You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

takunkumin dolen da ta mishi.

Yana rufe baki ta ce, "To saboda Allah wanne irin ha'kuri ne bata ba ka ba? So kake ta tabbata tana bin ka kana walagigi da ita? kuma ko don ka nuna na isa da kai, ka ji abin da na ke fada maka, saboda rayuwar 'danku ta inganta, yau yaro ba abu mai dadi a wajensa irin ya bude ido ya gan shi a tsakanin uwa da uba. Amma ku iyayen yanzu ba ku cika duba wannan matsalar ba."

Ajiyar zuciya ya saki, "To shike nan Hajiya In sha Allah zan je na yi istikara ba za ta gagara ba!"

Nan da nan Hajiya ta hau murna har da hawaye take sharewa tana kuma fadin, "Na gode, Allah ya tabbatar da alheri, da ikon Allah akwai alheri tsakaninku. Duk ba'kin cikin da na kwashe shekarun nan a cikinsa, wannan maganar kadai ta sanyaya min zuciyata, Allah ya yi maka albarka."


Ta mi'ka hannu ta dauko wayarta, "Kira mini Yayar ku".

Ya karbi wayar yana cewa, "Me za ki ce mata?"

"Na shaida mata wannan abin arz'kin mana, duk wannan bacin ran ai da ita muke yinsa!"

Ya kalle ta, "Amma Hajiya na ce sai na yi istikara fa, idan kuma ban sami nutsuwa da abin ba, a zo a ce na yi baki biyu? Ni dai na ro'keki, ki yi shiru da bakinki, mu yi addu'a nan da kwana uku muga mai Ubangiji zai rinjayar mana a zuciya."

Ajiyar zuciya ta yi ta ce, "Da ikon Allah ma alheri ne, jiya mun gaisa da Ahmad."

Ta fada cikin jin dadi,"Ai ni tun ina Bauchi rabon da mu gaisa ya ce mini wai satin sama zai zo."

Addu'a ta bi shi da ita kamar kullum, ya mi'ke, "Hajiya bari na tafi Magariba ta kawo kai"

"To ka gaida Farida, ya jikin nata dai?"

"Da sauki da na ce ta zo mu taho tare, ta ce yini ta ke so ta zo ta yi miki."

"Ina zuba ido Allah Ya kawota lafiya."

Ya amsa da "Amin!" Ya fice yana fadin, "Allah Ya tashe mu lafiya."

Ta bi shi da kallon 'kauna zuciyarta fes! Tamkar wacce aka mayar da aurensa da uwar dansa haka take ji. Ta san shi kansa sai ya fi samun nutsuwa idan yana tare da Sa'adah saboda ita shaida ce na tsananin son da yake mata.
ta tuna jinyar da ya yi a dakinta a dalilin rabuwarsu.

Abin kuma da ke ba ta mamaki yadda har yau bai ta ba bude baki ya ce ga sanadin rabuwar tasu ba, ita ma Sa'adah ba yadda ba a yi ba ta'ki fada, lamarin da kowa ya kyale su aka bi su da addu'ar alheri.

Duk irin sha'kuwa da aminci da ke tsakanin Sa'adah da Baffanta, ko shi ta'ki fada masa dalili. Haka ma Mk duk yadda yake jin nauyin surukin nasa bai iya fada masa dalilin rabuwar tasu ba, illa ya ro'ke shi, akan kar ya yi fushi ko ya ga laifinsa, ko rashin kirkinsa akan sun rabu da Sa'adah. 'Kadarrar su ce haka, shi ma kuma Baffan bai zafafa ba, bai kuma takura sai ya ji dalilin ba, ya yi ammana tunda suke boye sirrinsu da alamun za su iya yi wa junansu afuwa a gaba, duk kuwa da a farkon mutuwar auren hana Sa'adah zaman gidansa yayi.

****

Bayan yaron ya kawo mata littafin, ta dauko al'kalami ta fara, ta yi layi kamar uku ta goge tana ganin bai tsaru ba, ta ina za ta fara ne?

Daga haihuwarta har zuwa girmanta, ko kuwa daga rayuwar makaranta inda nan ne mafari tsakaninta da MK Bichi, ko kuwa ta rayuwar aurensu za ta fara?

Ashe rubuta labari da tsarawa ma iyawa ne? Lalle a gaida marubutanmu.

Sau uku tana yi tana sokewa, ta tabbatar dai ba za ta iya ba, tunda ba ta taba ba, ai ko za ta ne mi wata cikin fasihan marubuta, ta bata labarin ita kuma ta fasashi ya zama littafi. Ta tabbatar ba za a rasa darasi da jan kunne cikin rayuwarta ba.


Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️
[5/14, 15:55] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺



```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*SADAUKARWA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*.




11-12



A cikin wannan yanayin Zainab ta yi sallama a tsakar gidansu, sai da ta fara shiga gurin Inna ta gaishe ta, ta bar mata Khalifa, ta yi dakin Sa'adah.

Zaune ta same ta kan katifarta hannunta ri'ke da littafi da biro.

Gefenta ta zauna tana fadin
"Nazari kike ne haka?"

"A sanyaye tace
"Wai nan littafi zan rubuta amma na rasa ta inda zan fara."

Dariya Zainab ta yi tare da cewa, "Sa'adah manya, to wanne irin labari za ki rubuta?"

Kai tsaye ta ce "Akan rayuwata, wata'kila ba za a rasa matan da suke cikin rayuwar da na yi a baya ba!"

Ina fatan su ji labarina don su farka daga barcin makantar da suke, kafin su bude ido su gan su a *HALIN YAU* da nake fuskanta! Hawaye ya zubo mata ta sa gefen dan'kwalinta ta dauke a 'ko'karinta na kar Zainab ta gani.

Cikin sanyin murya da tausayawa Zainab ta ce,
"Amma kuma Sa'adah na dauka zuwa yanzu kin gane rayuwar nan bata da tabbas, bamu muke tsarawa kanmu rayuwa ba, da ace kowa shike sarrafa rayuwarsa da baku rabu da Uncle ba, da baki yi kukan rabuwar ba, Ni kaina ba irin kukan da ban taya ki ba, ba irin walankeluwar da ba mu yi ba a waccan lokacin, amma da yake a lokacin ubangiji bai nufa zamu samu cikar burinmu ba mun hakura kan dole. yanzu kuma Allah ya karkato da hankalinsa, maimakon ki yi wa Allah godiya, ki bishi sannu a hankali,har Allah ya taimake ki, ki koma dakinki, ki ri'ke 'danki, amma sai ki 'bullo da iya shege? Ni sai yanzu na gane ashe duk kuka da damuwar da kika yi ba har zuciya bane! Wallahi Sa'adah iskancinki ya fara damuna yanzu abin da kika mishi, da ya tsaya don ya taimake mu ya yi dai dai?"

Sai a lokacin ta bude baki ta ce "Idan dai taimakon daga gareshi ne ba na so, ya je ya rike dukkan taimakonsa, ke duk wani abu da ya shafe shi bana bu'kata. ya yi harkar shi na yi tawa, idan Allah ya so ma ba zan sake kuskuren bari mu hadu ba, ai wannan visiting 'din ma dole ne yasa na je, Inna bata nan, Anty Sumayya kuma tana da uzirin mijinta ba lafiya, dama su ne suke zuwa masa. Jawad ne yace, Malam ya ce masa baya gari ba zai sami zuwa masa ba, kin ji 'karfin zuwana." Ta ja majina ta ci gaba da cewa,

"Amma ban da haka ba zan je a ranar ba, balle mu hadu!
Zainab da ne na yi haukan banza na son na koma masa, amma a yanzu ko zan mutu ban yi aure ba, zan yi iyakar 'ko'kari na ga ko zaman mota bamu sake yi ba, balle zaman aure"

Muryarta ta karye alamun kukan da take ma'kalewa gaf yake da ya kubuce mata, ta ci gaba da cewa, "Ban taba dauka Mukhtar zai jefe ni, da abin da ya jefe ni da shi ba, in da tun farkon rabuwar mu na san kallon da yake mini ke nan da ko zan mutu ba zan bi shi ba, bare na ba shi ha'kuri, tunda na san shi ban huta ba.
Ban ga kuma da me na tsira a cikin zamana da shi ba, sai ko rabon Jawad da ya ratsa shi ma Ubangiji ne Ya 'kaddara ni ce uwarshi, amma a zuciyar MK, Farida yaso ta zamo uwarshi"

Sai lokacin Zainab ta katse ta da cewa, "Wallahi karya kike yi, ina ce ba dole aka mishi ya zabe ki a farko ya barta ba? kin dai san namiji ba a mishi dole, kuma ke da kanki kin tabbatar ke ce kike da alhakin mutuwar aurenki?"

"Tabbas ina da laifi amma ai shi ma ba za a rasa nashi ba, sannan kuma bi-ta-da-'kullin da ya bi ni da shi a idonshi da zuciyarsa ya sa na ji ko son shi ne ajalina sai dai na mutu da na koma masa, balle ma ba abin da hakuri ya bari"


"Ko za ki kwana kina rantsuwar ba kya son sa, ko ba kya son ki koma, ba yarda zan yi ba don kuwa 'karya ne tsagwaronta, don kuturun munafunci kun 'ki fa'dan mussababin rabuwar taku ai wannan ka'dai ya isa a san kuna son junanku tunda ba ku yarda aji sirrinku ba. Amma ban sani ba ko kin fa'da wa Halima tunda 'kanwar Inna ce ko kuma madadin Anty Sumayya"

'Kin tanka mata Sa'adah ta yi dan ta san magana ta fada mata a fakaice. Ganin haka yasa Zainab canja magana don tasan idan ta ci gaba da zungurarta yanzun nan Inna za ta shigo ta raba su don ba 'karamin aikin Sa'adah ba ne ta rufe ta da sababin da duk wanda ke gidan sai ya san an ta'ba ta.

Sai ta bige da lallashi, "Haba Maman Jawad na san ki da fa'da amma ba ki da ri'ko sam, na ro'keki kar fishi yasa ki yanke hukuncin da za ki yi kukan da ya zarce wanda kika yi a baya".

Ta nisa ta kalli Sa'adah, ta sake cewa "Idan ma wani Abu ya ce miki da ya miki ciwo wata'kila ya fada ne a lokacin da yake cikin fishi, ko kuma ya fada ne don ya 'kuntata miki, ki ji yadda shi ma yake ji. Amma shi ba abin a ranshi yanzu, tunda akan kunnenki Baba direba ya tabbatar da shi kanshi ya fahimci irin son da yake miki, ke ma kuma ya lura kina son shi, haba Sa'adah!"


Kukan da Sa'adah ke ma'kalewa ya kwace mata sosai, har Zainab ta ji to ko akwai wata magana data fada cikin kuskure wacce tasa ta kuka haka?

Amma da ta tuna Sa'adah sarkin kuka ce ko ba dalili, yasa ta samin nutsuwa.

Shiru ta yi, ba ta yi yunkurin hana ta kukan ba, ta san ko ba komai dai za ta sami salama a zuciyarta, sai da ta tabbatar ta yi ya ishe ta sannan ta ruko hannunta tana fadin ya isa haka, ki yi hakuri komai zai wuce ya zama tarihi, ki yi addu'ar zabin alheri, bawai zabin ranki ba."


Ta mike tana cewa, "Kin ji har ana kiran Maghrib bari na tafi sai na sake shigowa, ko kuma sai na gan ki."

Sa'adah ba ta ce mata uffan ba, ita ma Zainab din sanin halin 'kawarta tun fil'azal yasa ba ta damu ba. Ta juya ta fita, a tsakar gida ta tarar da Inna ta goya Khalifa ya nata barci,
"Ah goyo ki kayi haka Inna? Ai sai yasa miki ciwon baya."

Murmushi Inna ta yi tare da cewa, "Ku dai yaran yau da bakwa son goyo ne kuke kallon zai sa ciwon baya, alhalin shakuwa da tausayi ke 'karawa a tsakanin uwa da danta, amma ku boko da gayu ya hana ku goyo sai dai a hannu"

Dariya Zainab ta yi tana fadin
"Inna Allah ina 'ko'kartawa."

"Allah Ya sa!" Inna ta fada tana kunto shi, yaro yasa kuka, wai shi an saukko da shi, ai ko Inna ta ce, "Juyo na sa miki shi a bayan." Cike da kunya da girmamawa tace, "To"

Ta sunkuya ta sa mata shi har zanin Inna ce ta daura mata, sannan ta bar ta ita kuma ta hau kiciniyar gyara goyon.

A gurguje suka yi sallama ta tafi ita kuma Inna ta yi bandaki da buta a hannunta.


Ta idar da sallar Maghrib tana zaune kan sallayar tana jan carbi, wayarta ta hau 'kuwwa, hannu tasa ta janyo ta ganin sunan Hajiyar Bichi, yasa gabanta ya fadi, duk da suna waya lokaci zuwa lokaci, amma ba tasan dalilin faduwar gaban da ta ji a yau ba. katsewa ta yi sai ta kira ta, Hajiya ta ambata sai kuma tace, "Assalamu alaikum!" Ciki-ciki Hajiyar ta amsa. Sai jikin Sa'adah ya yi sanyi ta ce, "Lafiya kuwa Hajiya?"

"Ba lafiya ba Sa'a, yanzu a ce za ki tafi wurin Jawad amma ki kasa fada mini? Na san kuma kinsan ubansa baya nan?"

"Hajiya ni ban sani ba".

"kin sani mana ai ba zuwa kike ranar da ake taron ba, amma wannan karon kin je saboda wanda kike gujewa haduwar ta ki da shi ba zai jeba,
sai kuma Allah ya yi nufin haduwar taku wanda shi kadai ya san manufar hakan.
Ban ga kuma laifinki don kin kame kanki ba. Laifinki daya da kika san dukkan ahalinki ba za su sami zuwa ba, sai ki fada mini mu tafi bibbiyu, wannan abu da kika mini sai nake ganin kamar ni ma fushin da kika dauka ya shafe ni ganewa ne ban yi ba sai yanzu."

Cikin son kare kai da kuma iyakacin gaskiyarta tace, "Wallahi ko ka'dan Hajiya ba haka ba ne, ba abin da za ki mini nan duniya na yi fishi da ke, har gobe ke uwa ce. Tunani na bai ba ni na yi hakan ba, na ma yi tunanin direba zai kai ku tare da Antinsa, amma ki yi ha'kuri Hajiya"

Take ko Hajiyar ta ce, "Na huce dama rashin fahimta ne, ki gaida Innar taki, kuma In sha Allah ina nan tafe cikin satin nan"

"Allah ya kawo ki Hajiya!"

Ta ajiye wayar tana jin idan akwai asarar da ta yi cikin rabuwa da MK to kuwa rashin nagartatciyar suruka irin Hajiya na kan gaba, jin kanta ya mata nauyi ne yasa ta ci gaba da ambaton Allah.







Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍️


[5/15, 19:03] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺




```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/


*SADAUKARWA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*.


*ALLAH KA JIIKAN*
_HAUWA M. HASSAN_
*(FINE GIRL)*
_UBANGIJI KA ALBARKACI SU FA'EEZA_.




13-14



Tsawon kwanaki addu'ar za'bin alheri ya dinga yi tsakaninshi da Sa'adah ba 'kak'kautawa, kuma ALHAMDULILLAH, ya ji takurar da yake ji akan zama da ita ta kau, ya sami sau'kin nauyin da zuciyarshi ta yi akan ta.

Ranar Juma'a bayan an sau'ko Masallaci kai tsaye gidan su ya zarce kamar yadda ya saba a falo ya tarar da Hajiya zaune kan sallaya, tana lazimi. Ya jima yana zaune kafin ta shafa addu'arta ta juyo ta kalleshi, a nutse ya shiga gaishe ta tare da tambayar jikinta kasancewar kwanaki biyun nan fama take ta yi da zazzabin cizon sauro.


"Jiki kam na ji sau'ki sai rashin 'karfin jiki wanda sai a hankali."
Ta fada tana daddanna 'kafarta.

"Hajiya 'kafar ciwo take miki ne?" Ya fada cike da kulawa.

Ta ce, "Ba wani ciwo kawai kasala ce!"

"Sannu idan kin gama shan maganin ba ki ji daidai ba, sai na mayar da ke wajen likita."

Da sauri ta ce "Kai raba ni da zancen Likitan nan na ji sauki."

Dariya ya yi! dama tsokanace wannan zazzabin ma da 'kyar ta yarda ta je asibitin bare ta yarda ta koma.

"Har yau ba ka ce mini komai akan maganar Sa'a ba?"

Murmushi ya yi "Oh! Hajiya ai na ga ba ki da lafiya ne."

"A a
na ji sauki "

Gyara zama ya yi sosai ya fuskance ta, "Hajiya!" Ya kira sunanta.

"Na'am!" Ita ma ta amsa tare da mi'ka dukkan natsuwarta gare shi.

"Kamar yadda na ce miki zan yi addu'a, to na yi! kuma na ji tsoro da razanin da nake ji a tattare da zama da yarinyar nan ya gushe daga zuciyata, amma..." Sai kawai jin ta ya yi tana ambaton Alhamdulillah! tausayinta ya kama shi na ganin tsananin murnar da take yi akan abin da ba tabbacin yi yuwar faruwar shi.

Ya san Sa'adah, ta kyautata mata matu'ka. Lamarin da Hajiya ta tattara dukkan kaunar da take mishi ta mi'ka mata, duk irin laifin da za ta mishi tofa a idon Hajiya ba laifi ba ne sai ta ce ai yarinya ce, 'kuruciya ce ba kuma hankalinsu 'daya ba.

Har ya fara yi wa Sa'adah kallon macijiya ta sare shi, ta kuma koma gefe ta lullube uwarshi da alheri, haka nan hatta 'yan uwansa, mussaman Samira da Hafsatu basu dauki lamarin Sa'adah da wasa ba, saboda yadda ta kyautata musu iyaka, ya san ba ta da rowa, tana da saurin sabo, ba ta kuma sa ido a lamarinsa da 'yan uwanshi, komai zai musu kuwa, wani lokacin ma ita take ankarar da shi.

Shi har mamakin ta yake yi yadda duk wani rikicinta, fa'danta, rashin kirkinta, da kuma rashin ha'kuri duk akan shi ya 'kare.

Ta 'dago tana kuma ambaton ALHAMDULILLAH.
"Hajiya abin da nake so ki gane yarinyar nan fa yanzu gaba'daya ba yadda kike zaton ta ba ne, na tana son dawowa 'dakinta, don haka kar ki sa a ranki cewar za ta dawo, azo kuma abu bai yiwu ba, ki zo ki sake shiga damuwa kinsan dai kullum girma 'kara kama ki yake"

Shiru ta yi can ta nisa, "Shin kai a wurinka magana ta wuce ta 'bacin rai ba tashin tashina?"

Ya yi jim, yasan dole sai sun sake baje tashin hankalin da ya gitta a tsakaninsu, kafin a manta shi gaba'daya! Amma sai ya amsa mata da cewa
"Babu Hajiya! amma wallahi bazan ta bin kanta ta amince ba, don na lura yanzu wani iya shege ta ke ji"

Da sauri Hajiya ta 'daga mishi hannu,"Kai da'dina da kai ba ka fahimci yarinyar nan ba, kishi ne ke 'dawainiya da ita, ka duba mana kafin ka yi auren nan wanne irin bibiya ne ba ta maka ba? har kowa ya gane ita ce mai laifi a tsakaninku, duk da ba ku cewa kowa ga yadda abin yake ba".

Ta yi 'kasa da murya, "Yanzu fa duk girman laifinta, kama ta hukuncin da yanzu kai ne mai laifi a tsakaninku tunda ka mata kishiya, abin da nake so da kai, kar ka yarda wani borinta yasa ka yi 'kasa a guiwa, ka lallaba ta ka'dan, ni kuma sai na lalla'ba mana ita da yawa"

Dariya ya dinga yi,"Oh Hajiya saboda Allah ni da Sa'adah wa kika fi so?"

"Ai kai ma kasan ita na fi so! nan kusa za a dade ba'a samu mai girmama uwar miji da 'yan uwanshi irin ta ba. Ina fa ji ina kuma ganin yadda she'danun yaran yau suke wa iyayen mazan su iyashege kala-kala, har sunaye suka la'kaba musu, wai uwar miji ce Ulcer, BP, ciwon kai, da sauran sunaye na tsiya, amma Sa'a bata a cikin wannan layin".

Dariyar ya sake yi tare da cewa, "kun yi dace ne kawai ke da ita wasu laifin iyayen mijin ne ai, da basa 'dauke kai ga harkar gidan ya'yan su maza, sannan basa jan surukan nasu a jiki, basa kuma yi musu sassaci da uzziri.
Wasu kuma tabbas laifin *Matan Yau* ne da suke ganin uwar miji tamkar wata 'yar katsalandan ga rayuwar su sai afara zaman Allah ya kawo maraba. Allah dai ya rufa asiri kawai, amma Hajiya ita Farida fa?"

Da sauri ta ce, "Ita ma ba ta da laifi tana da irin nata alherin, amma..." Ya katse ta da cewa "Ba kamar Sa'a ba ko??"

Dariya ta yi tana cewa "Yaushe zaka je gun nata?"

"Zan je In sha Allah!" Jin yadda ya sau'ko ya kuma amince da maganar Sa'adah a karon farko tun bayan rabuwarsu, yasa bata matsa mishi da yawa ba, sai ta ce, "To ka mayar da hankali don Allah, a yi a gama komai cikin 'kan'kanin lokaci ku dai yanzu ba yara ba ne"

Mi'kewa ya yi yana gyara sakun hularsa tare da cewa, "Ke da kika ce za ki lallaba mana ita, ai ni ba sai na yi komai ba."

Cikin sauri ta furta, "Ai ko tilas kai ne mai magana a farko"

Murmushi ya saki tare da yi mata sallama ya fita yana fadin, "Sa'a ta same ki sosai Hajiya"

Gidansa ya nufa, a falo ya tarar da Farida cikin kwalliya ta burgewa tana zaman jiran shi, ta hau hidimar kawo mishi abinci, da abin sha, sai daya kammala, ta kwashe komai sannan ta dawo ta zauna tana tambayar Hajiya. ya amsa da cewa "Tana lafiya! ta ce a gaishe ki."

Murmushi ta yi tare da fadin "Na gode!"

Hannunta ya riko ya janyota sosai kusa dashi, "Ina son mu yi magana mai mihimmanci, ki nutsu ki ji me zance miki, ki kuma fahimce ni"

Idanuwanta masu sheki ta zuba masa tana jin a jikinta abin da ta dade tana jiran ya tabbata ne yake neman faruwa a wannan karon, kai ta gyada tare da cewa, "Ina jin ka."

Sai kuma ya kasa cewa komai tsawon lokaci, ita kuwa da ke ba mai gaggawa ba ce ba ta ce masa uffan ba.

Har ya gaji ya nisa don kanshi sannan ya ce, "Ba sabuwar magana ba ce mun sha yin ta, sai dai ta yau 'din ta sha banban!"

Nan ma cewa ta yi, "Ina sauraron ka!"

Abin mamaki sai ya ji shakkar furta maganar yake. Cikin dauriya ya ce, "Maganar Sa'adah ce zan fara magana da ita, idan Ubangiji bai 'karar da zaman namu baki 'daya ba, zata dawo "

Gabanta ya fadi duk da a kullum cikin tsammanin faruwar hakan take, amma sai da ta kadu matu'ka da gaske, amma da yake tana cikin jerin matan da Ubangiji ya ba su ha'kuri mai yawa da sanyin hali, da kuma ha'diye damuwa sai ta ce!
"Ai da ma ka sha fada mini a kowanne lokaci idan 'kaddarar zamanku ba ta 'kare ba za ka dawo da matarka, ni kuma na sha fada maka cewa ba zan baka matsala ba hakane?"
Ta tambaye shi, kai ya 'daga mata, "To a yau ma ina tabbatar maka baka da matsala da ni. amma zan ro'ke ka abu daya, na san kana son ta sosai, ni kuma ina son ka sosai, don Allah ka yi mini adalci"

Wani abu ya ji ya tsirga mishi tun daga kanshi har zuwa 'kafarshi. Gaba'daya ya janyota jikinshi yana jin tausayin ta na tsirga mishi a zuci da gangar jikinsa gabadaya.

Cikin murya marar amo ya ce, "Farida a tsayin zamana da ke kin san ina son Sa'adah amma abin mamaki ba ki san ina son ki ba?"

Luf ta yi ba ta amsa ba, saboda yadda take kokawa da zuciyarta da numfashin ta.

"Kai, kishi, bala'i!" Ta fa'da a zuciyarta, ban da haka abin da take da tabbacin zai faru ne, don yana neman faruwa kuma sai ya dame ta? kamar ba ita ce take ta mishi kau'din ya dawo da matarsa ba?

Amma a yau da ya amsa, har ya zauna yana fa'da mata da bakinshi akan zai dawo ita sai ta ji kishin da ba ta yi tunanin zai taso mata ba, ya taso da wani irin 'karfi mai gigitarwa.

Jin ta yi shiru yasa shi fadin, "Ban aure ki akan wani dalili ba sai don ina son ki, ina zaune da ke saboda ina son ki, ina kuma jin dadin zama dake, don haka ba wani abin dazai raba ni da ke matu'kar ba ke ce kika bijire mini ba. Ina son ki Farida irin son da zan iya sadaukar miki da komai, ba abu mai da'di a soyayya irin a so ka da kai da dukkan matsalarka, a mutuntunta ka, a kuma yarda ka isa koda kuwa a zahiri baka isan ba.

Ba abin da baki mini na kyautatawa ba, ba kuma zan manta ba, kar ki yarda ki sa a ranki wai zan juya miki baya akan Sa'adah, kar ki ji a ranki na fi son ta akan ki, ni ban san wacce na fi so ba, wacce duk ta kiyaye mini 'bacin Raina, ta zauna da ni lafiya cikin aminci, ta yarda bazan musguna mata da gangan ba, ba shakka itace zata jagoranci zuciya ta. Idan kuma kina da matsala

Please Login or Register in order to submit comment