You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a rana*
*#700 -sau hudu a rana*


_Kiyi man wanann number magana danjin ynda zaki biya 08160508316_.



*MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU KOFA A BUDE TAKE*
_TUNTUBI_
08032773332.



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.








36-37.




Sannu a hankali cikin nutsuwa MK ke tafiyar da Sa'adah, a sati sau daya yake zuwa zance. Duk da ya karbi lambar wayar Inna tun da yanzu koyaushe wayar na hannunta amma ba kasafai yake kiran ba, duk a kokarinsa na ganin bai raba mata hankali ba, musamman da kullum jarrabawarsu kara kusantowa take yi.

A bangarenta kuma sai ta ke ganin kawai rashin daukar ta da muhimmamanci ne yasa yake nuna mata rashin kulawa, musamman yadda Khalil ke kiranta safe da yamma sannan su raba dare ana musayar kalamai, shi yasa ya daina damuwa da rashin saurarar shi da ba ta yi a makaranta.

A haka har aka rubuta jarrabawar JAMB, duk kokarin da MK ya yi na ganin Sa'adah ta samu rubuta jarrabawar abin ya ci tura! Saboda yadda Baffa ya ce masa "Ni sakandiren nan ma a dole na bar ta ta kammala ,yar uwarta aji uku kawai ta yi na aurar da ita, don haka ni ba zan barta ta tafi wata babbar makaranta ba, ta zo tafi karfina".
Ya dan tsahirta sannan ya rufe maganar da cewa, "Idan Allah ya sa ta zo hannunka komai ma sai ta yi, amma ni a yanzu babban burina shi ne na sauke nauyinta da ya yi saura a kaina, na aurar da ita a hannun da ko ba na numfashi ba za ta koka ba".

Kan dole MK ya ha'kura da maganar amma ya kudire a ransa Sa'adah za ta yi karatu har sai ta ce ya ishe ta.

Gab da za su fara rubata WAEC wa'adin da MK zai yi a makarantar FGC ya cika, amma saboda yajin aikin da jami'o'i suke yi, yasa hukumar makarantar ta roke shi ya ci gaba da zuwa kafin lokacin da ASUU za ta janye yajin aikin. Kasancewar MK da sakamako mai daraja ta daya (First Class) ya fita, yana cikin wadanda Jami'ar Bayero za ta dauka don yin koyarwa.

A haka suka ci gaba da tafiya a baibai tsakanin MK da Sa'adah, shi yana ganin ya ba ta lokacin da za ta yi karatu sosai, ita kuma tana masa kallon wanda bai girmama lamarinta ba, hakan ya sa take saurarar duk wanda ya nuna yana son ta ba tare da tunanin ai tana da wanda take so ba! Musamman da a lokacin damina Baffa ya fi zaman Gogel saboda kula da noman da yake yi, ita kuma Inna zuciyarta daya ta dauka MK ne yake zuwa.

A haka har ta kammala makaranta gaba'daya, cikin wannan yanayin ta hadu da Alhaji Mamman! Asibitin (Arewa Surgery) suka je duba Mahaifiyar Safina ita da Halima, sun fito harabar asibitin suka hadu da shi, ya nemi su shigo mota ya kai su, Sa'adah ta'ki amincewa amma da yake tare suke da Halima sai da ta rinjaye ta suka shiga motar, a hanya ya nuna ra'ayinsa akan Sa'adah, wanda sam-sam bai kwanta mata ba, musamman da yake ta gan shi dattijo da alamun yana da iyalai masu yawa a karkashinsa.

A lokacin wayar hannun ba ta da yawa sosai kamar yanzu, sannan mai madannai ce komai tsadar wayar. Ya tambayi lambar wayarta, Sa'adah ba ta ce komai ba sai da ya sake tambayar a karo na biyu sannan ta ce "Ba ni da waya."

Bai yi mamaki ba tunda a lokacin ba ta zama ruwan dare irin yanzu ba, ko iyayenta ma Sumayya ce ta sayo musu don ta ri'ka gaisawa da su tun da ita ba mazauniyar gari ba ce. Ita kuma ta gaje ta Inna.

Halima ta ce "Ba Inna na da waya ba?"

Shiru ta yi da alamun dai ba ta son ba da lambar ne, shi kuma sai ya ce "Yawwa 'kawarmu a taimaka a ba ni lambar Innarmu!"

Haka Halima ta bude wayarta ta karanto masa lambar Inna saboda ta ga alamun za su sami kudi a tare da mutumin.

Duk kokarinsa na son sai ya kai Sa'adah har kofar gidansu, amma hakan bai samu ba, saboda ta kafe akan idan aka gan ta cikin motar da ba a san mutumin ba, za ta fuskanci tashin hankali, wannan kalaman ya sake jin son ta sosai, ya san daga dukkan alamu da ga Babban gida ta fito ma'ana gidan tarbiyya.

Kan dole ya kai su gidan su Halima wanda ita ko dar ba ta ji ba, hakan ya sa yake ganin anya iyayen Sa'adah ba tufka suke wannan 'kawar tana musu warwarba? A dan haduwar nan tasu ya lura da kamewar Sa'adah, ya kuma gane rawar kan Halima, a ransa yana rayawa da zarar ya sami Sa'adah zai raba ta da wannan kawar da idan kawancesu ya ci gaba da wanzuwa, zai ta ba tarbiyar Sa'adatu.

Halima ta shige gida ta bar su, bai wani jima ba shi ma ya ce zai tafi don ya lura da Sa'adah kamar a tsorace take, kudi ya dauko har kimanin dubu talatin ya ba ta ya ce ta bawa kawarta goma a ciki. Ta tattaro dukkan kunya ta yaba a fuskarta tare da cewa, "Ka bar su ba zan karba ba!"

Shi kuma ya na ta fadin "Idan ba ki karba ba, ba zan ji dadi ba Sa'adatu."

Da kyar tasa hannu ta karba ta yi godiya bayan ya karbi address din gidansu, wanda kai tsaye address din gidansu Zainab Ma'aji ta bayar.

Jiki na rawa ta shige gidan su Halima ta tarar da ita a falo da kaninta suna kallo kasancewar mamansu tana wurin aikinta, haka suka shige dakinta, kudin ta ciro ta nuna mata suka hau ihun murna! Halima na cewa "Ai tunda na gan shi na san akwai rodina tare da shi sannan ba matsolo ba ne."

Dariya Sa'adah ta yi tare da cewa, "Kin ga kuwa takanas ya ba da naki sakon."

Dadi ya cika zuciyar Halima da ta ji yawan kudaden da ya ba ta, haka ta sake jan Sa'adah zuwa Country Mall wanda a lokacin aka bude shi, suka kashe kudin nan tas a wurin siyan kayan kwalliya, da takalmi da jaka. daga Country Mall suka rabu kowa ya yi gidansu, Sa'adah zuciyarta sai wasiwasi take yi mai za ta cewa Inna akan wadannan kayan?

Ta tabbatar uwarta ba sakaryar uwa ba ce! Duk wani motsinta akan idonta ne, wa za ta ce ya ba ta wadannan kayan? A ina ta zubar da nasihar da kullum take yi mata idan za ta fita na kar ta tsaya da saurayi a hanya, ko dazu kafin ta fita sai da ta jaddada mata duk mai son ta ya zo gidansu ya same ta, kar ta yarda a tsayar da ita a hanya.

Ta gama tunaninta kaf ba ta sami kalaman da zai shiga zuciyar mahaifiyarta, ta fahimce ta ba, don haka kai tsaye gidan su Zainab ta sauka, ta ba ta ajiyar kayan tare da ce mata khalil ne ya ba ta, ba ta son a gani a gida, don ta san idan ta fada wa Zainab gaskiyar magana sai ta iya zuwa ta fada wa Inna tunda ta tsani abotarsu da Halima, kullum sai tace mata, "Sa'adah ki kiyayi kawance da Halima Mu'az ba wayewarku daya ba, ba kuma irin tarbiyarku daya ba"

Da kyar Zainab ta karbi kayan bayan ta gama mata mitar ita a rayuwa ba ta son shiga shirgin rashin gaskiya, ban da rashin gaskiya ina ke ina sauraran wasu mazan tunda dai kin san namiji daya za ki aura! Kuma kin tsayar da wanda kika aminta da shi.

Sa'adah da yake mafita ta ke nema sai ta yi mukus ta kasa tanka wa Zainab tamkar ba ita ce mafadaciyar nan ba.

Tana isa gida ta tarar da Baffa ya dawo daga Gogel, ta yi farincikin dawowarsa amma a gefe takaicin yadda za a ci gaba da yin tuwo ba kakkautawa take yi.

A kwanakin da baya nan hilatar Inna ta ke yi ba sa yin tuwo amma yanzu kam ba hilar da za ta mata ta yarda, tunda tafi girmama ra'ayin Baffa fiye da komai, sannan kuma ba za ta bari ta yi nata girkin ba, ce mata ta ke yi nan ba gidanki ba ne, ki bari idan kin yi naki gidan sai ki yi yadda kike so.

Kallo daya Inna ta mata ta gano rashin gaskiya a tare da ita, ba ta mata magana ba, sai da ta gama da hidimar Baffa ya fita waje. Sannan ta iske ta a daki tana game a waya, ta zauna kusa da ita ta kamo hannunta ta ce, "Iya na ga sauyi a tare da ke mai kike ciki ne da har ban cancanci na sani ba?"

Duk da yadda Sa'adah ta maze akan ita ba komai, bai gamsar da Innar ba, amma sai ta ce, shike nan Iyah! Ki sani tun kafin ki san kanki na san ki, tun kafin ki yi dabarar boye mini halin da ki ke ciki nake tattalin ki, don haka komai za ki yi, zan gane. Ki sani idan har mu ba mu san mai kika yi ba, Ubangiji ya sani! Shi ne kuma zai kama ki saboda ha'intar da kike kokarin yi Mana."

Ta fada tana kallon ta irin kallon nan mai tsanani.

Jikin Sa'adah ya yi sanyi sosai musamman kallon da uwar take mata mai kama da ban yarda da ke ba, sai ta ce,
"Ni fa Inna ban je ko ina ba."

"Iyah ai ban ce kin je wani gun ba amma fada mini ina kuka biya daga asibitin sannan bayan Zainab da wa ku ka hadu a tafiyar?"

"Yan makarantar mu ne kawai Inna"

"To wa ye kuma ya ce yana son Zainab?"

"Babu!"

Ta sake ri'ko hannun ta sosai sannan ta ce "Waye ya tsayar da Iyah?"

Kai tsaye ta ce "Kai Inna ni fa ban kula shi ba, wani mutum ne tsoho ne fa!"

"To tsohon ba namiji ba ne?"

Idan har nagari ne kuma kina son sa ai magana ta kare! Ba za mu miki dole ba, don haka ko waye ya tsayar da ke idan kin ga ya miki ki turo shi wurin mahaifinki, laifin da za ki mana shine ki yaudare mu, ki yi abin da kika san ba za ki iya yi akan idon mu ba, ina abin da ya ba ki?"

Dariya ta kwace wa Sa'a ta ce
" Ban karba ba Inna"

Ita ma Innar dariyar ta yi tare da cewa "Ban yarda ba Iyah! Na san ki da martaba kalmar nan ta ba kyau mayar da hannun kyauta baya, amma na san Iyah ba za ta boye mini duk wata kyauta da za ta samu ba.
Don ta san ba zan ki ta da alheri ba, sai dai na kiyaye ta daga fada wa hatsarin MAZAN YAU musamman da ba gidansu aka biyo ta ba."

Tana fadin haka sai ta mike ta fice ta bar Sa'adah da sanyin jiki da kunya iri-iri suna saukar mata a lokaci guda.
A ranta kuma fadi take, "Ko yara nawa ne irinta suka dace da samun tsayayyiyar uwa mai sa ido akan duk wani motsin 'ya'yanta?" A fili kuma ta furta "Madalla da uwa irin Inna!"

Tana Jin komai za ta yi In Sha Allah ba za ta tozarta tarbiyar da Inna ke yi a kanta ba gajiyawa ba, amma kuma ba ta jin, za ta ki karbar duk wata kyauta da za a mata kawai dai boyewa ne ba za ta sake yi ba. don haka da kanta ta fada wa Alhaji Mamman gaskiya cewa gidansu na gaba kadan da wancan da ta fada masa da farko, haka nan hatta Khalil ta ba shi damar zuwa, ta gaji da boye-boye tunda wanda take yi domin sa ba fin su son ta ya yi ba, ita ce dai tafi son sa.

Yawan wayar da Alhaji Mamman yake mata ba kakkautawa, sau tari ma gajiya take yi da amsa kiran nasa, ya sake sa ta raina kulawar MK, tunda dai yanzu ai ta gama karatun tunda ada uzurin kar ya raba mata hankali a karatu ya gabatar.
Amma har yau ya ki canjawa idan ya kira ta da safe ba zai kara kira ba sai da daddaare shi ma a ya dade su yi maganar mintina uku, sabanin Khalil da Alhaji Mamman sai su shafe fin awa akan waya suna neman saye zuciyarta tamkar ba kati suke sawa ba.

Tana yawan tambayar kanta shin Uncle MK soyayya ne bai iya ba, ko kuwa matsayinta ne a zuciyarsa bai kai ya mata yadda su Khalil ke mata ba?

Zuwan ma bai canja ba sau daya a sati, duk da kullum sai ya zo unguwar, sannan ba ya mata kyautar bajinta kololuwar kyautar sa dubu biyu, sai dai karshen wata ya kan hado mata shopping din kayan kwalliya masu matsakaicin kudi da tarkacen alawowi masu dadi da biscuit, wanda ba sa dadata da kasa saboda yadda Alhaji Mamman da khalil mai sato kudin iyayensa suke mata barin kudi.

Wani zuwa da Alhaji Mamman ya yi ya fa'da mata matansa biyu, da yara bakwai, bai boye mata shi dan majalisar jaha ba ne mai wakiltar karamar hukumar Gezawa, uwargidansa na can Gezawa yayin da amarya ke nan cikin Kano a kwatas din 'Yan Majalisu na Farawa.

Da daddare Sa'adah na kwance a daki tana hira da Khalil, cike da nishadi take amsa wayar don kuwa tabbas tana jin son Khalil, kawai sanin ba za a masa aure yanzu da kuma soyayyar MK da ta danne tasa ne! Amma tana son sa yana burge ta ya dace da tsarinta na Luxury Life.

Tana ganin kiran MK sai shigowa yake yi amma ba ta katse ba, tunda ta san shi ba wani lokaci mai yawa zai dauka yana lallabar ta ba, sai daga baya ta katse kiran Khalil bayan ta dauki excuse akan ya ba ta mintina biyar tana zuwa.

Tana kiran sa ya katse ya kira ta bai mata complain din da wa take waya ba, hakan ma yasa ta sake jin haushinsa, ya tambayi lafiyarta, ya kuma sanar mata cewa gobe zai zo abokinsa na son ganin ta, to kawai ta ce, a ranta kuma tana cewa abokinsa ne yake son ganina ba shi ba.

Washegarin kuwa suka zo shi da amininsa Mahmoud Karfi, wani abu mai kama da almara Mahmoud na dora ido a kan Sa'adah ya ji son ta ya cika zuciyarsa, ta zo masa a yadda yake burin samun matar aurensa ta kasance.

kwalliyarta, yangarta, shan kamshinta duk sun tafi da shi, amma sai ya yi yaki da zuciyarsa ya danne ta yana nanatawa kansa MK ya wuce ya hada soyayyar mace da shi, ya tabbatar idan MK ya gane yana son ta to tabbas zai bar masa.

Idan kuwa haka ne shi ne ya kamata ya haramta wa kansa wannan yarinyar da a yau ya dora ido a kanta, a daddafe aka yi hirar Mahmoud ya ba ta kyautar kudi dubu biyar suka tafi yana ta neman tsarin shaidan da zuciya da suke sake kawata masa Sa'adah.

Madalla da aboki irin Mahmoud wanda yake daraja abota da kuma sadaukarwa, ba wanda zai zagaye ya yi wa abokinsa kafar ungulu ba.


*BAYAN WATA UKU*.

Zuwa wannan lokacin Sa'adah ta canja sosai domin ba karamin kudi Alhaji Mamman ke sakar mata ba, ta mallaki zobunan Dubai Gold a boye har guda biyu. Ta mallaki waya mai kyau Sliding 'kirar Nokia da SIM a ciki, wayar dai Inna ta sani amma zobuna ta kife ta musamman da Innar ba ta san Gold ba.

Tun MK bai lura da canjawar Sa'adah ba har ya fara ankara da yadda kwallliyarta ta karu, ta daina dokin amsa masa waya, ta daina mitar rashin zuwansa, sannan dan flashing din da take masa ta daina idan zai kwana ya yini bai kira ta ba, baya taba ganin text ko flashing dinta.

Duk da bai san tana da waya ba har zuwa wannan lokacin shi da layin Inna ya ke kiran ta, so yake ya mata bazata jiran fitowar results dinsu yake yi, idan har ya yi kyau, waya zai siya mata, idan ma bai yi ba dai zai siya mata. Ashe shi bai san ta kerewa rike kananun wayoyi irin wanda yake harin siya mata ba.

Jikinsa ya fara sanyi don haka ranar wata Laraba ya kasa jiran Juma'a ta zo, ya shirya ya nufi gidansu da yamma.
Sai dai yana zuwa ya tarar da Alhaji Mamman zaune a kan tabarma, yana tsayawa a bakin zauren ita kuma ta fito daga cikin gidan ba ta 'karasa isowa zaure ba, amma idanuwansu sun sarke da juna, bai ce kala ba ganin Alhaji Mamman bai ganshi ba sai kawai ya yi murmushin da babu nisha'di a cikinsa ya juya abin sa.

Sai ta tsinci kanta da diriricewa, ta ji tamkar ta ruga da gudu ta ce masa ka dawo, kai nake fatan ace kai ne a zaune ba wannan mutumin ba, amma ba damar yin haka, a daddafe ta gaishe shi, ta gabatar masa da uzurin zazzabi take yi don kar ya ji ba dadi ne yasa ta daure ta fito. Ya gamsu a yadda ya ga duk jikinta ya saki ta yi wani iri, tashi guda, don haka ya fita ya je mota ya kwaso mata sayayyar da ya jido mata, bayan ya ajiye mata rafar yan 200 sabbi kal.

Tayi godiya ta shiga gidan zuciyarta daya tunda Inna ta je cikin Unguwa yinin biki don haka ta rage wasu kayan ta boye akan sai wani zuwan ta nuna mata.

Jikinta na rawa ta shiga lalubo lambar MK, amma har ta katse bai dauka ba, ta sake kira har sau uku nan ma bai dauka ba.


Alkalamin
*SURAYYA GWARAM*
✍️✍️.


🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan, ba tare da iznin mai Hakkin mallaka ba*.




*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.


*Fatan alheri ga*
*Asma'u Sani*
*Aisha Lagos*
*(Mrs Dan manya)*.
*Shafin na ku ne ku yi yadda kuke so da shi*.



38_39.




Haka ta ci gaba da kiran har ta gaji, tana 'kiyasta adadin kiran da ta yi masa ya kai ashirin, jikinta ya mutu tamkar marar laka, zuciyarta ta cunkushe da fargaba, tasan tana son MK sosai amma a yau ta sake sanin son da take masa marar adadi ne, duk da kasancewar ba lokacin zafi ba ne sosai, amma zufa sai karyo mata take yi. Waya kuma na hannunta, tana ci gaba da kiran sa.

Tunda ya bar gidansu Sa'adah Masallaci ya nufa da 'kyar ya karasa saboda yadda zuciyarsa ta daure, ba abin da yake bukata sai kadaici. Ya Jima a zaune yana ta ambaton Allah har ya sami sassauci sannan ya dauki Qur'ani ya fara karatu a fili, a hankali, duk kiran da Sa'adah ke yi masa yana gani, duk da a silent ya mayar da wayar.

Bai bar massalacin ba sai da aka yi Magariba zuwa wannan lokacin ya samu saukin daurewar da zuciyarsa ta yi a dalilin kishi, ya fito daga Massalacin ke nan kiran ta ya ci gaba da shigowa ba kakkautawa.

Gefe sosai ya samu ya zauna ya fito da wayar ya katse kiran nata sannan ya kira ta.

Jikinta har rawa yake yi wurin amsa kiran wanda ta dade ba ta ji zakuwa da dokin amsa kiran sa ba kamar a wannan lokaci.

Muryarsa ba amo sosai ya mata sallama tare da cewa, " Sorry Sa'adatu! Kin kira na bar wayar a caji ne tun dazu sai yanzu na ga tarin missed calls."

Wani nauyin jiki ya kara kama Sa'adah, ta rasa kalmar da za ta furta saboda abubuwa biyu, na farko bai nuna ta masa laifi ba tunda da ban ha'kuri ya bude maganarsa bugu da kari ma katse kiran ta ya yi, ya Kira ta.

Na biyu ya ambace ta da Sa'adatu rabon da ya kira ta da hakan tun lokacin suna yar tsama, ita kam ya binneta, ha'kuri za ta ba shi ko kawai sharewa za ta yi kamar yadda ya yi?

Da kyar ta bude baki ta ce "Ai na dauka kana sane ka 'ki amsawa."

Tana rufe baki ya ce
"Ko daya to mai kika mini?"

Ta san sarai a cikin fishi yake, don haka sai ta lankwashe harshe ta ce "Ka yi ha'kuri don Allah!"

Da sauri ya cafe da cewa
"Ni fa ba ki mini komai ba, laifina ne da na zo kai tsaye ban sanar da ke ba, sannan ai yaudarar kai ne na yi tsammanin ni kadai kike kulawa, ke allura ce a cikin ruwa don haka feel free you did nothing."

Ta kasa gane inda ya dosa shin gatse ya ke mata ko kuwa da gaske hakan yake nufi a zuciyarsa?

Don haka sai ta ce "To ka dawo na ganka dama ai na kwana biyu ban gan ka ba"

Kai tsaye ya ce, "Ai ba na zuwa zance da daddaare"

Shiru ta yi sannan ta ce "To gobe za ka zo?"

Tana rufe baki ya ce "Ina da schedules masu muhimmamanci a gobe."

Kawai sai ji ta yi kuka ya zo mata, cikin rawar murya ta ce "Har sun fi ni muhimmamanci?"

Cike da rashin kulawa ya furta "Wadancan tabbas ne, ke kuwa gaibu ce."

Ta yi shiru amma kuka take yi, yana jin yadda ta ke jan majina da shassheka, amma ya yi burus da ita, yana fatan ta ji a ranta cewar ita ba wata tsiya ba ce a gunsa.

Cikin kuka ta ce "Ni ka ke kwatantawa da gaibu?"

Ko dar bai ji ba wurin ba ta amsa da cewa, "E!" A gajar ce.

Bai sani ba ko kishin dake cin zuciyarsa ne, ya sa bai ji kukanta ya taba shi sosai ba.

Yayin da ita kuma bakin cikin yadda yake nuna mata rashin kulawa yake dada addabar ta.

Duk da hakan sai ta daure ta ce "Jibi Juma'ar za ka zo?"

"Zan zo idan ina cikin masu rai da lafiya idan kuma uzuri ya taso ban sami zuwa ba, to sai satin sama."

Ta yi shiru tana jin ta rabu da wannan mutumin da yake nuna mata ita ba komai ba ce a idonsa, sanin ya gan ta da wani ta san dole zai ji ba dadi yasa ta ajiye komai ta neme shi.

Har ha'kuri ta ba shi amma shi ya nuna ma ba laifi ba ne bai yi fishi ba, anya kuwa yana son ta, anya ba ita ke bankaura akansa ba?

Jin ta yi shiru ya sa ya magantu da cewa, "Sai yadda ta yiwu." Ya katse wayar! Bakin ciki ya kama ta sai kawai ta kife kai a kan filo tana kuka.

Shi kuma ya mike ya mayar da wayar aljihunsa, yana sake jin sau'kin radadin da zuciyarsa ke yi masa, tunda dai ya tabbatar ita ma ta shaki takaici.

Washegari tun safe Sa'adah ke zuba idon kiran MK har aka yi sallar Isha bai kira ba, a lokacin ha'kurinta ya gaza, ta dauko wayar Inna ta shiga kiran sa, sai da ta gama ringing bai dauka ba, tana shirin sake kira sai ga kiransa ya shigo. Ba ta tsaya jan aji ba ta dauka da sauri sai kuma ta yi shiru ta ki yin magana.

Sai da ya yi sallama har sau biyu sannan ta amsa ciki-ciki, mamakin ta ya kama shi amma ya waske ya ce, "Mura ki ke yi ne?"

Nan ma ta yi shiru ya nisa ya ce, "Yau yini guda ban zauna ba, ina ta yunkurin kiran ki, sai wani al'amarin ya mantar da ni.

Yanzu kuma na dauko wayar da nufin

Please Login or Register in order to submit comment