You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



*Fatan alheri ga marubuciya*
*Zainab Ilyas Mazawaje*.





23_24.





Tsananin matsin da Uncle Mukhtar ya mata yasa ta zama shiru shiru, ta matu'kar rage kaudi da iyayyi.

Kullum tana ri'ke da littafan koyon turanci, ire-iren su Teach ur self.

Ta sake mannewa Safina Bunkure. kasancewar Safeena girman Lagos ce, mafi yawan maganarta turanci ne, dan haka ba ta yarda su yi magana da hausa tare da safina, itama kuma Safina ba ta gajiya da gyara mata a inda ta ji ta yi kuskure.

Ba'a dauki lokaci mai tsayi ba,ta fara rage tsoron kar ta yi turanci a mata dariya, ganin ta na iya mayar da magana cikin harshen da ke mata nauyi, sai kuma ta mai da hankali akan ragowan darussan gaba 'daya.

Ta matu'kar rage shiririta, yanga, da hirar soyayya, da duk wata sharholiyar da su ke, abu 'daya ne ba ta bari ba, kwalliya, wadda wannan kam a jinin ta ne.

Su Halima cewa su ke basu ga Malamin da zai uzzura mu su, babu dalili basu yi maganin sa ba.

Ita ko tsaki take ja a fili, ta yi shiru.
A zuciyarta ko cewa take ai ku ya ga kun iya turanci, kuma yana ganin yadda ake zuwa 'daukan ku a motoci na garari,
ni kuwa ya ga ba ko 'daya, ba dole kowacce shara ya debo ya juye a kaina ba.
Tabbas tana takaicin yadda ita kadai ya ke gallazawa.

Shikuma ganin yadda ta yi laushi ta kuma maida hankali kan karatun ta, sai ya sassauta mata, duk kuwa da zai yi wahalar gaske ya yi darasi bai ce ta tashi tayi bayanin yadda ta fahimci darasin ba, kawai dai kyara da disgin ya rage.

A haka har suka yi jarrabawar mock wadda duk 'dalibi ya ke tsoro da fargaban kar ya fa'di.

Ana yin hutu da kwana biyu mijin Sumayya ya turo takanas a dauki kannen shi 'yan mata guda biyu da yar autar dakin su, da kuma wadda suka hada uba yar amaryar Baban su, sai ya ro'ki Baffah! akan ya basu Sa'adah ta yi musu hutu tare da 'kannen shi. ba musu ya amince, har gida suka zo suka dauke ta, sannan suka dauki hanyar jos kwata, ta yamma da Bauchi😀.

Wannan hutun yana cikin abubuwan da Sa'a bata Mantawa da shi, domin kuwa ta yi matu'kar jin dadin zama da 'kannen Idris yadda suka kasance yara kamammu, marasa hayaniya amma kuma yan kwalliya ne na sosai, shiyasa abotar su ta yi da'di.

Sumayya kuwa ba ta matsa musu, hatta abinci wadda suke so shi zata ce su yi, mai gidan kuma kusan kullum sai yasa direbansu ya zaga dasu, sunga gari, da wuraren sha'katawa , sannan kuma duk fita sai ya basu kudin kashewa, wadda ba abin da suke siya sai kayan kwalliya ko dai abin da ya shafi sutura.

Ba abin da ya dame su illah tunanin mock exam din da suke fargaban fitowar ta, tunda dukkan su set daya suke Amma makaranta daban daban.

Haka suka 'kare hutunsu cikin jin Dadi da mutunta juna, da kanshi Idris ya kawo su har gida tare da kayan tsarabar ni'ki ni'ki, barin ma dankalin turawa da dangin su cabbage da Kara's, harta atile kamar wadda za'a ci a tsawon wata.

Baffa da Inna sai godiya suke,tare da sake godiya ga Allah, na yadda Sumayya ta sami mijin daya San alheri yake kuma rama alherin da kyautatawa da mutunci.

Barinma idan ta zauna tana bawa Inna labarin daular da Anti Sumayya ke ciki, sai dai ta yi murmushi mai nuna yadda zuciyar ta ke cikin farin ciki.

Ba zata yi magana ba sai dai ta bige da cewa kema Allah ya ba ki mijin rufin asiri, yasa ki dace kamar na yar'uwarki.

Ita kuwa kai tsaye take cewa
"Amma fa Inna gaskiya ni bana son irin tsarinsa, ace mutum duk inda matarka zata fita kace sai ta zumbula hijabi har 'kasa, kuma wai dole sai ansa safa? ko 'dan wanne mazahaba ne?"

Cikin mamaki Innar ta zuba mata ido, tare da tafa hannu tana sallallami tace
"ke kuwa Iyah wannan tsarin da yake yi na martaba shari'a ne bai Miki ba?

Na mijin kwarai shi ke kishin matarsa, ya 'dora ta akan ka'idojin shari'a, wadda zasu gudu tare su kuma tsira tare!
"Daular da ya sanyata a ciki ta burge ki, kina kuma fatan ki samu irinta, amma abin mamaki, hijabin da Ubangiji ne yace a saka shine bai miki ba?
Anya Iyah, Baffan ku bai yi kuskuren barinki shiga wannan makarantar da ta ke sake girmama burinki ba?"

Da sauri tace
"Haba mana Inna! ni fa ba cewa nayi kar asa hijabi ba, gani na yi tana da tsala tsala dogayen riguna tunda ga kan yan 'kasashen Oman, Qatar, Saudi, Dubai, masu tsadar gaske masu kauri, amma wai dan 'kauyanci kuma sai akawo hijabi a maka, bayan su karan kansu hijaban ne".

Ta fa'da tana fashe wa da dariya.

Allah ya shirye ki kawai, Inna ta fada tare da mi'kewa ta yi tsakar gida, tana fadin wannan dogon burin na ki yana ban mamaki Iyah.
Ban da 'karya da fariya, da kai kanka inda Allah bai kai ka ba, gidan uban wa kika san 'kasashen da suke sarrafa riguna masu tsada?

Naga dai ke kam baki da halin samun su, ban da Allah ya miki gata ya baki yar'uwa mai halin girma tana baki kuncen su, wasu ma ko saka su bata yi, ta ke baki, amma har ki zauna ki karkace baki kina min lissafin inda ake sarrafa su?".

Ta cika fam saura 'kiris ta fashe cikin turo baki tace
"Amma Inna abin har da gori?"

Da sauri tace

"Eh dole na goranta miki, dan na ga nema kike ki manta cewa ke'din ba yar kowa bace, face malam Basiru mai 'yar tireda😀wadda ko hanyar inda jirgi ya ke sauka ba ki ta'ba zuwa ba,
Amma kina bada labarin 'kasashen duniya, wallahi Iyah ki canja wadannan halayen da nake ganin kina sake arowa kina yafawa".

Shiru Sa'a tayi amma takaici ke cin ta shikenan sai mutum ba zai fadi ra'ayin sa ba?
Sai a hau mishi gore-gore, har a nemi cewa ya raina shari'a?

Hawaye ya siraron mata, ta goge ta tashi ta yi 'dakinta, tana fatan Allah ya bata miji mai kula da iyali kamar Idris, amma ba mai a'kidunsa na asalin bahaushen arewa ba.

Kayanta na makaranta ta shiga fitowa dasu tunda ga kan uniform, sandal, school bag dukkan su sabbi ne, ta shiga shirya su ta yadda gobe sai dai ta dauka a kammale.

Ba tasan meyasa ta ke 'dokin komawa makarantar ba wannan karon? domin kuwa tunda Mk Bichi yaje makarantar ko hutun weekend ne fargaban zuwan Monday take yi.
Wata'kila kuma dan ta sami sau'kin kunyata ta da yake yi ne.

Amma Kuma duk da sau'kin da ta Sami a bangaren shi, haushin shi da tsanar shi na nan cike a zuciyar ta.
kwanukan abincin su ta wanke su tas kafin ta kammala wanke wanken har gawayin ya fara kamawa, dan haka ta cika tukunya ta dora ruwan wanka, tana gama wanke kwanukan, sai kuma ta hau share tsakar gidan hadi da wanke dan matsakaicin bandankinsu, kafin wannan lokaci kuma ruwanta yayi zafi, ta juye ta shiga wanka! bayan ta maida ruwan kunu da ta jefa mishi tsamiya kan wutar.

Tana fitowa a wanka innarta ma ta fito tsakar gida, tana ganin yadda Sa'a ta gyare mata gida tsab.

Da'di ya kamata na yadda ko kadan Iyah bata da son jiki.
Ba zato ta ji anrungumeta tare da cewa

"morning Innah"
Ture ta tayi tare da cewa

"oh ni kam Ina kallo a gun ki".

Dariya tayi tare da fadin "Inna gaisuwar kawai shine abin kallon"?

Wuceta ta yi tana bude ruwan dake Kan gawayi, ganin yana shirin tafasa yasa ta fara shirin dama kunun, ita kuma sa'a tayi 'daki tana shiryawa.

Cikin 'kankanin lokaci da dama kunun, ta kuma dauko fulawar data kwaba a 'karshen dare dan yin fanke, ganin ta tashi sosai yasa ta maida mai kan wutar tana shirin suya, tana kwashe kaskon farko Sa'adatu na fitowa ta shirya amma bata sanya uniform ba.

Ganin yadda innarta ke kwaso fanke yayi brown ya tashi sosai, da'di ya kama Sa'adatu.

Sai kawai tafara rawa tana juyi tana wa'kar

"Mamana, mamana! mai sona, mai tattalin zuciyata".

Kwafa Inna ta yi tana fadin "zanga sadda za ki girma Iya"

"Idan Kinga na girma sai kin haifa min 'kani ko 'kanwa".

Ta wuce ta dauko, kofi da plate tana fadin "Allah Inna Ina son 'kanne gashi Anti Sumayya tayi min nisa bare na dinga debo su Khalifa".
Ta fa'da cikin muryar tausayi tamkar hakan zaisa innar ta haihu yanzu yanzu.

Numfasawa Inna ta yi sannan tace
"Ai kin kusa samun 'ya'ya ma indai kina da rabo, ba'di iyanzu ai kina dakin ki ".
Daure fuska tayi, sannan tace
"Nifa sai na fara karatu".

Da sauri Inna tace "Inma karatun za ki zama sai dai a dakin ki, tun yanzu kina ruwan ido kowa ya zo kice ba kya sonsa, amma kuma kina son duk wani abu da zai 'kullo ya baki".

Mi'kewa ta yi bayan ta debi kunu da fanken tana cewa
"To Inna ai ba ro'konsu nake yi ba, Kuma Annabi yace ba kyau mai da hannun kyauta baya"

"Wannan maganar dai kin fi ri'keta a duk maganganun Annabi. saboda ta dace da ra'ayin ki, amma saka hijabi da ke yaci karo da tsarin ki, ai jiyan nan a gabana kika ce 'kauyanci ne"

Kasa magana tayi kawai ta shige 'dakinta, ta fara cin abincin ta, tana ayyanawa a zuciya duk saurayin da yayi gigin yi mata kyauta, ita ko ba zata 'ki amsa ba, tunda dai ba ro'kon su take yi ba.

Tana gama karyawa ta fita da kayan sannan ta sake yin brush wadda sau biyu take yi a kullum safiya tun Inna na mitar barnar makilin har ta gaji, ganin hakan yasa Baffa ya ware mata makilin din ta yana cewa uwar masu gida dole a bata komai, indai ba wadda ya wuce ka'ida bane.

Sai da ta shirya tsaf ta fito tana fadin Inna zan tafi, kallo daya ta mata taga yadda ta yi kyau tamkar ba uniform tasa ba, tasan 'yarta mai kyau ce fiye ma da Sumayya dan dai kawai ita duhun fatar mahaifin su ta kwaso amma Ubangiji ya mata cikkaken diri.

Ta nisa tace
"Iya! wannan turaren na ki bana zuwa makaranta bane,'kamshin sa bana shiga cikin maza bane".
"To Inna" ta fada a gajarce ba dan ta gamsu ba.

" 'Daga can ki dauki kudin makarantar,yau Baffan ku jana'iza ya tafi tun sallar asuba bai dawo ba".

Turus tayi dan kuwa ba yadda za'ayi tasa hannun ta a wurin sana'ar Inna tunda ta riga ta shirya.

Ganin yadda taja ta coke tasan ta'bawa ne baza ta yi ba, kwafa tayi sannan ta mi'ke ta 'daga daron kayan, ta 'kirga kudin ta mi'ka mata, maimakon ta karba sai ta mi'ka mata pos din akan ta sa mata a ciki, hakanan tasa mata tana mata adduar shiriya, tun tana yar 'karamarta, bata son daddawa da kuka, da kubewa bushasshiya, da Inna ke 'kullawa tana siyarwa.

A bakin titi suka hadu da Zainab kamar kullum,suka rankaya suka tafi.
Suna Isa makarantar suka tarar da dodon na ta on duty, yana sizing kayan da makaranta ba ta yarda dasu ba.
Kowa yazo sai ya gaishe shi, hatta Zainab Ma'aji sai da ta risina ta gaida shi cike da girmama wa, amma ita banda kirne fuska ba abin da ta yi. kallo ya bi ta dashi yana raya wadda duk ke mata gugar kaya, ya kamata a bashi sarautar shugaban masu guga.
Ita ko sanin ba wani abu na karya doka a tare da ita yasa bata ji 'dar ba.
Har sun wuce sai yasa baki yace "Gogel"
Zuciyarta ta buga tare suka juyo da Zainab, amma sai yace Zainab ta tafi, itakuma ta dawo, tsaye ta yi mishi 'kerere fuskar nan tamkar gobara, ta gefen idonshi ya ke 'kare mata kallo baisan mai yasa kyaun da ta yi cikin sabon uniform 'dinta ya mintsine shi ba.

Sassanyan 'kamshin da ke tashi a jikin ta ya matu'kar ta'ba shi, ta na zuwa gaba daya gun ya cika da 'kamshi. ita kanta bata san tsadadden turare bane dan kuwa na Sumayya ne ta dauko mata.

Ba tare da ya kalle ta ba yace
"On ur kneels"
Nan da nan hawaye ya cika idon ta wanne irin mugun mutum ne wannan? mai ta mishi zai wula'kantata daga dawowa? haka ta zube cikin 'kasa da ciyayi bai sallame ta ba, sai da ya tabbatar ta shiga sahun 'yan late comer's(makararru).
bayan ya mata bulala biyar a hannu masu zafin gaske, yana ce mata
" for ur indispline manners, u are not here only to learn, but da tarbiya in ganeral".
Haka nan dai aka sake mata punishment (horo)na latti. a wannan rana haka ta yini da ba'kinciki, murna da ake na shigar su aji shidda ita kuka ne ya maye gurbin, hankalin Khalil dana 'kawayen ta ya yi matu'kar tashi sai lallashinta suke.
dukkan su tsanar Mk ta cika 'kalbin su mussaman ma Khalil da ya ke jin tamkar ya yi hayar yara a bishi unguwar su a mishi dukan kawo wu'ka.





Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼



`Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼
[5/22, 12:02] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*!🌺



·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



25_26.





Kwanci tashi har jarrabawar mock ta fito cikin ikon Allah Sa'adatu ba ta sami matsalar komai ba tasan kuma MK ya taka muhimmiyar rawa ga samun nasararta, tunda a sanadin matsin da yake mata yasa ta zama cikin jerin daliban da suke nacin karatu.

A wannan term din kuma ta tsinci kanta da jin haushi idan ta gan shi da Farida, gashi dai ta tsane shi, amma ko yaya ta gan shi da ita, musamman da ya kasance Farida Prepect ce, kuma mafi yawa idan shi ne Duty Master, to kuwa za ta kasance Duty Prefect, sai ta ji ranta ya mugun 'baci.

A yanzu tafi jin takaicin 'kokarin da Farida take da shi fiye da komai cikin FGC.

Kasancewar Farida na cikin daliban da suke wakiltar makarantar gaba'daya, dan yanzu ma shirin tafiya Lagos gasar Cowbell Competition suke yi, tunda sun cinye na jahar Kano, yanzu matakin 'kasa zasu tafi, kuma Uncle MK din na cikin tawagar Malaman da za suyi masu rakiya zuwa birnin na Ikko.

Wannan dalilin sai ta sake zama so mute, ita kadai ta san mai ta ke going through a zuciyarta.

Kullum idan ta zauna ta dinga bincikar kanta, me yasa ilimin Monica Paul bai dame ta ba?me yasa Khalil Ibrahim da yake da 'kokarin shima bai dameta ba, tunda har da shi za'ayi ma tafiyar?
Kanta har zafi yake dauka akan wannan tunanin.
Kyashi take mata ko kuwa hassada ne?.

Kullum kuma indai ta ga Farida, a ranta sai tace, oh ance mutum tara yake bai cika goma ba, komi da ake so Farida ta hadasu, doguwar mace, Fara tas, mai dogon gashi, mai ha'kuri, mai tarin ilimi gashi ta yi sa'ar fitowa a gidan wadata, kawai dai ba ta da dirin jiki, sai tsananin kyaun fuska.
siririyace ta sosai, shiyasa komi na jikinta 'karami ne.
Sannan kuma ta lura bata da cikakkiyar lafiya wadda takan shafe sati idan ciwon ya tashi ba tazo ba. wannan ciwon da rashin cika irin ta cikkakun mata, shine tawayar da tasa bata cike goma cif cif ba.

Tauraron Farida ya sake haskawa ne bayan sun yi nasarar zuwa na 'daya a gasar da suka yi, wadda itace tafi bada amsa a tsakanin Monica da Khalil.

Kowa nan nan yake da ita tunda ga kan principal da sauran teachers, dama student gaba daya.
Wannan ya sake sa tsanar ta a zuciyar 4stars da suke jin su din isassu ne.

A kuma wannan term din Sa'a ta dage, ta 'kure malejin jarumta, ta dau ki 8th position, wadda shine sakamakon farko mafi kyau a tarihin rayuwarta, dan ko a makarantar da ta baro, double lamba take dauka, bare wannan makarantar da ta ha'da za'kwa'kuran 'dalibai.

Wannan sakamakon shine mafarin dai na 'yar tsamar su da Uncle Mukhtar, duk 'karshen zangon karatu ya wajabta wa kanshi bawa daliban ajin nasa daga na daya zuwa na uku kyautar 'karfafa guiwa, a matsayin sa na class master dinsu, a A class ya bawa Farida.
A wannan karon har Sa'adatu ya bawa kyautar the most hardworking student in the class, Kamar kullum Khalil Ibrahim ke daukan 1st position, shi ya 'Kira a 'karshe bayan ya bawa Sa'a. da monicca as 2nd, da wani Abdulrashid da ya zo na uku.amma da yaje karba sai yasa left hand ya Kuma juya fuskar shi, wannan rashin 'da'a da ya nuna ya hassala Mk ya fasa bashi kyautar ya kuma hukunta shi ta hanyar sa shi, sharar school area.

Tunda ga nan aka fara cece kucen son Gogel yake banda haka, ta yaya ga Halima ta zo ta hudu bai bata ba, ga na biyar, duk ya tsallake ya tafi Kan 8? asalima sai da wannan kyautar ya kawo mata matsala tsakanin ta da Khalil da kuma Halima.

Na Halima kyashi ne, shikuma Khalil kishi ne, gani ya ke kawai soyayya suke yi amma ai kowa yasan yadda ya takura mata, menene dalilin gift din? alhalin akwai wadda suka fita cancanta amma bai basu ba.

Kusan wannan ta'kardamar ne dalilin afkuwar soyayyar ta su dan ta dade tana jin kishinsa akan Farida bata gane kishi bane sai a wannan lokacin daya sake da ita, ya gamsu tana karatu kamar yadda ya kamata.

Ranar juma'ar da akayi hutu, tana cikin ranakun da bata Mantawa cikin rayuwar ta a makaranta, a ranar ne ta nutsu ta 'kare mishi kallo na tsanaki, a lokacin da ya shigo dan ya musu bankwana sai kuma bayan hutu.

Dogon saurayi mai matsakaicin jiki, ma'ana siriri ne, amma kuma bashi da rama ko kadan kai tsaye za'ace mishi fari, duk da idan irin su Farida na gun, duhunsa za'a gani, doguwar fuska mai dauke da dogon hanci, da madaidaitan idanuwa, farare tas, da zagayayyen 'karamin baki mai dauke da 'kananun ha'kora jerraru, ya kuma zagaye bakin da gemu. yanayin sa tamkar 'kani ne ga tauraron wasan kwaikwaiyon nan Yakubu muhd saboda yadda suke yanayi.

sanye yake cikin shadda fara 'kal, ma'abocin tara suma, mai kuma yawan gyarata dan kullum comb din shi na aljihunsa, hular yan bautar 'kasa ya saka, kafar sa dauke da open takalmi ba'ki, hannunsa daure da agogon silver samfurin (D&G). tun kuma a lokacin yake amfani da turaren Versace,'kamshin sa na cikin abubuwan da dalibai ke magana akai.

A wannan kallon da ta mishi na 'kurillah ta janyo wa kanta, domin bata dauke idon ta akan shi ba, sai da son shi ya cika zuciyar ta dam, irin son nan da yake shiga ba tare da an ankaraba, lokacin da za'a ankare din ya riga da yayi illar da ba yadda za'ayi dashi.

Da kanta ta dinga cewa Madallah da 'ka'idojin musulunci, sai da akace kallon shari'a 'daya ne tak, amma ni na mishi kallon 'kwal uwar 'daka.


Nasiha ya musu, akan ko a gida su dinga bitar karatunsu, su kuma zama yara masu tarbiya, ta yadda duk inda aka ga 'dalibin FGC KANO aga ya banbanta da na kowacce makaranta soboda ladabi.

'karshe ya kulle bayanin shi da lallai su kyautata wa iyayen su, su musu biyayya, su kuma taimake su akan sha'anin ayyukan gida.

Ya kalli side din maza yace
"wadda kuke tu'ki, ku bi a hankali kusa nutsuwa".

Banda kallon shi ba abin da Sa'a keyi tana jin turancin sa tamkar Baturen da yanke wa yaren cibiya.

Yana kammala wa yayi waving hannun shi alamar bye, ya fice da sauri.

Basu bar class din ba sai da Safina ta yi sulhu a tsakanin Halima matazu da Sa'adatu Gogel, dan haka rabuwa suka yi ta salin alin a tsakanin su tare da al'kawarin zasu hadu a gidan su Humaira asabar din sama, bata gobe ba.

Tafe suke ita da Zainab da Asiya wadda yayar Zainab din ce.
kamar ance ta juya ta hango Uncle Mk da Farida a tsaye jikin wata bishiya da dukkan alamu ba a zo 'daukar ta ba, hira suke hankali kwance.

Take ta ji tamkar ta mutu, zuciyarta ta daure,'kirjin ta yayi nauyi ainun, tafiya kawai take amma bata sanin inda take jefa 'kafarta.
Suna tsaye a bakin gate din makarantar suna jiran abin hawa ta ga yazo ya wuce su akan mashin 'dinsa da a wancan lokacin ake mishi la'kabi da tsuntsun soyayya.
Hannu ya daga musu amma sai ta juyar da fuskar ta, tayi kamar bata ganshi ba, Zainab ce kawai tayi waving 'din shi.

Tana isa gida 'dakin ta, ta wuce ta fa'da kan katifarta wani kuka ya kwace mata, tayi abinta ta 'koshi kasan cewar Innar ta na wanka, daga kukan barci yayi gaba da ita, sanin da mahaifiyar ta yi na fashin salla take yasa bata tashe ta ba.

Haka ta yi hutun nan su ku ku, ciwon so na wahalar da ita, a tunaninta tasan so akan khalil, Ashe ba son sa take ba, kawai shakuwa ne da kuma yadda yake mata hidima, a yanzu ne take dandana azabar soyayya, yanzu ne take jin so tun daga zuciyarta, idanuwanta, da gangar jikinta gaba'daya.

Idan ta tuna Farida yake so, sai taji tamkar za ta sume.
A yadda ta ji ciwon ganinsa da Farida a tsaye yana mata magana cikin walwala komi yana iya faruwa da ita idan ya kasance kullum zata na ganinsa tare da ita.

Zaune ta ke tana fargaban komawar ta makaranta wani satin, a da ta dauka zullimin zuwa makaranta ya 'kare tunda yanzu ta tsira daga tozarcin Uncle Mk! ashe tsugunne bata 'kare mata ba?.

Agogon bango ta kalla taga 2:30pm da sauri ta 'mike ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin lallausar atamfar quali-wax mai kalar samaniya(Skye blue)da ratsin ja, Riga da skirt ne, dinkin yayi matuqar zama a jikinta,'katon jan 'dan kunne mai round tasa, a lokacin yayin kwalliya irin ta wannan zamanin ba tazo ba, amma duk da hakan ta she'kawa fuskar ta kwallliyar da ta dace da ita.
Mayafi jah ta ya fa, sumfurin(internet). ta sanya takalmi half-cover amma hills. da yar mitsitsiyar jakarsa wadda zuwanta jos ta siyo su masu Jan duhu. ta fesa turare ta fita zuwa 'dakin Inna.

Inna na shirya, mi'ke wa tayi daga kishingidar da ta yi, hannun ta ri'ke da carbi tunda ta idar da sallar azahar bata tashi ba.

"Yanzu Iyah ba za ki daina zabga turaren nan idan zaki fita ba?
Ba kyau fa, ki kiyayi taba shari'a wallahi"

A hankali tace
"Allah Inna 'dan ka'dan ne, kawai 'kamshi ne dashi".
"To tunda kin san yadda yake dole ne, idan zaki fita sai kin saka?
Ki fa dinga jin tsoron ubangijin ki, kina kiyaaye ka'idojin shari'a".

Kafin tayi magana, ta sake cewa
"A gabana kika ce da Baffan ku, bayan la'asar za ku dawo, ki sani idan kika wuce wannan lokacin ba zan 'ki fada mishi ba"

"In sha Allah bazan kai maghrib ba Innah"

"Sannan kuma kiji tsoron Allah idan mu bama kallon ki, shi yana kallon ki.
inda kika tambaya nan kawai aka lamince miki zuwa.
Sai kin martaba kanki, kafin wani ya martaba ki, sannan kuma
duk saurayin da ya tsayar da ke kice mishi yazo gidan ku, ya nemi izinin magana dake a wurin mahaifin ki."

A sanyaya ta amsa da
"Zan kiyaye Inna"

Sannan ta juya ta tafi, tana rayawa ko sai yaushe Inna za ta dena mata bitar wannan nasihar a duk sadda zata fita?
Jikin ta yayi sanyi, nasihar ta matu'kar ratsata.
take ta ji ta fasa zuwa inda ta yi niyya, tunda gidan su Halima zata je su hadu da Khalil dake duk kusan unguwar su daya.

Tunda akayi hutu basu hadu ba, a dalilin fushin da yake yi da ita, yana zargin soyayya suke ita da Uncle Mukhtar.

Baisan gidan su ba, kullum cewa take ba a barinta yin zance, sannan indai aka ganshi yaje gun ta za ta Sami matsala babba, nan kuwa gani ta ke da kunya yazo ya ga gidansu.
Nasihar Inna tasa ta canja shawara gara kawai yau ta kaiwa Zainab Ma'aji

Please Login or Register in order to submit comment