You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su ita da Hajiyar Bichi".

Ya sauke ajiyar zuciya, hankalinsa ya sake tashi, tabbas akwai wacce ta zo take kokarin birkita masa zaman lafiya a gidansa.

A zahiri sai ya murmusa ya ce " Ashe adduar Innace ta sauka akan mu, ba wai akuya na maida ki ba".

Ta tura baki gaba, tana jin ba zata sake yarda ta yi irin wannan gangancin ba a gaba.


A kicin ya ga tray din da aka ci indomie mai dauke da fork guda biyu.

duk yadda akayi wadannan bakin da ta yi ne, suka kitsa mata maganganu, tunda duk boren da ta masa a farko, ai tunanin ta bai bata irin wannan kalamin ba.


Bai sake shan mamaki ba, sai da suka kwanta, ya ji ta ce zasu yi magana, ya ce "Ina jinki".

"Uncle so nake yi nima na cike jamb foam".

Ya ji zuciyar sa ta buga, sai ya danne, cikin dabara dan ya fahimci inda ta dosa.

Ya ce " da kam ina da buri ki yi a wannan shekarar, kafin lokacin da komai zai kammala na samun admission kin yaye Jawad sai ki fara karatun ki, ba wata matsala".

"Yanzu kuma shikenan sai ba zan yi ba?"
Ta fa'da da gatsali.

"Ya sake dannar zuciyarsa ya ce " za ki yi mana, amma dai sai next year".

Ta tunzuro sosai ta ce "kenan sai nan da shekaru biyu kake nufi zan fara?"

Ba ja in ja ya ce " eh".

Jin haka ta fara sakin magaganu "Ni wallahi bazan yarda ba, kafin nan da shekaru biyu only God knows mai zaka mayar da Ni".

Ya yi shiru yana ta neman tsarin Allah ya kare zuciyar sa daga sharrin shaidan da fishi.

Jin ya mata shiru ba'kin cikin ta ya karu,ta fashe masa da kuka mai sauti, tana fadin son kansa ya yi yawa, duk 'kawayenta kowa na karatu sai ita kadaice mai zaman banza da kashe wando.

Rukota yayi zuwa jikinsa tana fizgewa, kan dole ya kwantar da ita, yasa hannun sa ya zagayeta.

Ya ce "Duk kawayen na ki fa'da mini me kamar Jawad? fa'da mini mai miji irin naki da yake tsananin son ki".

Ta yi shiru tana jan hanci, sai kuma ta ce "su ai ba'a tauye su ba, ba a rufe su a gida ana shirin tsofar da su ba".

Ya yi shiru, yana nazarin maganganunta, da ya tabbatar kitsa mata aka yi.

Ya sake fadin yanzu zaman aure ne ya zama abin kashe wando da tauyewa a gurinki? duk yadda Allah ya miki ni'ima, kin raina?"

" Kawai ni son kanka ne ya dame ni"

Mai na yi miki na son kai a zamantakewar mu?"

"Gasu nan kala kala, ka sani haihuwa dole, sannan ka rufe ni a gida, kai kuma kullum kana ganin yanmata, wataran sai inji zaka w amarce da mai degree".

"Su Halima sun zo too nan ko?"
Ya fada ba tare da yasan a fili ya fada ba.

"Ba su zo ba".

"Hmmmm! kawai ya fa'da ya fara lalubarta a kokarinsa na son ya kawar da bacin ran dake neman taso masa.
Ai kuwa ta buge hannun sa tana cewa " Dan Allah ka bari, kullum aikin kenan, ka fitine ni da daddare, danka ya tsotse ni da rana, ga kuma wadda yake cikima bai barni ba, so haba da wanne zan ji".

Ai kuwa hakurinsa ya 'kwace ya ce "Duk ma wadda suka zo suka miki famfo, ke kuma kika yarda ina tabbatar miki kidahuma suka mayar da ke, sannan maganar karatun da kike ganin sun tsere miki da shi, su a gidajen iyayen su aka basu damar su yi".

Maganar ta mata ciwo ainun a harzuke ta ce "wato ni iyayena basu bani dama ba kenan?"

"Eh" kawai yace ya tsuke bakin sa, ai kuwa ta kara 'karfin kukanta, tana ta yunkurin tashi amma ya danneta ya'ki bata dama.

Sosai suka yi rikici, saboda ya ki amincewa da ra'ayin ta, na ta yi jamb a wannan shekarar.

Sai dai kan dole ya ajiye nasa fishin, Yana fadin ta yarda da shi, bazai taba juya mata baya ba, ita kanta yake so ba wani abu na kyan surarta ko zurfin ilimi ba.
indai zata biyewa maganganun wasu, ba abin da zata ci ribarsa a rayuwar ta, ko karatun take yi, wasu sai sunce ta 'ki aure da sauran maganganun marasa Da'di.

Sannan ba abin da yake ruguza Jin dadin zamantakewar aure irin ka bawa wasu dama su shigo cikin matsalar gidanka.

Tun a daren suka shirya, ya saukar da ita, daga famfon su Halima.

Haka rayuwar ta cigaba da gungurawa da su,har Allah ya sauki Sa'adah lafiya, ta haifi kyakkawar yarinya mai kama da ita kwabo da kwabo, sai dai yarinyar da lalura ta zo, ko kuka bata yi ba.

Aka ri'ke su a asibiti, ko numfashi sai da oxygen take zuka, kwanata biyu tace ga garinku nan.

fadin irin tashin hankalin da Sa'adah ta shiga ma, bata lokaci ne, domin tunda ta dora ido akan yarinyar nan, sonta ya shigeta fiye da na Jawad.
Ashe mai gajeran kwana ce.

Kan dole ta ha'kura, ba kunya ta karbi Jawad a hannun Inna ta cigaba da shayar da shi ba tare da an ro'ke ta ba.

Mk ya dinga tarairayarta da lallashi, da nuna soyayya har ta warware ta cigaba da jegonta cikin salama.

Da yardarsa da amincewarsa suka je asibiti aka aunata, aka dora ta kan maganin tsarin iyali da ya dace da jininta, duk dan ta samu ta huta ta gyagije, shima ya samu hutawa da ita, da sau'kin gorin da ta ke masa na ya maida ta akuya😃.







*SURAYYA DAHIRU*.
✍🏼✍🏼
25/03.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*.


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.







63/64.




*Shekara daya a gaba*.


Zuwa lokacin shekarun su uku da aure, a shekarar Allah ya yiwa Hajiya Babba rasuwa, a dalilin ciwon siga da ya kamata, ba'a gane da wuri ba, har ya taba kodarta, kwananta uku a asibiti ta rasu! mutuwar da ta gigita dukkan yan gidan su Mk dama wadda yasan Hajiya, barin Hajiyar Bichi da akayi zaman makoki ita tana gadon asibiti.

Kwarai suka shiga alhinin rashinta, sai dai ita mutuwa duk yadda zaka yi, ba zata dawo da mutumin data dauka ba, dole aka ha'kura aka bita da addu'a.

Mafarin dawowar Hajiyar Bichi Kano gaba'daya kenan, kullum ta Allah sai ta yi kukan rashin Hajiya, ko na ido, ko na zuci, karshe sai ta musu addu'a tare da mijinsu, tana fatan itama ta riske su cikin aminci.

Mutuwar Hajiya Babba yasa Hajiyar Bichi ta gane abubuwan da Hajiyar ta kare , mussaman na rashin tasowar fitina a tsakanin yaran, tunda ta kwanta dama, yaran gidan kansu ya fara rabuwa mussaman manyan yaransu mata na 'dakin Hajiya Babba, da suke ganin dama kamar mallake musu uwa Hajiyar Bichi ta yi, kawai Samira a cikinsu bata biye musu to kuma itace karamar su.

Haka Hajiyar Bichi take ta ha'kuri da su tunda dai uwarsu ba abin da bata mata na alheri ba, duk yadda suke 'da'darewa da ita, yi take yi kamar bata gane manufar su ba, Abbas da Akil ne basa bata matsala, ko dan su maza ne?

Su Halima sun sami nasarar samun admission, dan haka ba sosai suke zuwa gidan Sa'adah ba, saboda sun koma new side.
Amma duk ranar da suka sami sararin zuwa gidanta sai Mk ya gane saboda yadda take daukan sabbin dabi'u.


Ranar wata litinin Safina da Halima sunje students affairs na cikin Jami'ar, gun a cike da dalibai kowa na yin abin da yake gabansa.

Suna daga can baya, kamar ance da Safina 'daga kai, sai ta hango Farida Torondi, da Uncle Mk na Sa'adah, da wata da bata ganeta ba.
A hanzarce ta zunguri Halima da hankalinta ke kan waya ta mata nuni da abin da ta gani.

"Munafiki dama ai nasan cin amanar Gogel yake yi, marar mutunci, ba dama aje gidansa ya dinga 'dacin rai da muzurai kenan, banda rashin gaskiya, menene na zargin mutane suna zuga maka matarka, ai dan yasan yana rashin gaskiya a waje ne".

Kafin su kammala, har su Farida sun gama sun fice tare da Mk.

Halima so take su wuce gidan Sa'adah, yayin da Safina tace ita ba zata iya zuwa ko'ina ba tare da taci abinci ba, dan haka suka zarce capteria.

Anan ma suka sake yin tozali da Mk da su Farida suna cin abinci suna hirar su cikin nisha'di.

Suka kewaye su, suka tafi can baya suka zauna, ta inda su Farida baza su gansu ba, yayin da sukuma idonsu na kan duk motsin su, suna daukarwa Sa'adah rahoto.

Halima fadi take "wannan mutumin mugune, ya rufe yar mutane ya hanata fahimtar komai. ashe shi yana nan yana sheke ayarsa"

Safina ta furzar da hucin takaici tace saboda Allah kiga ya hanata karatu, shima daf yake da ya kammala Masters dinsa, (Jami'ar ce ta dauki nauyin karatun nasa). Sannan yana tarayya da mai yin degree a fannin hada magunguna (pharmacy), above all daga rich family ta fito, oh Allah sarki! na tausayawa poor Sa'adah".

"Ka'dan kenan a sharrin namiji" inji Halima da take jin tamkar taje ta rufe su da duka.

Suna zaune suka ga su Mk sun mike, sun fita, a motarsa ya 'debi su, kuma Farida ce ta shiga gaban motar.

Ba'kin ciki ya kamasu da gaske suka ji, suna taya kawarsu kishi, Safina tace "takaici na daya, da bamu samu damar yiwa Gogel bidiyon su ba".

Halima ta amsa da cewa "wlh kuwa basirar yin hakan ba ta zo mana ba"

Daga capteria, basu zame ko ina ba, sai gidan Sa'adah, suka kwashe komai suka fa'da mata, a kokarinsu na tserar da ita daga cin amanar namiji, ita kuma bata gane duk mai zuwa ya fa'da maka abin da zai ruguza farin cikin ka, ba masoyi na hakika bane, mai sonka idan yaga abin da zai tayar maka da hankali! 'Boye maka yake yi mussaman a fannin auratayya tunda dai kowa yasan namiji is entitled to 4 wives, dan angan shi da budurwa matu'kar ba ba'dala suke yi ba Ina ruwan ki?

Kuka ta dinga yi, tana fa'da musu kwanaki biyun nan wulakanci ya ke tata mata, ya tsiri ya yi wanka da magariba ya she'ka kwalliya ya ce mata ya tafi shago, ba zai dawo ba sai after 11.

Suka hada baki wurin cewa "karya yake miki ba wani shago, wurin Farida yake zuwa, yau munga zahiri".

Safina da ta fi Halima kishi tace duk ranar da ya wuce goma na dare bai shigo ba, ki rufe gidanki, ya koma can su kwana tare, ai dan ya ganki sanyi kalau ne ya samu damar yin wani abin"

"Wallahi kisan me kike ciki akan makaranta, baya son ki dinga ganin mai yake yi, shiyasa yake ta miki yawo da hankali akan karatunki, oh mai za'a yi da irin su Mk".

Ita dai banda kuka ba abin da take yi, tana jin wani irin kullutu ya tokare mata wuya da zuciyar ta, ya sababa mata nauyin kirji, da kyar take zuko numfashi.

Haka suka tafi suka barta da kunan rai, suna jaddada mata tasan matakin dauka akan mijinta🤔

Wawiyar kuma ta cika fam! tana jin yau ko yafi gyatumarsa kokari, ba zai yaudare ta da kalamansa na yaudara ba, ya maida ta wata nympho, da sun fara rigima sai yasan yadda ya yi suka kusanci juna shikenan sai ya kashe fa'dan, da zarar ya hau samanta bata sake tuna komai na bacin rai a tsakaninsu.

Ta ci kukanta ta 'koshi bayan tafiyar su, sai ta yi dabarar fara karatun kura'ani dan ta sami sau'kin 'kullutun dake neman fasa mata zuciya da makoshi.

A haka ya dawo ya tarar da ita, ta sami sau'kin bacin ran da ta ke ji.

Kusa da ita ya zauna yana sauraron kira'arta mai dadi, sai da ta kai Aya. sannan ta ajiye kura'anin ta mike tace "sannu da dawowa".

Ya amsa da "yauwa! Na gaji yau dinan sosai, na sha zirga zirga, ba tare da kalle shi ba, tace " wata'kila har wanka ya hau kanka".

Zuciyarsa daya ya ce "gaskiya kam idan na yi zanfi wartsake wa", ya kalli agogo ya ce bari na yi sauri na watsa ruwan kafin a kira sallah".

Ya mike ya yi dakinsa, ita kuma ta bishi da kallon tuhuma, da takaici mai yawa.

Da ya dawo bai nemi abinci ba, ta kara gasgata su Halima, ya taba jikin Jawad da yake kwance yana fama da zazzabin hakorin fi'ka, ya kalleta yace a kwance ya yini ne?"

Kai kawai ta daga masa, ya riga da ya saba da halinta na rashin bashi amsa da baki wani lokacin, dan haka bai damu ba.

Wani ikon Allah yau da wuri ya dawo, kamar yasan anshirya masa ya kwana a waje, haka suka kwana bai gane kan gimbiyar ba, ya daure, shima ya 'kyale ta.

Washagari suka tashi Jawad yana ta suma! ga wasu irin abu sun feso masa kamar borin jini, asibiti suka kai shi, aka bashi magaunguna bayan anmasa allurai, sunje siyan magani, suka tarar da Farida a pharmacy din, da azama ta zo gunsu ta karbi Jawad da yake hannun sa ta dudduba jikinsa tana fadin "Abban Jawad wannan ai 'kyanda ce(measles)".

Da kanta ta hado maganin da aka rubuta musu, har ta kara musu da wani sabulu da zai taimaka wurin baje fatar.

Lokacin da take yiwa Mk bayanin maganin da yadda za'ayi amfani da su, Allah kadai yasan yadda zuciyar Sa'adah ta ke tafasa, ko da Farida ta karaso fuskar Sa'adah a daure ta gaisa da ita, har Mk yaji kunyar yadda ta mata a gaban jama'a.

Ya mika kudin Farida ta ce "A a Uncle ka barshi, da dai na Gogel ne sai na barka ka biya! Amma ai Jawad 'dana ne nima", ta fa'da da sigar tsokana da wasa.

Ya yi godiya ta rakasu har mota, ya karbi Jawad a hannun ta, ya mika ma Sa'adah ta hakince a gaban mota, suka tafi.

Suna Isa gida bata jira ya gama daidaita parking ba, ta dauki ledar maganin da Jawad ta fice.

Tana kwantar da Jawad da yake ta barci tunda aka masa allura, ta samo biro, ta yiwa magaungunan nan shaida ta yadda ita kadai zata gane, ta daure ta ajiye su.

Ya shigo ya zauna, yana son yi mata magana amma ganin yadda ta 'daure fuska tamkar wadda ya zagi iyayenta, yasa ya mi'ke yana cewa " na tafi! Dan Allah kar kiyi wasa da bashi magani".

Ci kanka ba ta ce ba, ya gaji da tsayuwursa ya fita, yunwar da yake ji dole ya fita da abarsa, dan yasan tunda take wannan fishin ba yi zata yi ba, yasan ganin Farida ne ya sake tunzuro ta, tunda tun jiya take ta faman 'kunci, a ransa yana ayyana da jiya kuma ta ganshi yana taimaka wa kanwarta da ta samu admission zata karanta economics fa? Farida ba tasan komai a new side ba, tunda ita a old side take karatunta, shikuma sai ya rakasu a kokarinsa na kyautata mata kamar yadda take girmama shi a matsayin malamin ta.

Shi bai san har anzo anfesa mata ba.😄

Da yamma ya dawo, ya ya tarar da ita goye da Jawad, kayan da ya barta da su ya dawo ya same ta da su. kallo daya ya mata, ya gane bata ci komai ba, sannan bata yi wanka ba.

Ya rasa gane wannan masifar da ta 'dorawa ranta, da 'kyar ta bude baki ta ce "Sannu" ya amsa da yauwa ya isa bayanta yana duba Jawad da yake ta Nishi, shi dai ta masa wanka fes yake, sai dai jikinsa kamar wuta.

"Kin bashi maganin kuwa? na ga jikin, har yanzu bai sauka ba".

Ko kala ba ta ce ba, ya isa inda ledar maganin take ya bude ya ga ba wadda aka taba, bare a sha.
Ransa ya baci matu'ka da gaske, ya nunata da yatsa ya ce " Wai ke wacce irin yarinya ce marar mutunci?"

Ta yi 'kasa da kanta tamkar wadda ta saduda, yaci gaba da fadin "kin fara kaini bango Sa'adatu, kullum a cikin zullumi nake zaune da ke, masifar yau daban, ta gobe daban, haka ta jibi".

"Ai kaci moriyar ganga, sai ka kawo karshen zaman zullumi Mk" ta fada kanta tsaye.

A razane ya zuba mata ido, yana kallon ta, itama ta kafe shi da idon da suka cika da 'kwalla ba alamun tsoro ko shakka a cikinsu.

Ya kasa cewa komai, dan kuwa a yadda yake jin bacin rai zai iya na'da mata dukan tsiya, abin da baya fatan ya aikata kenan, dukan matar aurensa.

Ya mika hannun yana fadin "bani yaron, kai tsaye ta ce "idan kai ka haifar min, ba sai ka 'kwata ba".

Ya yi kanta yana fadin "Me kika sha ne? Bari na sauke miki iskancin da kike fama da shi".

Ga mamakinsa ko motsi ba ta yi ba, sa'banin da, idan ya mata irin haka take kwasa a guje ta 'buya.

Ya isa kusa da ita ya kama kafadunta ya girgiza da karfi har sai da Jawad ya motsa, ya ce " fada min me yake faruwa, me na miki har ya shafi wannan yaron da bai san komai ba?".

Tsaki ta ja, tare da fizgewa, ta koma gefe tana sake 'daure goyonta sosai.

" What! Ni Kika yiwa tsaki Sa'adatu? abin da kinfi kowa sanin na tsani a mini?"

Ai kuwa ta sake jan wani fiye da na farko, sannan tace " ka kashe ni! an maka tsaki Mukhtar".

Wani irin shock ya kama shi, a farko da tace Mk gatsal mamaki ta bashi, amma a yanzu da ta ambaci cikakken sunan sai ya gane ashe Mk din a mutunce ta fa'da.

" Allah ya tsare ni da kisan kai, duk bala'in da kike nufi na da shi, in sha Allah ba zai same ni ba".

"Tunda abin har ya kaimu ga haka, to shikenan! ki yi harkar ki na yi tawa, sauko shi na bashi maganin, sai ki mayar da shi".

"Baka ji mai nace tun farko ba? ka 'kwata' a shirye nake da mu karya yaron nan! idan har ni na tsugunna na haife shi wallahi ba zai sha wannan maganin ba".

"Ya zuba mata ido, yana jin haushin ta na samu gurin zama a zuciyarsa, ya ce "idan na siyo masa wasu zai Sha?"

"Idan na tabbatar da sahihancin su ba".

Ya dauki ledar maganin ya fita ba tare da ya sake cewa komai ba".

Bai wani jima ba, ya dawo da su, a wata ledar mai tambarin lamco pharmacy.

Ya mika mata, tare da cewa "gashi" ya juya ya fice.

Ta dudduba ta tarar da su dinne, illah ledar da ya canja, ta yi 'kwafa ta dankwarar da su.

Ana idar da Isha ya dawo, ya tarar da maganinsa akan kujera ita kuma ta shige 'daki ta rufe kofar, Jawad sai kuka yake yi.

Ya duba maganin ya tabbatar ba'a bashi ba, ya hau dukan kofar, amma banda kukan yaron ba ya jin komai.

Ya kirata ya fi sau hamsin amma tamkar bata gidan.

Ya hassalo sosai ya ce "wallahi idan yaron nan ya mutu, ke kika kashe shi, da hannuna zan mika ki wurin hukuma".

Sai lokacin ta ce "yi sauri kar 'kuda ya riga ka, wato ka maida ni bagidajiya, ka fita da magani kamar gaske, ka sake dawo min dashi, idona tar yake, bazan bashi ba".

A fili ya dinga fadin "Innalillahi wa Inna ilaihir raji'un".

Ya fice zuwa dakinsa, yana karfafawa kansa guiwar ya rabu da ita, ai ta fishi son yaron.

Karfe shadayan dare ya dinga jin kukan yaron, da farko ya yi biris, amma da ya dinga jin 'ka'karinsa baisan yadda akayi ba sai ganin kansa ya yi a jikin kofar dakin Sa'adah yana bugawa, yana cewa "ki dubi girman Allah ki bude min kofar nan, komai na yi miki, na yarda kimin komai, amma banda yaron nan, ki ji tausayinsa, ki ji tsoron hakkinsa".

Har ya gama bilayinsa bata tanka ba, tana jin ta shirya faruwar komai ciki har da rabuwarsu.

Cikin ikon Allah, sai Jawad ya sami barci adalilin ta bashi tea, ta bashi maganin zazzabin sa da yake da shi.

Da asuba kukan Jawad ya sake tayar da hankalin Mk, ya rasa inda zai tsoma ransa, a take ya kira Hajiyar Bichi a waya, bai fa'da mata komai ba, ya ce dai kwana suka yi Jawad bai yi barci ba.

Ba bata lokaci, ta taho,har da garin kunun ko zai dinga sha, tare suka shiga falon, ya dinga kiran Sa'adah amma ta 'ki budewa, sai da taji muryar Hajiya tana cewa"Sa'a, menene yake faruwa ne?"

Da sauri ta bude 'kofar, ta fito idonta, yayi luhu luhu, yayi ja tsabar kuka.

Ta mi'ka mata Jawad ta zauna a gefe tana kuka tamkar wadda aka yi wa mutuwa.

Hajiya ta kalleta, taga ta fita a hayyacinta, ta rame farat daya, ta maida kallonta ga Mk taga shima a firgice yake.

Tace ciwon Jawad ne ya susuta ku haka, ko kuwa wata matsalar ce?"

Ya dauko maganin ya mi'ka ma Hajiya ya ce "Dan Allah ki bashi maganin nan", ta karba, ai kuwa Sa'adah ta saka uban kuka tana cewa "Kar ki bashi Hajiya".

Hajiya ta rasa maganar wa zata dauka a tsakanin su, ta dubi Sa'adah tace "Yi shirunki bazan ba shi ba, fada min me ya faru?"

Ta kasa magana sai kukan da take yi mai dauke da shesshekar ajiyar zuciya.

Ganin hakan yasa Hajiya ta rufe Mk da fa'da, ta inda ta shiga, ba tanan take fita ba, tana jaddadawa laifinsa ne, tunda Sa'a ba me fitina bace.

Ya yi shiru ya dauki laifin da bai yi ba.
da lallashi, Hajiya ta samu Sa'adah ta fada mata dalilin da bata son maganin alhalin ba expired suka yi ba.

Da rawar murya ta ce " Budurwarsa ce ta siyi maganin, akan idona suka yi zance ta siya ta bayar".
Ta karasa cikin gunjin kuka.

Dariya abin ya bawa Hajiya, amma sai ta dake, ta dinga salati tana fadin "kice cin fuska ya miki? banga laifin ki ba, dole ki guji magani, ko nice haka zan yi".

Shi dai Mk ya zama tamkar gunki, yana kallon shari'ar son rai a wurin Hajiya.

Ba zato Hajiya ta ce yaje ya siyo wasu maganin.

Ya ce " Bafa su bane, tunda take wannan bala'in na zubar da su, na siyo masa wasu, amma ta "ki bashi"

Da rawar murya ta ce "Billahillazi, baka canjo wasu ba, duk abin da ya fito ta hannunta, na tsane shi, zan kuma gane".

Jin haka yasa Hajiya fadin "Bar Wannan gadddamar je ka siyo wasu a bashi ya dan sami sauki"

Bai q musa ba, ya mike, ya dauki ledar maganin, ya fita.

Sai da ya fita Hajiya ta dinga mata nasiha, tare da cewa "ki rage nuna masa kishinki a fili, sai ya samu dalilin da zai dinga musguna miki".

Ta kalleta tace "tunda da wuta jona ruwan zafi kuyi wanka".

Ta mike ta cika buta ta jona, mintina kalilan ta kashe kanta, ta juye, ta sake maida wani, kafin ta fito, Hajiya ta wanki Jawad a bandakin tsakar gida.

Ta dama musu kunu, ta juye a flask din shayi, ta zubawa Jawad a kofi, ta bashi, ya shanye tas har da kari, ta tabbatar shima har da yunwa ta sake gigita shi.

Sa'adah ta fito sanye da riga da zani na atamfa, dinkin ya zauna sosai, mussaman da bata cika daura zani ba.

Ta mikawa Hajiya kayansa, sai da ya koshi ta koge masa baki sannan ta saka masa kaya, dai dai lokacin kuma, Mk ya dawo dauke da magungunan, leda biyu, ya mikawa Hajiya, sai da Sa'adah taga na wurin Farida, ga kuma wadda ya sake siyowa, sannan ta saki ranta, a ransa fadi yake masifaffiya kawai.

Take Hajiya ta bude ta bashi, ta shafa masa na shafawa, barci ya dauke shi mai nauyi.

Sosai Hajiya ta musu fada, kuma duk na Mk yafi yawa, jan kunne 'daya, ta yiwa Sa'adah, kar ta sake saka Jawad a cikin fa'dansu, ta ki cin abinci, shi akan mai zata hana shi?

Ta cika kofi, da kunu ta mika wa Sa'adah tace "Shanye ki bani kofin".

Ta karba, ta fara sha, ya mata dadi sai kamshin kayan yaji yake yi.

Shi dai Mk yana kallon ikon Allah, anbawa Jawad, da Sa'a, shi ko oho.

Sai da Sa'adah ta shanye sannan Hajiya ta mike ta ce "zan tafi nasan ki da jin

Please Login or Register in order to submit comment