You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kawo hakan, amma abin yana mini yawa mussaman da kullum'kara yin nisa muke yi! Idan anturo ku dinga tarawa, idan antambaya ku yi sharing, yanzu aka fara, labari na gaba, JAZAKUMULLAHI KHAIR.*



*Comments din ku na sani nisha'di na gode sosai fans Allah ya fini yabawa*




*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.





29.





Ta jima zaune a gun, tana jin wani irin nisha'di tare da shauki yana ratsa zuciyarta da gangar jikinta gaba'daya, tana tuno yadda ya lankwashe murya yana fadin,

"Ke ce Bebina ba Farida ba"

Cike da farin-ciki ta na'de tabarma ta shiga gida, dakin Inna ta fara shiga ta shaida mata ta dawo sannan ta jigine mata tabarma inda ta dauka.

'Dakinta ta shiga, ta fara tattara uniform din da ba ta wanke su ba, ta fita tsakar gida ta hau wanki, hatta sandal sai da ta wanke ta shanya, tana gamawa ana kiran Maghrib. Koda Inna ta fito ta ga shanyar uniform uffan ba ta ce mata ba.

Sai da Baffa ya shigo bayan sallar Isha ta je ta durkusa gabansu, ta shaida musu gobe za ta je makaranta, Inna dai ba ta tanka ba, Baffa ne ya ce,

"Allah ya kai mu"

Ta dade a tsugunne tana jinta wani iri, ta san fushi suke da ita dukkansu musamman Inna. don haka sai ta sanyaya murya ta ce,

"Don Allah ku yi ha'kuri na san ban kyautata muku ba, na yi musu da ku, ku yi mini afuwa"

Ta fada cikin muryar kuka, kasancewar Baffa ya fi mata sassauci, shi ne ya fara tankawa da cewa,

"Ni ban san inda kika samo dabi'ar yin musu da iyaye ba Iyah? Ni da kaina na rarrashe ki akan wannan maganar kika kafe, kika nuna mini ni ne zan bi ki ba ke za ki bi ni ba".

Jikinta ya yi mugun sanyi ta shiga kuka na sosai tana jin kunyar maganganunsa na matu'kar ratsata, musamman yadda komai take so yana kokarin yi mata duk kuwa da wani abin don ya faranta mata yake yi, ba don yana so ko yana da karfin yi ba. Cikin kuka sosai ta ce, "Don Allah ka yi ha'kuri Baffa In Sha Allah ba zan sake ba."

Ya nisa ya ce, "Shike nan na yafe miki, amma ki kiyaye, wannan ba dabi'ar kwarai bace, musamman kasancewar ki mace, ko wani daban wanda kika san ya girme miki ya ce miki kar ki yi kaza, ai kin mutunta shi ki bar abin kasancewar ya fi ki hangen nesa, bare kuma ni mahaifinki da ba zan cutar da ke ba ta kowacce fuska".

A hankali ta ce, "In Sha Allah zan kiyaye, na gode Allah ya kara lafiya da nisan kwana Baffa".

Cike da tarin soyayya mai yawa ya amsa mata da,
"Amin Mamana!"

Sai kuma ta juya ga Inna da ba ta tsoma musu baki ba ta ce, "Don Allah Inna ke ma ki yi ha'kuri da bacin ran da na saku".

"Ni ba ki yi mini komai ba Iyah, amma tabbas inda ta ra'ayina za a bi kin gama yin boko tunda ke naki karatun na raini ne, haka siddan ana wahala da ke rana tsaka ki hau iyashegen ke ba kya son makarantar sai an canja miki, alhalin tun farkon samun wannan makarantar kin san ta fi karfinmu, amma kika kafe sai ita, kina kallon yadda yar'uwarki da mijinta suke 'dawainiya da ke, mu ma muna irin namu kokarin tunda wahalhalun makarantar yawa ne da su, sai kuma don kin raina mu ki ce lallai sai kin bar makarantar kin koma wata saboda ki nuna duk wahalar da ake yi akan makarantar ba karatun da'a kike koya ba, na raini ne da iyashege."

Jikin Sa'adah ya sake yin tubus ta san Innarsu mai zafi ce amma a yau yadda take furzar da magana ta san ba karamin fishi ta yi da ita ba. don haka sai ta sake yin kasa da kai ta ce, "Ki yi ha'kuri Inna"

Ta nisa ta ce, "Ke ce da ha'kuri Iyah, domin ina lura da take-takenki, kwatakwata ba ki ajiye kanki kusa ba, ina jiye miki kar ki jefa kanki a *HALIN YAU* na nadama marar amfani".

Sai da Baffa ya sa baki sannan ta ha'kura ta ce ta huce magana ta wuce, Sa'adah da kyar ta mik'e bayan ta musu godiya tare da tabbacin ba za ta sake 'ba ta musu ba.

Kasancewar sanyi ake kadawa yasa uniform din, nan da nan suka bushe, kafin ta kwanta barci sai da ta goge su tas! Sai da ta kammala komai ta kwanta ta fara tunanin yadda za ta kaya a tsakaninsu, anya ma ba zai ga rashin ajinta ba? daga magana daya sai ta hau bare-bare, kodai ta ki zuwa makarantar ne a iya gobe ta yadda idan ta koma zai gane ba saboda shi ta koma ba, tunda yanzu kam ta gane, ba karamar wauta ta yi na barin karatunta saboda wani dalili marar kangado ba?

Da sassafe ta tashi ta yi ayyukan da ta saba yin su, ta karya sannan ta shirya, ta yi wa iyayenta sallama ta karbi kudin makaranta ta tafi bayan sun bi ta da addu'ar albarka da dacewa.

Kai tsaye makarantar ta yi saboda ta san Zainab ta riga ta tafi, tunda ta sha biyo mata, tana cewa ba za ta je ba. Ba irin banbakin da Zainab ba ta mata ba, har ta gaji ta fusata ta daina biyo mata.

Tana shiga class dinsu aka hau ihun murna tare da fadin "Gogel is back!".

Ba su sarara ba sai da Uncle MK ya shiga don yin attendance, ya shiga rarraba ido, ya hango ta zaune kan desk dinta sanye cikin uniform sai daukar ido take yi, ga mamakin ta sai ta ga ya yi kamar bai gan ta ba, bare ya nuna wata alamar ya ji dadin ganin ta.

Ya shiga kiran sunayensu, har aka zo kanta, tana amsawa kuwa ya ba ta umarnin ta mike tsaye, sai da ya kammala gaba'daya sannan ya tambaye ta dalilin rashin zuwanta makaranta tsawon sati biyu, cikin rawar murya ta ce, "Am sick!"

Ya daure fuska sosai, cikin harshen turanci ya ce, "Waye ya zo ya fadi cewar ba ki da lafiya? Ina kuma shaida daga asibiti da makaranta za ta gamsu da gaske rashin lafiya kika yi? Ta rasa me za ta ce, sai ta yi shiru tana mamakinsa, ganin haka yasa ya ce ta fito, ta bi shi zuwa Staffroom.

Bai dake ta ba amma ya yi punished din ta, ta hanyar sata wankin staff toilet wanda duk dalibi ya tsani a sashi wannan aikin. Tana gamawa ya sake cewa ta wanke window glass din Staffroom wanda duk malamin da ya zo wucewa sai ya gan lta, wani ya tambayi me ta yi, wani kuma ya wuce. Mrs Ngozi, Maths Teacher dinsu kuwa sababi ta yi ta mata, tana cewa, "You again? You're rude student." saboda yadda kwanaki ta musu case da Farida.

Zuciyar Sa'adatu kamar ta fashe don bakin ciki, tana aikin tana kuka tana raya ashe da ma so yake ta zo ya ci ubanta shi yasa ya yi tattaki har gidansu ya mata kalamai wanda duk karya ne tsagwaronsu?.

Har aka tashi, tana wannan aikin, kuka ta yi shi kamar idanuwanta su fado kasa.

Koda aka tashin, da kyar Mr. Charles (Chemistry Teacher) ya ro'ki MK akan ya mata afuwa, ya bar ta haka nan, wanda ita a lokacin ta riga da ta fusata ba ma ta bu'katar ya mata afuwar, ai duk tsananinsa dai ba zai raba ta da numfashi ba, sai da aka gama watsewa sannan ya ce ta tafi. Tana kuka sosai ta wuce shi ya ce, "Sa'adah dawo, ba za ki gode mini ba? Takaicinsa ya sha'ke mata wuya, amma sanin halinsa na zai iya janye afuwar da ya yi mata sai ta ce,

"Thank you!" Cikin kuka.

Zuciyarsa ta yi rauni amma sai ya dake ya kalle ta tana tsugunne cikin kasa, ya tuna yadda ta zo cikin tsabta tana daukar ido amma yanzu ta yi futu-futu ta fita a hayyacinta. Sai ya ce ta jira shi a gate, wajen makarantar ke nan.

Takaicinsa ya sake kamata, amma sai ta amsa da to ba don za ta jira shi 'din ba.

Tana tafiya ita ka'dai kasancewar duk 'daliban sun tafi, tana rayawa ita kuwa mai zai ce mata? Ai kuma ba zai sake yaudararta a karo na biyu ba.

Makaranta dai za ta ci gaba da zuwan ko don zaman lafiyarta da iyayenta, amma In Sha Allah za ta yi iyakar 'ko'kari ta cire MK a ranta, tana shirin tsayar da abin hawa ya cimma ta kusa da ita ya tsayar da mashin dinsa.

Ta dauke kai tamkar ba ta gan shi ba ya ce, "Hau na kai ki".
Fur ta 'ki, don haka ya sauko ya kafe mashin din, suka gangara inda ba wucewar ababen hawa sannan ya tsaya ya dube ta ya ga yadda ta hade rai tamkar hadari.

Ya nisa ya ce, "Sa'adah are you angry with me?"

Hawayen ba'kin ciki ya ziraro ta ce, "A a, Am happy with you".

Ya san inda ta dosa, don haka sai ya ce, "Saboda Allah kinga ya kamata, ki yi laifi na kasa hukunta ki alhalin dokar makaranta kika karya? Kin san fa, if you want to show an example, you have to start it from your section for them to know you are not a selfish.
Ke yanzu na san dauka zaki yi da gayya na miki hakan, Ni kuma na rantse miki, ba zan yi son zuciya a cikin aikina ba, don haka ki ri'ke, ki kuma kiyaye".

Ta tura baki irin na sakarci da nuna takaici ba tare da ta ce uffan ba.

Ya nisa ya ce, "Ba za ki daina wannan fishin ba?"

Sake daure fuska ta yi tare da 'kin tankawa.

"Amma kin san na yi farin cikin zuwan ki makaranta yau?"

Sai a lokacin ta fashe, cikin kuka ta ce, "Ni kuma ban yi farin-ciki ko ka'dan ba, sai tarin ba'kin ciki da nadama."






Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*.
✍🏼✍🏼
[5/26, 20:33] Aminan Ibrahim: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*



*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.








30-31.





Kuka sosai ya kwace mata, wanda ya yi matu'kar taba shi, tun a wannan ranar kuma ta gane rauninsa yana motsawa ne idan ya ga tana kuka.

A ki'dime ya shiga tattaro duk wata kalmar sanyaya zuciya, da nuna kololuwar kulawa, duk da ba ha'kuri yake bata ba, tunda shi ya san akan 'ka'idojin makaranta ya hukunta ta, ba ya kuma fatan ya ci amanar aikinsa.

Tsawon lokaci tana kuka, ta koma ajiyar zuciya tunda dama tun safe take yinsa.

Da kyar ya shawo kanta ta yi shiru, sai da ya ga ta nutsu sosai, sannan ya samu sukuni a zuciyarsa, yana mamakin yadda yake jin matsananciyar soyayyarta na ratsa dukkan jikinsa gaba'daya.

Cikin murya marar amo saboda shauki ya ce, "Jiya na ce miki zan zamu yi magana ko?"

Bai jira amsarta ba ya ci gaba da fadin, "Ban yarda ki fada wa wani ko wata cikin makarantar nan abin da ke faruwa a tsakaninmu ba, wannan sirrinmu ne ni da ke da ba zan so ya shiga kunnuwan students ba."

"Sannan bana bu'katar, ki nuna wata alama da students za su fahimci akwai wani abu a tsakaninmu, lastly ki rabu da fitunannen yaron nan (Khalil), ki fita harkarsa in dai kina bu'katar kwanciyar hankalina".

Ta yi shiru tana nazari maimakon ta fahimci inda ya nufa sai ta karkace, zuciyarta ta shiga kissima mata ai saboda Farida ne yasa zai ce bai son aji yana sonta banda haka mene ne na boyewa tunda dai aure za su yi ba wata 'barna ba.

Ya gaji da shirunta, ya ce,
"Kina tare da ni kuwa?"

Nan ma shiru ta yi, bai ji dadin shariyar da ta mishi ba, amma sai ya waske, ya san dama haka take, bare kuma yau ya ta'bo ta.

'Kasa ya yi da murya sosai ya sake cewa, "Magana fa nake miki, amma kin yi mini shiru".

Cike da fishi sosai ta ce
"To ni me zance?"

Zuba mata ido ya yi, yana kallon yadda take ta cika tana batsewa har wani huci take yi, jikinsa ya yi sanyi bai cika son mace mai fusata sosai irin haka ba, sai dai son da yake mata ya riga ya yi bunkasar jurewa duk wani kalubale daga gare ta.

Wannan karon ido ya zuba mata, tare da bude murya sosai ya ce, "Ina ta miki magana amma kina jina kin mini shiru, kar ki bari na ji a zuciyata son da na ce ina yi miki shi ne dalilin da za ki fara raina ni".

Kawai sai ganin hawaye ya yi yana tsere a kan kuncinta, tana ta yunkurin bude baki don ta yi magana amma ta kasa.

A ransa yake fadin akwai aiki a gabana, a kankanin lokaci ya gane shagwababbiya ce ta gaske, banda haka mene ne kuma abin kuka a maganar da ya yi? kan dole ya yi ta rarrashi akan ta fada masa abin da yasa ta kuka cikin maganganun da ya yi.

Cike da kukan kuwa ta hau cewa, "Ai an sha fada mini duk saurayin da yake boye kanshi kar a san yana son mace, to ba da gaske yake ba, yaudarar ta zai yi".

Ta 'karasa maganar cike da gunjin kuka, mamakin ta ya kama shi sosai ya ce, "Amma na sha fada miki gidanku ba gidan da zan yi wasa ba ne, tunda kina shakku a kaina a satin nan zan gabatar da kaina a gaban Baffa shike nan?"

Ta goge Hawayen da ya'ki tsaya mata, a hankali ta ce
"To saboda kar Farida ta sani ne kake son a boye?"

Takaicinta ya kama shi, amma kuma ya kasa yi mata jan ido, sai ma lallaba ta da ya shiga yi, ta hanyar fadin. "Sa'adah ya kamata ki dinga fahimta ta, inda Farida nake so, nake burin aure ba abin da zai kawo ni gunki tunda ba dole aka mini ba! Ribar me zan ci idan na zo don na miki karyar ina son ki? Mahaifinki mutumin kirki ne, na san shi, tun kafin na san ki, akan me zan yaudari yarsa? Ina son ki yarda da ni, yarda ita ce matakin farko a soyayyar gaskiya, abin da yasa nake son mu bar maganar a tsakaninmu ba komai ba ne illa don na kiyaye dokar makaranta!

Ba makarantar da ta yarda malami ya yi soyayya da 'daliba, ni kuma zan yi iyakar'ko'kari na kiyaye kowacce irin dokar makaranta, ta kowacce fuska wannan shi ne gaskiyar magana".

Ta yi kasa da kanta, tana jin nutsuwa da maganganunsa.

Ya nisa ya ce, "Kin yarda da manufata?"

Kai kawai ta 'daga mishi alamar eh, sai ya ce "To ba ki ce komai akan wancan yaron ba"
Ta sake yin kasa da kanta ta ce,

"Ai ni ba saurayina ba ne".

Da sauri ya ce "Magana muke ta gaskiya fa Sa'adah! kin san har letter da kika masa wacce na dauka tana nan, kawai idan kin amince kina sona, to ki fita harkarsa, kin san dai yaro ne karami, da ba zan iya hada soyayyarki da shi ba, ga shi dama ba tarbiya ce ta wadace shi ba".

Kanta tsaye ta ce " To! na ji zan rabu da shi, kai ma kuma ban yarda na dinga ganinta tare da kai ba, kodayaushe tana hanyar staffroom saboda kai, kai ma da ka motsa sunanta ne a bakinka, to ba ita kadai ba ce mai 'kokari ba, ire irenta suna nan, wasu da yawa ma a cikin makarantar sun fita kokarin, ita zubin Sadakar Yallah da kuke gani a tare da ita yasa kuke ga kamar ta fi kowa".

Mamaki da dariya suka kamashi lokaci guda, amma ya dake bai bari dariyar ta fito ba, ya ce, "Amma ai na tabbatar miki ba son ta nake ba, sannan kin san dole wani abin zai hada mu tunda dai ni malaminta ne, abin da za ki yarda da shi shine wallahi ba budurwa ta ba ce, ba ni kuma da niyyar auren ta".

"Amma da bakinka kace mini za ka iya maye gurbina da ita".

"Tabbas na fadi hakan amma ki sa a ranki sai idan ke ce kika so faruwar hakan, ina nufin kika juya mini baya, sai na yi maleji da ita a rashin ki, kin san Bahaushe ya ce a rashin uwa, akan yi uwar'daki".

Da'di ya kamata har murmushi ya subuce mata, shi ma ya taya ta murmushin tare da cewa,

"Na rantse miki ban taba ganin wacce ta fi ki kyau a duniyata ba, musamman idan kika murmusa".

Kunya ta kamata tasa dukkan hannunwata ta rufe ido tana jin kamar su tabbata a haka.

Ganin sun dan fahimci juna ka'dan ya ce "To muje ki tafi gida kar aga kin dade da yawa, tunda ba za ki yarda na kai ki ba".

Sai da ya sa ta cikin Adaidaita Sahu ya biya kudin, sai da ya ga sun tafi sannan ya koma ya hau mashin dinsa yana jin shauki na shigarsa, yana kuma jinjina kishin Sa'adah.


WAYE MK BICHI?

Haifaffen karamar hukumar Bichi ne, a jahar Kano. Mahaifinsa Alhaji Kabiru Wadata, Bafulatanin Bichi ne, mai arziki ne a lokacinsa, don zai shiga cikin jerin attajiran Bichi shi yasa ake masa la'kabi da Wadata. 'Dan kasuwa ne mai sana'ar fata, yana fataucin ta zuwa jahohin Arewa.

Mukhtar shi ne babban dansa na namiji, shi ne kuma na biyar a dukka gidan, an haifi mata hudu kafin shi.

Matan gidan biyu ne Hajiya Babba (Indo), tana da yara bakwai wadda ukun farko dukkan su mata ne, Zainab, Khadija, Amina, kuma duk sun girmi MK, sannan Abbas, Akil, Sameera, da auta Bilkisu.

Sai dakin amaryar gidan wacce ita ce mahaifiyar MK, Hajiya Rabi yaranta uku kacal, Hafsatu ce Babba, sai Mukhtar sannan auta Ahamad, da Mk ya girme masa da shekaru kusan goma

Mahaifin MK mutum ne mai sau'kin kai, mai kokarin wadata iyalinsa da komai na bukatar rayuwa, dukkan su, sunyi karatu, matan dai suna kammala sakandire yake aurar da su, yayin da mazan ke zurfafa karatunsu a jami'o'i daban-daban a cikin kasar nan.

Gidansu akwai zaman lafiya, duk da ba a rasa yan kananun gutsuri tsoma irin na gidan Polygamy Family, amma dai nasu da sauki ainun kasancewar iyayensu matan ba su cika samun sabani ba. Idan ma sun samu to suna bari a tsakaninsu ba tare da sun bari yaransu sun shiga rigimar da ba tasu ba.

Wannan dabi'ar tasu, tasa hankalin mijinsu ya kwanta da su, inda yake musu hidima su da ya'yansu kan jiki kan karfi.

Mahaifinsu a tsaye yake kan sha'anin tarbiya, sannan ya dace da mata na-gari da suke taya shi, dora yaran akan kyakkawar turba, domin kuwa duk yadda namiji ya kai da kula da tarbiyar yara in bai yi dace da mace ta-gari ba, to da wahalar gaske yaran su bi tsarinsa.

Mukhtar ya fara karatunsa a kwalejin ilimi ta tarayya dake garin Bichi, bayan ya kammala sakandiren hadaka ta gwamnatin jaha (Unity Boys Karaye). Sai da ya kammala NCE, sannan ya yi JAMB ta D.E, ya yi sa'a ya samu level 200 a jami'ar Bayero, inda ya karanta harshen turanci (English Language), yana shekara ta biyu ne Allah Ya yi wa mahaifinsu rasuwa a hadarin mota ya je dauko Bilkisu a makarantar kwana, wacce tare suka rasu da Bilkin.

Wannan mutuwa ta matu'kar taba ahalin wannan gidan, dole suka tattara suka ha'kura suka bi su da adduar samun rahamar Ubangiji.

Haka iyayensu mata suka ci gaba da zama suna ci gaba da kula da ragowar yaran da ke gabansu wanda Sameera ce kawai ta rage ba a aurar ba sai maza su kuma suna ta karatunsu cikin nutsuwa.

Da ma can suna da sana'oinsu, sai suka samu sau'kin tafiyar da gidan da kuma tallafin 'ya'yansu maza da mata, musamman MK da ya kasance shi ne babba, kuma shi ya debo kusan halin mahaifinsu, na hakuri da yawan kula da lamarin gidan.

Yana da sau'kin kai ta yadda duk yan'uwanshi suna jin da'din mu'amala da shi, kafin ya fusata yana jimawa, amma fa idan ya yi fishin wuyar sauka ne da shi.

Abu mafi kyau cikin halayyar MK Bichi, ma'abocin addini, mai kokarin kiyaye dokoki ne na gaske, sannan duk layin da ba gaskiya, ba za ka same shi a ciki ba. Akidar son bokon da ya taso da ita bai sa ya yi watsi da kyawawan al'adun Malam Bahaushe ba.

Sannan MK ma'abocin 'kamshi ne tun yana Secondary, da kamshinsa ake gane ya zo guri, bayan haka kuma He is Frank and friendly to all.

Wannan ke nan.




Alkalamin
*SURAYYA DAHIRU*
✍🏼✍🏼.

🌺 *HALIN YAU*! 🌺




•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•





*_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._*




*KAR KU BARI A BARKU A BAYA WURIN KARANTA LABARIN HAZI'KAR MARUBUCIYA*.

*⚜️BUƊAƊƊIYAR SOYAYYA⚜️*

*Jameey yar'mutan kankia*.


*Promo* *Promo* *Promo*


_Daga yau 21/5/2022 promo dinmu zai fara,har zuwa 30/5/2022 inshaa Allah,ga yanda promo din yake_.

*#300-sau biyu a rana*
*#500 -sau ukku a rana*
*#700 -sau hudu a rana*


_Kiyi man wanann number magana danjin ynda zaki biya 08160508316_.



*MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU 'KOFA A BUDE TAKE*
_TUNTUBI_
08032773332.





*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.




32-33.





Tana isa kofar gida ana kiran La'asar, sai da gabanta ya fadi saboda yadda za ta sha tuhumar inda ta tsaya har zuwa wannan lokacin a wurin mahaifiyarta.

Ilai kuwa a tsakar gidan ta tarar da ita sai safa da marwa take yi, jin sallamar ta yasa ta tsaya cak, tare da zuba mata ido, amma ganin ta futu-futu kuma idanuwanta a kumbure sai ta sami sau'kin tashin
hankalin da ta shiga, don ta tabbatar Iyah ba za ta iya biyawa wani wajen a haka dukun-dukun ba, amma duk da hakan sai da ta ce "A ina kika tsaya har zuwa wannan lokacin?"

Fuska daure ta ce "kwanakin da na yi ban je makarantar ba shine suka ci zalina."

Ajiyar zuciya Innar ta sauke sai kuma ta ce "Madalla da wannan cin zalin."
Sannan ta dauki buta ta zaga ban'daki.

Sa'adah daki ta yi tana tube kayanta, zuciyar ta fes ,tana tuno hirar su da MK da ya mantar da ita takaicin da ya kunsa mata a safiyar yau.

Tana idar da sallah ta wanke uniform din da ya baci da 'kura sannan ta zuba abinci, kai tsaye falonsu ta shiga wanda ba komai sai leda a shimfide da labulaye, sai yar karamar talabijin kirar (sharp) a kan dan karamin tebur, kusa da mahaifiyarta ta zauna da ta ke kulla bushasshiyar kubewa.

Ganin Innar ba ta 'daga kai ta kalle ta ba yasa ta fadin, "Inna ko ki tambaye ni, ko na ji ciwo a cin zalin da aka mini?"

Cike da rashin kulawa ta ce "Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka, tunda kin yi girman da za ki zabawa kanki abin da ya dace da ke ai magana ta 'kare"

Jikinta ya mutu ta ce "Inna kin ce magana ta wuce, amma kina ta share ni kina nuna ko oho da ni" Ta ture abincin tare da fashewa da kuka.

Da farko share ta ta yi, amma jin yadda take ta sauke ajiyar zuciya, ga kuma hawaye nata tsere a fuskarta, sai ji ta yi raunin da bata son ta nuna mata ya kubce mata cike da tarin soyayya irin ta uwa ta tausasa murya ta ce "Share hawayen kin san dai ba na son kukan ki ko?"

Ta tura baki cike da shagwaba ta ce "Inna ai da ne ba kya

Please Login or Register in order to submit comment