You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zata yi rainata ta yi shiyasa zata doke shi akan idonta.

Cikin Sa'a Jawad ya ankara da
yadda ta tunkare shi a fusace, ai kuwa ya kwasa ya yi gate a guje, ba'kin ciki yasa ta bishi itama.

Suna fita suka yi kicibus da Mk a waje zuwan sa kenan parking ya gama yi.

Ai kuwa ya ruga ya buya bayan Babansa.
Mk ya ri'ke shi yana fa'din "menene?"

Ya kalli Sa'adah da take hawayen takaici, tana rantsuwar sai ta dake shi.

Jawad ya ce " yau zan bika mu tafi Malam kar bar ni anan duka na zata yi"

Mk ya daure fuska ya ce " me ka yi mata?"

Jawad ya turo baki gaba irin na gado ya ce " wani gajeran mutum ta ce na gaisar shine na ce ai ba uba na bane.
Shikenan zata doke ni, Ni kuma bana sonsa ne, haushi yake bani, I hate him so much".
Ya fa'da da karfi tare da buga kafa.

"Kar ka bari ta doke ni Malam domin ni sonsa ne bana yi, ba laifi na yi mata ba".








Surayya Dahiru.
✍️✍️


🌺 *HALIN YAU*! 🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai dai da satar Dukiya._*

_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.


100_101.


Cikin mintina kadan Mk ya fahimci dalilin wannan takaddamar tsakanin Jawad da uwar da yake mata wani irin so marar misaltuwa.
Kishin Babansa da yake yi ne sanadin da zai iya yin fito na fito da ita.

Da'di ya yi matu'kar kama Mk ashe dai soasai Jawad ke sonsa, ba uwarsa yake so ba kawai, ya lura bai son kowa ya ratsa tsakanin su, ya fi son ya gansu a tare muddin rai.

Ya ja numfashi ya kalli Sa'adah da idonta ya kuje dan tsananin bacin rai, ya yi jah tabbacin ba yanzu kawai ta yi kukan ba.

Cikin rarrashi ya ce "Wai sai yaushe zaki girma ne? Yau kuma a koke koken na ki har Jawad zaki yiwa?"

Da kuka sosai ta ce "Ai kaine ka ke hure masa kunne ka ke so ya raina Ni. Dama na san da biyu ka tattaro mini shi, to burinka ya cika. Sai dai duk abin da ya mini har zuciyata ta baci, na yafe masa, in Sha Allah ba abin da zai same shi, amma tabbas sai na zane shi, domin ai wannan ba tarbiyar kwarai ya dauka ba, ya dinga yiwa manya rashin mutunci".

Kafin Mk ya yi magana Jawad dake ri'ke da Babansa ya ce "Ni bana raina manya, ba haka kawai na ki gaishe shi ba, sonsa ne bana yi, bakon jiya da na ga mai farin gemu ne ai na gaishe shi saboda ana yawan fa'da mana mu girmama tsofaffi masu farin gashi".

Sa'a ta kai masa wawura amma ya zille, da taimkon Mk.

Mk ya shanye dukkan dariyarsa ya ce yanzu a gabana sai ki doke shi? Kin san dai bana so ko?".

Cike da shagwabar da ba ta yi zaton zata sake yiwa Mk ba ta ce " Billahillazi sai na doke shi, zaman ka lafiya ka miko mini shi".

Ta fa'da cikin dire 'kafa da goge hawayen idonta.

Ta sake cewa "Baka son na dake shi. Amma ka 'ki yi masa fa'da".

Ya ce "cool down Ummu Jawad"!

Ta katse shi da cewa "kar ka kuma ambata mini wannan sunan, ka 'Kira wadda take maka alkunya da shi".

Ya ce "To Na ji".
Amma abin da nake so da ke, ki yi hakuri, yaro ne ai, tunda dai kin rantse, to zan kubutar da ke daga yin kaffara, zaki doke shi, amma ba da wannan wayar ba".

"Ni kuwa da ita zan dake shi" ta fada da sauri.

Mk Yana so ya ce to shi ta dake shi da ita, Yana jin tsoron kar ta zabga masa ta rashin tausayi tamkar ta 'KARFI.

Ya ce "A a Sa'adah kin so ki yi rikici ne kawai, yaushe zaki dake shi da wannan uwar wayar da alamun ta suka nuna ta A.c ce. Zo ki ga yadda za'ayi".
Bata san ya akayi ba, shauki ya kwashe ta, ta isa kusa da su, domin ganin da ta yi Jawad na rungume da shi, sai ta ji tamkar ta tabbata tana ganin su a haka, sune cikon farin cikin ta, ta yarda.

Mk ya rungume Jawad sosai ya ce "Dan yi masa dundu amma ba wadda ya zarta 'kwarin 'kashinsa ba, duka duka ma yaushe kika haifo mana shine?"

Ai kuwa kamar sokuwa ta yar da bulalar ta yi masa dundu har uku, za ta yi na hudu ya ce " oh sorry ya isa haka nan, ni ma zan yi masa fa'da ai".

Ta koma gefe tana harara tamkar idon zai fa'do.

Mk ya saki Jawad da suka kankame juna tamkar zasu zama halitta guda, ya ce " shiga ciki muna zuwa".

Ai kuwa ya tafi da gudu ya na dariya. Abin da ya sake kular da Sa'adah.

Ya kalleta ya ce "wannan ka'dai ya isa ki gane shima yana dandanar azabar da nake sha idan na ganki da wani".

Ta tabe baki ta ce "Allah ya bawa wadanda aka 'ki su, ake zaune da makiyansu ha'kuri".

Ya kasa cewa komai.

Ya saki maganar da cewa "ina son azo nema mini auren ki, jiya Baffa ya ce mini wai Gogel za'a je domin Yayansa dan wan Babansa ya ce wannan karon can za'a je".

Ta murmusa sosai ta ce "Ashe duk wasa ka dauki maganata? Wallahi bana fatan zaman aure ya sake hadamu, na riga da na yarda kaddarar haihuwar Jawad da kanwarsa ya sanya na yi muku kutse cikin soyayyarka da Yar mutanen Yemen".


A sanyaye Mk ya ce"Amma ai na sha fa'da miki sunan kanwar Jawad Aisha ko? Tunda ta zo da ranta, ko bata zo da rai ba matu'kar yaro ya yi motsi a ciki to a sanya musu suna saboda zasu tashi da sunan su ranar Gobe, dan haka sunan Hajiya Babba ta ci, Nana Aisha ce ina fatan ta zame mana sanadin shiga aljannah babu Hisabi".

Sa'a ta amsa da Amin a zuciyar ta.

Ya nisa ya ce "ke yanzu da gaske kike yi ba kya so na?"

Yana rufe baki ta ce "Wallahi ina sonka Mukhtar! amma bana sonka da aure, ina neman tsari da kaddarar da zata sake hadamu. Ka sani sarai, ina da kishi, idan na dawo ma ba abin da zan tarar sai bacin rai, na ro'ke ka mu rufe wannan maganar tun da sauran mutunci a tsakanin mu".

Ya matsa sosai kusa da ita murya a dakushe ya ce "Na miki tanadin farin ciki marar yankewa, kin sani Ina son ki, son da ya zarce kwatance, kin sani har zuciyarki ban zalunce ki ba, ke ce kika musguna mini, amma ina tabbatar miki Sa'adah zan sake ninka miki soyayya akan wadda na miki ta baya, zan sake tausaya miki, zan kuma yi iyakacin kokarina ban yi abin da zai yawaita motsa miki kishi ba, na dade ina roka miki sau'kin kishi a wurin ubangijin da yake sarrafa zuciya. Ko baki dawo dan ni ba, ki dawo dan Jawad, ki dawo ko ubangiji zai azurta mu, da sama masa yan'uwa".

Jikinta ya yi sanyi sosai da kalamansa, wadanda ta tabbatar babu yaudara ko da'din baki a cikin su.

Amma sai ta waske da cewa "Ina yiwa Jawad fatan samun yan'uwa ta bangaren Farida. Domin kuwa ni dai ba da kai zan samar masa ba".

Wani irin abu ya soki Mk tunda ga kan kansa har kan yantsunsa .

Ya dinga jin kansa na yi masa nauyi, ganinsa ya koma dususu, jiri ya fara katantanwa da shi.
Cikin hikimar ubangiji sai kawai ya zauna dabas angurin, farin yadinsa na tissue original din, ya debi 'kura da ciyayi amma baima sani ba.

Yana zaune sai zufa ke karyo masa, take kuma hakoransa suka dinga kadawa tabbacin zazzabi ya kawo gudunmawa a tashin hankalin da yake ciki.

Da kyar ya ciro wayarsa ya mika mata ya ce "Taimaka ki lalubo mini Abbas".

Jikinta a matu'kar sanyaye har bari take yi saboda halin da yau ta ga Mk a ciki ya matu'kar kidima ta.

Bugu daya Abbas ya dauka. Cikin karfin hali Mk ya ce taimake ni ka zo ka dauke ni, ina nan gandu gidan nan na layin Madugu, ba zan iya tuki bane".

Ya kashe wayar ya kalleta idonsa ya ka'da sosai ya ce "kin manta duk rayuwar da kika yi ta jin da'di a hannuna, kin manta alheri na, kin manta duk kalolin soyayyar da nake gwada miki, kin dora kuskurena akan dukkan wadannan abubuawan".

Ta kasa magana, ya sake kallon ta soasai fuskarsa duk gumi tamkar ya yi alwala ya ce "ki manta dukkan dadin da nake raba dare ina jiyar da ke, kin ri'ke sharri na guda daya. Har yau din nan ban ji a jikina na zalunce ki ba, na san dai babban laifi na auren da na yi ne, aure kuwa ko muna tare idan bu'katar yinsa ta zo ba zaluntarki na yi ba. Amma duk da hakan na yi ta baki ha'kuri, na fada miki kaddara ta ce auren nan da na yi. Amma ubangiji shine shaidata akan ba abin da ya ragu na daga son da nake miki, bana jin kuma a cikin wannan duniyar akwai abin da zan so ya zarta ki".


Ya nisa ya ce "Amma duk kin yi fatali da komai, kin dage sai kin yi ramuwar gayya. Abin da baki sani ba, shine ba ni da karfin guiwar juriya akan kishin ki, amma tunda kin dage shikenan, kawai ina jiye miki fargar jaji ne, ina jiye miki ki maida 'danki maraya. Shiga gida na gode sosai".

Ya yi shiru, zufa na sake karyo masa ta ko ina.

Kafin ta yi magana Abbas ya iso a adaidaita sahu.

Ya gaisheta, tare da tambayar ahalin gidansu.

Mk ya mika masa hannu, shikuma ya mikar da shi.

Suka doshi mota ba tare da Mk ya sake cewa komai ba.

Abbas ya dinga jin tausayin wadannan masoya, a ransa ya dinga musu addu'ar samun daidaito ko hankalinsu ya kwanta.

Kwanan Mk biyu a kwance Farida na jinyarsa domin a wnanan karon har ruwa aka kara masa, a gida.

Mahmoud ya damu sosai ya sake komawa wurin Sa'a Amma ta kafe ita fa ta riga ta ha'kura da Mk.

Haka da Baffa ya tambayeta ta ce ita kam bata sonsa, abin ya farantawa Inna rai, ba irin kabalin da Baffa bai yi ba ta ce ita kam ta riga da ta shafe babinsa. Lamarin da ya farantawa Inna rai ba ka'dan ba.

Da ta ga da gaske Baffa zai mata fin karfi ta shirya suka tafi Gogel ita da Sumayya, ta kai korafi wurin Yayan Baffah da ya ce a Gogel din za'a daura aurenta wannan karon.


Baffah bai san da gaske Iyah take ba, sai da ya ji kokenta akan a roke shi ya barta ta auri wadda zata nutsu da shi.

Ya dawo gida a sanyaye, ya tarar da su duk suna gidan har Sumayya.

Ya zauna a cikinsu, suka gaisa.

Ya kasa daurewa ya ce " Iyah na ji sakon ki, na san wannan hukuncin da kika yanke a iya fatar bakin ki ne, amma tunda kin yarda da shawarwarin makusantan ki, kin tauyewa zuciyar ki, da 'danki fari ciki shikenan. Ai dama ke ce kike da hakkin zabawa kanki miji domin kin girma hankali ya ratsa ki".

Ya daga kai sama ya ce "Allah ka zame mini shaida, na yi iyakacin kokarina, na mikata inda zata sami nutsuwa amma basu fahimce ni ba, Allah ka sani ban yi fishi ba, Ina dai roka mata sassauci kar abarta da zabinta, a bata mafi alheri."

Ya sauake idonsa a akanta da duk jikinta ya mutu, kunyar 'karar da ta kai shi na kamata, ba ita kadai ba har Sumayya, Innace kawai take kan ba'kanta gara da suka yi hakan.

Ya nisa ya ce" ki cewa wadda kuka aminta da shi, ya tura iyayensa Gogel wajen Babanku Ayuba, ni ba sai sun zo mini ba".

Ya mike ya barsu da sanyin jiki.

Yana fita kuwa, ya kira Mahmoud ya zo ya same shi.

Ya kalli'Karfi ya ce "Mahmouda Ina ba'kin cikin sanar da kai cewa duk yadda nake ganin Zan shawo kan Iyah akan al'amarin ta da Mutari abin ya ci tura, na rasa inda zansa kaina kunyar yaron nake ji. Yau din nan sun je can gida sun fa'dawa Yayana Akan na matsa sai ta auri Wanda ba shi take so ba, na samu umarnin akan lalle na barta ta tura musu iyayen wanda take so".

Takaici ya kama Baffa ya kasa cigabada maganarsa.

Sai ya nisa ya ce "Bazan iya fa'dawa Mutari wannan maganar ba, domin ya riga da ya gamsu na isa da ita, to gashi sun hade min kai, sun nuna mini *HALIN YAU* na rashin girmama ra'ayin magabata. Dan haka ka fa'da masa ya yi hakuri dan Allah, yau ma zan sake maimatawa da ina da wata yarinyar da na bashi, in fatan ubangiji ya albarkaci Jawad da ya ratsa a tsakanin mu".

Jikin 'Karfi ya mutu kwarai da gaske! Kenan biyu babu zasu yi? Mk ka'dai zai iya sadaukarwa da Sa'adah, amma matu'kar ba Mk ba kuwa zai shiga ya fafata da kowanne mahalu'ki dan ya tabbatar ya hana shi daukarta, a yanzun ma abin da zuciyarsa take kissima masa kenan indai yana raye bai kamata ya bari ta subucewa Mk din ba.

Ya riga da ya hakura da ita, badan ya daina sonta ba, sai dan ya san ubangiji ya dubi girman hakurinsa ya bashi mace ta gari, matar da ako ina zai bugi kirji ya ce ta gari ce, matar da take sonsa da dukkan zuciyarta, take mutuntunta shi, take hakuri da dukkan matsalolinsa, ya sani ba iyawarsa ba ce, horewar ubangiji ce.

Ya nisa ya ce "Baffah mu bamu sare ba, har sai ranar da muka ga an daura mata aure".

Ka cire kanka cikin maganar kawai, ka barmu da ita, yanzu ne zamu kafa alkalamin mu cikin tawada, jikina yana bani bakin alkalamin mu bai bushe ba".

Baffah ya nisa ya ce "To Ubangiji ya dafa muku, ya yi zabin alheri".

Kwanaki uku kenan 'Karfi ya kasa fa'dawa Mk sakon Baffa adalilin har yanzu jikin nasa ba kwari, jiyama sai Mahmoud din ne ya mayar da Jawad makaranta, da hutun ya kare a jiyan.

Sai da aka sake yin kwana biyu'Karfi ya tarar da Mk har gidansa suka tattauna sakon Baffah! A farko maganar gaba'daya rikicewa ya yi, amma 'Karfi ya shawo kansa ta hanyar fa'din ina tare da kai Bichi banji a raina zamu rasata ga'badaya ba, fatana mu yi addu'a, mu bi hankali kar kuma mu sare, mu yi ta binta tunda mu muke nema, sannu a hankali har mu samu mu damketa".

Mk ya nisa, ya ce" tunda na rabu da yarinyar nan wani abu mai tsananin nauyi ya tokare ni a kirji da makoshi, har yau din nan bai fada min ba, sai kara girmama da abin ya yi a yanzu da nake ganinta da wasu, wai ya zanyi ne? Wallahi na fara debe kauna da rayuwa domin Ni ka'dai nasan azabar da nake hadiya mussaman ace dare ya yi lokacin da zan samu na huta, a lokacin ne nafi shiga tasku bana iya barci, yanzu kuma abincin ma baya shiga".

'Karfi ya nisa ya ce "ka daina damuwa komai zai wuce, idan ka ga ka rasata, to kawai ka dauka babu alheri ne a kasancewar ku, ubangiji ne ya karar da zaman. Sai ka duba ai ka rayu shekaru bakwai babu ita, kuma baka mutu ba, idan har ita zata iya yin jarumtar hakuri da kai gaba'daya, bayan ta sha dukkan ba'kin ciki da tashin hankalin son komowa gareka, to kuwa kaine ka fi cancanta da irin wannan jarumtar".

Mk ya yi shiru yana gasggata Sa'a ta fi shi jarumta, tunda har zuciyarta bata buga adalilin aurensa ba, don kuwa shi yanzu ya gama yin imanin duk ranar da aka daura aurenta da waninsa tabbas a ranar ajalinsa zai sauka adalilin bugawar zuciya, ko hawan jinin da ya zarce kima.

A raunane ya kalli 'Karfi ya ce "Ai ita mace ce, ubangiji ya sanya musu wani irin karfin jure dukkan kalubalen tarbiya da kishi, amma mu ba a bamu wannan ba, namiji karfin gwagwarmaya aka bashi, da karfin tsayawa iyalinsa akan dukkan bu'katun yau da kullum".

'Karfi ya nisa ya ce "Hakane! Abin da nake so yanzu da kai shine, ka dora jarumtar gwagwarmaya a zuciyar ka, tunda ka gamsu muna da karfi da juriya anan bangaren, to idan kuwa hakane, zamu yi gwagwarmaya har mu samu mu kwato abin da yake namu ne".


Tun daga ranar suka fara yiwa Iyah wani irin naci, mai cin rai.

A Rana su kanje sau uku, kowanne lokaci zuwa suke yi, tun Inna tana ganin zasu gaji su daina, har ta fara ganin ba zasu gaji ba, domin kuwa kullum zaryar kara gaba take yi, ba baya ba.

Haka gidan Sumayya, hatta Idris a yanzu tausayin Mk yake ji, shiyasa ya fa'dawa mai gadin gidan matu'kar Mk ne suka zo, to ya bude masa gate kai tsaye.

Tsawon sati uku ana wannan zaryar bai fi kuma sau biyar suka samu nasarar ganinta ba, a cikin zuwa fiye da arbain.

Duk inda hankalin Mk yake a tashe yake, yayin da Mahmoud yake ta karfafa masa guiwa duk da shima bai yi zaton kafiyar Sa'adah ta kai haka ba.

Ranar alhamis da hantsi suka isa gidan Sumayya, sun shafe lokaci mai yawa a zaune, sannan ta fito, sanye da hijabi fuskar nan a daure, ta iso, da alamu tilas aka yi mata.

Dr Karfi ya mike ya na fa'din barka da fitowa sarauniyar mata. Ta yi shiru tamkar ba da ita yake ba, domin ta lura shine jagoran wannan nacin da suke mata kamar ba'kaken mayu.

Ya ce "Allah ya huci zuciyar giwa kuma gimbiyar Mata, ba zamu gaji da bada hakuri ba, ba kuma zamu gajiya ba, har sai kin dawo mana da walwalar da ta yi mana tutsu. Ki yi ha'kuri, ki zo ki haska mana zuciyar aminina da gidansa gaba'daya, Ina rokon ki, badan mu ba, sai dan ubangijin ki, ni shaida ne na irin tsananin son da yake Miki".

A tunzure Sa'a ta ce "ka dinga jin tsoron ubangiji Baban Dady! Sai yanzu! Sai yanzu! Sai yanzu zaka tirsasa ni, me yasa a wanccan lokacin baka tirsasa shi ba, me yasa ka bari na wulakanta, na tabbatar ba zaka so ayiwa kanwarka abin da aka yi mini ba. Amma yanzu da yake farin-cikin abokinka kawai ne a gabanka, ka na'de 'kafar wandon yi mini dole, kasan ina jin nauyinka, akan me zaka takura ni irin haka, an ta'ba yin aure dole, to ko Baffah ma na tabbatar masa bana son wannan mutumin, kaima na fa'da maka, ka sakar mini mara, na ro'ke ka".

Ta karasa cikin kuka sosai, Dukkan su sun yi laushi, mussaman Mk da yake jin tamkar ya hadiyi zuciya saboda yadda yake jin ciwon yadda take fadin bata sonsa, a gaban kowa.

Mahmoud ya kalli Agogon hannun sa, ya ce "hakuri zaki yi, ba yadda zamu yi ne, ki 'kara hakuri, ubangiji zai baki ladan masu hakuri.

Ya kalli Mk ya ce " ina da appointment nan da mintina talatin a makaranta, zan wuce, idan ka gama kawai mu hadu a gidanka bayan azahar".

Daga haka ya fice da sauri, da mukallin motar Mk a hannunsa.

Tana tsaye tamkar soja. A hankali Mk ya ce "zauna mana Dan Allah".

Bata yi musu ba, ta zauna.

Ya zuba mata ido yana kallon yadda ta ke cika tana batsewa ya saki ajiyar zuciya mai zafi ya ce "A gaban kowa kike fadin ba kya sona, Ni kike wulakantawa haka? Kada kishi yasa ki manta ke ce kika mini laifi?"

Da kuka ta ce "Ni na maka laifi tabbas, ka kuma hukutan ni, to menene kuma ba sai a barshi a hakan ba, gaskiya kun matsa mini, tsakani da Allah kun shiga rayuwata, sau nawa zan fa'da maka bana sha'awar sake rayuwa da Kai? Na ha'kura, na bar mata, Ni ma ka bar ni, Dan Allah".

Kafin ya yi magana ta sake cewa "kafin ka aure Ni ka kira ni Ballagaza, na yi hakuri saboda ina ta'kama da Budurci, yanzu kuma ka ce ina ha'intarka, fa'da mini dame zan kare kaina, tunda ba ni da Budurci a yanzu?"

Da sauri Mk ya karaso kujerar da take zaune, ya zauna a hannun kujerar ya sassauta ya ce " Na da'de ina fada miki, bacin rai ne, ba ina nufin haka har zuciyata ba, ki yi hakuri. Na janye kalamina, wallahi tallahi ke din katangaggiya ce, ki bar wannan maganar, ko tunawa bana so, hankali na tashi yake yi. Na janye! Na janye! Na janye Dan Allah a rufe wannan maganar har abada".

Ta dinga kuka sosai mai cin rai, ta kasa cewa komai.

Ya nisa ya ce" kukan ya isa haka, ki yi hakuri ina fatan wannan ne kukan ki na karshe akan wannan matsalar".

Ta kifa kanta a dayan hannun kujerar tana sake tsananta kukan sosai, Ta ce "indai baka rabu da ni ba, na tabbatar zan dauwama ina kuka ne, domin zan rayu ina raba ka da wata ne, Ni kuwa da haka gara na auri me mata uku na zama ta hudu".

Mk ya rasa mai zai yi, ko ya ce, gaba'daya tunaninsa gaba'daya ya kulle.
Ya tabbatar auren Farida ne cikas dinsa a gurinta, shine yasa ta kasa amincewa da shi.
Ba yadda zai yi akan Farida kuwa domin bai aureta dan ya saketa akan wani 'karamin dalili ba.

Ya sassauta ya ce "Yarda da 'kaddara na cikin sharuddan cikar imani, ki ture komai, ki kalle ni har yanzu ba abin da ya canja na soyayyar ki a tare ni, ki bani amanar kan ki wallahi ba zaki yi nadama ba".

"Ko yanzu kika amince mini, wallahi na sha wahala, na azabtu, yanzu haka ina daf da kamuwa da ciwon zuciya, ba komai bane ya janyo mini ba, illah ganin ki da wasu mazan".

Ya sauko ya dur'kusa a gabanta karon farko ya ce "Ga ni akan guiwata, ki yi hakuri, ki yafe mini, ki sake bani wata damar, ni na san kina so na. Plz Sa'adah let Gone by gone, ba zan iya wannan rikicin ba, na horu hakanan, ki fa'dawa Baffa mun shirya, na kuma kawo miki Baba Isa gaban ki, ki fa'da masa mun shirya, kin yafe mini, Ni kuma na miki al'kawarin zaki rayu cikin soyayya mai wuyar samu a Yau".

Ta dago ta kalle shi a durkushe a gabanta, da'di ya kamata, amma sai ta waske ta ce "Ni fa ba zan yafe ba, matu'kar ba wani ne ya aure ni ya ta'ba ni kamar yadda kake ta'ba wata macen ba".

Ya mike da sauri ya ce "shikenan, dama ke ai ba'a taba rarrashin ki, kin gamsu cikin da'din rai ba, kaddara ce ta hau kaina ban kuma isa na kauce ba, tunda kin kasa fahimta shikenan, amma ki sani idan fa 'kaddara ta gwada iko akan ki, kika dawo mini, ba zan gamsu kin mini uzziri ba".

Ta tura baki gaba sosai ta ce " Da ikon ubangiji ma ba zata faado kaina ba".

Ya koma ya zauna a inda yake zaune tun farko yana tunanin mai kuma zai yiwa wannan yar darun ta fahimce shi, shi tashin hankalinsa daya ya ganta da wani, ba dan haka ba, da ya daure ya kyale wannan yarinyar da take neman manna masa ciwon zuciya.

Sun Jima a zaune ba um bare um um.

Ya mike ya ce "zan tafi ina fatan idan na kira wayar ki, ki dauka.
Allah ya huci zuciyarki".




****
A cikin wannan yanayin shari'ar Sanata Ibrahim Hassan ta sake zagayowa, bayan doguwar muhawara da tarin hujjojin lauyoyinsa, kotu ta wanke shi daga dukkan tuhumomin da ake yi masa.

Sa'aadah ta bukaci a bashi naira miliyan hamsin a matsayin diyyar bata masa suna da lokaci.

Jajircewar da Sa'a ta yi a wannan shari'ar yasa sunan ta ya shahara, ta yi farin

Please Login or Register in order to submit comment