You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

idan ta yi za'a ci cikin dadin rai ba wai iyawa ne ko kadan bata yi ba. Amma harkar cake da su meatpie hadi da su samosa tafi karfi anan.

Wannan karon har wani cake ta yi masa na mussaman, tamkar na murnar zagayowar haihuwarsa saboda girmansa da kyaunsa.
An rubuta welcome to Home Dear Jawad!.

Lamarin da ya farantawa Mk rai ba ka'dan ba, ya dinga gode mata, tare da yabawa.

Yana futa ta zube kan kujera, tana son ta ga dame Mk ya rageta?

Ta gama tunaninta ta gamsu bai rageta da komai ba, ko a harkar auratayya kuwa, anan bangaren ma ta lura yana daga mata kafa soasai saboda lalurarta, amma bu'katar sa ta zarta yadda yake mu'amalantar ta saboda rauninta da yake gani.

Tsananin son Jawad da yake yi ne kawai yake dan mintsinin zuciyarta, domin ta gane son uwarsa ne ya shafe shi. Ta kuma amince ba laifi bane yin hakan, sai dai zuciya da bata da kashi, yasa take jin rashin da'din soyayyar, duk da kuma zata shaidi soyayyar Jawad bata rufewa Mk ido ya kasa tsawatar masa ba, yana iyakar kokarinsa wurin saita yaron, ko akan al'amarinta ma ba ya yi masa ta Da'di.

A bangare 'daya ne, take ganin raunin Mk akan 'dan nasa, matu'kar suka fita shopping, indai ya ga ta zabi kaya to kuwa sai ya daukarwa uwarsa irin kayan sai banbancin kala, Mk kuma baya iya hana shi, ko cewa ya yi ya rage, da zarar ya bata rai shikenan zai ce ya dauka.

Ta dinga jin sha'awar haihuwa na mamayarta, ta daga hannu ta ce "Na sani sarai baka manta da ni ba ya Allah! Idan ka tashi bani, ka bani mai lafiya, mai jin kai, mai kuma albarka. Ina neman tsari da wadda zai gigita zaman lafiyata da ta mutanan da suke kewaye da shi, Ina neman tsari da marar lafiyar da jinyar sa zata shagalar da ni yin ibada da yawan tuba da godiya bisa ni'imomin da ka mini marasa adadi".

Hawaye ya ziraro mata ta sa tissue ta goge idanuwanta, ta sake cewa"Allah kar ka bari na kunyata, kai ka halattawa maza yin mace sama da daya, albarkacin yarda da hakan da na yi Allah kar ka bari na wulakanta akan wata da muka yi tarayya a jinsi guda".

Kuka sosai ya kwace mata saboda kishin Sa'adah na neman hanata sukuni a zuciya.

Ta Dade kafin ta tashi ta yi wanka, ta doro alwallah ganin takwas har da rabi sai tada sallar walaha, tana ta rokon a sau'ka'ka mata kishi, a kuma karawa Mijinta sonta da tausayinta.

Ta rufe addu'ar da yiwa Mk fatan samun cikakkiyar lafiyar da zai gamsar da su, da kuma budin arziki, ta sake rokar masa ikon yin adalci, tana kuka take cewa Allah ka hana shi zaluntata, Allah ka bashi karfin zuciyar da zai yi adalci na gaskiya.

*Ko mata nawane masu irin wannan dabi'ar?*
*Shin kina sallar Duha kuwa?*
*Idan ba kya yi maza ki fara domin Allah ya yi rantsuwa da lokacin, sannan kin yiwa gabbanki sadaka a yinin gaba'daya*.

Sun iso Wudil, Mk ya ji bari ya ziyarci tsohon amininsa da suka yi F.C.E. Bichi tare.

Ya laluba ba lambar wayarsa, ya dai dinga shiga hanyar ya gano gidan.
Ai kuwa a kofar gidan ya tarar da shi yana alwalar sallah juma'ah.

Da wata irin murna ya kar'bi Mk! Ganin lokacin sallah ne kawai sai suma suka yi alwalar suka zarce masallaci.

Suna dawowa aminin nasa ya baibaye su da abinci tamkar dama yasan da zuwansu, Mk ya dinga tsokanar su da cewa wai har yanzu baka kara aure ba? Kullum uwargida na office?"

Dai dai lokacin matar gidan ta dawo sanye cikin uniform tabbacin Ma'aikaciyar lafiya ce. Mk ya tasa ta gaba yana fa'din " bazai yiwu kullum kina barin aminina shi ka'dai a gida ba, dole zamu lalubo wadda zata zauna ta kula da shi.

Tababa da ke mai kunyace ta fice ta bar Mk na yi musu sha'kiyancinsa da baya gajiya.

Za su tafi ta kawo turare ta bawa Jawad, da wata kullin leda mai dauke da man shafawa da na zafi ta ce na Hajiyar Bichi.

Mk ya tsaya cak yana fa'din" Tababa ta Malam ki ji tsoron ubangiji, ita kuma Farida ina nata sakon, gaba'daya kin saka son zuciya a lamuran ki, saboda ba kawar ki ba ce ita"

Da sauri ta koma daki ta dauko kyawawan mafitai guda biyu ta ce ga shi nan, ta yi maka fifita ni bana son sarhutunka".

Ya karba yana fa'din kin fanshi kanki, yayin da mijinta ya yi gaba yana fa'din ranar da za'a mata amarya ai ban san irin boren da zata yi ba, idan ka ga yadda ta yi kukan aurenka sai ka yi mamaki, ta taya Sa'adah kuka irin wannan ina kuma ace ita za'a yiwa?'

Mk ya murmusa ya ce ai kuwa dai Tababa kwantar da hankalin ki, daga yadda na ga kin iya karrama ba'ko , zaki dade kina jan zarenki, muma kaddara ce ta fado mana, Ina fatan idan kuma kaddarar ta fa'do muku ba zaki yi watsi da kyawawan dabi'unki ba".

Ya damkawa yarinyarta karama kudi, Yana ta godiya da karamacinsu, ya tafi ya barta da sanyin jiki tana addu'ar kasancewa ita ka'dai.

Har la'asar Mk na Wudil domin tare da aminisa suka je ainihin gidan su Baba Isa ya ziyarce su, suka dinga sa masa aalbarka ya ajiye musu buhun shinkafa da katon din taliya, har da ku'di a kanin Baba Isa Wanda shine babba a gidan yanzu.


Sai da suka fito ya ajiye Aminin nasa a kwanar gidansa, suka yi sallamah.

Sun tsallake gadar Wudil ya samu wuri ya tsaya. Ya ce "Jawad dawo gaba kusa da ni, kana mini hira".

Hakanan kuwa aka yi, sun zo dai dai Yar gaya, Jawad ya ce "Allah sarki Muhsin Yargaya! ko yana ina yanzu?" Ya dinga bashi labarin Muhsin da irin halin da yake ciki da matar Babansa.

Nan Mk ya fahimci inda Jawad ya samu dalilin juyawa Farida baya, ya dinga jin tausayin yaran da suke fuskantar kalubalen rashin rayuwa tare da uwarsu.

Cikin hikima ya ce "Ashe Muhsin ya fa'da maka u have to be careful with Aunty saboda kar ta raba mu?"

"Eh mana Malam! Saboda na san kai baka san hakan zai iya faruwa ba".

Mk ya yi murmushi ya ce "Jawad kowa da halinsa! Da zata raba mu da tuni ta yi hakan, fa'da mini ta ta'ba dukan ka lokacin da muke Uk?"

Ya girgiza kai alamun a a, Mk ya zarce da fadin "abinci ne bata baka ko?"

Da sauri Jawad ya ce "Ah Malam tana ba ni, every day sai ta cika mini lunch box dina, abincina ya fi na kowa yawa, kullum sai na dawo da shi".

"Ka ga kenan ba halin su daya da Waccan da abokinka yake baka labarinta ba".

"Amma Malam ai ita kake so ba Mami ba".

Jikin Mk ya yi mugun sanyi a shekaru sha uku Jawad ya yi wannan maganar? Al'amarin yaran yau idan kana daukar maganar su tabbas zasu raba tsakanin ka da jama'a ne, ka yi ta ganin tamkar kitsa musu magana ake yi. Ko kuma ana koya musu iyashege ne alhalin kuma abin a jikinsu yake, sai dai ayi ta nuna musu kyakkawar turba cikin azanci da nasiha.

Mk ya nisa ya ce "wa ya fa'da maka bana son Mami? Ita ce fa ta haifa mini kai! Kasan kuma u are my only son, dole kuwa ta zamo very precious to me".

Da'di ya kama Jawad ya ce " To yaushe zata dawo gidan mu, tunda we are Muslims, polygamy is allowed, above all ma ka mini al'kawarin zan dawo hutu na ganta a gidanmu ba a gidan Baffah ba".

"Eh na yi maka ban kuma manta ba. Amma matsalar itace bata mini magana, bata gaishe ni, har Baffa yana mata fa'da amma still bata ji ba".

"Ni zan fa'da mata ta daina yin haka tunda kullum sai ta ce mini arogance ba kyau, ba dabi'ar mutanan kwarai bane".

" Yauwa sannan ka fa'da mata, kana son ganinta a gidanmu, if not jirgin nan da zaka siya mata zai zama nawa".

Dariya Jawad ya dinga yi yana cewa" Malam ka damu da jirgin nan, amma ai yanzu na ce har da kai zaka shiga. Ni ban san me yasa ta daina son dawowa ba, bana manta sadda take kukan so take ka zo ka dauke ta mu koma gidanmu"

Jikin Mk ya yi sanyi ya ce "tafiyar da muka yi, muka barta ne, amma idan zan sake komawa da ita zan tafi, kai kuma ka zauna tare da Anti a anan".

"A a Malam gaskiya ba a yin haka, da ni za'a tafi"
" To na yarda da kai zamu tafi, yanzu idan ka je gurinta sai ka yi ta bata hakuri ta dawo ta zauna da mu".

Murna tamkar Jawad ya zuba ruwa a kasa ya sha, wani irin farin-ciki ya bayyana a dukkan jikinsa

Sun iso kano Mk ya kalli Jawad cikin uniform dinsa sai ya dinga tuno shima lokacin da yake makarantar su ta 'Karaye. Haka yake tamkar Jawad, sai dai da alamu Jawad yana iya zarta shi tsayi domin a yanzu ma ya kusa kamo shi. Tsayin Jawad da saurin da karatunsa ya yi sai ake ganin tamkar ya zarce shekarunsa.

Da tarin kauna ya ce " A ina kake son yin hutunka?"

Kai Jawad ya sunkuyar ya ce "gidan Hajiya".

Mk ya ce "Antinka fa tana can ta shirya maka something special".

"Zan je amma ni gidan Hajiya zan zauna".

"Me yasa to ba zaka je unguwa uku ba?"

Ya marairaice tare da cewa "
Na san idan na ce can zani ba zaka yarda ba".

Da sauri Mk ya ce na yarda Jawad! Ka yi hutunka duka acan idan kana so".

Jawad ya kalle shi da mamaki! ya ga seriousness a fuskar Baban nasa ya kasa gasggatawa ya ce " please Malam are you serious, are u sure?"


Da sauri Mk ya kada kai ya ce very sure Babana! Yanzu zamu je gida kaa ci abin da Anti ta shirya maka, daga nan sai mu zo ka gaida Hajiya, sai mu koma ka kwana tare da mu, tomorrow morning da kaina zan kaika gidan Baffah ko gidan Anty Sumayya ko ina kake so nan zaka je".

Ya dinga murmushi irin murmushin Sa'adah, wurshiryar da ya samu daga gareta ya sake kawata murmushin nasa".

Da farin ciki sosai Mk ya ce "kyaun ka na bayyana idan kana smiling my boy".

Jawad ya sa hannunsa ya rufe fuskarsa wai shi kunya.


Da murna sosai Farida ta karbi Jawad ta dinga ina ka saka da shi, karshe ya shige dakinsa da komai na ciki blue ne, irin kayan alatun da aka shirya masa duk dan a hilace shi ya daina gudun gidan basu yi tasiri ba.

Wanka ya yi, ya shirya ya fito ya tarar da kayayyakin da aka tanada dan shi kala kala.
Farida ta dinga rawar jikin kyautata masa adalilin taga sassauci a tare da shi fiye da wattannin baya da ko kallon inda take ba kaunar ya yi. Ta ji farin-cikin sauyin da ta gani a tare da yaron.

Sai yamma lis suka fice da Babansa.

Basu dawo gidan ba sai dare sosai domin har sai da Jawad ya yi barci a dakin Hajiya.
Da ya zo yana tashinsa Hajiya ta ce
"Barshi mana tunda ya yi barci".

Da sauri ya ce " A a Hajiya bari kawai mu tafi lalla'ba shi nake yi ya daina gudun Farida, ta dora hankalinta akansa, amma yana gudunta tamkar kunama, yau dai na ga ya fara saukowa, gobe zan kai shi wurin uwarsa dan hankalinsa ya kwanta".

Hajiya ta ce "dan hankalinsa ya kwanta, ko dan ka samu dalilin ganin uwarsa babu hijabi?"

Mk ya ce "haba Hajiya"
"Haba Hajiya ko dai haba gaskiya?"

Washagari kuwa ya kai shi gidan da tarin tsaraba Niki niki tamkar wadda zai shekara, har da cake dinsa na murnar dawowar sa gida, bai ci ba, Mk ya ce ya taho da abinsa. har cikin gidan Mk ya shiga ya tarar da Innah na yin wainar shinkafa irin ta garin su Shafa'atun Bauchi ko da yake itama Innar ai daga Gamawa take kenan Inna Yar Bauchi ce. Sa'a na kicin na hada miyar cin masar.

Ya dinga tuno yadda Sa'adah take yi masa waina da miyar ganye da yake santi, haka nan ya yi kewar dambunta, ya yi kewar farfesu mai daddawa, ya yi kewar kunun danyar gyada da shinkafa, da alkubus. Traditional dishes da ya yi kewar su ba za su lissafu ba, hatta shinkafa da wake har yau bai sake cin mai gardin ta Sa'adah ba. Haka nan kwa'don zogale da Rama. Yana matu'kar jinjinawa Inna yadda ta horar da Sa'adah nau'in abinci kala, kala masu dan karen 'dan'dano da kashe kowacce irin yunwa, ga kara lafiya.

Sa'a tana jinsu ta rakube, ko kwakkwaran motsi ta ki yi dan kar a hangota.

Baffa ya fito yana marabatarsu, yayin da hankalin uba da 'da ya karkata a son ganin Iyah.

Lura da hakan da Baffah ya yi yasa ya kirata, ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa, dinkin free ne amma ya matu'kar yin kyau.

Da sauri Jawad ya ruga ya rungumeta yana fa'din "Daure ki gwada daga ni sama Mami".

Baffah ya yi saurin cewa "wannan shine gangan Jawad, a gabana ka ke son ka kayar mini da uwa?"

Mk ya murmusa ba tare da ya ce komai ba, bagarar da shi da Inna ta tsiri yi masa na matu'kar damunsa.

Duk yadda Inna take jin haushin Mk bai hana ta zuba masa waina ba, ta zuba masa masar a ledar ta sake kara wata ledar, ta mike ta dauko flask ta shiga kicin ta zubo miya, ta kawo ta ajiye masa a gabansa, a hankali ta ce ga waina, ta koma ta cigaba da aikinta.

Baffah kuwa fa'di yake "wannan tafiya zai yi da shi zubo masa wadda zai ci yanzu"

Da sauri Mk ya ce "Na riga da na karya, na gode, a ransa kuma fa'di yake yaushe zan iya cin abinci a gaban ku?"

Idon Baffa ya sa Sa'adah cewa Mk "Ina kwana".
Ya amsa da sauri, cike da walwala.

Ta shige dakinta Jawad ya bita, ya kwanta a shimfidarta, yana cewa "I miss your scent, I missed everything about you my Iyah".

Ta ce "Ashe ban hanaka fa'dar Iyan nan ba?"

Ya turo baki irin yadda ta ke yi ya ce "Iyah means mother, means uwa, Mami da Iyah all the same".

Ta ce "To dai ban son sunan a bakinka barwa Baffa da Innah kawai".

Mk suka fita tare da Baffah! Jawad ya fito da sauri ya bisu, daga kofar gida Baffa ya wuce inda za shi, yayin da su kuma suka tsallaka zuwa shagon Mk .
Jawad ya yi mamakin yadda aka sake kawata shagon, komai na wurin na zamani ne, ya zauna yana cewa " Azo a wanke mini kafata".

Harara Mk ya galla masa ya ce " Saminu ba ya nan, ina fatan ba Uncle Akil kake nufi ya wanke maka kafar ba?".

Jawad ya yi shiru! Yayin da Mk ya zarce da fa'din, kullum ana idar da Sallar la'asar ka tabbatar ka zo nan kana koyon aiki, zan fa'dawa Akil duk ranar da baka zo ba, ya yi dealing dinka well well, kasan dai shi no nonsense ne baya wasa da yara, ba kamar Uncle Abbas bane da yake yi muku yadda kuke so".

Jawad ya nisa ya ce"Malam ni bazan iya yiwa mutum aski ko wanke kafa ba, zan bata jikina ne kawai".

Mk ya zuba masa ido yana kare masa kallo, a zahiri dai yaron kamarsa ya yi, amma dabi'unsa sak na uwarsa ne, gayu da pride dinsa na Sa'adah ne.

Ya daure fuska sosai ya ce "Jawad ai baka kai a baka yin aski ko wankin kafa bama tukun, share wurin zaka dinga yi, kana wanke towels din da aka yi amfani da su, sannan ka dinga ganin yadda ake gudanar da aikin".

Ya shagwabe fuska ya ce"Haba mana Malam a shagonka zan dinga irin wannan wahalar?"

Mamaki ya kama Mk amma da yake yasan a iya shekarun Jawad da iya tunaninsa shi hakan abin kunya ne, a gurinsa.

Sai ya sassauta ya ce, "Jawad Ni dai a tarihin Nigeria ban taba ganin wadda ya yi karatu mai zurfi ya mallaki jirgin sama ba, Amma na san yan kasuwa da suka fara da kananun business, a hankali business din y tunbatsa har suka sayi jirgin sama. Na san kai kuma burinka ka samu damar siyan jirgi, fa'da mini idan ba ka koyi business ba, how ur dreams will be reality one day?"

"To zan dinga zuwa, amma plz Malam! tell Uncle Akil to be gentle, I really dislike his hershness"

Mk ya sake daure fuska sosai ya kafe shi da Ido, har sai da Jawad ya dinga jin wani irin abu na ratsa shi, ya sunkuyar da idonsa kasa ya ce " very sorry Malam".

Mk ya nisa ya ce "Akil din ka ke fa'din haka akansa? Kanina, kanina Jawad? ashe kuwa nima na shirya, domin Ni da shi ai daya ne a gunka! Ko Ahamad da yake karamin mu ban za ci zaka iya fa'dar wani abu da bai maka a tare da shi ba".

Ya ru'ko hannun Mk ya ce "ba zan sake ba Malam! Plz forgive and forgot".
Ya na fada yana leka waje, yana fatan Akil din bai iso ya ji me ya ce ba".

Mk ya ce daina ma wani lekawa dan kuwa zan fada masa.
Nan da nan kuwa ya fara kuka yana fa'din sorry Malam, ya tsorata sosai, domin Akil mala'ikan Yara ne, baya musu ta Dadi shine discipline master a family din nasu.

"Ok stop crying! Ba zan fa'da ba, amma idan ka sake, ko idan ka zo ka ga baya shago ka ce zaka dinga yiwa su Saminu rudeness to ka tabbatar zai ji komai".

Ya goge fuskar sa yana fa'din " Thank you! Komai suka ce na yi, yi kawai zan yi".

Mk ya ru'ko shi yana fa'din "good boy! Sannan islamiyar nan ta safe zaka dinga zuwa. 9 ake faraawa, a tashi 1pm.


*A samarwa Yara lokacin da zasu dinga zuwa wurin koyon sana'a domin hakan zaisa su taso da burin tsayuwa akan kafafuwansu, zai rage musu burin su kammala digirin farko su zauna zaman jiran gwamnati ta basu abin yi, lokaci ya yi da zamu daina yaudarar kanmu cewa gwamnati zata iya WADATAR da kowa*.


Haka kwanaki suka dinga shudewa, har shari'ar mahaifin Khalil ta zagayo, aka yi ta cakudawa bisa taimakon lauyoyinsa mussaman Sa'adah suka samu kotu ta bada belinsa, bayan sun kawo wadda kotu ta bu'kata a matsayin sharudda.
Kotu ta sake zabar ranar 28/08 a matsayin ranar yanke hukunci na karshe.

Wannan shari'a ta matu'kar Jan hankalin yan siya domin gaba'daya al'amarin siyasa ne, belin da ya samu ya matu'kar daga darajar lauyoyinsa mussaman Sa'adah da ta kasance mace tilo, duka shafin jaridun kasar nan shafin farko sai ka tsinci hoton Sanata Ibrahim Hassan da lauyoyinsa.

Mk da ya tsinci hoton Sa'adah a tsakanin manyan lauyoyi gefe kuma ga mahaifin Khalil sai ya ji tamkar ya shide dan tsananin takaici.

Ya sani tabbas burinta ne tun tana secondary ta zama lauya, shiyasa a lokacin da zai samo mata gurbin karatu ya yi iyakacin kokarinsa ta samu fannin shari'a, Dan ta sami sau'kin halin da take ciki a wanccan lokacin.

Sai gashi duk irin fa'di tashin da yayi akan karatun nata, ashe a mahaifin wannan Dan isakan yaron da ya tsana, zai fara yi wa rana? Ya sake zubawa hoton idon suna kallon juna ita da Bar. Mustapha, da ya kasance saurayi, wani irin al'amari mai nauyi ya danne masa zuciya, idan ba Sa'a ba kishin Sa'adah ne sanadin mutuwar sa domin zuciyar sa zata iya bugawa.

A fili ya dinga ambaton "wallahi ba zan iya ba, ba zan jure ba, dole ki ajiye aikin nan, inko ba haka ba rana daya za'a tarar na zama gawa".

Karfin addua ne kawai ya daidaita Mk.

A yammacin ranar ya shirya ya nufi gidansu yana jin yau kam dole sai ya ganta.

Yana zuwa ya tarar da wani bacin ran domin tarar da ita ya yi tana zance da Anwar da ta ganshi kuma ko dar bata ji ba, bare ta sallami bakon ta saurare shi.


A sanyaye ya juya ya tafi, cikin sanyin jiki.

Hankalin Mk ya yi matu'kar tashi domin ya fara gasgata Sa'a cewa da gaske take zata dora ikon da Sharia ta bata akan ikon Baffa.

Ya kasa jurewa, washagari da yamma ya bita gidan Sumayya, da kyar ta saurare shi adalilin Idris din Sumayya na gidan ya masa masauki a katafaren falonsa na kasa.

Sumayya tana ta fishin akan me zai saurare shi, bayan ya san duk irin ba'kin cikin da suka sha adalilin sa.

Haka dai ya lallaba su tare da fa'din ai mahaifin Jawad ne, dole kuwa ayi taka tsantsan.

A rikice Mk yake fa'din "ya kike so na yi miki ne Sa'adatu? Ke fa kika mini laifi, ke kika zalunce ni, yanzu na samu, na farfado daga gashin Kumar da kika mini, shine kike son sai kin Kai ni kasa, wai me na miki ne da ban cancanci na sami nutsuwa da ke ba?".

Ya nuna kansa da yatsa ni kike cewa ba Kya so? A akan idona kike hira da wani namijin, kika wulakantani a gabansa? Ashe ba ni da wata alfarma a gurinki komin kankatarta, sai na fa'di na mutu ko sai na hadu da mummunar jinya sannan zaki gane ina son ki?"

"Ki na fadawa mutane ba Kya so na ko?"

Ya fa'da da wata irin murya mai nuna sarewa kwarai da gaske.

Ya mike shikenan Sa'adatu, shikenan, na yafe miki komai, ko na mutu ma, na yafe miki".

Ya tafi ko waiwaye bai yi ba.


Kwana ta yi tana jin fargabar ko ya tafi kenan?

Washagari Jawad ya biyota gidan Sumayya ya tarar da ita a compound din gidan tsaye da Alh Mamman da alamu rako shi ta yi zai tafi.

Wani iri Jawad ya ji, ya zo zai wuce su, ba tare da ya musu magana ba.

Alh Mamman ya ce" zo mana tare da yafito shi. Jawad akan dole ya karasa ya ce "ina yini a tsaye kerere, sannan fuskar nan a hade tamkar bai san murmushi ba, bare dariya.
Alh ya ce " da gani wannan shine 'Dan nawa ga shi nan sak Babansa".

Ya zura hannu ya dauko bandir din Yan dari biyu sabbi ya mikawa Jawad yana fa'din ka sha Ice-cream".

Jawad ya sake daure fuska fiye da dazu "Ya ce Babana zai mini fa'da ka ajiye' ka bawa masu bara".

Ya juya ya bar Alh Mamman da kudi sororo yayin da kunyar duniya ta kama Sa'adah, ta kasa cewa komai, mussaman yadda take bashi labarin hankalin Jawad da yadda yake sonta yake tausayin ta.

Haka Suka rabu ita a kunyace, shi Kuma jikinsa a sanyaye na mamakin iskancin karamin yaro irin wannan wato ya san kishin uban sa?

Sai da ta bari sun kwanta ta dinga yiwa Jawad nasiha da nuna masa rashin tarbiyar da ya yi ka iya ta'ba cigabaansa. Ya amsa da ya daina.


Bayan kwana biyu ta je kotu Anwar ya dawo da ita.

Jawad na compound din suna ball da su Ayman da Anis har ma da Khairat, suka ga shigowar motar Su Sa'adah.

Dukkansu yaran suka ruga wajen Yi mata oyoyo tare da gaida Uncle Anwar, soasai suke sonsa saboda yadda yake ciko musu leda da kayan ciye ciye.

Jawad ne kawai bai doshi inda suke ba sai kawai ya ja ya tsaya ya rungume hannunsa a kirjinsa.

Sa'a ta yafito shi da hannu, ya karaso ya tsaya bai ko kalli inda Anwar yake ba.

Ta ce Jawad ga Uncle kullum na tambayar ka".
Ya sake dauke kai ya ce "na ganshi sannunsa".

Ba'kin ciki tamkar ta hadiye zuciya.

Ta ce "ba zaka gaishe shi ba?"

Ba kunya ko shakka ya ce "Ai ba ubana bane" a hankali, sai dai dukkansu sun ji shi.

Ya juya ya barsu.

Anwar da ransa ya baci sosai, dole ya mata sallama ya tafi.

Ta shiga gidan a fusace tana neman Jawad tana jin tamkar zuciyar ta ta Fado dan tsananin bacin rai.

Ta nemi shi ta rasa amma ta kudiri aniyar yau sai ta masa dukan kawo wuka, gobe idan akace ya sake wulakanta ba'kinta zai ji shakka. Ta rasa irin wannan rashin tarbiyar da ya tsira a yan kwanakin nan.

Shikuma yana can ya buya a boys quarters.

Sai yamma lis ya fito, ai kuwa ta hango shi ta windo ta dauki wayar wuta ta fita domin ta san bata isa dukansa a gaban Sumayya ba, cewa

Please Login or Register in order to submit comment