You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.


*TALLAH*.

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._










47-48



A gigice ya ga ta nufi titi gadan-gadan tamkar zararriya, zuciyarsa ta buga, da azama ya bi ta ganin da gaske tsallakawa za ta yi ba tare da ta duba ba. A ki'dime ya fuzgo ta, ganin mota na shirin yin wasan-kura da ita, amsa-kuwwar motoci sun cika gun, har sai da mai motar ya tsaya ya fito ya dinga zazzaga mata sababi, yayin da ita ko kallo bai ishe ta ba illa fizgewa da ta yi daga ri'kon da MK ya yi mata, ta koma gefe tana hawayen ba'kin cikin maganganun da ya gasa mata.

Sai da ya ba wa mai motar hakuri ya tafi sannan ya tsayar mata da Adaidaita Sahu, juyin duniya ta ki hawa, har mai Adaidaitan ya ji haushi ya yi tafiyar sa.

Ya kalle ta ya ce, "Watau da ma zuwa kika yi ki sake tayar mini da hankali ko?"

Yana rufe baki ta ce "Kadai so hankalin naka ya tashi ne, ha'kuri na zo ba ka, ka ki ha'kura. Ka bi ni da kalaman muzanci, to ai sai ka yi tafiyarka tunda da ma ba kai ka kawo ni ba balle ka ce sai kasa na koma dole."

Ya kalle ta ya ga tana cikin fishi irin wanda bai taba ganin ta yi irinsa ba, sai ya sassauta ya ce,
"Na ji ba ni na kawo ki ba, amma kin ce gurina kika zo, idan kuwa haka ne to ba na son zuwan. Ki koma gida ni zan zo."

Kamar ta ce "Ba na son zuwan naka ni ma!" Sai ta daure ta kalle shi ta ce, "Nasan ba da gaske ka ke ba."

"Zan zo mana da gaske nake."

Ta yi shiru tana rantsuwa a ranta ba za ta yarda da maganganun da ya yi mata ba. Dolensa sai ya janye ko ya ga tashin hankalin da ya ke kirari.

Ya kalle ta ya ga ta turo bakin nan gaba, mamakin yadda ta ke son mayar da laifin da ta masa ya koma kansa ya ke yi.

"Kin yarda na tsayar miki da abin hawa?"

Shiru ta yi masa alamun ba ta yarda ba. Ya kalle ta ya ce, "Magana nake miki."

A gajarce ta ce "Ban yarda ba!Yawon ballagazan ci zan wuce."

Ji ya yi kamar ta wasta masa ruwan dalma a zuciyarsa, ya hassalo sosai ya nuna ta da yatsa ya ce, "Ni kike yi wa magana kamar kina yi da sa'anki? Saboda ba kya ganin girma da mutuncina?"

Ta yi mai shiru ta kasa cewa komai. Ya sake cewa "Ki dinga sanin abin da za ki na fada mini ba na son kau'din baki."

Duk yadda ya so ya tafi ya bar ta a gurin kasawa ya yi, ita kuma ta kafe akan ba za ta tafi ba, shi ya yi tafiyarsa ya 'kyale ta.

Da kyar da jubin goshi ta yarda ya tarar mata Adaidaita, bayan ya rantse zai zo gida ya same ta, sannan zai 'dauki kiran ta.

Yana tsaye yana kallon su har suka bar wajen. Wata ajiyar zuciya da bai san yana ri'ke da ita ba ta kwace, a fili ya ce "Wacce irin yar daru na kwaso wa kaina ne? Da motar nan ta taka ta, ina take son na sa raina? Me zan ce da iyayenmu idan aka gane muna tare ta sami wannan hadari?

Ya dade a tsaye yana mamakin irin son da yake wa Sa'adah. Ya dauka idan ya gan ta ba zai ji komai ba, ya dauka kaifin son ta ya dakushe, ashe ya nan daram. Musamman da ya ga mota na shirin take ta sai ya ji zai iya rasa ransa don ya tserar da ita, ko muzuran da ya mata na karfin hali ne kawai da son kwatar kansa a idonta.

Tana isa gida ana sallar La'asar, sai da suka yi sallah sannan ta ba wa Inna sakon da ta karbo, ta koma daki ta hau kiran MK.

Sai da ta kira har sau uku bai 'daga ba, shi kuma ya fito a Masallaci ke nan kiran ya shigo, bai daga ba sai da ya koma dakinsa ya kwanta sannan ya 'kira ta.

Har ta fara hasashen da ma zai iya rantsuwa akan 'karya? Sai kuma ta ga kiran sa ya shigo, da sauri ta dauka sai kuma ta yi shiru ta tura baki gaba tamkar yana ganin ta.

Shiru ya biyo baya tamkar ba kudi ke bin iska ba.

A shagwabe ta ce, "Na gode!"

Ya ce, "Godiyar me kike yi?"

"Ka cika al'kawari, don Allah ka yi ha'kuri wallahi na horu ba zan sake yi maka laifi ba."

Ta fa'da da rauni a muryarta.

Jikinsa ya mutu, wata irin kasala da ba ta da nasaba da gajiya ko barci ta lullube shi, murya a dakushe ya ce, "Kin bata mini rai, kin tayar mini da hankali, kin jefa ni cikin wasi-wasi mai yawa, kin janyo mini raini."

"Ka yi ha'kuri!" Ta fada da sauri.

Shiru ya yi ba tare da ya yi magana ba, saboda yadda ya ke fama da kansa, ji yake ina ma ya jita a jikinsa.

Murya ba amo sosai ya ce, "zan fada miki, ba na son yaron nan. Ina bakin cikin tarayyarki da shi, wannan ne karon karshe da zan miki afuwa a kansa, ba don girman son da nake miki da kunyar Baffa ba da na ha'kura da ke Sa'adatu. Saboda kina cutar da ni, da ni kika gani da Farida da ban san kalar tashin hankalin da za ki mini ba. Amma saboda yadda nake son ki, na ke gudun bacin ranki haka na rufe ido na rabu da ita da dukkan lamarinta. Ni kuma kin kasa tsayawa gare ni ni ka'dai."

Yanayin muryarsa da yadda ya ke maganar cike da rauni sai ita ma ya jefa ta cikin wani irin yanayin da duk mai lafiya ba zai iya kauce masa ba, tsikar jikinta har tashi take yi.

"Am sorry!" Ta fada a gajarce tana jin ina ma inama...

"Shike nan ya wuce amma kisa a ranki cewar yaune karon karshe da zan saurare ki na miki afuwa akan Khalil".

"Na gode my love!"

Mamaki ya kama shi, karon farko da ta kira shi da wani suna bayan Uncle.
Ya ce, "maimata abin da kika ce?"

Dariya ta yi "Thank you na ce!" Sai ya saki maganar ya ce, "Ba ni labari."

Haka suka sha hirarsu cike da Begen juna, dukkansu sun tabbatar sun yi missing din juna, sun kuma yarda farincikinsu na hannun junansu.

Washagari da yamma ya zo, ba Sa'adah kawai ba, hatta Inna sai da ta yi murnar zuwansa, hira suka yi cikin tattalin juna, har ya ba ta labarin irin gyaran da yake mata a gidan da za su zauna.

Tun daga wannan lokacin Sa'adah ta yanke hul'da da Khalil saboda ba karamin tashin hankali ya janyo mata ba.

Hankali ya kwanta sun shirya da MK amma ta 'kullaci kalmar ballagazancin da ya jefe ta da ita ba ka'dan ba, ta kuma ci alwashin maganar ba za ta bi iska ba, lokaci ta ke jira.

Haka kwanaki suka yi ta zuwa suna wucewa, har watan azumi ya kama al'ummar Musulmai kowa ya koma ga Allah ana fatan dacewa da Rahamar Ubangiji.

Zuwa wannan lokacin shirye-shirye ya yi nisa a bangaren MK, an kammala gyaran gida, gyaran da ya dawo da gidan tamkar sabo.

Mahmoud ne ya hado wa Sa'adah kayan shan ruwa da kayan sallah masu tsada har set biyar da takalmi da jaka set uku sai tarkacen kayan kwalliya da turaruka. Tare suka kawo mata, da za su tafi kuma ya sake ba da kudin 'dinki wanda ta 'ki karba sai da MK yasa ba ki sannan ta karba.
Yawan kayan da kuma tsadarsu ya dan rage mata damuwar rashin lefe musamman idan ta tuna tana da kayan wurin Alh Mamman a ajiye.

Ana yin sallah da sati 'daya iyaye da 'yan'uwan MK suka hada kudadensu, aka sayo dukkan abin da za a bukata, tun daga kan gado da kujeru masu kyau da aminci suka sayo aka shirya gida ya fito sosai, labulaye da carpet suka ajiye sai satin biki za a zo a saka.

MK da ya je ya ga irin kayan da aka zuba masa sai da ya yi hawayen farinciki, ya duba ya ga an 'kawata dakin Sa'adah da dan'kareren gadon da duk fariyarta ba za ta raina ba, ga kujerun ma masu kyau, ba irin gama gari ba, dayan dakin ne kawai aka malale shi da carpet aka bar shi empty, bai sha mamaki ba sai da ya shiga dakin dake tsakar gida wanda shi ne mallakinsa, an saka masa gado amma bai kai na dakin amarya ba, kowanne gado kuma da dimemiyar katifar Vitafoam a kai.

Ya zauna a bakin gadon yana goge idonsa, yana mai yin addu'a ga dukkan ahalinsa, sun masa zumunci ba ka'dan ba.

Ya zauna yana ganin TV da Fridge kawai ya rage wanda su kuma yayarsa Hafsatu ta ce ta aiko da su. Isowa ne ba su yi ba tunda a Lagos take.

Alhaji Isa shi ya sake komawa wurin Baffa ya ce idan ba damuwa suna son a yi auren a cikin sati biyu masu zuwa.

"Yadda ka ce ba ka bu'katar komai a gurinmu sai sadaki, mu ma muna ro'kon ka!Yarinyar kawai muke so don Allah!"

Suka rabu cikin walwala, tare da addu'ar albarkar Ubangiji a cikin auren.

Duk da Baffa ya ce ba zai mata kayan 'daki ba, kan dole ya karbi tsalelen gadon da mijin Sumayya ya aiko masa. Sumayya na zuwa ta nunawa Inna ku'din da za ta kashewa Iya, ita ma ta fito da nata ajiyar ta hada suka shiga kasuwa tare da Sa'adah, suka zabo kayan kicin na garari duk a 'ko'karinsu na kwantar mata da hankali, tunda sun san halinta na son kayan 'kawa.

Hatta kayan fitar biki masu kyau aka tanadar mata shike nan sai hankalinta ya kwanta. musamman da Sumayya ta ha'kur'kurtar da Baffa ya yarda za a kai mata gadonta 'kirar Dubai.

Kafin ranar 'daurin aure gidan amarya ya fito fes komai ya ji, Sumayya ta yaba 'kwarai da kokarin MK da iyayensa, saboda haka sai ta sa aka mayar da gadon dake dakin MK zuwa dakin dake cikin falon wanda babu komai a ciki, shi kuma aka saka masa hadadden gadon Dubai.

Kicin aka sake 'kawata shi da tsirarrun kayan alfarma, aka rufe gidan ana jiran isowar TV da Fridge da kuma amarya! don Mk tuni ya tare a cewarsa gadi yake yi.😁


*05/06*

Ranar aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi da Sa'adatu Bashir Gogel, a Masallacin Sahaba dake Kundila, kamar yadda Baffa ya ce ba za a yi party ko ka'de-ka'de ba hakan ce ta kasance.

Amma kuma ya tsaya an yi abincin 'daurin aure da yini na fitar kunya, duk wanda ya halarcin auren Sa'adah mace ko namiji ya ci abinci mai rai da lafiya don kuwa Bijimin sa Baffa ya yanka, duk tanadin Baffa a shirya abincin fita kunya ya kare. A lokacin sarkar gold din dubu hamsin babba ce, ita ya siyawa amarya da shawarar Sumayya da take ta 'koda irin kokarin da MK da iyayensa suka yi. Sai kuma 'dinkunan da ya mata na kwalliyar amarci.

A Daren da aka daura aure suna zaune a gabansa ita da Sumayya da mahaifiyarsu, bayan ya yi addu'a ya ce, "Duk wani burina a yau ya cika Iyah, ina kyauta zaton na dan'ka ki a hannu na gari don Allah ki bi mijinki, nasan kinsan idan mijinki, ya yarda da ke to Ubangijinki ma ya yarda da ke, idan kika ri'ke wannan kadai za ki gane komai za ki yi a 'dakin mijinki ibada ne.
Ibada kuwa sai an daure domin za ka ci karo da abin da kake so da wanda ba ka so. Na ro'ki ki yi koyi da yar uwarki wurin boye sirrin aurenta, har yau din nan Sumayya ba ta taba fa'din ga laifin mijinta ba, mun sani ba fa don ba ya mata laifin ba ne, haka shi ma yana ri'ke da ita cikin ha'kuri da girmamawa. Ina sake miki nasiha ki zama mai ha'kuri, baki da'yan aure wallahi hakuri ne ya fi yawa, ina fatan ki yi ko yi da mahaifiyarki wurin ha'kuri da biyayyar aure!"

Ya janyo ledar dake gabansa ya fito da sallaya da kur'ani ya mi'ka mata, ta miko dukkan hannunta biyu da suka sha adon lalle ta kar'ba, yace "Ki rike ibada da kyau ita ce za ta jagorance ki duniya da lahira."
Ya kalli Sumayya yana fadin "Ina abin da nace ki ajiye?"

Da sauri ta mi'ka masa dama ta shigo da shi ya karba ya sake mika wa Sa'adah yana fadin, "Ki rike tsabta da kwalliya da ma ba na jin ki a wannan bangaren. Inda nake da shakku akan biyu ne. ki 'karanta buri Iyah kin dai san ni ubanki ba kowa ba ne, ki yi alfahari da abin da yake hannunki, ki daina sha'awar wanda suka fi ki ko kuma wanda ba tsarin tarbiyarku daya ba, a yanzu da za ki koma 'karkashin mijinki, ina hada ki da Allah kar ki dinga dora masa hidimar da ba zai iya ba, ko ba ra'ayinsa bane. Da ace za ki rabu da harkar kawaye to ina tabbatar miki za ki 'karantawa kan ki buri saboda ba kya hangensu. A karshen karshe na yafe miki dukkan kurakuran da kika mini, ina fatan Allah Ya lullube rayuwarki da albarkaSa, ya ba ki zuri'a mai albarka, ya kuma hore miki ha'kurin zaman aure."

Daki ya yi shiru sai shesshekar kukan Sa'adah, Baffa ya nemi Inna ta ce wani abu, ta girgiza kai tare da cewa, "Duk abin da zan fada na dade ina mata bita indai mai ji ce ai ta haddace su. Fatana Allah Ya albarka ci aurenta."

Cikin soyayya mai yawa Baffa ya kalli Sumayya ya ce, "Saura ke babbar yaya uwa ta biyu!" Ta yi murmushi cikin sanyin murya ta ce, "Komai kun fada Baffa, fatana a ce duk ta ji ku da kunnen basira, ta kuma ri'ke 'yan'uwansa da girma, musamman iyayensa. Ki rike su da mutuntawa komai za su miki kar ki nuna kin ji haushi ki yi hakuri, ki sake ninka kulawarki a kansu, duk kuma wanda ya je gidan, ki karbe shi da sakakkiyar fuska su ji tamkar a gidan yar'uwarsu mace su ke saboda sakewa da walwala."

Baffah ya nisa yace " idan Kika bi maganganun mu kin tsira! Idan kuwa kika je kika biyewa 'kawayen banza da son zuciya ki tabbatar ke 'kadai za ki dauki 'bacin ran da zai same ki, ki bi mijinki ko zaluntarki yake yi ki bishi da addu'a idan abin ya gagara, sai mu shiga, amma idan ke Kika bijire to fa kisani baki da wurin zama a gidannan".

Ya rufe zaman da doguwar addu'a ya kuma rike ta a hannunsa ya tafi kai ta 'dakinta da kansa a motar Alhaji Isa da ya zo daukar Amarya.

'Yan'uwan Baffa da na Inna da suka zo, sai mamakinsa suke yi da ya hana su zuwa kai amarya, ya tafi da kansa ya kai 'yarsa dakinta.

A lokacin kam ya zo da sabuwar dabi'ar da ta sha banban da al'ada, ashe shi yasa yasa aka kai su suka ga gidan amarya tun jiya?






*SURAYYA DAHIRU*.
✍️✍️


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•


*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*



*TUKUICI GA*
_*AISHA IBRAHIM BAFARAWA*_
(*BEAUTY*)
*MK DA SA'ADAH NA GAISUWA*
👍




49-50.




*GIDAN AMARYA*


A gidan su Baffa suka tarar da su Baba Umaru da Baba Idi da kuma MK. Tunda Baffa ya fa'da musu a wurin 'daurin aure cewar shi zai kai amarya 'dakinta kar a turo mata, sai suka fasa komawa Bichi a yau, suka ce su za su karbi amarya da kansu.

Haka Baba Umaru ya tisa MK da jan kunne iri-iri akan ya ji tsoron Allah ya ri'ke matarsa cikin tausayi da adalci, komai za ta yi ya dauke kai ya fahimtar da ita cikin ruwan sanyi.

Baba Idi ya nisa ya ce, "Sannan zan fa'da maka gida naka ne, amma kayan ciki na matarka ne, kana dai ganin irin mutunci da karamcin da aka maka, to ina ro'konka! ka nuna kai ma ka san mutunci ta hanyar zama da yarinyar nan da kyautatawa, ba hankalinku 'daya ba, mata lamarinsu yana da gigitarwa.
Amma idan aka yi ha'kuri da su, aka musu afuwa sai a ji dadin zama da su, saboda masu rauni ne, kuma masu tausayi ne".

Alh Isa kuwa cewa ya yi, "Abin da zan fada muku ni ne uban Mukhtar, ni ne uban Sa'adatu, sannan ni ne alkalinku dukkanku 'daya kuke a gurina. Ba zan saurara wa duk wadda ba shi da gaskiya ba".

Ya kalli Sa'adah da take gurfane a lullu'be cikin lafaya, "Sa'adatu duk da ba na fatan matsala, amma duk abin da ya taso na rashin jin dadi, ni ne Babanki, ni za ki fadawa kar ki ji nauyi ko kunya, waya kawai za ki mini, ni kuma zan miki maganin ko mene ne, domin duk girman Mukhtar yaro ne karami a idonmu, na san kuma mun isa da shi".

Baffa dai bai ce komai ba, da'di ya cika zuciyarsa, Allah Ya kai Iyarsa cikin ahalin da suka san mutunci suke kuma rama shi da alheri.

Bai ce komai ba sai da suka mike, ya kalli Mukhtar ya ce, "Ban baka aure ba sai da na tabbatar kana da nagarta, ina kuma zaton kai din adali ne saboda ka siffantu da kyawawan dabi'u don haka ni ba na shakku a kanka. Sai dai kar ka bari jan kunnen da ake ta faman yi maka na ka kyautata mata, ya yi dalilin da za ka bari ta yi abin da ta ga dama, ka bude kunne ka ji ni sosai. Duk 'kawa ko makwabciyar da ka ga dabi'arta ba ta yi maka ba, ka shata wa matarka layin mu'amala da ita, idan ka bari ta fi karfinka to kai ne za ka sha wahalarta".

Su Baba umaru suka hada Baki wurin cewa, "Ba ma za ta bijire masa ba, ai barewa ba za ta yi gudu d'anta ya yi rarrafe ba, In sha Allah, irin halin gidansu na girma za ta yi ba *HALIN YAU* ba".

Aka rufe maganar da doguwar addu'ar zaman lafiya da neman tsari daga sharrin shaidan, da shaidanun mutane. Suka tafi MK ya bisu a baya, yana ta musu godiya tare da fadin duk abin da suka fada zai kiyaye, bai juyo ba sai da motarsu ta bace wa ganinsa. Sannan ya bi bayansu zuwa bakin titi ya karbo gasassun kajin da tun yamma Mahmoud ya yi masa booking, ya hado da yougurt din L & Z da kuma lemon 5alive, yana tafe yana ayyana bai taba ganin nisan bakin titi zuwa gidan nasa ba sai yau. yana isa ya rufe gidan.

Kamar a guje ya fada falon! ya tarar da ita zaune a inda suka bar ta, tana rufe ruf cikin lafaya.

Gefe daya ya ajiye ledojin hannunsa, ya isa kusa da ita ya tsaya, a zuciyarsa yake ta fadin Alhamdulillah! sannan ya sunkuya ya 'dago ta tare da fadin , "Assalamu alaiki! Barka da zuwa gidanki, ina miki murnar wannan rana mai cike da farinciki".

Ta yi shiru, ta kasa amsawa saboda yadda zuciyarta, take a cunkushe da alhinin barin gida.

Ya ri'ke hannun ta yana janta zuwa cikin 'dakin da shi ne mallakinta, a bakin gadon ya zaunar da ita tare da fadin, "Haka na ga ana yiwa amare." Yana warware mata laffayar zuwa kafadarta, fuskar ta masa kyau duk da ta kode saboda kukan da ta ke yi. Kusa da ita ya zauna sosai har jikinsu na gogayya da juna ya dan ri'ko ta ya ce, "Kukan na mene ne tamkar ba gidanki za a kawo ki ba, ke da kika yi sa'a a gari za ki zauna duk lokacin da kika so zuwa gida, zuwa za ki yi to menene abin kuka sai ka ce ba gidana kika dawo ba".


Tissue ya dauko a kan madubi ya shiga goge mata fuska, yana ta fadin maganganu masu taushi.

Ya kalli agogo ya ga tara saura,ya mi'ke ya dauko ledar kajin da ya bar su a falo, sai da ya shimfida musu abin zama sannan ya janyo ta ta sau'ko 'kasa, ya bude ledar ya tura mata gabanta yana cewa, "Nasan tun safe ba komai a cikinki. Taimake ni ki ci"
Ya zabura ya nufi kicin ya samo 'yar roba ya wanke hannu sannan ya zubo ruwa a ciki ya dawo, da rarrashi da hikima ya sa ta cin kazar nan, har ta manta ita ba'kuwa ce, dama kuma azabar yunwa ce a cikinta. ya sake lallabawa ya tura mata yougurt, sai da ya ga ta nutsu sosai sannan ya kalle ta ya ce, "Ga toilet nan ki shiga ki yo brush ki dauro alwala"
Ya mike yana fa'din ni ma bari na yi alwalar.

'Kirjinta ya buga fargaba ta kama ta yau gata a daren farko da ta ke karantawa a cikin littafai ko ya ya nata daren zai kasance?

Har ya dawo tana zaune a inda take.

"Kin yi alwalar kuwa?"

Shiru ta masa ya tabbatar ba ta yi ba sai ya ce, 'Tashi mana!" Ya sa hannu ya 'dago ta, sai da ya raka ta har kofar bayin da ke cikin dakin sannan ya dawo yana tattare kayan da suka yi amfani da su, ya shimfi'da musu sallaya ya koma gefen gadon ya kishingi'da yana jin matsanancin bege na ratsa shi.

A bandakin ta tarar da sabon brush da makilin, sai da ta wanke bakin sannan ta 'dora alwalar sai kuma ta tsaya a bakin 'kofar ta kasa fita. Wata irin fargaba ce ke haniniya da ita.

MK da ya ga shirun ya yi yawa, sai ya tashi ya tura kofar ganin ta a tsaye, yasa shi yin turus, bai ce komai ba ya ru'ko hannunta yana fadin, "Ba na son ba'kon yanayin nan da nake gani tare da ke a yau".

Laffayar ya mi'ka mata ta fara kokarin na'de jikinta, ya kalle ta ya ce, "kin ga ba sai kin yi wannan na'din ba, kawai ninka ki yafa".

Ba ta musa ba saboda yadda bakinta da jikinta suka yi

Please Login or Register in order to submit comment