You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuma bana jin zan iya cigaba da zaman mu tare, iya adadin zaman da 'kaddara ta hukunta za mu yi kenan, ka fa'dawa Hajiya sai muje ka raka ni wurin Baffah, duk da bana jin dadin jikina".

Ya fada a sanyaye cike da yankewar Buri.

"Mukhtar Nima ba zan iya fa'da mata ba, da wanne baki zan fadi wannan 'bakin labarin?"

"Cike da rauni ya ce " daurewa za ka yi Mahmoud".

Shiru ta ratsa dakin a karo na biyu, nazari soasai Mahmoud ya ke, yana tunanin wacce irin 'kaddara ce mai zafi ta raba Mk da Matar da ya shaida yafi sonta akan kansa?

Yana son jin menene ummul aba'isin wannan matsalar, amma kuma tunda Mk bai bu'da masa ba, shikuma ya yi al'kawarin ba zai tambayi komai ba, zai kuma yi dukkan mai yiyuwa dan ya sulhunta tsakanin su.

A dabarance Mahmoud ya 'daga murya ya ce "Sam bazan iya fadawa Hajiya wannan tashin hankalin ba, kai da ka yi, kaine mai fa'da ba Ni ba".

Ai kuwa wannan kalamin na Mahmoud ya janyo hankali Hajiya, da azama ta fa'da 'dakin tana fadin " menene ba za ka iya fada mini ba Mahmoud! wanne tashin hankalin ya rakito?"

Dukkansu suka yi shiru aka rasa mai bakin magana, ta zauna da'bas a 'kasa tana salati, da fatan ba wani rashin gaskiya Mk ya aikata ba.

Ganin irin damuwar da ta shiga yasa Mahmoud yin 'kundunbalar fadin "Hajiya ki yafe mu, ina ba'kin cikin sanar da ke yau Allah ya 'karar da zamansa da Sa'adatu".

Salati mai 'karfi Hajiya ta rafka, tana cewa "Kar ka jinginawa Allah'karar zamansu, jingina masa, dama ya da'de yana fatan rabuwar, ganin ya kasa samun damar shine yanzu ya murde zaman da 'karfin tsiya."

"Oh ni Rabi'atu ina ganin tasku, da wanne 'bakin ciki zan ji? da wadda yan'uwanka suke guma mini, ko da naka? Alhaji da Hajiya Babba sun mutu sun barni da ku, kuna neman kashe ni da ba'kin ciki".
Ta fara hawaye, tana gogewa da hannun zaninta .

Da ga Mk har Mahmoud sun yi laushi tubus da jin kukan Hajiya, hankalin su kuma ya sake tashi matu'ka, da rawar murya Mk ya ce "Na roke ki, ki daina zubar da hawayen nan dafi ne a rayuwa ta, da kinsan azabar da nake 'dan'dana na tabbatar da sai kin sassauta mini, ki yi hakuri Hajiya ba yadda zan yi ne, abin ne ya fi karfina, ki mana addua ki kuma yafe mini".

"Yanzu ina Sa'a din ta ke?"

Mahmoud ya ce "tana gidansu, yanzu ma komawa zamu yi dan bamu sami Baffan ba".

Hajiya ta sake sa salati tana tafa hannu, tare da cewa "yanzu idon ku, idon tsohon nan ku iya fa'da masa kun mayar masa da 'ya Bazawara? kaico na taya ku jin kunya".

"Yanzu ku tashi ku kaini gurin Alh Isa".

Sai da Mahmoud ya taimakawa Mk sannan ya mike.
Fada sosai Mk ya sha a gurin Alh Isa, sai daga karshe ya sassauta ya ce " Ka yi kyan kai da ka yi saki 'daya tal, fatana ka janye ka mayar da matarka, kowa hakuri ya ke yi da abokin zamansa ,ta ci darajar mahaifinta".

Kan Mk na kasa baice komai ba sai da Baban ya kammala sannan cikin ladabi ya ce "A mini afuwa Baba, a yi hakuri, a sani cikin addu'a ina cikin ru'dani mai yawa, ina rantsuwa da ubangiji ina cikin ru'danin da nake jin inama ajalina ya riske ni a yau saboda tsananin asarar da nake jin na tafka, ba yadda zan yi ne, abin ne ya fi 'karfina"

Dukkansu jikinsu ya yi sanyi mussaman yadda yake maganar cikin rawar murya tamkar ba Mukhtar ba, namiji mai karfin zuciya.

"Allah ya daidaita ya kawo mafita " cewar Alh Isa da ya rasa mai zaice, dan ya lura Mukhtar na cikin rashin nutsuwa da firgici, ya tabbatar kuma yana da gaskiya, sannan mai 'daki shi yasan inda yake masa yoyo.

Dukkansu suka amsa da "Ameen, ya yin da Hajiya ba haka ta so ba, so ta yi ya wula'kanta mata shi, ya kuma tirsasa masa ya mayar da matarsa ko ba ya so.

Har da Alh Isa suka 'dunguma zuwa gidan su Sa'a, Hajiya ce kawai ta ce ba zata je ba, bata san da idon da za ta kalle su ba.

A tsakar gidan Baffa ya jagorancin zaman, Alh Isa ne ya yi karfin halin bayyana mutuwar auren wadda ya matu'kar dukan zuciyar iyayen na Sa'adah, juyin duniya ba wadda ba'a yi musu ba, amma sun 'ki bayyana menene dalilin da ya haifar da wannan tashin hankalin, kukan da Sa'a ke yi tamkar za ta shi'de ya sake 'daga hankalinsu.

A hankali Mk ya ce "Baffa Ina rokon ka, kar yanke mini kauna, ka yafe mini, kaddarar muce ta zo da hakan, har wayewar garin YAU bamu san zamu tsinci kanmu a cikin wannan mawuyacin HALIN da muke ciki ba, ina kuma fatan itama ka yafe mata, ba laifinta bane Baffah".

Gurin ya yi tsit sai shshshekar kukanta kawai ake ji, Mahmoud ya kamu da ciwon tausayin masoyan biyu, mussaman Sa'a kallo daya za ka mata kasan tana cikin tsaka mai wuya.

Baffa ya nisa ya ce "Ba aurenta ne ya hadamu ba Mutari, ba kuma zai zama dalilin rabuwarmu ba, nasan halin girma irin naka, tsiyar a gunta take, yanzu kuma zata gane tsiyar har wasali gareta, domin na tabbatar laifin nata ne, ba zata 'ki zaman aure ta yi tunanin zata zauna a gabana ba".

Ga mamakin Mk sai ya ji kalaman Baffa sun sake girgiza masa zuciya.
Da sauri ya mi'ke ya koma kusa da shi ya ce "Baffa Dan Allah dan Annabi ka yi ha'kuri, idan ka yi haka bazan yafewa kaina ba, ka yiwa Allah ka barta ta ji da tashin hankalin da na jefata, ba laifin ta bane, nawa ne, Ni za ka hukunta ba ita ba".

Ido kawai Baffah ya zubawa Mk da yake gurfane a gabansa yana rokonsa idansa jawur, ga wata irin rama da ya yi ta farat daya.
A ransa fadi yake Iyah kin tafka asara, kubucewar miji irin Mutari abin ki shimfi'da tabarma azo a miki jaje ne.

Ya tabbatar laifin na Iyah ne, amma ya 'boye laifinta, ya kuma tsaya kai da fata wurin nema mata sassauci da aminci a gurinsu.

Baffa ya dafa kan Mk ya ce " Madallah da mutanan kirki irin ka, madallah da mutane masu irin dabi'ar ka, madallah da zuciya mai adalci irin ta ka! Saboda kai zan bar Iyah ta zauna a gidan nan, ban taba jin takaicin rashin ya'ya da yawa ba sai yau, da ace Ina da wata 'yar! da wallahi taron nan bazai watse ba sai na musanya maka da ita".

Kwalla ta 'kwacewa Mk ya na jin kunya da tausayin Baffa na sake masa rubdugu, wacce irin kauna ya ke masa haka, anya bai yi rashin kirki da ya kasa yin ha'kuri da 'yarsa ba?"

Ba zato suka ji Mk na cewa "Baffa me yasa ba zaka ba ni umarni na mayar da ita ba, sai ka yi fatan ka bani yar'uwarta idan hakan ya yiyu ka haramta mini ita gaba'daya fa?".

Ba ki 'daya jikinsu ya dan yi karfi saboda kalaman Mk, wadda suke bushara da zai iya daidaitawa da matarsa, yanzu ko anjima.

Inna ta ce "Tunda baka da wata da za ka bashi, ai sai ka mayar masa da wadda ka ke da itan".

Cikin kuka sosai Sa'adah ta ce " Na gode Innah".





*Surayya Dee*
✍️


🌺 *HALIN YAU*! 🌺

NA

*SURAYYA DAHIRU*.

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/



*_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai da satar Dukiya._*

_*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_





*Gaisuwa da fatan alheri ga wadannan groups din*
*LAFAZEE FANS*
*DANDALIN MUM KHADY*
*HAFSAT SODANGI fans*
*DAGA DAJI 1&2 fans*
*PAID GROUP na BINTA ABBALE*
*DANDALIN SADA ZUMUNTA NA ANNURI.*
*JIDDA REAL FANS*
*FADILA LAMIDO FANS*
*SADNAF NOVELS GROUP*
*TASKAR AISHA MICHIKA*
_*Dama sauran wadanda ban ambato ba, mu hadu a shafin gaba, Kuna da yawa Allah ya bar kauna_*.
*MK, SA'A DA FARIDA NA GAISUWA*


*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



79_80.


"Ba zan ba ka umarnin da na san kunya da nauyi ne zaisa ka yi shi ba.
Ba ni na maka umarni ka auri Iyah ba, ku ka hada kanku, ka aureta bisa ra'din kanka, ka zauna da ita cikin shekaru bakwai, Ni da mahaifiyarta shaida ne akan kyakkawan rikon da ka mata, haka nan, ka na girmama mu da dukkan zuciyarka, kana jin nauyi na tun kafin na baka aurenta, idan har za ka iya sakin Iyah, to ni kuwa bazan yi son zuciya ba, na tabbatar abin ne ya fi 'karfin ka".

Ya nisa ya cigaba da cewa
"Zan so kwarai ace na mutu na barta a hannun ka, domin Ina da yakinin ba za ta wulakanta ba, amma ya na iya da HALIN 'dan YAU mai yin aiki da son zuciya, daga baya kuma ya jinginawa tsautsayi da 'kaddara".

Alh Isa ya muskuta ya ce "Tun kafin mu zo nan, na umarceka da ka janye, ka mini gardama, amma yanzu kana cewa ya baka umarni ka mayar da ita, Ni baka jin nauyi na Mukhtar?"

Kunya iri iri ta sake rufarwa tashin hankalin da Mk ya ke ciki, a sanyaye ya ce " A a Baba bayan nauyin ka da nake ji, wallahi kallon uban da ya isa ya zartar da hukunci akai na na ke maka! Abin da yasa ban amsa ba, ina jin tsoron kada na mayar da ita a yanzu auren ya lalace gaba daya, saboda zuciyoyin mu cike suke da bacin rai mai ya.."

Cikin dimaucewa Sa'adah ta
katse shi da cewa "Ni zuciyata ba komai sai salama da nadamaar *HALIN* da nake ciki, na yi al'kawari zan jure duk wani kalar fishinka, ba zan yi abun da za mu kai ga lalata auren mu ba".

Tausayinta ya ratsa su dukkan su, gurin ya dauki shiru, sai fama suke da tausayin su, kowa ya lura laifin Sa'adah ne, amma Mk ya kafe laifin sa ne, su gafarce shi, haka aka tashi ana addu'ar, Allah ya daidaita su.


Bayan tafiyar su Mk, kukan Sa'adah ya karu, sosai ta ke rusa kuka, yayin da iyayen ta suke fadin ba ki ma fara kuka ba, domin sai nan gaba za ki gane asarar da ki ka yi ba 'yar 'karama bace.

Zazzabi mai zafi ya rufe ta, hakoronta suka dinga karo da juna, jikinta sai rawa yake tamkar mazari.

Da farko shareta suka yi, sai da suka ga abin na sake 'kamari sannan Inna ta kai mata 'dauki, tana sa hannu a jikinta ta ji zafi zau.
Har dare tana cikin wannan yanayin, kan dole Baffa ya 'kira wani jami'in lafiya, mai chemist a unguwar ya zo ya bata taimakon gaggawa.


Haka al'amarin ya kasance da Mk, bayan sunje sun sauke Baba Isa, yace da Mahmoud gidan Hajiyar Bichi zai maida shi, suna shiga falon nata ya yanke jiki ya fadi, alma'arin da ya matu'kar tayar da hankalin su, 'Karfi ya fita a gigice, ya yi sa'a ya tarar da Abbas na gida, ya 'Kira shi suka ciccibi Mk zuwa wani asibiti mai zaman kansa mafi kusa, dole aka kwantar da shi sakamakon jininsa da ya yi mugun hawa, baya ga haka yana cikin damuwa da ya ke bukatar hutu..

Abbas ne ya zauna da shi, sauran yan'uwansu kullum suna zarya a asibitin, haka nan Mahmoud kullum sau biyu yake zuwa duba shi.
Har zuwa wannan lokacin Jawad na gidan 'Karfi bai san me yake faruwa ba, takanas Mahmoudya je ya debo masa uniform da kayansa kullum da safe zai kai shi, idan anta shi kuwa mai aikin matar ke hawa adaidaita ta dauko shi, idan ya tambayi Mamin shi ko Malam sai ace sun yi tafiya ne, bai damu ba, tun tafiyarsu Abuja ya saba zama gidan Mahmoud Karfi.

Kwanansa uku aka sallame shi, tare da gargadin ya rage damuwa, ya kuma kula da shan maganinsa.

Haka ya tattare dakin Hajiya, tun tana ki, har ta ha'kura ta barshi, kan dole ta koma kwana a babban falon su, da suke zama ayi dab dabla lokacin Hajiya Babba.

Kwanansa biyu a dakinta yana warware wa, a cikon na uku ne ganin ya dan sami sauki har ya ci abinci, yasa ta bijiro da maganar Sa'adah.

"Matu'kar kana son mu shirya to ka dawo da matarka, rashinta ne duk ya susuta ka haka, idan kuwa ka 'ki jin maganata kar kuma takowa inda na ke, ko gaisuwar ka bana so".

Hankalin sa ya tashi, ya fara 'ko'karin fahimtar da ita da hujjoji, amma fur ta hau dokin na 'ki.

Ganin da gaske ta ke yi, shikuma a yanzu wani irin tsoro da firgicin zama da Sa'adah ne ya ke kama shi, bai ta'ba tunanin za ta yi abin da ta yi ba, mussaman yadda ya ke wadata da komai, uwa uba kuma yadda ya ke tarairayarta da gudun zuciyar ta, idan har hakan bai sa ta kiyaye masa amana ba, bai ga kuma me zai mata ba.

Kansa har zafi yake wurin tunanin, me yasa ta yin hakan? Ya tabbatar shi baya ha'intar ta akan me ita zata ha"ince shi?

Wani irin tsimin bacin rai ya taso masa, mai hade da kishin da ya haddasa tsanar Sa'adah, ya kasa bu'de baki ya yi magana kawai ya kife kansa akan guiwowinyasa ya fashe mata da kuka tamkar yana cikin shekarun 'kuruciya.

Wannan kukan ya matu'kar ta'ba zuciyar Hajiya, ta shiga ru'dani da wasiwasi akan lamarin Sa'adatu, kan dole, ta ha'kur'kurtar da zuciyar ta, ta ce ta janye takunkumin dolen da ta yi masa.

Amma a zuciyarta sai hasashen wanne irin abu ta yi mai muni haka?.

Sati guda da faruwar wannan lamarin, amma har lokacin Sa'adah na kwance ba lafiya., saboda ta 'kuntata zuciyar ta, ta 'ki cin abinci, kullum cikin kuka ta ke, ta yi wata irin rama mai tayar da hankali, kuka ta yi shi irin wadda ba ta yi tunanin akwai mahalu'kin da ya yi irinsa ba, ko ya ya ta ayyana Mk ya saketa, shikenan sun rabu? sai dai Inna ta jiyo ta 'barke da kuka tana fadin na tafka asara, na yi nadama.

Sannu a hankali zance ya shiga kunnuwan dangi, kowa ya ji mutuwar auren sai ya shiga alhini saboda yadda aka shaida soyayyar da Mk ya ke yiwa Sa'adah, mussaman Auntyn Lagos, Maman Gombe da Samira, hankalinsu ba karamin tashi ya yi ba, da kuka Antin Lagos ta 'kira Hajiya tana tambayarta gaskiyar magana, cike da tausayi Hajiya ta tabbatar mata sun rabu tabbas.
Da rawar murya take fadin "Hajiya ki matsa masa ya dawo da ita, na tabbatar duk inda ya ke, ba ya cikin nutsuwa, yana sonta".

"Hmmm kawai ki musu addu'a amma lamarin na su akwai tashin hankali." Inji Hajiya .

Wata guda Mk ya 'dan wartsake, ya koma harkokinsa da 'karfin zuciya irin ta namiji, sai dai abin na nan ma'kale a zuciyar sa yana jin har ya koma ga mahallicinsa ba zai manta ba, idan ya tuna dalilan da zai hana Sa'adah ta bashi wayar nan sai ya ji bugun zuciyar sa ya karu, wani lokacin har jiri ke dibansa.

Ga Sa'a kuwa wannan watan ta cinye shi ne a kwance tana 'dan'danar azabar ciwon so da nadama, tunda gyatumarsu ta kawo ta duniya bata taba fuskantar tashin hankali irin wadda ta ke ciki ba, fata take mutuwa ta dauketa ta huta da wannan zugin da zuciyar ta take mata, inama ta bashi wayar nan ya gani?
Wata'kila da ba zai zafafa lamarin har haka ba, tun shekaranjiya da ya aiko mata wasu cikin kayanta shake cikin akwati babba, yini ta yi a ranar tana kuka, ba abin da ta ke fata irin ta ji ko da Muryar Mk, amma abin ya faskara, ga tunanin Jawad rabon da ta ganshi tun ranar da suka rabu da Babansa, ta yi dalilin da suke rayuwa a wuri daban daban, wannan kadai ya isheta ladabtarwa.

Cikin wannan 'kangin ta sake cinye wani watan har da 'karin kwanaki goma, zullumi ya ishi Sa'a, saboda kwanakin iddarta na gab da kammala, duk wadda ya ganta yanzu, muddin ya santa a wattannin baya, sai ya tausaya mata, gashi dai ba ta rasa komai ba, amma ta rasa kwanciyar hankali, satin ta biyu a gidan Mk ya aiko da kayan abinci kala kala wadda za su kwashe rabin shekara suna ci, sai kuma ya mata siyayyar komai na bukatunta tun daga kan kayan shayi har sabulai, da tarkacen abubuwan da zata bu'kata, amma ko taba su ba ta yi ba, hakanan abinci sai Inna ta tausaya mata, ta zauna kusa da ita, ta matsa mata sannan za ta yafita .

A lokacin Sa'adah ta fahimci ba abin da yafi nutsuwar zuciya da'di, addu'a ta ke sosai akan ta sami sau'kin tashin hankalin da take ciki, idan ta ji yo su Baffah na hira har da raha shi da Inna sai ta tambayi kanta yaushe za ta fara dariya ne ita?.

Yanayin da ta ke ciki ya fi kama da na mai takabar da mutuwar managarcin miji ya zo mata kwatsam.

Daidai wannan lokacin Sumayya ta iso Kano dan jajantawa yar'uwarta halin da tsinci kanta a ciki.
Halin da tarar da Iyah a ciki ya bala'in girgiza ta.
Cike da tausayawa tace " Na sha fada miki halin da kika jefa kanki ba inda zai kai sai nadama, gashi tun ba a je ko ina ba, kina fuskantar Halin Yau! duk wadannan kawayen na ki da kika mayar allon kwaikwayon ki YAU suna Ina?"

Karon farko da Sa'adah ta fara jin sassauci domin sai a ranar ta Sami wadda ya mata fa'da, iyayen ta sun zuba mata ido, ba wadda ya buda baki ya mata fa'da, sun mata dungu suna gasa ta da idanuwan su kawai, hatta Baffah da ta tabbatar ba abin da yake so a duniya irin ta, wannan karon ta na hango ko oho da yake yi da lamuranta.

Ta ri'ke hannun Sumayya ta na wani irin kuka, tana fadin "kin fada mini, ba irin gaskiyar da ba ki fada mini ba, sai dai an riga an kadddara mini yanka kazar wahala, dole kuwa sai na figeta tas, Mukhtar mutumin kirki ne, laifin duk nawa ne, sai dai nima kadddara ce da bazan iya kauce mata ba, ki taimake ni Aunti! ki bashi ha'kuri, Tunda Baffa ya barni da kaina".

Ta shide tsabar kuka! Hankalin Sumayya ya ru'banya tashi, amma hakan ta daure, ta tausasa murya ta ce " ki daina irin wannan kukan, idan har kin yi amanna kaddara ce ta hau kan ki, to ki yi hakuri ki bita da istigifari, yawan kuka da 'kauracewa abinci da takurawa zuciya ba abin da zai haifar miki sai ciwon da zai kayar da ke, ina tabbatar miki duk wadda zai shiga damuwa a dalilin rashin lafiyar ki, ke ce dai mai jin jiki?"

"Na gode sosai Anty dan Allah ki 'kira shi, ko zai ga girmanki".

Sumayya ta nisa ta ce "Bana jin girmana zai sa ya janye kudirinsa tunda har bai janye saboda Baffah ba".

Hawaye ya kwaranyowa Sa'adah ta ce " Baffa ba ya son na koma ne, a gaban mu Mukhtar ya ce ya bashi umarnin ya mayar da ni, amma 'kememe Baffa ya 'ki, ya barni na ji da dabarata".

Sumayya ta yi shiru, tana jin tausayin 'kanwarta na sake kamata, ba ta gane muhimmancin mijinta ba sai da ya kubuce mata, ta tuna wani lokaci da ya shude tana mata fadan ta bi mijinta su zauna lafiya.

Ta nisa ta sake tuno amsar da Sa'adah ta bata a waccan lokacin, "Anty ki ta cemin na bishi, na masa biyayya ko da yana cutar da ni, akan me zan yi irin wannan rayuwar auren alhalin ko yau Mukhtar ya barni Ina da yakinin zan samu wadda ya fi shi."

Ta dago ta kalle ta, yau Mukhtar ya barta, da ya tashi barin nata ba shi kadai ya tafi ba, sai da ya yi awon gaba da dukkan nutsuwa da walwalarta, bugu da 'kari hatta kyaun da ya sa take ta'kamar zata samu wadda ya fi shi, ya tsiyaye tas, ta kai duba ga kirjinta , ta ga sun yamushe a cikin riga, mamaki ya kama Sumayya bata taba sanin nonon Iyah zai iya zubewa haka ba, domin ko da take shayarwa a tsaye kuma a cike suke, irin wadda suke ma'kale ne a kirjin mace, amma tashin hankalin da take ciki suma ya tabasu, hakanan gashin kanta sai saukewa yake yi, ga uwar rama sai ido gwara gwara tamkar idon agolan Banufe.

Ta ke Sumayya ta dinga neman tsari da shiga tashin hankali kwatankwacin irin wadda Iyah ke fuskanta, ta kuma nemawa yar'uwarta samun sassauci da mafita.

A hankali ta ce "zan 'kira shi, sai zuwa dare tunda yanzu yana gurin aiki, fatana dai ki kwantar da hankalin ki, ki karbi kaddarar ki da hannu biyu, yanzu a ina Jawad ya ke?"

" Ni ma ban sani ba" Sa'adah ta fada a sanyaye.

A daren ranar kuwa Sumayya ta 'kira layin Mk, da girmamawa ya amsa wayarta, suka gaisa, ta fara da tambayar Jawad, ya amsa da yana nan lafiya Lau, shima ya tambayi nata iyalan, da 'kyar Sumayya ta iya masa maganar Iyah, ga mamakinta sai taji ba alamun zafafawa, ya ce "Anty ku bimu da addu'a da ga ni har Sa'adatu abin ya zo mana a ba zata, muna bu'katar mu nutsu, zuwa gaba muga me ubangiji zai zartar mana, har yau ina sonta, Ina fatan mu sake zama, sai dai muna bu'katar hutu da nutsuwa, idan dukkan mu mun fahimci manufar auren, zamu dawo mu sake zama abu guda, amma for now, ya kamata mu bar komai a hannun mai juya al'amuransa ya mana zabi".

Sumayya ta amsa da "Hakane" tare da yi masa godiyar amsa 'kiranta da ya yi, ta rufe maganar da ro'kon ya kawo mata Jawad yaranta suna ta tambayar shi. Ya amsa da gobe juma'ah zai kawo shi ya yi week end tare da su".

Ta ajiye wayar, tana kallon Sa'adah da ta yi mata 'kuri tana son jin abin da ya ce.

Kasancewar Sumayya na cikin jerin mutanan da basa yiwa 'karya kwaskwarima dan su da'dawa wani, kai tsaye ta ce "Iyah ki barwa Allah zabi kin ji, idan zaman ku bai 'kare ba, za ki koma dakin ki, idan kuwa iya adadin da aka deba muku za ku yi kenan, ina tabbatar miki ba za ki koma ba, hakan kuma ba shine 'karshen farin ciki ba".

Kuka sosai Sa'adah ta yi a wannan daren, kafin ta tashi ta 'doro alwallah ta fara sallar nafila, idan ta na addua a fili take fadin " Allah ka rufa min asiri, ka mayar da ni 'dakina, Allah na tuba".

Sumayya kawai kallon ta take tana sake jin tsoron ubangiji na kamata, yau Iyah ke wannan haukan akan Mk, Ashe duk wani kau'di da ginshirar da take yi shine kanta ya dawa?

Ko yau Mk ya mayar da ita, ta yi amanna ya karya duk wata fuffukar da take ji da ita, za kuma ta nutsu ta daina fitinarsa, tun lokacin da ta haihu amma ya iya hana ta zuwa ta dubo ta, ta tabbatar Sa'adah ta fara kai shi bango ne, ta kuma koya masa rashin kirki.

Washagari kuwa ya kawo Jawad har kofar gidan Baffa da 'yar karamar jakar kayansa da kuma ledar biskit da alawowi ga su Ayman.

Da gudu ya shiga cikin gidan! Mk na tsaye yana jin rashin dadi, yana son ya shiga ya gaida Inna, amma kunya ya ke ji, hakanan ya ke ganin rashin kyauta wa idan har bai shigan ba, saboda ya saba duk sadda ya kawo shi zai shiga su gaisa sannan ya tafi, haka idan zai dauke shi.

Har ya juya sai kuma ya dawo ya shiga, ya dade a tsaye a zauren, yana tuna moments dinsa da Sa'adah a cikinsa.

Dukkansu suna tsakar gidan Suka ga Jawad ya shigo a guje, suka rungume juna da

Please Login or Register in order to submit comment