You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

littafin, ya ru'ko ta jikinsa ya ce, "Ke ce uwargida kuma amarya ta, da gaske nake kin cike mini gurbin mata hudu, ki daina wasiwasi akan maganata, ko an kaddara mini zan 'kara aure ina tabbatar miki, ba zan hada ki da kowa a gidan ba, daga ke sai yaranki ki yi yadda kike so".


"Ban cike gurbin mata hudun ba kenan?"

"Oh Sa'adah! kin zarta mata hudu ma, kawai ban son na miki al'kawarin da za'a jarrabe ni da rashin cikawa ne, kinsan bamu muke tsarawa kanmu rayuwa ba, idan haka ne kuwa bai kamata mu yi katsalandan akan goben mu ba, Ina tabbatar miki a burina ke kadai kin isheni rayuwa, sannan har yau ban taba jin son wata a zuciyata da ya kai matsayin da zan aurota ba".

Ta lafe a kirjinsa tana jin dadin yadda ya ke rawar jiki idan za ta botsare masa.

Kudin da Mk ya samu sun yi albarka kwarai da gaske, ya fadada shagon askin sa, ya sake budewa Ahamad wani shagon, hatta gidan da suke ciki ya sha gyara na mussaman, ya sakewa falonsu kujeru da sauran abubuwan more rayuwa da ya dace da ra'ayin gimbiya Sa'adah.ya kuma biya kudin aikin Hajj.

Sa'a kam ba a maganar yadda take lasar kudi har gold ya sai mata, waya ce dai bai siyi wacce take so ba, amma ya bata waccan da ta raina da kuma ainihin tata da ya karbe.

Baba Isa da su Baba umaru duk Sun Sami tagomashin inconclusive, duk da dai dama akai akai yana waiwaryasu da abin da zai iya na Alheri da neman albarkar su.


Shigowar what'sapp ya taimaka wurin tabarbarewar tarbiya, a farkon shigowar sa ya rudi mutane da yawa mussaman Mata dan hatta abinci sai andauka an dora a WhatsApp, gida mai kyau kuwa kullum cikin tallansa ake yi. Ya zama ba sirri, mussaman idan mace tana cikin wadata ta hanyar status take bayyana matsayin ta, hakan ya sake jefa Sa'adah cikin buri sosai kullum cikin kara son kayan garari ta ke .
Sannu a hankali aka fara bude groups daban daban ciki har da na tsofaffin dalibai, babbar mastalar group din su Sa'adah hade yake da mazan set dinsu tunda makaranta tasu hadaka ce da maza.
A haka Khalil ya samu numban ta, suke gaisawa lokaci zuwa lokaci, duk da baya nan yana Egpt yana karantar sociology.

Ta hanyar what's app ya mallaki hotunanta dana Jawad, idan ta yi status zai yi saving, ba a karan kanta ta ke tura masa ba.

Haka Kuma taron tsofaffin dalibai (reunion) sai ya zama ruwan dare, ko Ina taron tsofaffin dalibai ba 'kak'kautawa.

A wannan lokacin FGC Kano ta shirya nata tunda ga kan daliban farko har zuwa daliban da suka kammala a shekarar taron.

Taron ya kai taro, mafiya yawa daliban ma'aikatane ko manyan Yan kasuwa' har tsoffin Malaman duk sun halarta, dan haka Mk ma ya je, manyan mata masu aji, wadda suka yi wanka da ilimi da gogewar rayuwa duk sun kewaye harabar makaranta.

Sai farin ciki ake yi, mafiya yawa kuma cikin shiga ta alfarma suke, Sa'adah na cikin jerin da basu da makusa tun daga kan suturarta har zuwa fatar jikinta, kawai na'kasun ta 'daya ba a motar kanta ta je gurin ba, bata ji muzanci ba, sai da Mk yace mata zai tafi idan sun kammala ta wuce gidan Inna zai 'dauketa acan.

Kusan 'Yan set dinsu kowa da mota ta je har 'yanmatan cikinsu, Halima a motar Safina suka je, motar da Sa'adah taga Farida a ciki ta matu'kar tsaya mata a rai.

Hira ake ta yi, ana zuga wadda rayuwar su ta yi nasara ta hanyar kambaba lamarinsu, wasu kuma ana yi musu gadar zare, daga gefen su Sa'adatu, wasu matan ke hirar da ta ja hankalinsu, duk da seniors din sune sosai, 'daya cikin matan ta ce

"Ni da aure kuma mun yi hannun Riga, ba komai a cikinsa sai jidali, da hawan jini, baka da ikon yin komai na ra'din kanka, sai ka jira namiji, sannan baka da 'yanci ko kadan a aure".

'Dayar wadda da alamun ra'ayin su daya da wadda ta kammala bayani itama ta cafe da cewa "ai kuwa dai lubna da gaskiyar ki, dare, asuba, tsakar rana kowanne lokaci miji saka'dar ka yake yi tamkar jaka, amma da za ka bijiro da bu'katar ka, ba za'a maka ba, ko za'a maka din kuwa sai ka gama wulakanta".

Lubna tace da Asiya "Ashe kin gane karatun! dan haka tsakanin mu da namiji a hadu ayi ar'kallah kowa ya kama gabansa, yanzu kiga da ka ke cin gashin kanka cikin kankanin lokaci ka mallaki abubuwa masu daraja, wadda macen aure sai ta shekara fiye da ashirin ba ta mallake su ba".

Wata cikin su, tana bude Baki ta ce "Amma kuma matan aure sun muku zarra da mutunci da kuma 'kima, macen aure tana tsufa tana sake daraja, adalilin gatan da musulunci ya mata".

Dukkan su suka sa mata dariya, suna ganin wautarta, Lubna ta ce "kai ku rabu da Hajara kunsan tunda ta gama wannan makarantar ba ta sake shiga aji da nufin zurfafa ilimin ta ba, kenan kanta a duhu yake bata san komai ba, tana cikin jerin matan da maza suka rufe a gidaje suke gallaza musu, suka kuma hana su fahimtar cigaban da duniya ta samu"


Su Halima da suke jin tattaunawar suka kwashe da dariya suna fadin "ai yanzu duk wadda ta zauna namiji na mata mulkin kama karya mata ta rako duniya, a wannan karnin da ilimi shine komai yaushe zaka yarda a barka da jahilci, barin ma idan mijin naka mai ilimi ne? Da zarar muguntar namiji ta motsa sai dai ki ji ya amarce da mai ilimi, ko kiga yana jin kunyar ya saka ka a al'amuransa".


Jikin Sa'adah ya yi sanyi ganin itama cikin rukuninsu ita kadai ce mai sakandiren, haka akayi ta kutsiri tsoma, ba a gama da wannan maganar ba, a saketa a kamo wata, da za su tafi, a motar Safina suka dunguma har kofar gidansu suka kaita, a hanya suka yi hirar Humaira Suraj da a yanzu take aure a sokoto, dama can ne garinsu aiki ne kawai ya kawo mahaifin ta Kano.

Tun wannan lokacin Sa'adah ta fara canjawa, ita da kanta tasan ba abin da ta nema ta rasa illah motar kanta ba wai ta Mijin ta ba, amma zuciyar ta sai tsalle take mata tana ganin kamar ita ta wuce komai sai ta jira iznin miji kafin ta zartar, tana bu'katar ta zama yantacciyar mace mai yin komai babu 'dar balle fargaba.

Kullum a WhatsApp su Halima na sake kuranta kyakkawar siffarta, har suna cewa ba wadda zai ganta yace ita ta haifi Jawad, ko su da suke 'Yan mata basu fita komai ba.

Suna cikin wannan zaman na ba yabo, ba fallasa, Su Halima suka zo mata da kaya cike da katuwar leda, kana ganin ledar kasan tafiyayyace, sai da aka bude kaya, suka ga kayan Jawad ya kai set biyar, sai agogo na English gold, da kuma waya blackberry bold 4, da tarin alawowi da biscuit duk tsaraba ne inji Khalil abawa Jawad waya da agogo kuma nata ne.

A kidime Sa'adah ta ce "Na shiga uku Safina idan Malam ya gani fa, da me zan kare kaina? Gaskiya bazan karba ba tsoro nake ji.

Harara Suka galla mata, Halima tace "to kuma barinsa zaki yi ya gane daga inda suka fito, sai an kwana biyu kice Anty Sumayya ce ta aiko muku, waya kuma ki boye abarki sai ba ya gida, ko idan zaki je taron fitar kunya, na gaji da ganin ki da karamar android shiyasa na fa'da masa baki da wayar shiga taro".

Safina ta dora da cewa "Da yake ya damu da farin cikin ki kasa da awa ashirin da hudu da fa'da masa ya siyo, ya bayar akawo miki, gaskiya Gogel kin tafka asarar masoya, na tabbatar ko yanzu da kika zama uwa, Khalil zai aure ki a matsayinsa
na saurayi".

Suka hada baki wurin cewa "duk da ke 'din ma kinfi 'yanmata da yawa nagarta".


Tun lokacin hankalin Sa'adah yafi karkata kan wayar nan, kullum Mk ya fita za ta fito da wayar ta, ta yi komai, mussaman take da layi na daban a ciki, amma da layinta ta bude komai.


Tun Mk na tambayar ba'asin canjinta har ya gaji, yana ganin ya kyaleta ya huta shima, dan taga yana damuwa ne shiyasa take masa wulakanci, dan haka ya rungumi sabuwar rayuwar da ta bude musu, hatta a shimfida ta canja, ba wai gudunsa take yi ba, kawai zama take yi tamkar gunki, sai dai ya yi kidansa ya yi rawarsa shi ka'dai.

Haka nan abu kadan Jawad zai yi ta rufe shi da duka tamkar wadda take dukan babba.

Wadannan dabi'u suna matu'kar ciwa Mk tuwo a 'kwarya mussaman dukan yaron da ta tsira, ko abu ne ya hadasu sai ta huce akan 'dansa.

Rannan suna kwance sun gama mu'amalar da ba gishiri a cikinta balle Maggie, ran Mk a bace yake sosai, ya rasa mai zai mata kuma, ya riga ya kai gejin rarrashinta, ya gane gaba'daya kwakwalwar kifi ne da ita.

Ya yi gyaran murya ya ce "tsakanin ki da Allah ki fada min me kike nufi da ni, rokon ki nake yi, yanzu na tabbatar ba kya sona Sa'adatu".

Yana rufe baki ta ce "Kaine dai baka sona, komai zan yi a laifi na ke, 'dazu ba ka ga irin 'barnar da Jawad ya mini ba, dan na dake shi, ka hayayya'ko mini, salon kasa ya raina Ni".

"Amma tun ba yau ba ki ke wannan fizgewar, yaushe rabon da ki saurare ni cikin da'din rai, kullum da bacin rai kike yarda da ni, ko kin yarda kai tsaye to sai dai ki zame mini tamkar gawa, anya kuwa dama kina sona? anya kina jin tsoron hakki na akan ki, amma na yafe miki, na kuma dauki laifin ko menene ki yi hakuri ki yafe mini".

Ta tura baki ta ce"Tun yaushe nake ce maka zan dubo mahaifiyar Halima da ta yi hatsarin mota, duk yan ajin mu sun je banda ni".

Murya ba amo ya ce " Hana ki dubo uwar Halima yasa ki ka na'de kafar wandon yin min wula'kanci haka?"

Ta yi shiru ta kasa cewa komai saboda ta ga ya hassalo sosai, ya furzar da iskar bacin rai ya ce "Shikenan ko da wani laifin bayan wannan?"

Kamar shasha ta ce "yauwa ni fa yanzu nake son motar nan, na ga kai kuma kana nufin kamar sai anja lokaci, kawai ka dakatar da ginin ka siya mini".

Ya kalleta ido cikin ido ya ce "yin hakan shine sharadin samun zaman lafiya a tsakanin mu?"

Ta kasa amsawa tsawon lokaci, dan haka ya ce "Ba wadda zan miki ko 'daya, idan ya so zaman namu yafi haka muni".

Ta tashi ta fita tana 'kun'kuni, akan sai ta je, ta gaji da 'yadda ya maidata bagidajiya marar yanci, kansa ya sara yana jin ba'kin cikin ta na neman kassara shi.

Haka har kwanaki uku suna zaman doya da manja, Rannan cikin dare ta ji hannunsa na lalubarta, ta zabura kuwa ta bige hannun, tare da fadin "Bana so".

Bai saurare ta ba ya damko ta, ya fara kokarin gwada mata 'karfi saboda ya gaji da rarrashinta.
Ganin da gaske zai cimmata alhalin ta riga ta kudiri aniyar ba za ta saurare shi ba.

Dan haka ta fashe da kuka ta ce " raping dina za ka yi? na fahimci bani da mutunci a gurinka indai ba bu'katarka ce ta ciyoka ba, na daina ganin aibun 'yantattatun mata wadda suka juyawa aure baya, saboda sun san ba komai a cikinsa sai ba'kin ciki da takura da kuma 'bacin rai".

Jikin Mk ya mutu yana rike da ita, da ta lura, tashin hankalin da ke zane baro baro a fuskarsa ba zai bari ya ci gaba da rarrashinta a YAU kamar yadda ya Saba ba.

"Matan da suke zaman kansu, duk abin da suke so, aguje suke samu, amma matan aure sune agaba wurin samun hawan jini saboda tsabar bakin cikin da mazajensu suke 'kulla musu".

'Kololuwar tashin hankali Mk ya shiga, ji yayi jiri ya kwashe shi dan ma a zaune yake, ya tafi luu ya buge 'keyarsa da fuskar gado.

Da kyar ya dauki hannunsa ya ri'ke kansa da yake tsananin sarawa, da karfi ya dinga ambaton" innalillahi wa Inna ilaihir raji'un".

Ya dade yana nanata kalmar, har ya dan sami nutsuwa kadan, ya mike ya saka rigarsa da wando, ya ware murya sosai ya ce "Ni ki ka fadawa wannan maganar? Ashe kuwa har yau baki gane ni ba, zan nuna miki ba a bariki muke ba, ba kuma auren bariki na ke yi ba, ki ri'ke dukkan abin da ki ke tun'kaho da shi bana so, ki ji'ka ki shanye abin ki, amma ki sani yau da Gobe zasu biyar da ke indai kina sha'kar numfashi".

A daren ya dauke dukkan abin da yake nasa ne a cikin dakin Sa'adah, sai Agogon hannunsa da yake cikin wadirof dinta ya manta bai dauka ba. har ya kwanta ya tuna bai dauko tawul dinsa ba, ya koma ya dauko, kafin ya fita ya tsaya ya kalleta tana zaune duk jikinta ya saki da alamun ba tasan girman munin maganar data furta ba, sai bayan ta fada.

A kausashe ya ce "Na tsane ki, na tsani na bude ido na ganki, ba dai kin fi sha'awar rayuwar 'kazanta akan ta sunnar Ma'aiki ba? kin raina duk kokari na, kin raina ni'imar da kike ciki, Na rantse miki! ba dan kunyar Baffa ba, da a yau na mayar da ke 'yantacciyar macen da kike fata, ni kaina NADAMAR auren ki na ke yi, amma na gode Allah da nake ganin sakamakon son zuciyata a duniyar nan, ba sai naje lahiraa ba,'kiri 'kiri na nunawa mai sona da gaskiya HALIN YAU, na butulci".

Ya juya ya fita ya barta cikin rashin sukuni mai yawa.

Tun daga ranar ya bala'in dauke mata wuta, idan ya fita tun safe, sai dare ya fara turawa zai dawo, sannan matu'kar yana gida to kuwa kofar dakinsa a gar'kame ta ke hatta Jawad ba kasafai yake ganinsa ba, kullum cikin tambayar Sa'adah Ina Malam ya tafi?".

Wannan ne karon farko da ya yi fishi ba waiwaye, hatta fuskarta baya son gani a yanzu, sabanin da da ganinta shine cikon farin cikinsa, har yau fama yake da ciwon da bakaken maganganun suka sababa masa a zuciya yake yi.

Ana haka mijin Sumayyah ya yo waya akan bata da lafiya sosai, haihuwa ne ta zo mata da tangar'da anmata C's an fito da yaro amma kuma bata da lafiya.

A ranar Baffa ya sanar da Mk, akan gobe za su yi asubanci zuwa Gombe shi da Inna, idan ba damuwa ko zasu tafi da Iyah ta gano jikin yar'uwarta.

Bai yi nauyin baki ko kunya ba, ya ce "Zan zo na kai ku Baffah amma ita daga baya zata je".

Godiya sosai Baffa ya masa tare da fadin "ko bata je bama ai kai kaje , ka wakilceta".

Haka akayi tafiyar Sa'adah ko labari bata ji ba, a ranar Baffa suka juyo da Mk, da kuma Hajiyar Bichi da ke ta bisu, suka bar Inna dan ta kula da Sumayya, kafin Umma fanshekara ta je sai Innan ta dawo.

Ganin da innah ta yi har washagari Iyah bata 'kira ta yi jajen mai jiki ba, sai hankalin Inna ya tashi tana tunanin ko itama ba ta da lafiya ne?

Tana Shirin 'kiranta, sai ta 'kira suka gaisa, mamaki ya sake kama Inna ganin ba alamun ta samu labarin halin da 'yar'uwarta take ciki, dan haka sai tace "mijinki bai fada miki Ina Gombe ba?"

"Wallahi bai fada mini ba, wani abin ne ya faru?" ta tambaya a kidime.

A sanyaye Inna ta ce "yayar taki aka yiwa tiyata ga yaro nan lafiya lau, sai itace bata Jin dadi, amma dai da sauki".

Cikin muryar kuka ta ce" shine ba ki fada mini ba Inna?".

"Mijinki ne fa ya kawo mu, jiyan suka juyo da Baffanku, Kinga ai bana yi zaton ba ki ji ba, duk yadda akayi ba zaman lafiya kuke yi ba Iyah, tunda da bakinsa yace baza ki zo ba, sai muka dauka ko kema ba Kya jin dadi ne ya rufe mana, har da Hajiyar Bichi muka zo, duk jiyan suka juyo".

Kuka kawai Sa'adah ta ke yi, irin kuka na rashin madafa, sosai kukan ya ta'ba Inna, tashin hankalin ta ya 'karu ga na Sumayya da ta ke kwance bata san wadda ke kanta ba, ga na Iyah da ba tasan ha'ki'ka in matsalar ta ba.

A sukwane ta kira Baffa tace lalle akwai matsala tsakanin Iyah da Mijinta, cikin rashin daukan maganar da muhimmanci ya ce "Mijin ta bai kawo 'kararta ba, ita ba ta ce ga laifinsa ba, sai kawai naje na hau bincinkarsu, tunda sun iya 'boye sirrinsu, sai a bisu da addu'ar Allah ya daidaita su".

"Ka shiga maganar nan, da alamun fa abin babba ne, hatta zuwan nan da ya yi Gombe bata sani ba, kar a zuba musu ido fa".

"To" ya ce mata a gajarce ya katse wayarsa! yana cewa lamarin mata yana da ban mamaki, kawai dan kina so a tursashi ya barta taje inda baya so taje sai kice naje na shiga tsakanin su, duk tsawon lokacin da suke tare waya ya san yadda suke zaune?

Haka kwanaki suka yi ta shudewa a cikin Wannan hali tsakanin Mk da Sa'adah, kullum 'kara nesanta kansa yake da ita, zuwa yanzu da suka cika sati biyu cikin wannan halin, wadda ko a mafarki bata yi zaton zai iya shareta har haka ba, domin tun ranar da ta yi wannan katobarar bai sake bin takanta ba, asalima ta lura bai son ganinta ne har zuciyar sa, tana ganin idan ya dawo a gaggauce yake shigewa dakinsa ya rufe kofa, hakanan idan zai fita a hanzarce ya ke ficewa, duk yadda bai son ya ji kukan Jawad amma a yanzu duk kukan da zai masa ba ya tsayawa ya bi ta kansa.

Ta shiga damuwa da tsoro irin wadda bata taba shiga ba, tsoron ta 'daya idan iyayenta suka ji mai ya jawo wannan tashin hankalin, wanne irin kallo zasu yi mata,?

Ta 'kudiri aniyar yau zata bashi, ha'kuri ta kuma nemi ya barta taje ta gaida Aunty Sumayya.

Haka akayi, taran dare ta yi wanka, ta shirya cikin kwalliya ta burgewa, tana jin dirin motarsa da kiciniyar bude gate, ta fita a hanzarce ta shiga kicin mai ma'kwabta ka da 'dakinsa ta tsaya.

Ai kuwa ya shigo da sauri, ganinsa rungume da kayan wankinsa da ya kai wanki, jikinta ya sake yin sanyi, komai zata yi masa, idan zai kai wanki zai shiga har 'dakinta ya hada kayanta akan nasa ya kai musu wankin amma banda Wannan karon.

Kafin ta yi yunkurin shiga dakin nasa sai ta ga ya fito ya fita da alamun ya yi mantuwane, dan haka sai ta yi wuf ta shige 'dakin, yana shigowa kuwa ya rufe 'dakin bayan mukulli har da sakata ya sanya.

Yana shigowa ya ganta lafe jikin wadirof, ga mamakinsa sai yaji kwalliyar da ta yi, bai ji komai na burgewa akanta ba, hakanan kamshin ta da ya cika masa hanci bai yi tasiri a jikinsa ba, kyakkawar fuskarta da ke sanya shi nisha'di, a yau ba'kanta masa rai ta yi, hakanan surarta da ke jefa shi cikin shauki, a yau takaici ya ji ya maye gurbi.

'Bacin ransa ya dawo sabo fil tamkar yanzu take gasa masa maganganun da suka zame masa tamkar 'digar dalma a zuciya, suka yi awon gaba da kaso mai yawa na matsananciyar soyayyar da yake mata.

Baice mata komai ba, ya shiga rage kayan jikinsa, ya shige wanka, tana tsaye ya fito ya shirya, ya tada sallar shafa'i da wutiri.

Sai da ya idar ya zauna bakin gado ya kalleta, ya ga duk ta takura, ta susuce, ta lalace, idonta ya fada alamun dai tare suke 'dan'danar 'bacin rai.

Kafin ya yi magana ta rigashi! Ta tsugunna ta ri'ke gadon ta ce "Dan Allah Malam ka yi ha'kuri, ban taba jin nadama irin wadda nake ciki ba".

"Ba ki mini komai ba, abin da ke zuciyarki ki ka amayar, sai dai ina so ki sani wallahi ba ki fara nadama ba, ina tabbatar miki za ki shiga NADAMAR da ta zarce wadda kike ciki, da kinsan yadda na tsani ganin ki da hakan ka'dai ya isa ya saki nadama, da kinsan yadda kika wanke kanki a zuciyata da kin gane asarar da kika yi ba ka'dan bace".

Kuka ya goce mata, ta rarrafo da nufin ri'ke shi, ya zabura ya mike tsaye cikin bacin rai ya ce "idan kika yi kuskuren sa hannun ki a jikina, na rantse miki sai na miki abin da za ki gamsu ba ki da sauran 'kima a gurina. domin duka zan miki irin yadda ake na'dawa 'yantattatun matan bariki idan angama cin moriyar su".

Kukan ya tsaya mata! da gaske ta yi kuskure, irin kuskuren da ake yi sau daya amma sai an nemi hanyoyi gyara dari bai gyaru yadda ake so ba. daga jiyo magana a bakin shedanun mata ta ara ta yafa, har ta zo ta fa'dawa mijin aurenta wadda da gaske samun irinsa zai yi wahala.

Ta zauna 'dabas tsakanin gado da wadirof ta dinga kuka, mai cin rai, na tsantsar nadama.

Daga inda yake ya ce "Ta shi ki bar mini 'daki ban bukatar ki a cikinsa".
Ta kasa koda kwakwkwaran motsi. tace "ka yi hakuri ba dan ni ba, ka dubi girman Allah ka yi hakuri".

Jikinsa ya yi sanyi yace "Na ji, amma dai tashi ki fita, ina bukatar ka'daici ne, duk sadda nake da bu'katar ki a dakin I will let you know".

"To ka daina rufe 'dakin, na yarda duk sadda na zo ka kore ni, amma ka daina rufewa".

Ya zuba mata ido yana jin takaicinta na sake kama shi, amma da yake so yake ta fita ya shaki iska marar takura sai yace mata to a takaice.

Ganin ya amsa mata sai ta tashi ta bude 'kofar ta fita tana fadin " ka yi hakuri, ka yi barci mai cike da walwala".


Ya bita ya rufe kofar, ya dawo ya karanto adduar barci ya kwanta.

Washagari da sassafe ta shirya masa abincin karyawa ta zauna zaman jiran ya bu'de 'kofar, ai kuwa yana budewa ya ganta da tiren abinci, a bakin kofar dakin, yasa kai zai wuce ta ce, " Ina kwana?"
Ya amsa a gajarce, "ga abinci na gama". ya girgiza kai ya ce
"ki daina wahalar da kanki wurin yin abinci saboda Ni, na riga da na 'yanta ki daga dukkan yi mini hidima kowacce iri ce".

"Cikin rawar murya ta ce "kace fa ka yi hakuri?"

"Da ban yi hakuri ba, da baki ganni akan 'kafufuna ba, da ina can akan gadon asibiti saboda ba'kin cikin ki, da ban yi ha'kuri ba, da ban tsaya ina miki magana ba".

Ta goge hawaye ta ce "ka kara hakuri dan Allah nasan na yi ba dai dai ba".

Ya girgiza kai ba tare da ya ce komai ba, ya fara tafiya, da azama tace " Malam! Umman fanshekara gobe zata tafi Gombe, dan Allah ka bar ni mu tafi tare, ni sai na dawo ko jibi ne".

Ya juyo a zabure tamkar wadda ta fadi mugun abu ya nunata da yatsa ya ce" dama nasan duk wannan saukar da kan da kika yi, kina da bu'kata ne, ba kya tashi mutunta ni, ko kwantar mini da kai sai kin ganni da kudi, ko kina son na barki kije wani guri".

Cikin kuka sosai ta ce "Haka ka dauke Ni?"

"Kin wuce hakama ke kam, saboda ke ciki ce mai manta kyautar jiya, mai manta alheri, da kina da hankali, da baki cemin za ki tafi yawo Gombe ba, kawai tafiya za ki yi kanki tsaye".

Ta zuba masa ido ta ce "dubo Anty Sumayya ne yawo?"

A kausashe ya ce "ke kika san Sumayya, ni mai na hada da ita! ko dole nace?"

Tashin hankali 'baro 'baro ya bayyana a jikinta gaba'daya, lalle da gaske Mk ya shiryawa tashin hankali iri iri, wai Anty Sumayya ce yake fadin sunan ta gatsal, duk da ya girmeta da shekaru biyu amma Anty yake cemata, sannan kuma har yana cewa mai ya ha'da da ita?.

Ta kalleshi baki na rawa ta ce "Dan Allah Malam ka yafe mini, mu zauna lafiya ba zan iya kar'ban wannan tashin hankalin daga gareka ba, na

Please Login or Register in order to submit comment