You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na kira sai kika riga ni, Ina fatan kin yini lafiya?"

Haushin sa ya kama ta sosai ta kasa tanka masa, amma tana raya cewa wai ya manta da jin muryarta.

Jin ta sake masa shiru sai ya kashe wayarsa.

Ita ma ta ajiye wayar daga kunnenta, tana gaskata zarginta na zaton MK da gaske ba son ta yake yi ba.

Kafin ta yi yunkurin yin wani abu kiransa ya sake shigowa ta yi kamar ba za ta dauka ba sai kuma zuciyarta ta kasa jarumta. Haka ta sa hannu ta amsa, ba tare da ta yi magana ba.

"Kina jina?"

Abin da ya furta ke nan, ta sake yin shiru! takaici ya kama shi cikin fa'da fa'da ya ce, "Kin san ba za ki yi magana da ni ba mene ne zai sa ki kira ni?"

Sai kawai ta saka masa kuka mai tsananin gaske irin mai cin rai! Ya yi shiru yana jin kukan nata wanda yake rasta dukkan sassan jikinsa musamman yadda take yi tana ajiyar zuciya.

Jikinsa ya yi sanyi sosai sannan kuma hankalinsa ya tashi, duk da ya san ma'abociyar kuka ce ita din, amma wannan ba na zallan shagwaba ba ne, da alamun damuwa sosai a cikin kukan.

Ya yi kasa da muryarsa sosai ya ce, "Me ya faru, fada mini mene ne yasa ki kuka haka?"

Jin ya karya murya yana tambayar ta sai wani kukan ya sake kwace mata sosai wanda ya tayar da hankalin MK sosai.

A gigice ya dinga fadin "Don Allah ki yi shiru ki fada mini me ya faru, kin tayar mini da hankali."

Ta kasa magana saboda kukan ya ci karfinta ita kanta so take yi ta daina amma ta kasa sai shesshka da ajiyar zuciya ta ke yi.

Ya yi shiru yana jinta, yana jin shi ma tamkar ya rushe da kukan ko ya sami sau'kin yadda zuciyarsa ke bugawa.

Ya lankwashe murya ya ce, "Sa'adah! so ki ke ni ma na yi kukan ne? Don Allah ki taimake ni ki yi shiru haka nan , ko so ki ke kanki ya yi miki ciwo?"

Cikin kukan ta ce, "Ka damu da ni ne da har kake gudar mini jinya?"

Ya ce, "Haba Sa'adah wacce irin magana ce wannan! Ai ni gani nake yi Baffa da Inna ne kawai suka fi ni damuwa da ke "

Ta yi fit ta ce "A hakan?"

Ya nisa sannan ya ce, "Ke matsala ta da ke ba ki fahimce ni ba, har yanzu kin kasa gane manufata. Kowanne Dan adam yana da tsarinsa, don ina sonki ba zan miki karya ba, abin da nasan zan iya shi zan miki, amma tun ba mu je ko'ina ba, na gane kin raina kulawar da nake ba ki gaba'daya"

Ya dan yi shiru sannan ya nisa ya ci gaba da fadin, "A farko tsakanina da Allah kamar yadda na fada mikil saboda jarrabawar da za ki yi yasa ban cika yawaita zuwa da kuma kiran ki a waya ba, sai ke kuma hakan ya zama dalilin da kika mini kishiyoyi, alhalin kin san har a gidanku na bayyana kaina ina son auren ki"

Ya fada muryarsa da rauni sosai.

Yayin da ita kuma kukan ya tsaya mata cak, tana jin wani irin abu na taso mata da ta kasa tantace mene ne shi.


Ya sake cewa, "Sa'adah duk motsin ki akan idona kike yin sa, ta ya ya ki ke tsammanin zan saki jiki da ke alhalin na tabbatar zuciyarki tana rawa a kaina! Na dade da gane kin samu mai kudi, na dade da sanin kina tare da Khalil har yanzu, ba don ina son ki sosai ba ai kamata ya yi na janye kaina a cikin 'yan takara amma kullum ina karfafa wa kaina guiwa da cewa idan rabona ce ke zan same ki, duk da haka dole na yi kaffa-kaffa don ba ni da tabbacin kina so na bare nasa rai Sugar Daddy ba zai kada ni ba!"

Kunya ta lullube ta, da kyar ta iya cewa "Ba ka da tabbacin Ina son ka fa ka ce?"

Da sauri ya amsa da cewa, "E wallahi da kina so na ba za ki saurari kowa ba, kin ga ni namiji ne zan iya hada mata biyu ko sama da hakan a rana na aura, amma tunda ke nake so, ke na aminta ta zamo mini uwar 'ya'yana ban sake kula wata da sunan soyayya ba. da na lura ba ki ba ni irin wannan matsayin ba, shiyasa na ke janye jikina, musamman yadda kika ci gaba da kula fitanannen yaron nan."


Kalamansa sun sa mata kasala sosai bayan kunyata ta da suka yi.

Da kyar ta bude baki a hankali ta ce, " Na daina!"

Ya yi murmushin da ya iso har cikin kunnenta, ya ce, "Mai ki ka daina din?"

"Abin da nake yi da ba ka so! Sannan kai ma ka daina mini wulakanci, kana nuna mini ba ni da daraja a gunka"

Ya sake murmusawa ya ce, "Akwai darajar da ta wuce na aure ki, na killace ki a gidana?"

Kunya ta kama ta, ta yi shiru dadi na cika mata zuciya.

Ya lankwashe murya sosai ya ce, "Ke ba ki san idan na tsananta zuwa ina kallon ki, za a samu matsala ba? Ko fa waya mu ka yi mai tsayi sai wanka ya kama ni, ya kike ganin kuma idan kullum zan gan ki a kusa da ni?"

Kunya mai tsananin gaske ta kama ta ta kashe wayar tare da rufe idanuwanta tamkar yana tsaye a gabanta.

Ya kira tana gani har ta katse amma ta kasa dauka ya ci gaba da kira har sau uku ta kasa dauka saboda yadda ya ba ta kunya.

Sai ga text ya shigo ta bude ta karanta kamar haka

_"Da gaske nake yi Sa'adah, don haka na roke ki, ki daina kallon rashin zuwana akai-akai da sunan rashin daraja ki, kokari nake yi mu kiyaye dokokin shari'a! zan zo gobe bayan Masallaci amma plz kisa hijabi ki 'boye wadannan abubuwan da suke karya mini alwala. Good night!"_

Ta karanta yafi sau ashirin tana jin shauki mai dadi na fizgar ta, tana jin ta tamkar a gajimare take yawo tsabar dadin soyayya. Ta hakikance MK shi ne mabudin farincikinta, duk wata damuwar zuciyarta ya wanke mata tas.







Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



*TALLAH*

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._







40.



Washegari tun safe Inna ta lura da yadda Iyah ta tashi da kuzari da walwala, duk ayyukan gidan cikin kuzari take yin su sabanin kwanakin biyun da suka gabata da ta ke sukuku.

Kafin La'asar ta shirya, sai dai ta rasa hijabin da za ta saka. Gabadaya hijaban ta guda uku ne, biyu na Islamiyya ne, dayan kuma sallah take yi da shi, ta yi shiru tana nazari sai ta zabura ta fita. 'Dakin mahaifiyar ta shiga ta lalubo wani hijabinta da ta sayo a Jos amma ba ta taba sawa ba, a tsakar gidan ta ware shi kalar fari da maroon fulawa a jikinsa ya yi kyau sosai, ta saka ta ga ya zarta guiwarta da kadan, ta isa kusa da Inna da take zaune ta na tsinkar zogale ta ce, "Inna na dauko Hijabin nan."

"To." Kawai ta ce mata ta bita da ido, tana mamakin yau Iyah ce za ta saka hijabi ba don zuwa makaranta ba? 'Dakinta ta koma ta gama shiri, ta fito sanye cikin riga da siket na wani yadin material mai laushi, maroon colour! Hijabin ya hau sosai, ba karamin karbar ta suka yi ba.

Tana fitowa Inna ta juyo ta zuba mata ido tana raya komai Iyah ta saka sai ya mata kyau, ta ce, "Da kin san yadda Hijabin nan ya miki kyau da kin daina saka mayafi kin koma ado da hijabai."

Dariya ta yi tare da cewa, "Allah Inna tsokana ta kike yi"

"Da gaske nake yi miki, ba ki gan ki ba tamkar bakar Balarabiyar Habasha."

Dariya Sa'adah ta dinga yi sosai tana cewa, "Ashe har haka autar ki take da kyau Inna?"

Can kuma ta katse dariyar ta ce, "Inna Uncle Mukhtar ne zai zo kuma ya ce zai shigo ya gaishe ki."

Dadi ya sake kamata da sauri ta ce, "To! Kamo mini Baffanku a waya na fada masa."

"Kai Inna don zai gaishe ki ne za ki ce a fada wa Baffa?"

"Dole na fada masa mana tunda dai bai san wani zai shigo masa gida ba, idan bai amince ba ai kin san kuwa ba yarda zan yi ya shigo ba."

Sa'adah ta tura baki gaba alamun maganar Inna ba ta mata dadi ba ta ce, "Inna Uncle din ne wani?"

"Wani ne mana tunda ba mu da alaka da shi, sai ya aure ki tukun, zai zama cikin ahalinmu, amma a yanzu kam dole yana da iyaka."

Hakan kuwa sai da ta sanar da mijin nata, ya ce ya shigo idan ya zo babu damuwa. Ta kalli Iyah ta ce, "Komai aka yi shi akan ka'idojin shari'a ba a nadama, ke ma ki yi koyi da hakan. Kar ki yarda ki yi wasarere da hakkin mijinki, ko da baya gidan ki kiyayi duk abin da kika san ba ya so."

Sa'adah ta amsa da "To!" Sannan ta sauya maganar da tambayar, "Inna na dauko juice din?"

Da sauri ta amsa mata da cewa "Dauko mana ki hado da ruwa, ai ba sai kin tambaya ba."

"To Inna ai shekaranjiya na ga kin hana ni dauka ne!"

Tana rufe baki ita ma ta ce "Ai ba don shi aka saya ba, saboda Muutar ya sayo ya ce a ajiye idan ya zo ki dinga ba shi. Kin ga kuwa idan har ba Muutar ba ne ai ni ba zan bayar ba."

Wucewa dakin Sa'adah ta yi tana dariya tare da cewa,"Oh Innah maganar Baffa tamkar hadisi take a gunki!"

"Aljannata nake nema kin san kuwa aljannar mace ta fi samuwa idan mijinta ya yarda da ita."

Cikin dariya sosai Sa'adah ta ce, "Sadaqati Inna! Kin yi gaskiya In Sha Allah har a aljanna ke ce uwargidan Baffah."

Dariyar ita ma ta shiga yi tana fadin, "Allah ya shirye ki Iyah"

Daidai lokacin kuma waya ta hau kuwwa tana dubawa ta ga MK ne, ta amsa, ya sanar mata ya iso.

Ta mikawa Inna wayar tana cewa, "Ya iso."

Daki ta koma ta sake gyara fuskarta sannan ta feso turare ta fito, ta dauki tabarma ta na fadin, "Ki tashi Inna ki kintsa, na ajiye miki Hijabin da za ki saka a kan gado."

Harara ta galla mata tare da cewa ba zan saka wanda kika ajiye din ba 'yar fariya! Kin yi shigarki ta burgewa, amma kin tashi kin fesa turare."

Ta yi kwafa tana ayyana dauke shi za ta yi ta boye.

Murmushi ta yi tare da cewa, "Take heart mom!" Sannan ta juya ta tafi.

Ta isa da sallama yana tsaye yana amsa waya, ya yi kwalliya da yadin kufta kalar ruwan kasa (brown), ya dora hular da ta dace da kayan. Sosai ya yi kyau, musamman yadda sumarsa da hula ba ta rufe ta gaba'daya ba tana ta sheki alamun ta sha gyara na musamman.

Ya katse kiran yana zuba mata ido sosai sai kuma ya hau murza dukkan idanuwansa, ya sake kallon ta soasai, ya bude baki alamun mamaki tsawon sakanni goma sannan ya nisa ya ce, "Sa'adah ce kuwa, ko idona ne ya ke mini gizo?"

Ta tura baki tana dan murmushi tare da shagwabe fuska.

Hakan da ta yi sai ta sake burge shi ya ce, "Kin canja fa! Ba ki ga yadda kika yi kyau ba, ganin ki na yi tamkar 'yanmatan Ethiopia."

Da'di ya kamata musamman yadda bakinsa ya yi daidai da na Innar ta, ya lura da yadda take murmushi, ya fahimci tana son a ce ita mai kyau ce, ko ta yi kyau.

Ya ce "Ki fa daina wannan shagwabar ita ma tana sani a wancan yanayin!"

Ta rufe fuskarta da gefen Hijabinta, ba tare da ta iya cewa komai ba.

Ya sake cewa, "Idan ba so kike na zama agwagwa ba, to ki daina yin ta a yanzu. Ki tara mini ita zuwa lokacin da za mu tsinci kanmu a dakinmu!"

Ta sake rufe ido sosai tana ayyana wai shi ba ya jin kunya ne?

Ganin yadda ta rufe ido ta makale a bango sai ta ba shi dariya sosai.

Ya dan juya dan ganin ba wanda zai ji shi, ya yi kasa da murya ya ce, "Ba ki ji yadda na ji ba, ina ma ni kika makale ba wannan bangon ba! Kunyar nan ma burge ni take yi, komai na ki is special!"

Shiru ta yi ta kasa juyowa, bare ta tanka masa, tana ji a jikinta yadda idanuwansa ke yawo a kanta.

Da kyar ta bar jikin bangon ta shimfida tabarma tana cewa, "Bismillah!" Ya yi kicin-kicin da fuska tamkar ba shi ne mai walwala yanzun nan ba.

Ya ce, "Ba zan zauna ba!"

Ta dago ta kalle shi a kunyace ta ga yadda ya hade fuska, gabanta ya fadi, tana tunanin me ya 'bata masa rai kuma?

A hankali ta ce," Tafiya za ka yi?"

Ya girgiza kai sannan ya ce, "Zaman ne ba zan yi ba, ki dinga shimfida wa Honorable."

Ta yi shiru tana jin fargaba na taso mata!

Ta nisa ta ce, "Amma dai ai na ba ka ha'kuri, magana sai ta wuce."

Da sauri ya ce, "In dai sai na zauna a inda yake zama to kuwa magana ba za ta wuce ba!"

Ya juyar da kansa gefe guda, ganin yana Shirin dawo mata da yanayinsa da ba ta so na nuna ko in kula ta kalle shi ta ce "Bari na dauko maka wani abin zaman to."

Bai ce komai ba, ta nade tabarmar ta shiga da ita, ta dawo da kiret din lemon kwalba mai kwari, ta ajiye ta dora sallaya a kai, kamar ba zai zauna ba sai kuma ya zauna din.

Ita kuma ta zauna a kan wani dutse da ya ke zauren. Ta kalle shi ta ga bai ware ba, ta daure ta ce, "Ba don fishinka na gigita zaman lafiya ta ba, da haka zan so ganin ka kullum. yadda ba yanmatan da za su ga fuskar tunkarar ka, saboda kwarjini da tsare gida."

Dariya ta kwace masa, ya nisa ya ce, "Kina da son kai Sa'adah! Ba kya son na kula yanmata amma ke ba ki kiyaye kula wasu mazan ba."

Ganin ta yi kasa da kai sai ya canja maganar da cewa, "Mahmoud ya na gaishe ki"

A hankali ta ce "Na gode!"

Sun jima suna hira bayan ya sha ruwa, suka shiga ya gaida Inna, ya ajiye mata kudi, sannan su ka koma zauren, ba su dade da zama ba Baffa ya dawo, ya tarar da su, a kunyace, MK ya sauko daga inda yake zaune ya tsugunna ya gaishe shi. Baffa ya amsa cike da farinciki, har ya wuce sai ya dan tsaya ya ce, "Da ma kuwa ina son ganin ka, idan ka samu lokaci ka same ni."

Da girmamawa MK ya amsa da Fadin, " Koyaushe ina da lokaci."

Baffa ya ce "To bayan La'asar gobe idan ranmu ya kai."

Sai da ya shige sannan ya koma gun zamansa, Sa'adah na masa dariyar yadda ya takure.

Ya kalle ta ya ce, "Idan akwai abin da ya fi haka na kunya zan ji tunda yarsa nake so ya ba ni, ya kuma san abin da zan yi da ita!" Shike nan ya rufe bakinta ruf.

Ya zuba mata ido ganin yadda ta turo baki gaba alamun fishi-fishi.

Ya waske kamar bai gani ba, ya nisa ya kira ta da alamun seriousness "Sa'adah!"

Ta yi shiru, sanin halinta na shariya da sanin ta ji shi ya zarce da fadin, "Magana za mu yi ta gaskiya, ki nutsu ki ban hankalin ki."

"A kan kunnenki Baffa ya ce za mu yi magana, ga zatona mafi karfi ina ganin zai yi maganar idan mun shirya kanmu na turo da magabatana."

Nan ma ba ta ce kala ba.

Ya nisa ya sake cewa, "Kina ji na kuwa?"

Kai ta daga masa alamun tana tare da shi.

Ya ce, "Tsakaninki da Allah ki fada mini gaskiya don na san yadda zan tunkare shi. Mun kai lokacin da ya kamata a ce mun fahimci juna, maganar aure idan manya suka shiga ta kare fa! Ba maganar canjawa idan dai ba mayar da iyaye abokan wasa za a yi ba.
So nake yi, ki fada mini da bakinki idan Baffa ya tambayi mun shirya kanmu, me zan ce masa?"

Ta yi kasa da kanta ta kasa cewa komai, tsawon minti guda sannan ya dora da cewa, "Kar ki ji nauyin fadar gaskiya na yi miki al'kawarin zan fahimce ki, zan kuma fahimtar da Baffah yadda ba zai ga laifinki ba."

Ta kasa bude baki ta yi magana ita kanta ba ta san me yasa harshenta ya yi mata nauyi ainun ba? Tsawon mintuna yana dakon ta magantu amma shiru.

"Ina ta magana kin yi mini shiru kuma kin san ba na son ina magana kina ji amma ki yi kunnen uwar shegu."

Ta sake yin kasa da kai, da kyar kuma a hankali ta ce, "Ni to me zan ce?"

Bai ji dadin yadda ta ce ba amma sai ya ce, "kinsan me za ki fada mini da zai nuna kin aminta da Ni ko akasin hakan".

Ta kasa fadar ko daya, ya gaji da sauraronta ya ce "Shirunki yana nufin na yi hakuri, na sha kaye a hanun abokan takara".

Yana gani ta bude wayar dake hannunta wacce ta Inna ce ta fito da ita.

Ba zato ya ji wayarsa ta yi kara kadan, alamun shigowar sako (message) bai duba ba ga zaton sa MTN ne.

Ganin ta share ta hau daddana waya sai ya sake jin rashin dadi sosai, a tunzure ya ce,
"Silent again?"

A kunyace ta ce, "Ka duba wayarka!"

Bai yi musu ba ya dauko wayar sa ya shiga ma'adanar sakwanni (inbox) ya ga text din da ya shigo ita ta turo shi. Da sauri ya bude, harrufa uku kawai ya gani.

"*YES*"

Kawai ta rubuta wani irin dadi ya mamaye zuciyarsa da sauri ya ce, "Kin amince mini na turo Sa'adah da gaske?"

Kai kawai ta daga masa don ta sake ba shi tabbaci.

"Alhamdulillah!" Yake ta fadi tare da cewa "Na gode!" Ya bude murya sosai ya kira ta, bai jira amsawarta ba ya zarce da cewa, "Idan fa kin zabe ni har na turo aka nema mini aurenki, hakan na nufin kin rabu da Honorable, da wannan tabbataccen yaron! Da ma kowa da kowa, sai ni kawai.

Kin ga saboda na san kina da damar ki zabi wanda ya miki shi yasa nake danne kishina, amma tsakani da Allah idan har maganar aure ta kullu tsakanin manya dole ki rabu da kowa kin amince?"

Ba wani dogon Turanci ta ce, "E!"

Farincikinsa ya karu ya hau fadin, "In Sha Allah ba za ki yi nadamar zabe na a matsayin mijin aurenki ba."

Shauki ya debe su ba su ankara ba har aka fara kiran sallah sannan ya tafi yana cewa, "Duk yadda muka yi da Baffa za ki ji."





Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍️✍️.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.


*TALLAH*!

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._








41-42



A Daren ranar Baffa ya sake zaunar da Sa'adah tare da mahaifiyarta, ya ce "Ina sane na bar ki kina sauraran wasu bayan Mutari.
Saboda na ba ki damar da shari'a ta ba ki, na kar na aurar da ke bisa dole, duk da shari'ar tace ni na fi cancanta na zaba miki mijin aure kasancewar ki budurwa.
Amma tunda muna wani irin zamani da 'ya'ya suke ganin sun fi iyayensu sanin abin da ya dace da su, ya sa na ba ki damarki, na sha fada miki aure zan miki, ba kuma zan miki auran dole ba, sai dai na dora ki akan shawara mai kyau. Alhamdulillah lokaci ya yi, don haka ki fada mini a cikin masu zuwa wajenki wa kika zaba? Ina son ya turo mini magabatansa a tsayar da magana guda daya."

Ta yi shiru kanta na kasa, Inna ce ta tanka , "Ai na ga alamar sun daidaita da Muutar din."

Hannu Baffa ya daga mata alamun ta yi shiru, ya bude murya ya ce, "Iyah tsakanin Alhaji Mamman da Mutari wa kike so?"

Ta sake yin shiru, ya nisa ya ce, "Dole fa ki yi mini magana saboda duk hukuncin da zan yanke, ya kasance da yardar ki, ba na so daga baya ki ba ni matsala, kwanakin baya da Alhaji Mamman ya same ni ban ba shi amanna ba, amma na ce ya nemi yardar ki, saboda shi ma mutumin kirki ne, ya samu yabo a wurin mutanen da suke kewaye da shi. Yanzu kuma lokaci ya yi da zan sallami daya a cikinsu."

Inna da ta ke sauraran su ta ji tamkar ta ce Alh Mamman zai sallama amma ta yi shiru saboda bai ba ta damar yin magana ba.

Ya sake kiran ta a karo na biyu, "Iyah!"

Ta amsa murya a dakushe. "Wa zan sallama a tsakaninsu? Ko kuma dukkansu ba ku shirya ba?"

Ta jima kafin ta bude baki ta ce, "Dazu Inna ta fada ai."

Da'di ya kama dukkansu, ya ce, "Kina nufi da Mutari ku ka shirya?"

Kai ta sake yin kasa da shi ba tare da ta amsa ba, Inna ce ta yi fit ta ce

Please Login or Register in order to submit comment