You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana da su ba adadi tsadaddun gaske, da yawansu ma bata sake waiwaryasu ba.

Kayan kwalliya da waya tafi bukata a yanzu, sai hanyar da zata dinga samun ku'di tunda yanzu bata bu'katar na Mukhtar, tasan shima ba zai yi gigin bata ba.

Ta sani iyayenta da Sumayya suna iyakar kokarinta amma dai ba zai yiwu ace dukkan lalurarta sai an yi mata ba.

Saura kwana uku tafiyar su Jawad, Ahamad ya kawo shi gurin Sa'adah inji Hajiya ya kwana mata biyu, tare da sallama, tunda Mk ya yi aure Hajiya ta shiga cikin wani hali na kunyar Sa'a da iyayen ta, mussaman da Mk ya fada mata Baffan Sa'a ne ya biya masa sadaki, sai ta ji inama ace Hajiya Babbace a raye ita kuma a mace, tasan Hajiyar ta fita juriya da shanye 'bacin rai.

Sosai Sa'adah ta samu sau'kin zuciya cikin sati biyu nan, domin ko da ta ji tafiyar da Farida da Jawad za su yi bata wani damu ba, illah ta ji ba da'di, Jawad ne ma ya nemi karya mata zuciya da yawan tambayoyinsa akan me yasa ba zata bisu ba?

Da daddare suna kwance kansa na kirjinta yana bata labarin abubuwan da zai siyo mata idan zai dawo.

Can ya ce "to kawai Mami mu tafi tare mana, kema ai baki taba hawa jirgi ba".

A hankali ta ce "Malam bai ce na je ba, Aunty Amarya ya ce ta je".

"Mami idan kin je ai ba zai yi fa'da ba".

Cike da soyayyar 'danta ta ce "Ai bai biya mini kudin jirgi ba".

Ya yi shiru sai ya ce "Na ji kafin ya tafi ya fa'dawa Hajiya, Baban Antin ya ce shi zai biya kudin tafiyar mu".

Zuciyarta'daya ta ce " To ka ga ba ni a tafiya kenan tunda Ni Baffahna bashi da ku'di".

Ya yi shiru, can kuma ya kalleta tamkar wadda aka kitsa masa ya nisa! ya ce "Ni zan tara ku'di da yawa na kai ki, har jirgin ma zan siya miki".
Hawaye ya cika mata idanuwa, ta yi kokarin gogewa ba tare da ya gani ba.

Sai da ta shanye kukan da ya zo mata ta shafa kansa ta ce "Allah ya nufa Jawad, ubangiji ya maka albarka, idan ka je ka dinga sallah da wuri, komai Anti ta ce ka yi, kada ka yi mata musu kawai ka yi, ka dage da karatu sosai banda wasa, domin wadda zai siyi jirgi sai ya zama mai jin maganar iyayensa ya kuma yi karatu tukuru.

U.K.
A airport suka tarar da Mk yana fama jiran isowar su, da Jawad ya hango shi, da gudu ya nufe shi, da azama Mk ya daga shi sama domin abin da Jawad ya ke so kenan ya ga Babansa ya daga shi sama ya'ki yarda ya girma.
Taxi suka hau, zuwa gidan da zasu zauna, a hawa na takwas gidan yake dan haka Suka shiga lifta abin da ya burge Jawad, domin dai shine bai santa ba, tunda Farida ta saba fita kasashen waje.

Gajiyar hanyar da suka kwaso bai hana Mk sake dorawa Farida wata gajiyar ba, domin a matu'kar takure yake sai da ya samu ya zubar da abin da ya takura shi sannan ya ji shi daidai.

Rayuwa suke cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, Mk ya shayar da Farida mamaki da ya samar mata gurbin karatu a Jami'ar da yake inda zata yi masters dinta duk dai akan sanin magungunan (Pharmacy).

Ya ce " wurin aikin ki sun baki damar tafiya ne dan ki zurfafa ilimin ki, gara mu ki kiyaye ka'ida, sannan kema baza ki yi zaman kadaici idan bana nan, kuma Jawad yana school"

Cikin gaskiya da amana take ri'ke da Jawad komai yake so yi masa take yi, duk sadda ta je makaranta bata mantawa sai ta siyo masa abinda zai ji da'di, sun shaku sosai, da ke mai son jiki ne indai suna zaune to kuwa rabin jikinsa yana jikinta, sau tari Mk ke cewa "kina fama da kanki, amma sai ki kama katon yaro ki jingina wa kanki".

Murmushi take yi ta ce "Duka duka nawa ne adadin nauyinsa?"

Sosai ta samu saukin Ciwonta duk tashin da zai yi baya kayar da ita, kamar sadda take Nigeria, domin kwararren likitan ('kashi) take gani a asibitin jamiar, sannan zurfafa ilimin da take a fannin magunguna ya na taimakawa wurin sake sanin maganin da ya kamace ta.

Jawad yana ta karatunsa domin haziki ne sosai kamar Babansa bai yiwo shiriritar uwarsa ba, ko acan da suke da tsarin ilimi mai nagarta sosai yake ja, domin parfomance dinsa is very high hakan na farantawa iyayen nasa rai shiyasa komai ya ce yana so suke rige rigen yi masa.

Ba abin da yake damunsa sai rashin Jin muryar uwarsa a waya, tunda Mk yana ha'dasu da Hajiyar Bichi, da kuma Baffah, amma ya kasa samun layin Inna da Sa'adah ta ke amfani da shi, ita kuma tunda take ganin missed call din lambar waje ta kuma gane lambar Ingila ce sai ta yi blocking din layin shiyasa basa samun layin. kunyar Baffah take hana Mk tambayarta. Rannan Jawad sun gaisa da Baffa ya ce "Baffah ka bawa Mami wayar zan yi magana da ita".

Baffah da bai san Iyah ta rufe musu hanyar samunta ba ya ce "yanzu tana makaranta, Ni kuma bana gida ku nemeta a layinta ko na Innar ta.

Domin kuwa basu jima da barin kasar ba ta ce da Sumayya tana son waya, a satin ta turo mata da kudin waya mai tsadar gaske, tunda murna suke yi ta yarda zata ri'ke waya, alamun ta cire komai a ranta akan Mk, zata fuskaanci rayuwarta ta gaba.


Tsawon wattanni takwas kenan Jawad bai ji muryar uwarsa ba, a hankali sai abin yake 'dan ta'ba shi har abin ya fara bayyana a komai nasa, ya rage yawan surutu, ya daina walwala a tsakanin su, ya zama shiru shiru, sannan yafi son zaman daki fiye da falo.

Abin ya fara damun su mussaman Farida, ta yi tambayar duniya ya ce ba komai, Mk da ya gaji da yadda Farida take yawan damuwa da canjin Jawad ya ce "kifa daina damuwa, tunda dai ba wani abin aka masa ba, miskilin yaro ne na gaske, ni na yi mamakin yadda ya sake da ke tashi guda".

A marairaice ta ce "gaskiya akwai abin da yake damunsa domin ai ba haka ya ke ba, kamata yayi mu gano damuwarsa ko da cikin hikima ne".

Ranar alhamis da yamma, Mk da Jawad suna gida, yayin da Farida ta ke makaranta adalilin tana da lectures.

Cikin hikima ya hilaci Jawad akan ya ji me ya kawo changes din da suke gani a tare da shi, tunda bai fi sati da canjin nasa ba.

Cikin muryar kuka Jawad ya ce "Mamina! Na dade ban ganta ba, sannan tunda na zo bamu yi waya ba".
ya fada yana rushewa da kukan sosai.

Jikin Mk ya yi sanyi yasan Jawad ya yi kokari wattanni takwas da yawa, domin bai taba yin wata daya bai ganta ba, ko da yake hannun Hajiya duk karshen wata sai ya je ya yi kwanaki biyu.


Sannan tun farko yafi kulafacin uwarsa fiye da shi.

Jikinsa ya janyo shi yana fa'din ka yi shiru yau din nan zaku gaisa, ai da tun farko ka fa'da mini wannan ne damuwarka da tuni na magance maka ita.

Da kuka sosai Jawad ya ce "Am scared Malam".

Da mamaki sosai ya ce "Mai ya ke firgita ka?"

Last week na kalli wani firm a Fox movie (pendamic) yaron ciki ya tafi boarding school, shiru shiru bai ga mamar ta je ba, sannan baya samunta a waya Ashe she was died bai sani ba".

Kuka sosai ya sake barkewa da shi, zuciyar Mk ta dinga bugawa tamkar Sa'adatu ta mutu ne da gaske sune basu sani ba, domin yadda ya santa da Jawad bai zaci za'a shafe wannan wattannin bata nemi jin lafiyarsa ba.

Anya tunanin Jawad ba gaskiya bane?

Ya kasa cewa komai bare ya rarrashe shi wani irin abu ke masa yawo a jikinsa, ga dai sanyi a garin amma wata irin zufa ne ta fara karyo masa.

Ya dauko waya ya dinga gwada layin Inna amma sam baya tafiya.

Dabara ta fa'dowa Mk ya dinga lalubo lambar Zainab Ma'aji amma bashi da ita. Ya rasa yadda zai yi sosai Jawad ya firgita shi shima.

Da kyar ya shawo kan Jawad ya yi shiru bayan ya yi masa al'kawarin idan har ba'a sameta a waya ba, zai shirya musu tafiya Nigeria next week.

Duk kokarin Mk ya samu Sa'a a waya ya ci tura.
Tunda ko Baffah da ya mata maganar Jawad na ta cikiyarta ta daure ta kira shi su gaisa.

Kai tsaye ta ce "idan da rabon zamu gana zai dawo ya tarar da ni, Ni bazan kira shi ba, tunda ba shi da wayar kansa".

Daga Baffa har Inna ba wadda ya tilastata.

Mk da ya gaji da kiran lambar Baffah yana cewa tana Makaranta ko shi baya gida, sai ya kira layin Sumayya ya bawa Jawad suka yi magana yana ta mata kukan yana expecting Mami has gone.

Tausayinsa ya cika zuciyar Sumayya, ta dinga lallashinsa tare da al'kawarin daga yanzu zuwa kowanne lokaci zai ji muryar ta, tana nan cikin koshin lafiya.

Suna gama waya kuwa ta tura musu sabuwar lambar Sa'a.

Jikin Mk har bari yake wurin kiranta, amma sama da sau goma ta ki picking.

Tana kwance a dakinta tana kallon
Yadda Kiran ke ta shigowa.
A ranta tana fa'din har abada ban son jin ka, Jawad din ma na yafe maka shi".

Mintina goma sai ga kiran Sumaayya a layin Inna, ta dinga yi mata fa'da tamkar ta shigo ta wayar ta daketa, saboda itama ta kira layin nata bata dauka ba a tunaninta Mk ne.

"Iyah kalaman Jawad sun tayar mini da hankali tunaninsa mutuwa kika yi ake boye masa, idan kina haka har yanzu akwai kullin Mukhtar a ranki. Ki amsa masa waya Jawad ne zai yi magana da ke yafi sati yana cikin damuwar rashin ji daga gareki".

"Ni wlh Anty har Jawad din ma bana bu'katar jinsa ina masa addu'a, ina fatan ta zame masa garkuwa a ko ina yake".

Sumayya ta ce " To shi laifin me ya miki haba Iyah! Ki ji tausayi mana".


Da kyar ta shawo kanta ta yarda zata 'daga wayar.

Ba a jima sosai ba kuwa, 'Kiran ya sake fa'dowa wayarta.

Ta dauka ta yi shiru, sanin da Mk ya yi dabiarta ce ba zata fara yin magana idan ya 'kira a waya tun fil'azal sai bai wani damu ba, ya dinga yin sallamah, ya koma cewa hello nan ma shiru, ya mayar da wayar hand free, a tunaninsa jiyota ne ba ya yi. Yaayin da Sa'adah tsananin bacin rai ne ya kamata akan me zai mata magana, ya bawa Jawad din wayar mana.

Murya a sha'ke ta ce "Jawad!"

Ran Mk ya baci wato tana jinsa amsawa ne ba zata yi ba.

Amma a zuciyarsa ya samu nutsuwa kwarai da gaske da ya gane tana nan cikin koshin lafiya har ma tana da kwarin guiwar yin wulakanci, dan haka sai ya mi'kawa Jawad wayar a fusace.

Ya tsurawa Jawad ido yadda ya ke magana yana wani irin murmushi, ya sake kallonsa sosai yana ganin ba kammanin Sa'a tare da yaron illah wushirya da farcen hannayensa, inka dauke Wannan tamkar Mk aka raba biyu aka yi shi dan tsananin Kamar da suke yi.

Ya nisa ya tuno yadda Sa'adah ta tsaya a gabansa tana sheganta masa yaro, banda dai so baya shawara ai da bai kamata ya cigaba da son Sa'adah ba.

Ya muskuta yana kasa kunne yana sauraron hirar su inda ya ji Jawad na maganar da ta ja hankalinsa.

"Mami na tara ku'din da zai ishe ki zuwa, zan fa'dawa Malam zan zo na taho da ke".

Ya juyo murmushin Sa'a da yake kashe masa zuciya ta na cewa " A ina ka samu kudi?"

"Idan Malam ya bani bana kashewa, sannan munje gidan freinds dinsa na samo ku'di da yawa, kuma Anty ta je da ni gidan sister dinta nan ma anbani kudi duk na boye miki su".

Dariya ta kwacewa Sa'adah ta ce "Ka siyi abin da kake so ka ji Jawad! Kudin ba zai isa na zo ba".

Ya fara mata kuka yana cewa
"kudin fa da yawa Mami! a school ma da muka yi tseren gudu da quiz na zo na daya an bani kudi da yawa har da chain din gold, na boye miki shima".

Kukansa ya ta'ba ta sosai dan haka sai ta ce "To ka ai baka da kudin zuwa da na komawa, iya nawa ka tara ka bari sai ka sake tarawa sai ka zo ka dauke ni".

Cikin kuka ya ce "Zan fadawa Malam ya biya mini".

"To ka daina kuka, idan kana kuka, bazan yarda na zo ba, sannan ka bari sai anyi hutun school, dan kar a wuceka a karatu, kuma ko ba ka ji ni a waya ba, ka daina damuwa kasan Ni ma ina zuwa school, karatu ne yake boye ni, amma kullum ina yi maka addu'a".

Ya goge hawayen ya ce " Na daina kukan, idan zaki mini addu'ar, ki dinga addu'ar kudin nawa ya isa na siyi jirgin kawai. Kinga sai na yi ta yawo da ke har da su Inna da Hajiyar Bichi."


Suka dinga hira sosai, suna Shirin yin sallama ya ce na bawa Malam ku yi magana? shima ya damu da ba bamu same ki a waya ba".

Mk ya sake kasa kunne dan ya jiyo amsar da zata bayar.

"Ai mun gaisa kafin ya baka wayar, stay blessed my Boy".

Daga haka ta katse wayar.

Da wani irin kuzari Jawad ya mikawa Mk wayar yana fadin "thank you very much Malam".

Da zai karbi wayar sai ya hada da hannunsa ya janyo shi ya dora shi akan cinyoyinsa.

"Da sakakkiyar fuska ya ce " Me yasa ka damu sai Mami ta zo nan alhalin kasan bata son zuwan?"

Da sauri ya ce "Lah tana son zuwa fa, tana son ka mayar da mu gidanmu mu dinga kwana tare, da zamu taho na roketa ta biyo mu na san ba zaka yi fa'dan mai yasa ta zo ba".

Mk ya dinga jin wani iri, a karancin shekarun Jawad ya shaide shi ba zai wulakanta uwarsa ba, anya bai kamata ya sasanta da Sa'adah haka nan ba? Tunda ya lura a fili Jawad yafi son uwarsa akan komai.

A hankali Mk ya ce "To ya baku taho taren ba?"

Ta ce mini "Ba ita ka ce ta zo ba, Anty amarya ka ce ta zo, sannan bata da ku'din zuwa, na ce mata ai Baban Anti ne ya biya mana, shine ta ce ita Baffanta ba shi da kudin da zai biya mata!
Sai na ce to ni zan tara kudi na biya mata itama".

Jikin ya Mk ya yi wani irin sanyi, ya dinga jin kalaman yaron har cikin zuciyarsa.

A shekarunsa na goma sha'daya har yasan kishin uwarsa? ya tuna duk sadda ya samu kudi yake nacin shi zai ajiye abinsa ashe uwarsa yake yiwa tanadi? Ya nisa ya sake tuno lokacin da makarantarsu ta karrama shi da bashi chain din gold, da suka dawo gida ya shige dakinsa ya masa boyo na mussaman duk rarrashin da Mk ya yi masa akan ya kawo a ajiye masa, ya ce shi ya boye da kansa, ashe duk uwarsa yake yiwa? ba abin da ya tsayawa Mk a zuciya irin da Saadah ta ce wai ita Baffanta ba mai kudi bane.
Shiyasa 'danta ya kudiri aniyar ya tara mata kudi, dan ya huce mata takaici.

A ranar Mk ya ji ya yafe mata kaso sittin cikin kullacin da ya mata, ya samu saukin da zuciyarsa ta yi akan lamarinta, sai dai wannan tsoron nata da ya shige shi, bai ragu ba.
Ya lura idan bai bi a hankali ba, nan gaba ba karamin matsala Jawad zai bashi ba, mussaman da yana sane uwarsa tana son ya mayar da su gidansu, amma bai yi hakan ba.


***

Tunda suka yi shekara da aure ba labarin samun karuwa!

Farida ta fara jelen ganin gynecologist, duk wani gwaje gwaje anyi mata an tabbatar komanta lafiya kawai lokaci ne bai yi ba.

Zuwa wannan lokacin Mk ya samu budi sosai adalilin tallafin da gwamnatin tarayyar Nigeria take bashi, ga albashinsa, ga kuma wadda yake karba na gwamnatin kasar ingila. Bugu da kari ya na kasuwanci sosai, ya sake fadada shagunan askinsa, ya bude na shagon saida kayan maza masu daraja da kyau.

Dan haka ya kammala katafaren gidansa da yake ginawa akan hanyar zuwa sabuwar Jami'ar Bayero, fenti kawai ya rage da Yan kananun abubuwa da sai a shiga gidan za'a fi bu'katar su.

Gida ya yi kyau sosai, ya tuna Sa'a ce ta tsara yadda gidan zai kasance, a ransa ya gamsu Sa'adah tana da baiwar fashion and design hadi da creative.

Cikin abubuwan da Mk yake yawan tunawa ya Sha mamaki akan lamarin Jawad shine wani lokaci da yake daf da barin kasar ingila, ya fita da su shopping, shagon kayayyakin Mata da kananun Yara na alfarma suka je, Farida ta zabi dogayen riguna na alfarma da suka amsa sunansu, guda biyar ga turarenta designer na Amour amour, ta hada da wani dan kunne mai kawanya da alamunsa daham ne.

Kasancewarta bata amfani da kowanne irin mai sai veseline ta cakude shi da gilasirin, tafi bada karfi a shower gel.

Jawad na tsaye yana kallonsu. Mk ya juyo ya ganshi a tsaye bai dauki komai ba, ya kalleshi ya ganshi tsaye ya rungume hannunsa a kirjinsa.

"Jawad baka dauki komai ba".
Ko sai mun je wani mall din?"

Ya girgiza kai ya ce "I thought Anty ce kawai zata yi shopping yau".

"Kaima ka duba duk abin da kake so ka dauko"

Suna tsaye suka hango shi rungume da dogayen riguna irin na Farida sai banbancin kaloli guda hudu, sai takalma na mata masu tsananin tsada kafa biyu, dukkansu kirar kasar itali, ya ajiye gurin buga kudi, ya wuce ya dauko zobe guda daya da ya kusan ninka Dan kunnen Farida.

Mk ya kalle shi ya ce "Me zaka yi da wannan kayan? "

Ya shagwabe fuska ya ce "Malam so nake yi ba kai ka ce na dauko komai nake so ba?"

"Na fa'da amma ai naka na ce ko?"

"Malam ni wannan nake so a maimakon nawa, kaga rigunan Nan tsaraba zan yi da su, daya Antyn Lagos, daya Maman Gombe, daya kuma Anty Samira".

Mk da Farida suka zuba masa ido domin kuwa wadda duk ya ambato zai bawa Mk bai isa ya ce komai akan su ba.

Ya ce " Amma Jawad wadannan sunyi kudi da yawa".

Ya kwakkwabe fuska ya ce Ni dai su nake so Malam"

Mk ya ce "To wadannan ragowan rigar da takalman da ka kwaso fa, kasan ku'din takalmi daya ma kuwa?"

Kai tsaye Jawad ya ce "Mami zan siyawa a kudina tunda bata zo ba".

Mk ya yi shiru ya ce "to ai kudin naka ba zai isa ba, sai ka mayar da zoben".

Ya ce "Ka cika mini ko ka ara mini ni dai ina son su".

Kan dole Mk ya biya kudin kayayyakin nan, wadda ba karamin jijjiga asusun ajiyar sa yayi ba, hatta Farida sai da abin ya mintsine ta, ta lura kusan kullum idan suka fita siyayya irin haka sai Jawad yasan me ya siyo wa uwarsa, Mk kuma baya iya tsawatar masa, kafin su tafi ta san ba karamin kaya zai tara mata ba.

Kawai shanyewa take bata ta'ba bari abin ya bayyana ba, Amma abin na tsaya mata a Rai, sai dai ana jimawa take kokarin mantawa.

Mk bai sha mamakin Jawad ba sai da ya bishi dakinsa ya ga ya dauko katuwar ledar da yake tara kayan da yake siyowa da sunan Iyah kayayyaki ne masu tsadar gaske.

Ya zauna a bakin gado ya ce "to kawo kudin da kace na ara maka, tunda ai kasan ciko mai yawa na yi maka"

Haka kawai Mk ya fada Jawad ya fashe masa da kukan shi kudinsa Mami zai siyawa jirgi tunda antaho anbarta a gida kuma Baffa bashi da kudin da zai biya mata.

Jikin Mk ya yi sanyi ainun ya kasa cewa komai, da kyar ya ce "Ai ba a haka Jawad! kenan wayo ka mini? Kullum ka yi ta fa'din jirgi za ka siyawa Mami ko zaka biya mata, amma ni ko keke banji kana cewa zaka siya mini ba, alhalin na fita sonka".

Yana goge idonsa da rigarsa ya ce "Zan siya maka Malam amma dai ka yi ha'kuri na fara yiwa Mami, kai kana da ku'di, Baban Anty yana da kudi, ita kuma basu da kudi".

Mk ya ji haushin Sa'adah ya cika masa zuciya na yadda ta zauna ta yi maganganu da yaro 'dan karami, gashi maganar ta shiga zuciyarsa ainun, ya tsinci kansa da fadin "me za'a yi da halin wannan yarinya".

Jawad ya ce "wacece?"

Ga mamakin Mk sai ya kasa cewa Sa'aadah, sai ya buge da fadin "wata fitananiyar student dina ce mai baudadden hali, mai wuyar sha'ani".

Haka suka cigaba da rayuwar su har wa'adin da Mk zai yi a kasar ya cika. Ya tattara ya taho ya bar Farida da Jawad tunda ita saura wattani uku suka rage mata, Dan haka ya bar mata Jawad dan shima ya kammala third term dinsa.

Duk juyin da Mk ya yi da jawad ya bashi kayan tsarabar sa da ya tara cikin katon akwati, baisa ya bayar ba, ya ce shi da kansa zai taho da kayansa domin ba ya so a kaiwa Sa'adah kafin ya dawo.

Har Suka kammala watan ukunsu Jawad ba ya bata matsalar komai, sai duk sadda suke hira Rabin hirarsa kuwa ta uwarsa ne.

Da azahar Suka sauka a Kano.
Kai tsaye gidan Hajiyar Bichi suka zarce suka samu kyakkawan tarba daga Hajiya ga abinci ta tanadar musu ba karmin mamakin girman Jawad ta yi ba

Ta kalle shi ta ce yanzu a shekaru biyun nan ka yi wannan uban girman wa zai ce shekarunka sha biyu?".

Yamma na yi Mk ya dauki Farida zuwa gidansa da suka zauna da Sa'adah, bai san me yasa ya kasa shigar da ita wanccan gidan da Sa'adah ta tsara shi ba, sai ya gyara ainihin gidansa. gaba'daya gidan ya sha gyara na mussaman hatta fasalin ginin ancanza shi ya zama mai upstairs (bene) an mayar da shi na zamani kwarai da gaske , haka nan ba karamin jere na garari aka yi wa Farida ba. Duk wadda ya shiga gidan sai ya burge shi sosai saboda tsarin ginin tamkar gidajen turawa.

Duk yadda Mk ya so ya tafi da Jawad Hajiya kin yarda ta yi ta ce "Ai dama daga nan gidan ka dauke shi, dan haka dauki matarka kuje ta huta gajiya, sosai Jawad ya yi murna da hakan domin yasan goben nan zata sa Uncle Ahamad ya kai shi wurin Maminsa.


Leda guda Jawad ya ajiyewa Hajiya na tsarabar ta ta dinga murna tana fadin "Na san zaka yi Imani Jawad".


Washagari kuwa Hajiya tasa Ahamad ya kai shi da katon akwatinsa da sai da ya nunawa Hajiya duka kayan ciki, ko kadan bata yi ba'kin cikin uban kayayyakin da Sa'adah ta samu ba, a ranta kuwa murna take yi tana fa'din "Haihuwa wadar sarari ko kana gudu haifi ka Yar".


Murna soasai Sa'a ta yi tana fa'din "ai Ni ka yiwa tafiyar nan Jawad, ubangiji ya raya mini kai, ya maka albarka mai yawa".

"Amin Mami" ya fada yana kwanciya a jikinta, tare da sake cewa "kina addu'ar na samu kudin ya kai na siyan jirgin naki kuwa?"

Inna da take gurin ta ji Hawaye na neman kwace mata, ta mike ta shige dakinta, tana jin dadi da tausayin yadda Jawad yake girmama lamarin uwarsa.


Dawowarsu Nigeria ya sake wayo sosai, aka saka shi a makarantar Intercontinental college tsananin hazakarsa yasa suka dauke shi J s 3, maimakon aji biyu da zai shiga.
Iya turanci gangariya da Jawad ya yi ya janyo masa farin jini ainun a gurin malamai hatta student son abota suke da shi.

A haka ya Saba da wani dan ajinsu Muhsin Sani Yar-gaya, a hirar su da Muhsin Jawad ya fahimci Malam da Mami sun rabu ne, wato divorce ne a tsakanin su.

Kusan Muhsin ne ya cusa masa dabi'ar kin Farida a dalilin shi Muhsin din mahaifiyarsa ta rasu shekaru biyu, sannan amaryar Baban su

Please Login or Register in order to submit comment