa biyu alamun ta zo gare shi, ta tsaya tana kallon sa, ta kasa motsawa, yace "plz Dear come to me".

Cikin kunya ta isa gare shi, ya zaunar da ita kan cinyoyinsa ya rungume ta tamkar zai hade su.
Ta lafe a kirjinsa tamkar wadda zai shayar da ita, ya sunkuyar da fuskarsa daf da tata, numfashin su ya dinga haduwa, tsinin hancinsa akan nata, jikinsu ya dauki wani irin tsimi.

Ya raba hancinsu, amma fuskokinsu a hade. Cikin wata murya da Sa'adah bata sanshi da shi ba yace "Ina sonki, ina son na rayu da ke! Dan Allah stay with me".

Jikin Sa'adah ya yi la'asar, da murya marar amo tace "kana ganin zan iya barinka ne Malam?"

"Matu'kar kina tare da su Halima, kina basu damar da suke cusa miki ra'ayinsu Ina tabbatar miki zasu raba ni da ke" ya fada cikin rawar murya.
Kafin ta yi magana ya zarce da fadin "Ina miki son da zan sadaukar miki da komai, idan nace komai, ina nufin har rayuwa ta amma ke baki fahimci hakan ba"

Ya sake ri'keta sosai, cikin wata murya irin ta karaya da lamari yace "Bana son kaifin harshe Sa'a, bana miki akan me zaki dinga mini? zan ro'ke ki! dan Allah fada mini inda na kuskure miki da ban cancanci ki zauna da ni lafiya da kyautatawa ba?"

Ta yi shiru tana jin hawaye na cika mata idanuwa, haka kawai take jin tamkar wani abu na tashin hankali zai biyo baya.

Jin shirunta sai ya zarce da fadin "ki bude baki, ki mini magana, ki fada min inda na gaza sai na gyara tunda ubangiji ya dora mini sonki da son zama da ke".

Ta girgiza kai muryar ta na rawa tace "Ba ka gaza ba Malam".

Ya nisa yace "Am not good in bed?".

Kunya ta kamata, ta cusa fuskar ta a kirjinsa, yace "magana muke yi ta gaskiya".

Ta dinga dan dukan kirjinsa tana cewa "Ai kasan dai kure ni ka ke yi anan ma."

"Idan kuwa hakane, to mai ya kawo Kika canja, mai yasa kike bijire mini?"

"Ka yi hakuri zan canja".

Yaushe zaki canja din?".

Ta tura mai Baki gaba cikin shagwaba tace "Na canja fah".

Da'di ya kamashi ya dinga kai mata kisses ta ko ina tamkar mayunwacin zaki.hannuwansa suna ta kai komo a jikinta.

Da kyar ya sarara mata, dukkansu sai numfashi suke mayarwa, daga inda yake ya mika hannu ya janyo ledar yogurt ya bude ya fara bata a baki, Yana cewa "ke Amaryace yau! irin Amaryar da ta kerewa mata hudu"

Da'di ya kamata, ta sha iyakar shanta, ya shanye ragowan da ta bari daga nan ya sa harshe yana lashe mata baki, ya janyo harshenta Yana sucking irin deep din nan, daga haka suka fada zazzafar soyayya mai dimautarwa.

Haduwar ta zama so ma sha Allah, saboda hadin kai da Sa'adah ta bayar, sabanin kwanakin baya da take zame mishi very doll.






*Surayya Dahiru*
✍️✍️
07/04.


🌺 *HALIN YAU*!🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

lafazee writers.


*A guji taba Wañnan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*Doka mi lamba ta 68 ta yi nuna cewa satar fasaha Babban laifine da yake dai-dai da satar Dukiya*.




*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*


*Tukuici ga*
*HAJIYA RABI SANI*
*Bisa yaddda kike son rubutun Halin Yau, Na gode, Allah ya shirya zuri'a*
*SA'ADAH NA GAISUWA*.




71-74.




Wannan dare ya shiga cikin dararen da ba zai shafe a zukatan su ba, saboda sun jiyar da junansu farin ciki na ban mamaki. Sosai Mk ya bawa Sa'adah soyayya da kulawa mai yawa, kullum suna tare ba inda yake zuwa idan ba masallaci ba, itama kuma bata komai sai gyaran daki, wannan hutun ya sabunta soyayyar su, ya kara musu shakuwa, ya kuma goge dukkan tsattsar dake zukatan su, aminci da Nishadi ya cika 'kalbinsu.

Kwanaki biyar suka yi amma fahimtar da suka samu a cikinsu ya zarta na wattanni biyar.
Ana gobe za su dawo da daddare, suna kwance ya rungumeta sosai tamkar zai maida su halitta 'daya, hatta bugun zuciyar su suna ji, sai dai bugun da zuciyar Mk yake yi ta zarce ka'ida.

A hankali Sa'adah ta ce "Malam baka da lafiya ne?"

Murya a dakushe ya ce "me kika gani?"

"Bugawar da zuciyarka take yi yanzu ya sha ban ban".

Cike da rauni ya ce "fargaba nake yi Sa'adah! bana son mu koma Kano ki canja mini, na fi son wannan rayuwar da muke yi, mai cike da nutsuwa da girmamawa".

"Nace komai ya wuce fa, sannan ai na baka ha'kuri, mai yasa ba ka gamsu ba?"

Kai tsaye ya ce "ki mini al'kawarin yanke kawancenku da su Halima, Ina rokon ki, ki rabu dasu, sannan ki mini al'kawarin baza ki dinga 'daga mini hankali ba, komai kike so a hankali zan miki kin ji? Ni dai fatana mu zauna lafiya".

Haka kawai ta ji hawaye na zubar mata karon farko da ta ji tausayinsa ya cika mata zuciya, sai take jin tamkar mutuwa ce zata sure wani a cikinsu.

Jin 'dumin hawayenta na zuba akan kirjinsa, yasa nasa hawayen da tun dazu yake kokawa da su, suka kwace masa! kwatsam Sa'adah sai jin saukar hawayensa ta yi akan goshinta, karon farko da ta ga ko jin hawayensa a cikin shekaru biyar da ta yi tare da shi, hatta mutuwar Hajiya Babba da ta masa mugun bugu, ita dai bata ga hawayensa ba.

Kuka sosai Sa'adah ta saka tana cewa "Malam me kake yi haka, me na yi haka? me yasa kake zullumi har haka akaina? Kai baka ganin laifin kanka sai nawa ka'dai?"

Da rawar murya ya ce " Nan duniya ba wadda zai cusa mini ra'ayi akan ki na yarda, saboda na fishi sanin ki, hakanan son da nake miki ba za bani kuzarin da zan cutar da ke ba".

"Nima ba a cusa mini ra'ayi akan ka ba".
Murmushi mai sauti ya yi wadda baya dau'ke da nishadi ko ka'dan.
Ya ce "shikenan fatana dai ki kulle kofofin da kika bude wasu suke shigowa cikin matsalar mu, wadda Ni da ke kawai ta shafa".

"To Malam ya maganar makaranta ta?"

"Da gaske za ki yi, amma sai kin dawo mini Sa'adah ta, kinsan tun farko bana shiri da Gogel badan komai ba, sai dan rudeness dinta, shine yanzu zaki dawo mini a Gogel din?"

Ta 'dan dara kadan! kafin ta yi magana, ya rigata da cewa "Ban so na fada miki yanzu ba, amma bari ki ji, kinsan naje Abuja na yi jarrabawar scholarship, idan na Sami nasara, zan yi PhD dina tsawon shekaru hudu a kasar England, so nake idan na tafi, naga da yiwuwar ku bini ke da Jawad sai ku bini, sai kiyi karatun ki acan, amma ba al'kawarin hakan na yi ba, Ina fatan dai hakan ya kasance, muna komawa zaku yi passport, na riga na yi nawa, idan hakan bai samu ba sai kiyi anan, kafin na dawo kinci karfin karatun ki".

"Allah ya zaba mafi alheri"
Inji Sa'adah.

"Ameen ameen" MK ya amsa mata.

Da haka ya shiga lasarta cikin wani salo mai gigitarwa, tsawon lokaci yana sarrafata kafin su fada duniyar masoya mai nauyin bayyyanawa.

Karo na biyu da Sa'adah ta gasgata ana kwana ido biyu, a ranar basu runtsa ba, dan kuwa a kunnen su aka fara kiran sallar asuba, wanka Mk ya fito ya ganta kwance tamkar matacciya barci na kai mata caffa

"Daurewa za ki yi, ki yi wanka ki yi sallah, sai ki yi barcinki".

Da kyar ta tashi tana Jin dukkan gabb'anta sun mata nauyi wadda ba komai bane ya sababa hakan ba illah sububurdar da ta sha a hannun Mk hatta farcenta nauyinsu take ji, ya fice masallaci yana jaddada "kar fa ki koma".

Ta yunkura ta nufi toilet din tamkar mai koyon tafiya, da ruwan mai zafi ta yi wankan, ta jima zaune cikin ruwan saboda yadda take jinta a bude, tana ayyana me yasa shi baya kaita toilet ya gasa mata jiki, ai yasan yau bai mata da sauki ba.

A daddafe ta yi sallah, akan sallayar ta kudundune tana ta fama da kanta tare da fatan ta sami barci ko ta dawo daidai.
Koda ya dawo ya iske ta a kasa, murmushi ya yi sannan yace "ga ta da kwadayi ga kuma lalaci".

Ya dauke ta cak ya dora a gado, ya cire jallabiyarsa, sannan ya kwanta ya lullube su da bargo, a tsarinsa so ya yi su tafi daidai wannan lokacin, rashin barcin da bai yi ba, yasa ba zai iya tuki cikin nutsuwa ba, dan haka ya kwanta yana raya ko da la'asar zasu iya tafiya kaduna, su kwana acan, jibi da safe sai su wuce Kano, a lokacin hanyar Abuja zuwa kaduna cike take da aminci da tsaro, Allah mun tuba, Allah ka dawo mana da aminci da tsaro a yankin arewa da Nigeria gaba'daya.


Lafiya Lau suka dawo kano, a gidan su Mk suka fara tsayawa suka ci abinci, Hajiya sai Ina ka saka ta ke yi da su, mussaman ta dinga murnar yadda ta ga Sa'adah ta yi kiba ta yi kyau alamun ba ta da matsala.

A lokacin Sa'adah ta ga freezer Hajiya irin ta su ce, da alamun tare ya siyo musu, sai cinikin kankara da pure water take yi kuwa.

Ta gabatar musu da abinci wadda shinkafa da wake ne, da miya sai salad, yayin da Sa'a tace da mai da yaji take sha'awar ci, da hanzari Hajiya tace duk Ina da su, ta fice cikin sauri tana ayyana Allah ya sa ciki ne da ita.

Ta dawo ta ajiye mata tana cewa " jiya Mahmoud ya kawo mini Jawad, ku shiryawa darunsa dan yace ba ruwansa sa da ku, tunda kuka gudu kuka barshi shi ka'dai.

Suka zube mata doya da dankalin turawa da tuffa, sannan suka tafi, ga mamakin Sa'adah sai ta ga ya sauka kan titi ya fada layin unguwar su, farin cikinta ya kasa boyuwa ta ce "Na gode Malam ".

Tare suka shiga gidan suka gaisa da su Baffa da yake yana gida yana fama da mura, sun dan jima tare da Baffa sannan ya fice dan dubo shagonsa.

Hira sosai Sa'adah suka sha a lokacin kuma ta ga gyaran da aka yiwa gidan nasu.

Baffa ya kalleta yace "Iyah Dan Allah ki dinga yiwa mijinki biyayya, ki kyautata masa, ki zauna da kowa nasa bisa karamci, ki ga yadda Gidan nan ya dawo duk aikinsa ne, Ni kam ba abin da zaki mini ki sanya ni farin ciki irin ki zauna da mijinki lafiya da kyautatawa, mazajenku suna wanke mini takaicin rashin haihuwar Namiji, ba abin da zance musu sai dai Àllah ya yiwa nemansu albarka ya shirya musu zuri'a".

Inna ta amsa masa da "Ameen ameen".
Suna cikin haka almajirai suka shigo da doya da dankali.
Mk da Sa'adah sun sha albarka da nema musu tsarin shaidan da makiya.

Da zata tafi Baffa ya ce "kice da mijinki ranar juma'ah ya taho mini da Jawad na kwana biyu ban ganshi ba, kewarsa da ta surutunsa ne suka sukurkutani ba mura ba".

Dariyar jin dadi ta yi tare da cewa "Zan fada masa kuwa Baffa".

Ranar wata alhamis ta ce ya kaita asibiti ta cire abin tsarin iyalin da ke jikinta, da kansa ya ce ta bari suga ko tafiyar za ta yiwu, sai ta cire a can.
Sosai suke zaman lafiya, saboda Sa'adah ta daina zungurar rigima, shi kuma yana kaf kaf da farin cikin ta. A haka har suka kwashi wattanni biyar.

Rannann ya dauketa suka je filinsa da ake ta aiki, ya dinga nuna mata yadda fasalin ginin zai kasance, amma bata fahimci komai ba.

Sai da suka dawo ya dako littafin zanen gidan ya nuna mata, ta yi muranr ganin katafaren gidan da zai zama mallakinsu, sai dai ta kalubalanci ta yaya kafar bene zata zama biyu?.

"Ke kika ce kafar bene a falo kike so?
wannan kuma ta baya ne sai kin shiga corridor sai ki ga kafar benen, idan Ina sama, kina da bakin ki, zan fita ta bayan, ko kuma idan Ina tare da bakina baki da matsalar komai, bari a gama, na tabbatar zai burge ki.

Ta tura baki gaba ta ce"Na ga sama ma katon falo ne ga dakunan barci tamkar na 'kasa sannan har da kicin, ko dai na Amarya ne?"

Ta fada tana matso 'kwalla, ya wurgar da

Please Login or Register in order to submit comment