You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsinuwar mala'iku ne akan ki.
Haka kawai sai kin janyowa kanki ya gama zumudin ki, a titi, ke dai naga sadda zaki yi aiki da lura".

Kunya ta kama Sa'adah! Amma ta waske da cewa."To yanzu Inna sai a sake kai ni ba kayan d'aki alhalin yanzu Ina da kishiya?"

Ta fa'da a shagwabe.

Dake Innar mace ce nan da nan ta yarda da ra'ayin Sa'a na bai kamata ta je babu kayan d'aki ba alhalin tana da kishiya diyar masu kambun susa.

Ta nisa ta ce " Bari Baffan ku ya zo sai a siyar da dayan filin da ya rage, sai ki hada da albashinki na watan nan tunda ya raba tsakiya, ki yi abida ya sauwaka ayi tariyar nan cikin girma da arziki".

Ta turo baki gaba Inna ki bari dai nan da wata uku, kinsan ai na ce na barwa Baffah kyautar filin, yanzu kuwa ai ba zan koma na ce na fasa ba".

To kayan Baffanki ai naki ne, Ina jiye miki tsiyar namiji Iyah! Muutar din nan fa na riga da na gane shi bashi da kunya ko ka'dan, ba abu mai wahala bane a gidan nan ma, ya yi abin da ya ga dama tunda Baffanku ya daukake shi ba ka'dan ba".

****
Kwanakin mako da zuwan Mk wurin Sa'a har yau bai sake zuwa ba, bai kuna yi mata waya ba, abin da yake ta cin ranta kenan, ya sake tunzurota, idan bata tare ba, ai dai tana da hakkin ya duba lafiyarta, wato ya kawo mata kayan abinci saboda ita ci kawai ta sani da kwalliya.

A na cikin haka wata waki'ar ta kunno a jahar Sokoto inda aka samu matasa sun kasa ha'kurin hukuma ta dauki doka, saboda an tabowa musulmi inda basa iya ha'kuri matu'kar aka tabo wannan matsayin.

Dukkan hankalin musulmai a tashe yake an zuba ido, an kasa kunne domin aga irin hukuncin da za'a yiwa wadannan matasa.

Kungiyoyin musulmai kashi daban daban sai kiraye kiraye ake yi akan akaiwa matasan nan dauki.

Kungiyar lauyoyi musulmai reshen jihar Kano ta bawa wadanan matasa lauyoyi hamsin da suje su harci zaman kotun da za'a yi a gata, su kuma basu kariya.

Cikin wadanda aka tura har da Sa'adah.

Baffah da Innah sai murna suke yau ga yarsu zata je ta kare martabar Ma'aiki, ilimin Iyah bai musu da'di iri a wannan karon ba."

Da murna Baffah ya ce " yaushe zaku tafi?".

"Jibi zamu tafi, dan mu sami zaman kotun, tunda gata da sassafe za'a fara shari'ar".

"To ki 'Kira mijinki, ki sanar da shi, tunda dai ba zaki yi tafiyar bai sani ba".

Ta amsa da to badan ta so ba.

Tun yamma take kiransa yana gani, amma ya yi biris, bai dauka ba,sai bayan magariba wadda hakan ya sake fusata, Sa'a ta botsara.๐Ÿ˜„

Ya dauka, amma ta yi shiru, sanin da ya yi dabi'arta ce ba zata fara yi masa magana a waya ba. Sai ya ce "Ina jinki, na ga 'kiranki rututu, kin gama mini shirin ne, na zo na dauke ki.?"

Ba'kin ciki ya tokare mata wuya, wato shi a haka ya barta ma?

Ta daure ta ce "Dama Sokoto zani".

"Sokoto zaki je?"

"Eh" ta amsa a ta'kaice.

"To ba zaki je ba".

Daga haka ya kashe wayar ya barta da waya a kunne.

Ba'kin cikin da ya turniketa ba'a magana.

Hawaye ya kwace mata.

A hakan Baffah ya shigo ya sameta, ta fada masa abin da Mk ya ce.

Baice komai ba, ya fita waje.
Ya 'Kira Mk a waya, ya ce "lallai ka zo ina nemanka".

Mintina ka'dan ya iso tunda dama yana cikin shagonsa.

Ko gama gaisawa ba su yi ba.
Baffah ya ce "Iyah ta ce wai ba zata je sokoto ba?"

Ya sauya fuska ya ce "Eh haka na fa'da mata Baffa?"

Ai kuwa Baffah ya dauki salati yana fadin "Lallai kuwa, ka bani mamaki, ana tsayawa garabitin mutane a gaban shari'a, balle a taba janibin Ma'aiki. Ai kuwa shine mafi tsayawa a kare darajarsa."

"Da wata irin murya mai nuna mutun na wurin da zai yi shagwaba son ransa.
Mk ya ce "Baffah sanar mini fa kawai ta yi, ba wai izini ta nema ba".

A wannan karon ko ka'dan Baffa bai karbi uzzirin Mk ba, kawai umarni ya bashi akan lallai ya barta taje ta wakilce su, wurin bawa Ma'aiki kariya.

"Shikenan Baffah zata je, amma ban yarda ta yi tafiyar nan cikin kungiya ba, ta jira zan zo na kaita, idan sun kammala na dawo da ita"

"Yauwa Ubangiji ya maka albarka, ya kore shaidanun da suke ta tunzuraku, Suka 'ki su barku ku gane kun girma".

Mk Yana dariya ya ce "itace ai yar burutsa".

Baffah ya taya shi dariya sosai ya ce "Kai kuma baka iya rarrashinta ba".

"Hmmm Baffah ai ba zaka gane ba".


***
A lokacin da Baffah yake bayanin Mk ne zai kaita, Inna hankalinta bai kwanta ba gaba'daya, amma ba yadda za'ayi ta hana ta zuwa wannan shari'ar domin ba karamin daraja bane ace ka samu damar bawa Annabi kariya. Sannan kuma mijinta ne da shari'a ta bashi damar ya tafi da ita duk inda ya so.

Yayin da Sa'a ta ji takaicin wulakancin da Mk yake mata, zata bishi suje, Amma ko shine 'kuda wurin naci sai dai ya kalleta kawai, ba zai yiwu ya shareta na sati guda, sannan yanzu ya ce "tare zasu tafi ba".

Haka ce ta kasance lafiya Lau suka isa Sokoto. A hotel ya kama musu daki, ya dinga tuno moment dinsu a tafiyar da suka yi Abuja, a wanccan lokacin ba karamin hutawa da soyayya Suka sha ba, amma wannan karon ta yi kicin kicin da fuska, ko kallonsa bata yi.

Haka suka kwana! da wuri suka nufi kotun, ta shige cikin tawagar lauyoyi, shi Kuma ya zauna a sahun masu kallo, duk kuwa da an tsaurara matakan tsaro kwarai da gaske.

Da azahar suka bar kotun, saboda yadda aka 'daga Shari'ar zuwa wattanni biyu masu zuwa.

A hanyar su ta komawa ya ce "ba wadda zaki kaiwa ziyara ne a Sokoto?".

Fuska a daure ta ce idan ina da su kaini zaka yi ne?"

Da sauri ya ce "Eh Mana ranki ya Da'de, to menene aikina idana ba direbanki ba?"

Ta tura baki ta ce "Humaira Suraj da muka yi F.G.C anan take aure sai dai bani da contact dinta".

"Amma bari na kira uwar dakina idan tana nan ta mini kwatance muje mu gaisheta".

Da kulawa ya ce "Wacece uwar dakin ki ?"

Da murmushi ta ce "uwar marubuta, da makaranta da kuma marubuta masu tasowa, Umman mu Hajiya Saliha A.A Zaria."

Dariya sosai Mk ya saka tare da cewa dadina da ke ri'ke alakawari! Na tuno sadda kike karanta mini littafin Yarda da kaddara kina fa'din yadda Abba lawal yake yiwa Asama'u zan dinga yi Miki. Dole kam muje nima zan gaisheta, domin littafanta no yasa na samu tagomashi a wurin Sa'ade nah".

Ta yi masa shiru.
Ta fido da waya bugun farko Umma ta dauka, tare da cewa "maraba da diyata Sa'adatu".

Soasai Sa'a take jin da'din karamci da mutuntata Dan adam da Umman Sokoto take yiwa masoyan litttafanta, komin 'karancin shekarun mutum kuwa.

Cikin farin-ciki Sa'a ta ce "Gani a Sokoto, kuma ina kan hanyar zuwa gidanki dan gaisuwar girma.
Dadi ya kama Hazi'kar marubuciyar mu ta ce "na gode miki Sa'adah, ubangiji ya kawo ku lafiya.

Haka kuwa Mk ya tsaya ya tambayi adireshin da ta turo musu, ba wahala suka isa.

Murnar da Haj Saliha ta yi, ba yar kadan bace, a lokacin Sa'a da Mk suka gane ashe alherinta da suke ji a waya ba komai bane, sai ka ga zahirinta zaka san ita din Ummul khairi ce.

Ta dinga yi musu nasiha da jan kunne kan hakuri, da kuma gwaggaban ladan da mai yinsa ke rabauta da shi.

Da zasu ta fi ta bawa Sa'a abu a leda da ba tasan ko menene ba, ita kanta Sa'a da aka bata, bata kula da sadda ta ru'ko hannuta ta saka mata ba, saboda tsananin yadda Umma ta iya karrama dan Adam.

Suka tafi cikin Jin da'di kusan saboda nasihar da Umma ta yiwa Sa'a yasa, ta biyewa Mk a hanya suka yi ta hirar arziki, suna ta yiwa Haj Saliha addu'ar samun lafiya da nisan kwana mai albarka. Hadi da yiwa iyalanta addu'ar shiriya da tsari daga dukkan abin ki.

Ya ce sai "Ina kuma".

"Sai gidan kawar Anty Sumayya!
Anty Zalihatu Umar,
da k'awata Hauwa'u Umar matar Nasir,
Shinenan".

Ya ce "angama Hajiyata".

Haka yayi ta kewaye da ita tana samun karamci daga wurin mutanen Sokoto da basu san komai ba sai alheri.

Sai maghrib suka isa hotel dinsu. Ya dawo daga sallah isah, ya dinga yi mata rawar da lallashi kala kala, amma ta yi funfurunfus ta 'ki ko da kula shi, balle ta bashi hadin kai.

"Ashe duk nasihar Umma ta bayan kunnen ki ta bi? Duk yadda na gama yawo dake a gari, dan ki mini yadda nake so, sakayyar da zaki mini kenan?
Wallahi cikina ciwo yake yi, marata a daure take, ki yiwa Allah ki bani dama, ban son na yi miki dole plz my Sa'a".

Ko motsi ta ki yi balle ta tanka, ya gaji ya kwanta a gefenta, yana ta murkususu.

Can kamar awa daya ya kasa hakuri ya janyota, ya fara shafata, ta yi firgit ta tashi, ta fizge, ya kalleta ya gano har yanzu rarrashi baya tasiri akanta, dan haka ya bita ya danne yana jin komai zai faru a yau kam sai dai ya faru amma ba zai 'kyale ba.

Ya fara kici kici da doguwar rigar atamfar da ta sanya, wadda ta kamata soasai, amma dan ta takura shi, yasa da ta yi wanka ta daukota a akawatinta ta sanyata a daren ta kwanta da ita.


*Gashi nan har da na gobe*


SURAYYA DAHIRU.
โœ๏ธ.

*HALIN YAU*!

*NA*

*SURAYYA DAHIRU*.


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ยฎ_* โœ๏ธ
โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€โ”€
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ษ—amfare da bin ฦ™a'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
____________(โœช)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916




*Ga Dukkan daliban UNITY KACHAKO*
*Mussaman aji na 2008*.
*Fatan alheri a duk inda kuke.*


*Sakon taya murna ga dukkan ahalinmu bisa samun karuwar 'Ya mace da muka yi a ranar alhamis 21-7-22.*
*Ina addu'ar Ubangiji ya Raya Rabi'atu akan tarfin islama, ya albarkaci rayuwarta. Allah ya bawa mahaifiyarta lafiya, ya bawa Mahaifinta ikon kulawa da su*.

*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.


109-110.


Duk kokarin Sa'a ta kasa kwatar kanta a hannun Mk! Domin gaba'daya a rikice yake, ba zato ta ji yasa dukkan hannuwansa da 'karfinsa ya keta rigar nan, wadda sabuwace ko ruwa bata shiga ba.
Haka ya cire mata tare da yin wurgi da ita.

Ya matu'kar jigata kafin ya samu, ya isa inda yake nufin isa, saboda yadda ta ki bashi hadin kai ko kadan. Sai da ya gwada mata karfin kwanji.

Ya matu'kar jimawa yana abu guda, ba karamin kidima ya shiga ba, a lokacin da ya zo samun nutsuwa, saboda yadda ya ji wata irin jijjiga tunda kansa har kafarsa. Karshe ya kammala cikin kuka tamkar ba Namiji ba. Dukkansu kuka suke yi, mai tsuma zuciya, na Sa'a mai sauti, na Mk kuma hawaine zallah, na tsananin farin-ciki, ya da'de yana ro'kon ubangiji ya sake nuna masa lokacin da zai kebe da Sa'a a matsayin miji da mata.

Gefe kuma takaicinta ne ya kama shi na yadda ta wula'kanta shi, tamkar bata san shi ba, duk irin ro'konta da ya yi.

Ya yi shiru yana jin kukan da take tamkar wadda ba aure suka yi ba.

Ba'kin cikin ke nukurkusarta, mussaman idan ta hararo haka fa yake yiwa Farida.

Ta kasa daina kukanta, shikuma Mk wani irin zazzabi ba zato ya saukar masa, tun yana daurewa har hakoransa suka fara kadawa, jikinsa ya dinga bari.

A farko share shi ta yi, sai da ta ga tabbas jikin ne, tasa hannunta, ta ji zafi sosai a jikinsa, ga hawaye sai zubo masa suke yi.

Ta yun'kura ta laluba akawatinta ta dauko rigar barcinta ta saka, ta debo ruwa, tare da 'karamin tawul 'dinta, ta dinga goga masa a jiki. Hankalinta ya matu'kar tashi, ba ta san har yanzu haka son Mk yake da karfi a zuciyarta ba, sai da taga yana zazzabi nan, saboda gaba'daya jijjiga yake yi.
Damuwarta ta kai kololuwa, ta dinga jin inama ita take wannan ciwon shi kuma yana jinyarta.

Ta dauko paracetamol ta bashi da kyar. Tana hawaye, tana tofa masa addu'a.

Mk bai samu sassauci ba sai wajen 'karfe biyun dare. Barci ya yi awon gaba da shi.

Sai da ya yi barcin sannan itama ta kwanta kusa da shi, hannunta rike da nasa hannun.

'Kiran farko akan kunnensa, ya tashi baya jin ciwon komai sai kasala, ya jima yana zaune yana kallon yadda take barci, tana sauke numfashi a hankali. Gashinta da ya sha gyara, yanzu duk a hargitse.

Wula'kancin da ta yi masa na rashin yarda da shi a farko ya matu'kar tayar masa da hร nkali, zuciyarsa tana gasgata sonsa ne da gaske ba ta yi a yanzu.
Amma damuwar da ya gani a fuskarta a lokacin da bashi da lafiya, ya fahimci sonsa take da dukkan zuciyarta, kishi ne babban matsalar da idan ba'a yi taka tsan tsan ba zai sake ruguza musu rayuwar aurensu a karo na biyu.

Ya kudiri aniyar yi mata addu'ar samun sassauci akan kishinsa da take yi da ya wuce ka'idar Sharia da mizanin hankali, tunda ko aka ran kanta ba zata ji dadin rayuwarta ba.

Da kyar ya sauka ya shiga bayi, ya yi wanka, ya doro alwallah, sai da ya yi nafila, sannan ya tashe ta, ya fice zuwa masallaci.

Ya dawo, ya tarar da ita zaune akan sallayah da hijab a jikinta.
Ya cire jallabiyar jikinsa, ya kishingi'da a bakin gado, tana daga zaune a inda take.
Ta ce "Ina kwana, Ya jikin?"

A hankali ya amsa da cewa ", Lafiya lau Alhamdulillah".

Daga nan kowa ya yi shiru, sai tunanin zuci suke yi.

Tsawon lokaci kafin ta ji ya yi gyaran murya ya ce "Yau nake son mu tafi, amma jikina babu kwari, ba zan iya tukin nan ba".

A hankali ta ce "Ubangiji ya baka lafiya, sai mu jira zuwa gobe, mu ga mai zai zartar."

Ya yi shiru! Yana kallonta, yana jin sonta da tausayinta suna neman kassara shi.

A hankali ya ce "sanyi nake ji, da sauri ta mike ta fara kokarin ware bargo, Dan ta rufa masa.

Ya kalleta ya ce "Ba shi ba".

Zuciyarta ta buga, ta sani tun fil'azal idan yana zazzabi, sai dai ta cire kayanta ta mannu da shi, dumin jikinta shine maganin sanyin da zazzabi ke sababa masa ji.

Ta yi sororo bata san me yasa a duk sadda ya nemi ta'ba ta ba, sai ta ji wani irin bacin rai ya taso mata ba.

Tsayuwar da ta yi, yasa shi fahimtar abin da yake son ta yi masa ne, ya sake sanyaya jikinta.

Ya waske kamar bai gane halin da take ciki ba, ya sake cewa "Dan Allah".


A sanyaye ta cire rigar jikinta, ta bar pant dinta, ta isa gare shi, ta kwanta, ya yi mata wata irin runguma mai tsananin gaske.

Suka dinga sakin ajiyar zuciya! Ya dinga rada mata "Hold me tied please".

Amma Sa'a ta kasa yin komai, saboda rashin sukunin zuciya.

Tana jin yadda ya gyra kwanciyarsa ya fara laluben kirjinta da bakinsa, kan dole ta kyale shi ya zama tamkar sabon jariri saboda yadda yake tsotsar su.

Jikinta gaba'daya ya amsa, sai tsuma take yi, shi kuma rashin 'karfin jikinsa ya masa cikas din tafiya second round ko da ta 'karfi ne kuwa irin na daren jiya. A hakan da suke barci ya yi awon gaba da su.

9:18am dai dai Sa'a ta bude idonta, har lokacin kuma Mk barcinsa yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Fuskarsa na manne da kirjinta sai ka rantse baya samun iskar zukar numfashi.

A hankali ta zare jikinta, ta mayar masa da filo gurbinta, kamar yadda take yi masa a baya.

Bata tsaya a ko'ina ba sai a bayi, kai-tsaye ruwa mai zafi ta ha'da, ta yi wanka sosai, ta fito, ta shirya cikin matsakaiciyar kwalliya, ta zauna akan stool ta kasa daura dankwali saboda yadda take jin tsananin yunwa.

Bata son tashinsa, gashi kuma ji take tamkar ta ci babu saboda tsananin yadda cikinta yake yi mata karta.

Ta dauko hijabinta ta saka, ta dauko jakarta, ta nufi kofa da nufin fita ta nemi abinci.

Ta bude kofar kenan ya tashi, da azama ya ce "Ina zaki?"

Ta dawo da sauri ta ce "yunwa nake ji, tamkar an mini yasa a ciki".

Ya bata rai sosai ya ce "shine dalilin da zaki dauki hijab ki fita babu izni, alhalin kina kallona, Wai ke wanni irin raini kika mini ne? Ke ce zaki fita siyan abinci? Karatun naki abinda ya koya miki kenan?"

Ta yi shiru, ta kasa cewa komai. Idonta ya ciko da kwalla.

Ya ja tsaki ya mike ya shige bayi.
Bai wani jima ba ya fito, amma ita sai ta ga tamkar ya kusan awa guda.

Jallabiya ya zura ya dauko wallet din sa ya fice.

Mintina Kamar biyar, ya dawo dauke da ledoji a hannunsa.

Ya tarar da ita tana kan stool din mirror tana faman goge hawaye da tissue.


Ya ajiye ledar a gabanta ya ce "gashi sauko ki ci".

Ta yi tamkar ba ta ji shi ba, shikuma ya shige bayi, ya fara wanka.

Amma da yake yunwa ba kanwar uwa ba ce, sai ta sauko, ta hau duba ledar.

Leda daya dankalin turawa da kwai ne, 'dayar kuma doyace da aka soyata cikin kwai. Sai kuma leda mai dauke da daurin kunu biyu, na gyada da na tsamiya.

Doyar ta hau ci a yunwace, kafin ya fito ta cinye tass, sai ragowan kunun tsamiya a hannunta da take shirin zuke shi.

Sai da ya shirya, sannan ya zauna yana cewa "yanzu duk doyar nan kin cinye ke ka'dai, yaushe kika zama mai cin abinci haka? "

Takaici yasa ta cigaba da matso kwalla ta na gogewa, shikuma ya hau cin abincinsa hankali kwance, yana jin wani irin shau'ki. Bai san me yasa iskancin Sa'a ke tafiya da shi ba, ya lura a yanzu bata da burin kayayyakin 'kawa, ba ta harkar kawaye, cikin dabi'unta masu Muni kaifin harshe ne ya rage mata, shima kuma dole ta rage indai tana gabansa.

Amma sakalci, sai ya ga tamkar tana girma, yana sake bin jikinta ne. Ya tabbatar har kukanta yana jerin abubawan da yake kewarsu.

Sai da ya kammala ya dubeta ya ce " ke kam kin ji kunya wallahi! Ai bai kamata ki tisa ni gaba kina mini kukan shagwaba ba, tunda dai jiya ba irin ro'kon da ban miki akan ki taimake ni ki mini abin da zan samu nutsuwa, amma ki kika shafawa idonki toka. Sai dai kuma na nuna miki ba zanci gaba da zuba miki ido kina mini iyashege ba. Da ace kin ji rarrashin da na miki, da kin ga yadda zan tarairaye ki, na lallashe ki, amma yanzu ko bubburwa zaki yi ba ruwana da ke, bare na san kina sakalcin banza".

Da rawar murya irin tana gaf da fashewa da kuka ta ce "kin yarda da na yi da kai ya isa ka gane sonka ne ba na yi, haka karfin da ka gwada mini, da har yanzu nake Jin ciwo a inda ka bubbbga mini guiwar hannunka ya almata mini kaima sha'awa ta kawai kake yi, amma ba so ba".

"Eh bana son ki".

Ya bata amsa a ta'kaice.

Ba'kin ciki ya turniketa ta ce "Allah ya kawo zazzabi anjima zaka gane lalle nima bana sonka".

Ya ma'ke kafada ya ce "Ameen! Ciwo na kan kowa, nawa ya yi kyau ai. Kema kuma na ki na tafe, domin ciwo ai ba a fatansa, idan yau kaine, gobe na ga waninka. Idan ubangiji ya juya abin ya dawo kanki, a lokacin zaki gane tsiyar ki ka'dan ce".

Ya mike ya na cewa "To ni kam dama kwanaki uku iyalina ta san zan yi. Yau kam ko hayar direban da zai tuka ni zuwa Kano, zan yi, bare kuma Ina fatan ubangiji ya bani ikon tukin da kaina.
Don bana cikin mutane masu yiwa masoyansu 'karya ko butulci, ko danne musu hakkin su".

Zuciyarta ta buga da tsananin gaske, ta san shagube ya yi mata, sannan kai tsaye yake nuna mata yau gurin Farida zai kwana, domin kwana ukun da ta bashi ya cika.

Haka suka dawo Kano, ba wani jituwa a tsakanin su.
Ya sauketa a kofar gidansu ya ja motarsa ya yi gaba.

Tunda ya ajiyeta yake jin tamkar ya rusa ihu, shi dai ko zasu kwana suna Yar tsama yafi son ya ganta a kusa da shi, ko da ba zata kula shi ba, haka nan shima ko ba zai mata maganar ba, amma dai ya ganta kusa da shi shine samun nutsuwarsa, ko shareta da yake yi, Karfin hali kawai yake yi da son kwatar kansa a hannunta, tunda ya san halin iyashegenta.

*Bayan sati biyu*

Tunda Suka dawo kullum Mk sai ya Kira Sa'a a waya, sau tari bata dauka, ranar da ta yi niyya ta dauka, to kuwa zai ta yi mata magana ne, sai ta yi kamar bata ji shi ba.

Bai yi fishi ba, a hakan dai yake 'kiranta, zuwa ne dai ba ya yi. Wani lokacin ma zai je shagon Baffah su sha hirarsu, amma ba ya neman Sa'a.

Suna cikin haka tafiya ta same shi zuwa jahar Akwa-ibom. Zasu yi wani bincike a Jami'ar jahar na tsawon wata 'daya.

Ya gama lissafinsa ba zai yiwu ta tafi da Farida ba, domin aikinta ba irin wadda za'a yi masa shan ruwan tsuntsaye bane.

A zuciyarsa yafi dokin tafiya da Sa'a tunda dai har yau bata bashi dama ba, ko waccan ma, da tsiya tsiya aka yi, shikuma so yake, ayi da yardarta da amincewarta, ta yadda zata shayar da shi kalololin soyayyarta masu gigita shi.

Saura kwanaki biyu ya yi tafiyar ya iske Sa'adah a gidan Sumayya.

Suna zaune a falon mai gidan.
Ya sassauta murya ya ce "Tafiya ce ta same ni, zuwa south, shine nake son ki yi mini rakiya, zan jima domin zan shafe akallah wata guda".

Ta girgiza kai ta re da cewa "ba inda zani".

"Umarni fa na baki".

"Gaskiya ba zanje ba, tunda dai ban tare ba, umarninka baya kaina, ka je ka tafi da wadda idan ka yi tafiya baka wuce adadin kwanakin daka fa'da mata zaka yi, saboda sonta da isar da ta yi.

Ya numfasa tare da mikewa yana cewa "na gode sosai da wannan shawarar, ya ajiye mata kudi masu auki, ga su nan ko wani uzzirin zai taso miki, sai na dawo".
Har ya kai bakin kofa, sai kuma ya juyo, ya kalleta ya ce "zuwa yaushe kika shirya tarewar?"

Kai tsaye ta ce "idan abin da nake so ya samu nan da wattanni hudu".

Ba'kin ciki ya kama shi, amma sai ya yi nufin su raba bacin ran tare ya ce "To kawai a barshi a rabin shekara mana, wattanni shida kenan"!

"To kawai mu bar shi a shekarar kawai".

Ta fa'da a kufule sosai.

Ya yi tafiyarsa ba tare da ya sake cewa uffan ba".

Sai itace tana ganin fitarsa ta fashe da kuka sosai, tana gasgata da gaske ne yafi son Farida akanta.

Mk yana tuki amma a fili yake cewa " Ubangi ka mallaka mini zuciyar Sa'adatu da tunaninta, Allah ba zan iya ba, kaine mai sarrafa zukatan bayinka, Allah ka hore mini wannan yarinyar da take neman manna mini hauka, bayan hawan jinin da nake fama da shi adalilinta!
Kai ka jarrabi zuciyata akanta, ubangiji kar ka jarrabe ni a cikin hankalina da tunanina akan sha'aninta".

Haka ya tafi Uyo shi ka'dai tamkar ba mai mata biyu ba, amma a kullum yana ro'kon ubangiji akan a mallaka masa tunaninta tamkar yadda aka mallaka masa zuciyarta, hakanan duk sallar duniya sai ya roki Ubangiji akan a sassautawa Sa'adah kishin dake neman jefasu yanayin da yake tunanin sun yi bankwana da shi.

Satinsa biyu da tafiya Wanda ya yi dai dai da watansu daya da dawowa daga Sokoto.

Sa'a ta kasa gane kanta, bata ciwon komai, amma yini take tana zubar da miyau, da ta

Please Login or Register in order to submit comment