You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya kasa juyowa balle ya bude baki yayi magana saboda tamkar ya fashe da kuka haka yake ji.

Kuka sosai Sa'adah take tana fadin idan yafi karfinta ai bai fi karfin ubangiji ba, ya fa'da mata bakar magana, dan ta rama shine zai mata wannan wulakancin?

Har suka iso layin gidan Sumayya kuka sosai take yi, yayin da Mk ya biris tamkar bai ji ta ba, wani wula'kanci da Mahmoud ya yi mata, maimakon ya isa gidan sai ya samu gefe ya yi perking ya kunna musu a.c ya fice ya barsu, a kokarinsa na su dan sami daidaito shima kuma ya fita ya shaki isakar da zai dan samu sukunin zuciyarsa, da gaske da son Iyah zai mutu a ransa, wannan na cikin kaddararsa rashin cikar buri.

Tsawon mintina Sa'a na kuka sosai, Mk da ya tabbatar ta yi shi ba ka'dan ba, ya santa da son a rarrasheta.

Dan haka ya matsa sosai daga jikinta, ya yi gyaran murya ya ce " kukan ya isa haka My first love".

Wani azabben kishi ya duro mata na ba zata, ta sake karfin kukanta tare da cewa "karka kuma cemin first love dinka, domin ni ba ita bace, kaima kasan ba ni bace. First love dinka tana can tana jiranka wacce ba zata tsufa ba tunda bata da kamar Jawad, Ni barni a makiyarka domin bansan komai da ka mini, kuma kake kan yi mini ba Sai kiyayyya da zalunci hadi da wulakanci".

Jikin Mk ya yi sanyi ya ce da bakinki kika ce ban miki komai ba sai kiyayya da zalunci?".

Da azama ta ce "kwarai kuwa! zan kuma rokeka ka koma ka fa'dawa Hajiya da Baffah su janye dolen da suka yi maka, domin ni ba sonka nake yi ba, ko ina sonka to na ha'kura, domin a yanzu sun nuna mini ka fini a gunsu tunda sai yanzu ne zasu maka dole,to ni kuwa ina tabbatar maka na wuce haka wallahi".


Ya ce "Zan so kwarai mu fahimci juna, domin ni ban zo gurinki bisa ra'ayin wani ba, tsokanar ki nake yi, na gane ke ce cikon farin ciki na, ki zo mu rayu tare na sauran shekarun da ubangiji zai ara mana a gaba. kin san ina son ki, kin san ke kika mini laifi, na dauka ko wani kika ji ya ce na zalunce ki, zaki kare ni, amma fa'da mini me nayi miki na zalunci?"

Ta yi shiru tana kuka kasa kasa, tana jin tamkar ta tashi ta yi ta rawa dan ta nunawa duniya irin farin cikin da kasan zuciyar ta yake ciki.

Ta kasa cewa komai, ya nisa ya ce "Yanzu mu ba yara bane Sa'adah, ya kamata mu bar komai mu manta komai, mu gina sabuwar rayuwar da babu gillin bacin rai a ciki, ubangiji shine shaidata ba komai a zuciyata na yafe miki, na kuma manta komai".

"Kema ki daure ki manta duk wani zaluncin da kike ganin na yi miki, ina tsananin son na rayu da ke my Sa'adah".

Da kuka sosai ta ce "Ba haka bane a zuciyarka, kaima kasan ba haka bane, akwai dalilin da ya saka ka yafe mini amma ba dan kana sona ko dan kana son ka rayu da ni ba, daga ranar da ka jefe ni da mafi munin al'amari, a ranar na gane baka sona, wata kake so, kake neman hanyar da zaka rayu da ita, tunda ni amfani na ya kare a gurinka, ka riga ka dandana ni, shiyasa ka 'karanta tunaninka, ka kasa shaidata, ka kasa gane abin da zan yi da wadda ba zan yi ba, dama Kuma ai tun bamu yi aure ba, kake jifana da wannan zargin, yanzu kuma idan na koma maka ai cewa zaka yi har dakinka nake iskancin".


Ta nisa ta sake cewa "na tabbatar ita baka ta'ba dukanta ba, amma ni saboda rashin gata da 'kin da kake mini kanka tsaye kake duka na"

Ta fa'da cikin kuka, maimakon hankalin Mk ya tashi sai ya ji wata irin nutsuwa ta zo masa domin kuwa ya gane da gaske 'Karfi ya ke da ya ce akwai soyayyarsa mai yawa a zuciyarta duk da bakinta na kirarin 'kinsa.

Kishin Farida ke ya galgalata wannan kuwa ba yadda zata yi sai hakuri. Domin ya riga ya kudire ba zai ta'ba barin matsanancin son da yake yiwa Sa'a ya sa ya zalunci Farida ba, ba kuma zai yi kuskuren rabuwa da ita dan zai dawo da tsohuwar matarsa ba.

Bashi da burin auren mata biyu, amma tunda kaddara ta zaba masa to kuwa zai yi iya kokarinsa bai bari soyayyar daya tasa ya danne daya ba.

Cikin lallashi ya ce "sonki ne yake rufe mini ido shiyasa nake dukan ki, Amma ai kinsan iya bakinki nake duka dan shine mai dafi, amma ta yaya zan doki jikin ki alhalin shine abin hutawata. Na rantse miki banda tsoron ubangiji da a motar nan sai na shige, dan ki gane ba karamin kewar ki nake yi ba, har yau din nan 'kwarar Farida nake yi domin idan ina tarawa da ita bana samun nutsuwa, sai na ayyano ke ce a 'kasana amma kina fa'din wai ban miki komai ba sai zalinci".

Kuka sosai Sa'adah ta fashe masa maimakon ta ji da'din kalamansa, ai sai ta ji tamkar cin fuskarta yake yi, yanzu ya murde mata baki Dan ta yi jam'u ta ce wasu samarin alhalin yasan shi ka'dai ta cirewa samartaka. Amma shi yana fa'da mata yana tarawa da wata kansa tsaye.

A cikin kukan ta ce " in Sha Allah Babu sauran zama a tsakanin mu, zan yi dukkan kokarina naga ban jefa kaina a uku ba, a satin nan zan fitar da wadda zan aura, ba zan iya auren ka ba Mukhtar. Ka yiwa Allah ka rabu da ni bana sonka yanzu".

Cikin rashin damuwa ya ce "Ban damu da ki so ni ba, domin son da nake miki ya isa ya ri'ke auren mu, idan kuma kin kafe ba zaki yarda mu yi auren ba, shikenan amma ki sani ban yi al'kawarin zan iya cigaba da jarumtar kawar da ido akan ki ba, kin sanni sarai! Billahillazi ki shirya yin jegon da babu sannu, domin kuwa ciki zan miki, ki haifarwa Innah, kafin a ankara zan sake dirka miki wani sai akaiwa Hajiyar Bichi".

Gaban Sa'a ya buga da karfin gaske, mafarkin Innah ya Fa'do mata, amma sai ta waske ta daure fuska ta ce "saboda kana jin isa, ko dan ka raina gidanmu?"

Ya make kafada ya ce " whatever".

"Dan Allah Mukhtar ka bude min kofa zan fita na gaji da jin Wannan maganganun marasa azanci da kan gado".

Ya yi dariya ya ce "inace dan kin san bana son kina gatsa sunana ne yasa kike ta fa'da, to idan kin so kina iya cewa Mukhtar Kabir Bichi. Zan amsa miki amma nan gaba ka'dan Billahillazi idan akace ki fa'da ba zaki iya ba, zan fa'da miki wallahi ba zan ta bin kanki akan ki dawo gareni ba. Kina so, Ina so to karmu wahalar da juna dan wallahi kika ce zaki ja ni a kasa, ba zan yarda ba, ki rabu da Alh Mamman ban son ganin ki da shi".

Da guntun hawaye ta ce "sannu ubana, to shi nake so, domin kuwa kullum zai ta ganin yarinta ta ne, dama kuma ai tsofaffin sun fi dadiin harka.

Sosai ransa ya baci, a fusace ya dinga kwankwasa gilashin har Mahmoud ya ankra ya iso ya ja motar har kofar gidan Suka kaita, Mahmoud Yana ta faman tsokanarta ya san ai anshirya sai maganar shan biki, duk yadda take jin nauyin 'Karfi yau haushin sa take ji dan haka har ta sauka kala bata ce masa ba.

Da shigarta Sumayya ta dinga bin ba'asin kukan da take yi, bata boye mata ba, ta bata laabrin wula'kancin da Baffa ya janyo mata a wurin Mk na sawa ya kawota.

Ran Sumayya ya baci sosai ta ce "ai sai dai ki dau dangana domin kuwa Baffah burinsa bai wuce ki komawa uban Jawad ba. Duk irin bacin ran da ya jefa mu, duk irin yadda ya jingine ki shekara da shekaru, yanzu kuma dan gata da rashin kishin naka, Dan ya dawo sai ka sake bashi aure?".

Kwalla ta cika idon Sumayya tana ji a ranta Mk bai cancanci auren Iya ba, har ga Allah ta fi sonta da Anwar, amma ko ita ai ba karamin ba'kin cikin Mk ta hadiya ba.

Amma sanin maganar mahaifin su gaba take da kowa, yasa ta hadiye maganganun a zuciyarta, sannan kuma tasan komin borin da Iyah zata yi ba wadda take so irin uban na Jawad.


****


Sai bayan magariba ya isa gidansa, ya iske Farida cikin cotton din doguwar riga kirar Pakistan, kanta dauke da hular da ta dace da rigar, sai kamshi take yi, ta yi kyau sosai, amma saboda ba ita yake son gani a yanzu ba , sai yaji ba haka yake bu'katar ganin kirjinta ba, so yake ya kamo wadda zasu cika masa hannu kamar yadda dazu ya lalubo na Sa'a da nufin zai kamo bakinta.

Ya zauna a kujera ta tashi ta kawo masa ruwa da lemon coke, da cake da ta yi a yammacin yau.

Yana zaune ya rike kansa alamun yana cikin rashin sukuni.

A hankali ta ce "halan baka jin da'di ne?"

Dai-dai lokacin sai ya dinga jin muryar Sa'a na masa kuwwa tana fadin Alh Mamman take so, ai tsofaffi sun fi dadin harka.

A fusace ya mike ya ce mata "A a asibiti ne a kaina ban son katsalandan wallahi". Sannan ya wuce ya haye sama.

Jikin Farida ya yi mugun sanyi, ta zauna tana ambaton Allah.

Ta jima tana nazarin me ya same shi, kaso mafi yawa tafi zaton Sa'adah ce ta zaunguro shi, kishi ya kamata sosai, domin ta lura duk sadda ta ganshi a burkice to ba shakka itace ta birkita mata miji.

Haka ta yi ha'kuri ta kwashi abincin ta bishi da shi, abin mamaki kuma sai ya rungumeta yana fa'din ta kara hakuri da shi, Yana cikin wani irin al'amari ne da yake neman fin karfinsa Dan Allah ta kara hakuri, ta kuma yi masa uzziri.

Matsananciyar sha'awar Sa'a da ya taho da ita tasa ya kasa fita sallar isha, domin akan Farida ya sauketa, sai da suka samu nutsuwa, suka yi wanka sannan suka yi jam'i tare.




🌺 *HALIN YAU*! 🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai satar Dukiya._*

_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_


*Wannan shafin Tukuici ne ga*
*Amina Mukhtar Nashe*
*Bisa yaddda kike kaunar labarin, ki yi yadda so da shafin, Allah ya raya zuri'a*


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*


93-95.


Ana idar da Sallar isha Baffa bai tsaya a shagonsa ba, saboda yadda ya ke zumudin tattauna al'amarin da Mk ya zo masa da shi a yammacin yau, dan haka kai-tsaye gida ya dawo. Sai da ya kamallah cin abincin da aka gabatar masa ya wanke hannu da baki.

Ya kalli Inna ya ganta duk a takure tun safe haka ya ke ganinta sukuku.
Cike da kulawa ya ce "me yake damun ki ne Salamatu?"

A sanyaye ta ce "Ba komai jikin ne nake jinsa ba tsanani, amma lafiya ta kalau".

Nan kuwa mafarkin da ta yi ne ya saukar mata da rashin walwala.

"Allah ya rufa asiri" Baffa ya fa'da yana kallonta, ta amsa da "ameen a takaice.

"Ina tafe da albishir mai dadi wadda na tabbatar zai tsananta jikin nan naki saboda tsananin karfin farin-cikin da zai saukar Miki a zuciya da ma gangar jikin ki gaba'daya".

Ta gyara zama ta ce " Ai kuwa kana da Babban goro fari kal Baffan Iyah".

Da murmushi ya ce "Abin da muka Dade muna addu'a da fatan ya kasance ne zai tabbata bayan mun debe kauna da samunsa".

Zuciyar Innah ta sake takura amma sai ta shanye ta ce "Al'amarin ubangiji ya wuce hakan, yana zartar da komai a sadda ya nufa".

"Baffa ya ce "kwarai kuwa komai nufin Allah ne, bana dai kukanmu ya kare domin ubangiji ya nufa zaman Iyah yana daf da karewa a gabanmu, dazun nan Mutari ya zo mini da wannan albishir din, tun yamman na so na fa'da miki, ganin ki wani iri yasa na ce wannan maganar mai dadice bari na bari sai mun zauna".

Yana rufe baki ta fashe masa da kuka sosai fiye da wadda ta yi akan auren da Mk ya yi. Kuka sosai ta dinga yi, tana ambaton raini ne zaisa Mukhtar ya iya zuwa gabansa ya ce zai mayar da Iyah a yanzu, bayan ya gama wulakanta ta, ya gama cusa musu ba'kin ciki. Ba dan karfin imani ba da yanzu barin jikinta ba ya aiki saboda tsananin tozarcin da Muutar ya yiwa Iyah har da su, shine yanzu da aka samota da kyar zai dawo ya ce zai mayar da ita, saboda yana ganin komai ya ce maka haka zaka yi masa?"


Baffa ya yi shiru yana sauraronta, wannan ne karon farko tun aurensu da ta zauna take fa'da masa magana cikin kara'di da daga murya, kullum harshenta a kasa yake dan haka ya mata uzziri domin ba dabi'arta ba ce.

Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka sosai tamkar yarinya karama.

Ya ce "Yanzu wannan kukan na menene Salamatu?"

Kai tsaye ta ce "Na ba'kin ciki ne, saboda wallahi na tsani duk abin da zai hada Iyah da Muutar, Jawad ne a tsakanin su ubangiji ya raya shi, amma ni kam na rufe babin wannan yaron mai kafirin ri'ko, da 'Kullaci da kuma rashin ragayya".

"To kuma idan ubangiji bai rufe babinsa da Iyah ba fa? Ya ya zaki yi ne?"
Kafin ta yi magana ya sake cewa na bashi dama ya nemi amincewarta, zan kuma ta ya shi neman yardarta".

Ta kuwa sake fasa kuka tamkar wata sa'ar Iyah.

Ya hassalo ya ce "lallai kin bani Babban goro fari kal Salamatu! na gode miki, amma abin da zan fa'da miki, 'daya ne, Ni ne na haifi Iyah kuma nine wakilinta, ko da shari'a ta bata damar ta zabi wadda ta aminta da shi, a matsayinta na bazawara, Nima kuma shari'ar bata ba ta bata damar yi mini kwangen biyayya ba, dan haka ba zance miki komai a yau ba, sai ta zo gidan nan a gaban ki zan tambayeta ra'ayinta. Da ra'ayin ta zaku ga matsayata".

Haka tsofaffin masoyan suka kwana zuciyoyinsu ba da'di amma Inna ta ta nan kan ba'kanta tana fatan ko zaman mota kar Allah ya sake hada su bare zaman aure, shekaru bakwai yarinya na zaune, sai yanzu tana shirin tsayar da miji zai lallabo ya watsa maneman, kai Muutar ya cika tabbataccen marar kunya, kuma marar mutunci, ta tabbatar zai iya aikata abin da ta gani a mafarkinta sai dai da ikon ubangiji ba da Iyanta ba.

A bangaren Sa'adah kuwa ta shanye murnar dawowar Mk, domin sai da suka zauna da Suamayyah ta sake gane ba 'karamin wauta ta yi ba da ta bari ta ji da'din dawowarsa cikin rayuwarta, domin washagari da zata fita zuwa kotu hawaye Sumayya ta dinga yi tana cewa "Iyah yanzu dai da kike da shekaru talatin da biyu ai ya kamata ace kin fahimci ba abin da mace zata ri'ke a duniya sama da martabarta da 'kimarta. Domin kyau da arziki duk suna samun tawaya, amma idan mace ta ri'ke darajarta to ko da tsufa ya yi wa kyakkawar surarta tawaye wannan 'kimarta da ta ri'ke zata bata kariya. Kar ki bari matsananciyar soyayyar da kike yiwa Mukhtar tasa ki kasa gane a yanzu kinfi bu'katar ki yi daraja a maimakon samun son zuciyar ki.


Sa'adah da take jin magaganun Sumayya har cikin kanta ta dago ta kalleta, sai ta ji a yau tausayin Sumayya ne ya kamata saboda yadda take ganin rauni da wata irin fargaba a kwayar idanuwanta, tana kuma ganin wata irin soyayya da jini kawai ke samar da ita saboda tsananin karfinta da amincinta.

Ta matsa ta rungumeta cikin rawar murya ta ce "Na gode Anti! Ko yau Baffah da Inna suka barmu na san Zan yi kukan rashin ganinsu ne, da kuma adduionsu gare ni, Amma ba na rashin gata ko rashin samun wani abu ba, na tabbatar ubangiji ya zaba mini ke ki zame mini Yar uwa kuma garkuwa domin ya san idan ban samu irin wannan katangar ba zuciya ta tana iya tarwatsewa adalilin jarbawar rayuwata mai zafi ce, Ina tabbatar miki Anty ke ka'dai idan na kalle ki na ga tarin kaunar da kike mini fiye da ta ya'yan cikin sai na yi ta godewa ubangiji domin gatan da ya yi mini mai girma ne".

Suka dinga kuka tamkar anyi musu Rashi ne.

Da kyar suka rabu Sumaayya ta bita har hanyar waje tana fa'din ki rufe dukkan kofofin da kika san Mukhtar zai gan ki, idan kuma kaddara ta sake hada ku, to ki rufe dukkan kofofin da zai ji kayyawan kalmomin bakin ki domin shi din bai cancanta ba, bai dace da ke ba, shekaru bakwai da Kika yi, ba shi kika tsaya jira ya zo ya miki alfarmar mayar da aurenku ba. kin yi wadannan shekarun ne kawai dan gina Goben ki, da samarwa kai nutsuwa.

Sa'adah ta kasa bu'de baki ta yi magana domin kuka ne zai kwace mata mai karfi, saboda kalaman Sumayya tausayi su ke baata.

Tana tafe tana yiwa Sumayya addu'a da dukkan ahalinta tana fatan shakuwa da soyayyar da Jawad da Khairat suke yiwa juna ta bisu har girmansu dan su sake hada zuri'arsu ta zama dunkulalliya.

Tana isa kotun sai ta sake tarar da shari'ar da ta bata mamaki, mahifin Khalil hukumar ya'ki da yiwa kasa zagon kasa da ta'annati wato (E.F.C.C) ta gurfanar domin tuhumarsa da take yi da sama da fa'di da ma'kudan kudaden da ya wawure a lalitar gwamnati a laokcin da yake shugaban maaikatan gwamnati (Head of service).

Ido biyu suka yi da Khali cikin jerin mutanan da suke zaune suna dakon yadda shari'ar zata kaya. Rabon da ta su yi ido da ido idan har lissafinta dai dai ne, shekaru kusan goma sha hudu, tun ranar da suka je partin kammala sakandire a Hang out, ta tuno jidalin da Mk ya yi mata a lokacin. sai dai ta ganshi a hoto, sosai ya girma ya zama zabgegen saurayi na kece raini.

Wani irin abu ya dinga ta so musu dukkansu. Da sauri Sa'a ta wuce gaba inda tawagar lauyoyi suke zaune. Shi kuma ya bita da kallo yana fata iri iri akanta ya kasa daurewa a fili ya ce "Ba zai zama illah dan na auri age mate dina ba, domin har yau din nan da yake da yanmata daban daban yana jin son Gogel din sa, yana tuno moment dinsu kafin kutsen Mk Bichi cikin soyayyar su mai cike da kuruciya da Sanya nisha'di.

Sosai ta yi masa kyau, tafi Halima da ta ke budurwa komai da komai, domin ko a jiya sun hadu tunda basu da nisa . Hula da rigar lauyoyin nan ba karamin kyau da kwarjini suka kara mata ba, ga wani siririn farin glass a Idonta , kamshin ta na turaran Escada sentiment da ya santa da shi tun cikin kuruciya wadda a lokacin na Sumayya take daukowa bata san ma mai daraja bane, yauma kamshin ya shaka, tabbacin har yau da shi take tu'amalli.

A yanzu mahaifin Khalil Sanata ne mai ci, Dan haka yan adawa suka dinga rubuce rubuce akansa har sai da suka ja hankalin hukimar E.F.C.C ta damke shi, wata biyu ana ta dauki ba da'di tunda shi ya kafe ya'ki daukar lauya, ya kuma hana a daukar masa, da yake yana da kyakkawan alaka da gwamnatin jahar Kano sai ta bashi lauyoyi har guda biyar dan su tsaya masa, tunda mai girma gwamna da kansa ya gamsu Hon Ibrahim Hassan bai ci wannan kudaden da ake ambatonsu ba.

Manyan kwarrarun lauyoyi har guda uku masu mukamin (S.A.N.) sai guda biyu 'kananu amma hazi'kai, Bar Sa'adatu Bashir Gogel da Bar Mustafa Isa Gwaram.

Kotu ta 'dage sauraren shari'ar Alh Ibrahim Hassan zuwa 28/6 a shekarar da muke ciki, wattanni biyu masu zuwa.

Duk da adalilin Khalil ta rasa aurenta ta kudiri aniyar tsayawa mahaifinsa da dukkan iyawarta ko dan ta nunawa Khalil martanin kaunar da ya da'de yana yi mata da tarin hidimar da ya mata a rayuwa, ta tuno sadda suke FGC Kano ku'din break din Khalil akanta yake karewa, ta sake tuno sadda zai kwaso abaya da lace tsadaddu da mahaifiyarsa take siyarwa ya kawo mata.

Har gate ta bisu ta gaisa da iyayensa tana jaddada musu su kwantar da hankalin su zasu yi aiki tukuru har komai ya zama tarihi.
Suka yi musayen lamba da Khalil.

A gajiye ta isa gidan Sumayya, amma haka ta yi wanka ta Fara shirin tarbar Anwar da zai kawo mata ziyara.

Anwar bashi da mace amma ba saurayi bane, ya yi aure wata sha'daya da auren matar ta zo haihuwa ta rasu ta bar yaro yana hannun kakarsa wadda ta haifi marigayiya. Shekaru hudu kenan, tun akanta kuma bai sake kula kowacce mace ba, sai
SA'ADAH da yake sonta sosai, duk da dai har yanzu bai samu cikakken hadin kai daga gareta ba, amma dai yana ganin cigaba.
Anwar Ma'aikacine a ma'aikatar zabe(INEC).

*Bayan wata Daya*

Zuwa wannan lokacin Mk ya kasa gane manufar Sa'adah domin tun ranar da Baffah ya sa ya kaita gidan, Sumayya bai sake ganinta ba, a rana yana kiran layinta kamar sau biyar amma bata 'dagawa wani lokacin ma zai kira ya ji tana waya, amma da za'a jima ya sake kiran
sai dai ta gama ringing ta katse, tun baya jin damuwa sosai har ya fara ji har cikin ransa.

Ranar Talata yana zaune a bakin shagonsa kawai ya hango wata dalleliyar mota ba zato yaga Iyah ta fito sanye cikin shigar lauyoyi, kyau iya kyau ta yi daga nesa ya hangota amma ba karamin kwarjini ta yi masa ba.

Bai gama hasashen da wa suke tafe ba, kawai sai ya ganin wani matashin namiji y fito cikin fararen kaya kal, ba shi da gajarta amma sa Mk zai jera da shi sai aga gajartar tasa tunda Mk dogone mai cikakken jiki.

Ganin da ya yi matashin yana nuku nukun shiga gidan sai ya gane bazawarinta ne, domin sai da ta Fara shigewa sannan ya bita a baya, Mk bai san ya akayi ba sai ganin sa ya yi, ya tsallako titi yana leka gidan su Iyah, Bai gansu a zaure ba, kenan ciki suka shiga wani irin azabben kishi ya mamaye masa kalbinsa, ya matsa ya zauna a shagon faci na jikin gidansu, jikinsa ya dinga shaking wato har fa'da masa ta yi tana son namiji cikin fararen kaya? Shiyasa ya mata kwalliya da su. Duk addu'ar da ta zo bakinsa sai ya yi amma baya iya yinta cikakkiya, Karin tashin hankalinsa da Baffa ba ya nan yana Gogel, tunda daminace, shiyasa garin yake da dan sanyi, amma Mk sai zufa yake yi.

Mintina goma ya ji fitowarsu ya yi maza ya juya gefe daya, yana kallon kyakkawan matashin da ba zai nuna masa komai ba sai tsayi da shekaru, a kiyasin Mk zai iya bawa Anwar shekaru talatin da bakwai, shikuwa shekaransu arbain har da biyu kawai dan yana yawan motsa jiki ne ake ganinsa tamkar Yana cikin early 30th ne.

Ba bata lokaci Anwar ya ja motarsa ya tafi, Mk ya na zaune yana jin tamkar ya bi wannan matashi ya masa dukan kawo wuka, Sai ya ga wani saurayi da ba zai wuce sa'an Ahamad ba,

Please Login or Register in order to submit comment