You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce ki adana su sosai, likitan ya ce za ki iya shan wannan ba komai. Ganin da Sumayya ta yi Sa'adah ba ta bude ledar ba yasa ta ce "To ki bude mana na nuna miki yadda za ki sha".

Kin budewa ta yi, sai Sumayya ce ta bude ta fito da su, daya a cikin wata yar roba yake mai kyau an rubuta Women's Formula.
"Kinga wannan na robar Multivitamin ne 100 pieces ne kullum daya za ki sha"
Sai wannan ta nuna na kwalin shi ba kullum ba sai ranar da kika so. Ki kula da shi mai tsada ne sosai, daurewa na yi na siyo miki package dinsa, kafin ya kare dai na san za'a dade sosai".

Ba tare da ta kalli fuskar Sumayya ba ta ce "Na gane, na gode." Ta mayar da su ledar. ganyin wata takarda a ciki yasa ta janyo ashe recit din kudin ne, ganin yawan kudin da maganin suka lashe musamman na kwalin ya matu'kar ba wa Sa'adah mamaki.
Ta fito dana kwalin tana dudduba mene ne special a tare da shi da ya yi wannan darajar haka?

"Viagra"

Ta furta sunansa a fili, a kunyace ta sake cewa "Na gode sosai Anty".
Sumayya ta muskuta ta tsare Sa'adah da kallo mai tsanani sannan ta ce "Ina rokon ki Iyah kar ki jefa kanki a hallakar da MATAN YAU suka jefa kansu na shaye-shayen magunguna barkatai marasa fa'ida da inganci, da sunan mallakar miji. Kar ki yarda da wannan bankaurar wallahi ba a mallakar miji da wannan sai dai ki ta asarar kudaden ki, karshe ki hadu da ciwon da zai raba ki da mijin gaba'daya".

Cike da wauta Sa'adah ta ce "Fada mini abin da zan yi na mallake shi kamar yadda kika mallaki mijinki".

Dariya sosai Sumayya ta dinga yi har da kwanciya akan gado, lamarin da ya fusata Sa'adah, kawai sai ta fashe da kuka, da kyar Sumayya ta hadiye dariyar ta shiga rarrashinta.

"Yanzu mene ne abin kuka Iyah?"

"To akan me za ki mini dariya kamar mahaukaciya?".

"Tambayar ki ce ta ba ni dariya, amma nutsu ki ji mai zance miki. Mace tana kama mijinta da girki mai da'di, da kuma ba shi kulawa ta musamman a shimfida, da kuma tsaftar jiki da ta muhalli. Amma wadannan kadai, ba zai sa ta mallake shi ba, sai ta yi ha'kuri ta bi ra'ayin sa akan komai, ko da kuwa ita ba hakan take so ba, ya zama ba ta da ra'ayin kanta sai na mijinta, ta iya ladabi da biyayya, ta kiyaye harshenta akansa. Ina tabbatar miki idan kika hada wadannan abubuwan sai kin mallake shi fiye da yadda kike so".

Tura baki gaba ta yi tana goge hawayen idonta, ta sake cewa "To idan ina son ya zama mijin ta ce fa?"

Mamaki da tsoro ya kama Sumayya, wai wannan yar mitsitsiyar yarinyar auren jiya, ita ce ke son ta mallake miji, bayan mallakar kuma ta mayar da shi mijin ta ce. Wane irin son zuciya ne ya shigo wa matan wannan zamanin haka?

Sumayya tsintar kanta ta yi da ri'ko hannun kanwarta ta kalle ta da tarin kauna sannan ta ce, "Abubuwan da na fada su ne za su miki jagora akan komai, sai kuma ki hada da addu'ar Allah ya zaunar da ku lafiya cikin aminci da tausayi. Amma karki yarda da kawayen da za su ba ki maganin mata ko a saki a hanyar zuwa wurin malamai wallahi ba za ki samu yadda kike so ba, ba komai a wannan hanyar sai bata da lalacewa".

Ta dan tsahirta kafin ta zarce da fadin "Ki ba shi dama ya zama sarki a gidansa, ke kuma ki zama baiwa kuma bafadiyarsa, duk abin da kika san yana so, ki masa tun kafin ya bu'kata haka nan ki guji abin da baya so kafin ya ankarar da ke, ina tabbatar miki idan kin yin hakan bayan mallakar da za ki masa zai ya zame miki mijin kan ta ce ma, matu'kar yana rayuwa kan tsarin ilimi da shari'a ne.
Ga turaren wuta nan Inna ta ce a kawo miki sai dazu suka iso, ni ma na diba na ga masu kyau ne, har da na tsugunno".

Ta mike tana fadin, "Kin ga an dade da idar da sallah bari mu tafi".

Da za su tafi rungume juna suka yi kuka kowacce ta ke yi tamkar ba za su sake haduwa ba. A dole suka rabu Sumayya na mata fatan zaman lafiya da zuri'a mai albarka.

Ba su jima da tafiya ba ta zuba gawayi a kasko ta zuba kalanzir tare da kyasta ashana, ta barshi a tsakar gida, ta share falon inda su Khalifa suka bata. Sannan ta shiga wanka, sai da ta yi sallar Isha, sannan ta duba ta ga wutar ta kama, ta dauko ta zuba turaren. Kan ka ce kwabo gida ya cika da kamshi, sai kallon agogo take yi,har tara na shirin yi bai dawo ba.

Daidai lokacin ya dawo, waya ya kira, ta fita ta bude masa, kamar dazu ba mayafi a tare da ita.

Suna tafe yana fadin "idan za ki fito ki dinga saka hijab, ban son wani ya hango ki a haka".

Ta amsa da tom.

Tunda ga tsakar gida yake jin daddadan kamshi, suna shiga falon ya rikota yana cewa "Madalla da Antyn mu, irin wannan kamshi haka".

Ita dai ba ta ce komai ba, sai da suka zauna ta ce "Sannu da dawowa" Ya amsa mata cike da walwala.

"Shi ne ka tafi ka bar ni ni kadai har tsoro ya fara kamani".

Ta fada cike da shagwaba.

"Ai kuwa dai gara ki cire tsoro, kin san har sha dayan dare ina kaiwa a shago".

Murmushi ta yi kawai ba ta ce komai ba, amma a zuciyarta tana raya ba za ta yarda da wannan dogon zaman a waje ba, tana gida ita kadai.

Haka suka ci gaba da cin amarci ba kakkautawa cike da soyayya da kulawa, tun Sa'adah na jin zafi da tsoron haduwarsu har ta saba ta fara fahimtar dadi da nutsuwar dake cikin haduwar.





```Alkalamin
*Surayya Dee*.
``✍🏼✍🏼



[6/5, 14:08] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*


*A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*

*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.



*Fatan alheri ga Amare*
*Hafsa Sani Abubakar*
*Halima Sani Abubakar*
_Ubangiji ya albarkaci auren ku, ya Baku zuri'a mai albarka_.




53-54.



*BAYAN SATI SHIDA*


Zuwa wannan lokacin, sabo da shakuwa mai karfi sun shiga tsakanin ma'auratan biyu, soyayya da aminci sun sami wajen zama a gidansu, kowa kokarin kyautatawa dan uwansa yake yi.

MK ya dauki soyayyar duniya ya dora akan Sa'adah da da hali kirjinsa zai bude ya cusa ta, saboda yadda ya ke jin ta a zuciyarsa, musamman yadda ba ta gajiya da bukatunsa. Duk da dai ya gane ita ma mabukaciyar ce ta gaske ga tsafta ga iya sarrafa girkin gargajiya, saboda ire-iren su aka fi yi a gidansu.

Babban abin da ya ke gigita shi a kanta, shagwaba da iya kwalliya, kullum sabuwa take zama a idonsa, kullum da sabon abin da zai gani a tare da ita, babban abin birgewa ta kama dukkan ahalinsa ta ri'ke da hannu biyu, ta zama yar gida a gidansu, akai-akai take kiran Hajiya Babba da Hajiyar Bichi tana gaishe su. Sun zo sau daya sun ga gida, da amarya.

Tana kokari sosai wurin yin abinci akai gidan su Mk mussaman masar Bauchi da miyar ganye, da kuma Dambu. Kasancewar mahaifiyar ta daga Bauchin take, sosai ta iya masar Bauchi.

Kullum yana gida, hatta FGC Kano ma ya daina zuwa, shago kuma sai Azahar yake fita, da zarar karfe biyar ta yi zai juyo ya bar su Abbas da kula da wurin, Mahmoud ya masa tsiya ya gaji.

Shi kansa Mahmoud din tunda ya je ya ci girkin amarya, dambun shinkafa ta yi musu da ferfesun naman rago, sai kunun aya bai sake yi wa MK tsiyar ya zama bita-zai-zai ba, musamman yadda kamshin turaren gafgaf da kajiji ya kama gidan gaba'daya, dole idan mutum ya yi katarin samun irin su Sa'adatu ya manne musu ya kasa fita ko ina.

A wannan tsukun ASUU ta janye yajin aikin da ta ke yi, a kuma lokacin aka tabbatar da MK da Mahmoud da sauran da suka yi sa'ar samun koyarwa a Jami'ar Bayero takarda shedar fara aiki.

Ranar da ya fara fita aikin dukkansu sun galaibaita, sati shida kullum suna manne da juna, ko fita ya yi Allah-Allah yake ya dawo. Don haka yanzu ma da zarar ya ga yana da tazarar lokaci, sai ya dawo gida ya ci abinci, ya yi abin da zai yi, sai kuma ya yi wanka ya koma, idan kuma ba shi da sauran darasi shike nan sai ya yi zamansa gurin amaryar sa.

Watannin su biyu da aure Sa'adah ta tsiri fushin da babu dalili, share shi take yi, ta daina hira da shi daga eh sai um um, ta rage walwala idan yana gidan, idan tana falo ya zauna, sai ta san yadda ta yi ta bar falon, haka nan daki.
Ba ta gudunsa, amma shi kadai zai yi kidansa yayi rawarsa, babu gudunmawa daga gare ta.

Wannan canjin ya matu'kar 'daga masa hankali ya yi tambayar duniya tace ba komai, kuma lafiyar ta 'kalau.

Rannan da daddare ya dawo da ga Masallaci, jikinsa a sanyaye ya zauna kusa da sallayar da ta ke sallah ya jira ta idar.
Tana ganinsa ta yi kamar ba ta gan shi ba ta fara kokarin tashi a gurin ya kira sunanta a kaurare.

"Sa'adah zauna magana za mu yi".

Ba ta 'ki ba, ta koma ta zauna amma fuskar nan a 'daure, sannan ta juyar da kanta gefe, ta ki kallon inda ya ke.

"Na tambaye ki mene ne yake faruwa kin ce mini ba komai amma kuma kin canja mini, kin tayar mini da hankali, wallahi da kinsan yadda nake ji a zuciyata da kin tausaya mini cikin kwanakin ukun nan.

Shiru ta yi, tamkar ba da ita yake ba, ya matsa ya riko hannunta, ta fizge tare da zura su cikin hijab, wata irin fargaba ta kama shi, bakinsa har rawa yake yi ya ce "Har abin ya kai mu ga haka, laifi na yi ke nan?"

Nan ma shiru ta sake yi.
"Don Allah Sa'adah me na yi miki? Ki fada mini, ba ni za ki duba ba, Allah na hada ki da shi".

Jikinta ya yi sanyi sosai, ta kasa cewa komai sai da ya sake rokon ta sannan ta bude baki ta ce, "Ni gaskiya zaman ne ba zan iya ci gaba da yi ba, na gaji".

Gabansa ya yanke ya fa'di.

Murya ba amo ya ce "Me na yi miki?"

Shiru ta yi, hankalinsa ya yi mugun tashi ya fara fa'din,
"Ban miki komai ba fa Sa'adah, don Allah idan wasa kike mini ki bari bana so".

Yana rufe baki ta ce "
"Wallahi ba wasa na ke yi ba, zaman ya isa haka nan".

Ya tsura mata ido tsawon lokaci ba kakkautawa yana nazarinta, ya lura da gaske take yi, bugun kirjinsa ya karu, gumi ya fara karyo masa, jikinsa na bari ya ri'ke kafadunta da karfi, ya ce
"Kar ki mini haka Sa'adah don Allah, ina sonki fiye da kaina, fada mini inda na gaza, me na ke yi wanda ba kya so?"

Ta yi shiru amma fuskar nan a daure tamkar hadari, hannunta ya ruko da karfi ya dora a kan kirjinsa ta ji yadda zuciyarsa take bugawa da sauri.
"Kin ji yadda zuciyata ta ke bugawa, tun daga ranar da kika canja mini Sa'adah har yanzu ban huta daga wannan bugun ba, ya sake matsarta sosai ya ce "Ko aikina ne ba kya so? Idan shi ne sai na je na ajiye musu".

"Ni ban ce ba, idan ba ka yi aiki ba 'kasa za ka ci?"

"Me yasa kika cire kanki, da gaske za ki iya rabuwa da ni?"

"E mana indai zan tsira da mutunci na."

Kansa ya kulle ainun ya kasa gane me take nufi.
"Ban gane idan za ki tsira da mutunci ba?"

Ta zumbura baki ta ce "Kai ba Bahaushe ba ne?"

Ransa ya fara 'baci, ya kalle ta cike da bacin rai ya ce "Kar ki fara Sa'adatu, kar ki fara mini rashin kunya ba zan 'dauka ba".

Ya mike ya fice da ga falon ya nufi dakinsa.

Zuciyarta sai rawa take yi, ita kanta jarumta take yi, ta kuma riga ta kudire sai ya janye waccan kalmar da ya jefe ta da ita, amma ta lura ransa ya baci sosai don ta fahimci indai ya ce mata Sa'adatu to ransa ya baci da ita ne.

Da kyar ta tashi ta yi wanka, ta shirya cikin guntuwar rigar barci cotton marar nauyi, ta zauna shan black tea, amma zuciyarta na tunanin ko MK ya yi barci, ko me yake yi, ko shima fishin zai dauka yau ba zai zo 'dakinta ba?

Ta dade a falo kafin ta kashe fitila da fanka ta shige daki ta kwanta, adduar barci ta karanta ta shafe jikinta, tana ta tunani, sai ta ji shigowarsa, dadi ya ratsa ta har da sakin ajiyar zuciya.

Yana tsaye ya kunna fitila idonsu ya hadu, nan da nan ta dauke idonta, ya kashe fitilar ya nufi gadon yana kwanciya ya janyo ta jikinsa ya saki ajiyar zuciya tare da fadin

"Ni ba zan iya fushi mai yawa da ke ba, bacin ran da kika sa ni dazu na yafe miki kin ji My Sa'adah! Ke ma ki yafe mini abin da na miki, ki kuma fada mini din kar na sake maimatawa a gaba".

Uffan ba ta ce ba, amma farinciki ke ratsa ta yadda yake ta rawar jiki da neman sulhu.

"Kin ji"

Bai jira amsarta ba
ya sake cewa " Don Allah me na yi haka har zuciyarki ta gaji da zaman mu tare, ban yi zaton akwai abin da zan yi ki daina sona ba".

Haka kawai ta ji zuciyarta ta karye, hawaye ya cika mata ido, cikin rawar murya ta ce "Ban daina sonka ba ai, kawai ha'kura zan yi don shi ne ya fi alheri tun ba ka juya mini baya ka fara wulakantani ba".

Jikinsa ya yi sanyi kalau, a sanyaye ya ce "Mafarki kika yi akan zan juya miki baya, yanzu a zaman da muka yi ba ki fahimci irin son da nake miki ba? Kin fi karfin ki wulakanta a hannuna."

Ta kasa cewa komai saboda tana bude baki kuka za ta yi.

Ya sake cewa "Na ji dadi da ba daina sona kika yi ba, ina hada ki da girman Allah ki fitar da ni daga duhu, me na yi miki?"

Kukan da ta ke matsewa ya subuce mata, hawaye har a kan kirjinsa, ya rasa abin da ya ke masa dadi, hankalinsa, in sun kai dubu to a tashe suke.

Haka ya dinga jijjigata yana shafa gadon bayanta tare da fadin sorry, tamkar mai mata bita.

Da kyar ya shawo kanta ta bude baki ta ce "Tun farko na so na hakura da aurenka saboda yadda kake nuna mini am nothing to you, sai dai na san Baffa ba zai fahimce ni ba, tunda sai da ya tambaye ni na ce ina sonka, iyayenka sun zo gunsa to ba ni da sauran dama, ban isa na ce na fasa ya saurare ni ba".

Ta sarara, ta ja hanci sannan ta dora da fadin, "Muna cikin wannan yanayin, sai na yi kuskuren shiga motar saurayi, kuskuren da ni kaina na yarda ban kyauta ba, ba irin ha'kurin da ban baka ba amma ka 'ki, karshe na sake yin wani kuskuren na dauki jiki na bi ka har inda kake, don ka gane yadda fushin ka ya hana ni zaman lafiya.
Sai ka bi ni da wulakanci kala-kala har ka iya ce mini Ballagaza akan idona!"

Kukanta ya dawo sabo, ta shiga yin sa har da rerawa tamkar a cikin nisha'di take, don kawai ta sake tayar masa da hankali, ai kuwa gogan ya kasa cewa komai tsabar yadda komai ya tsaya masa, yana tuno Baba Idi da ya ce lamarin mata yana da gigitarwa, tabbas ya yarda ga shi 'yar yarinya karama tana neman zautar da shi.

Cikin kukan ta ce "Tun lokacin na tabbatar barin ka shi ya fi alheri, tunda za ka iya jifa na da wannan mummunar kalmar a ranka, sai kuma na ga gara na nuna maka ni ba ballagaza ba ce, hakan kuma ba zai yiwu ba sai mun yi aure dole, zuwa yanzu na san ka gane in ma ni Ballagazan ce ko a kasin hakan".

Tsawon lokaci MK ya kasa bude baki ya yi magana. Ya yi shiru yana jin kukanta har cikin kwakwalwarsa.

Da kyar ya bude baki murya ba sauti ya ce, "Ba har zuciyata nake nufi wannan kalmar ba, subul da baka na yi".

Da sauri ta ce"Ai sai da na tambaye ka, ni ce ballagaza, ka ce e, idan akwai kalmomin da suka fita muni na hada da su domin na siffantu da hakan".

"Billahillazi Baby kishi ne ya rufe mini ido a lokacin, amma ba har zuciyata hakan nake nufi ba, na yarda na yi laifi ki yi ha'kuri na tabbatar ke din katangaggiya ce".

Zamewa ta yi a jikinsa ta koma karshen gado tana sake sabunta kukan da take yi tare da fadin, "Ni ba zan hakura ba, kai ne za ka yi ha'kuri kar ka wahalar da ni".

Mirginawa ya yi ya tarar da ita a karshen gadon, ya riko ta tana tirjewa, kukan gaske take yi, har da bubbuga kafa tamkar yar karamar yarinya.

Kwantar da murya ya yi sosai tare da cewa "Babyna tsaya ki ji, tsakaninki da Allah, tunda muka yi aure wacce kalar soyayya ce ba na yi miki?"

Cikin kukan ta ce "Ai don ka ga zargin da kake mini ba gaskiya ba ne, bayan haka kuma kana hutawa da ni".

Ya rasa ta inda zai bullo wa wannan yarinyar, ya nisa ya ce
"Zaman da muka yi na wata biyu har da doriya, ban yi wani abin da kika gamsu son ki nake yi da iyakacin gaskiyata ba? Ko a lokacin da kike ganin ba na tarairayarki, ai kona mini rai kike yi, na ce ba na son ganin ki da dan iskan yaron nan, amma ba ki ji ba, haka na yi ta ha'kuri ba don ina son ki ba za mu yi auren ne?"

Ya sake tausasa murya ya ci gaba da fadin, "Saboda Allah indai dama ba wani abu ne a ranki ba, mene ne na dawo da abin da ya wuce, ba haka kawai na fada miki maganar da kika kullace ni a ranki ba, ke kika janyo, ko ba ni da alaka da ke zan yi kishi yanayin da na gan ki, a matsayinki na mace mai daraja".

Ya yi shiru yana jin shesshekar kukanta, tana ta ajiyar zuciya tamkar wadda ya yini yana dukanta.

"Na roke ki, ki daina kukan nan haka, na yarda ban kyauta ba ki yi hakuri".

Ta yi shiru, kamar yadda ya roka din har da gyara kwanciya, da lulluba alamun barci za ta yi, tana sakin ajiyar zuciya, a ranta kuma tana fadin sai kuma rikicin gobe.

Ya so su kasance tare, amma saboda tsoron kar ta ci gaba da masa kuka yasa ya kyale ta, ba a jima ba ya ji saukar numfashinta alamun barci ya yi awon gaba da ita.

Ya saki gauron numfashi, ya haska fuskarta, da hasken wayarsa ya ga hawaye duk ya bushe a fuskar, kuma wani abin dariya ita da kanta ta boye fuskarta a jikinsa. Tsintar kansa ya yi da gyara mata kwanciyar yadda za ta ji dadin barcin.

Ya dawo Masallaci, ya tarar ta dira sabon kuka ga akwati a kan gado sai zuba kaya take yi tamkar mai shirin yin balaguron wata guda.

Zama ya yi gefen gadon yana kallon ikon Allah, da Asubar fari za ta fara masifa tamkar jiya ba ta yi ba, duk irin ha'kurin da ya ba ta ashe bakam ta masa. Yana kallon yadda ta gama shirya akwatin ya kasa cewa komai saboda gaba'daya He is speechless.

Wanka ya ga ta shiga yana zaune ta fito, ta shirya cikin riga da skirt na English wears, skirt (purple) iya guiwarta rigar kuma body hug (pink) an rubuta *BABY GIRL* ta kama ta ainun musamman daga kirji, ta gyara zaman ribon dinta a kitsonta na shuku, ta masa kyau ba kadan ba, har ya dinga raya don ta tayar masa da hankali ne yasa ta yin wannan shigar da Asubar nan tunda ta san yau ya kwana bai taba ta ba. Ta shafe jikinta da turararuka kala-kala tun daga na jiki har na kaya, sannan ta dora bakar doguwar riga akan kayan ta yane fuskarta da dan mayafin rigar.

Ta dauko takalmi da jaka ta saka sannan ta ja akwatin ta nufi kofar barin dakin.

Wata irin fizga ya mata ta dawo da baya kamar za ta fadi sai kuma ta dire kan kafafunta. Kafin ta yi magana ya riga ta da cewa "Me kike shirin yi ne haka, ina ce tun jiya magana ta wuce?"

Hawaye yana zubar mata ta ce "Wallahi ba ta wuce ba don kuwa ni ba zan sake zama da kai ba".

Dariya ce ta subuce masa wadda babu nisha'di ya ce "Ok tunda haka ki ka zaba shike nan, sai na ga wadda zai raba ki da ni".

Ta juya za ta sake fita, wannan karon da karfin gaske ya janyo ta ya jefa ta gado tare da fadin "Wannan shi ne gangan, ba za ki fita ko ina ba, bai wani bata lokaci ba ya bita ya turmushe ya sakar mata dukkan nauyinsa.

Ta kasa koda kwakkwaran motsi, sai da ya tabbatar ta yi laushi sannan ya daga ta, sai kuka take masa mai sauti bai kula ba, sarrafa ta yake yi kawai, tun tana tirjewa har abin ya shiga jikinta ta yi lakwas ta sallama.

Tsawon lokaci kafin ya samu nutsuwa.

Sai da ya huta sannan ya tashi ya fita bayan ya zura jallabiyarsa, a shirye ya fito hannunsa ri'ke da mukallin mashin, tana kwance inda ya barta tana kallon sa, ta tura baki gaba ta dauke kai.

Murmushi ya yi ya ce "Kin ga kwana uku ke nan ina fita da yunwa amma yau a koshe zan fita, kullum haka zan dinga miki".

Harara ta watsa masa tare da cewa "Idan na zauna ba".

Murmushi ya yi tare da fadin "Ba inda za ki iya tafiya ki bar ni, wa zai iya da wannan fitinar ta ki ai sai ni din".

Ganin magana yake nema yasa ta daina tankawa.

"Zan tafi, ki tashi ki yi wanka ki karya, idan na dawo ban tarar da abinci ba, ki tabbatar ke ce abincin."

Ya fita yana fadin "Sai na dawo." A fili sharewa ta yi amma a zuciyarta addu'a take masa.

Yana barin tsakar gida ya janyo kofar ya rufe ta da kwado ya saka mukallin a dan jikin flowers, ya fitar da mashin dinsa, ya bar kofar gate din ba tare da ya rufe da jamlock ba.

Wanka ta sake yi, tana yi tana tsaki, haka kawai an mayar da mutum kamar agwagwa wanka dai wanka dai ba kakkautawa.

Ta mayar da kayan da ya cire mata bayan ta shafa mai, doguwar rigar ta ninke ta mayar durowa, sai da ta gyara gidan fes ta share ta goge ko ina. Ta kunna risho ta dora tukunya don dafa indomie, dogon Hijabi ta dauko ta saka, ta dauki kaskon turaren wuta, lekawa za ta yi ta samu yaron da zai samo mata garwashi a gidan Maman Nana, jan duniya kofa ta'ki budewa ga shi kuma ba da mukulli aka rufe ba, kan dole ta ha'kura bayan ta hango kwado ta yar karamar kofa, murmushi ta yi tana fadin
"Ya dauka da gaske tafiyar zan yi".

Tana karyawa ta yi wanke-wanke, ta dora abincin rana, farar macaroni ta dafa ta fito da miyar kifi daga fridge ta dumama ta bar ta akan rishon, ta juye macaronin a foodflask ta ajiye, ta tsinci kanta da son hada masa zobo, nan da nan ta dafa

Please Login or Register in order to submit comment