You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

akan dawowarta fada mini zan iya fasawa, idan har hakan zai fi zama masalaha."

Rungume shi ta yi sosai ta na jin wata irin nutsuwa ta na shigar ta.

Ashe har haka matsayinta yake, ashe darajarta ta kai haka? kai ta hau girgizawa, ta ce, "A a ban da matsalar komai wallahi, kawai dai fargaba nake kar ka canja mini kar ka juya mini baya".

Murmushi ya yi yasan tana da hujjarta tunda an yi hakan a baya, don haka sai ya ce, "Aure ya wuce wasa ba na fatan kuma na rabu da matar aure na akan wata matar, ki cire wannan tunanin don yanzu ke ce matata, zan iya ha'kura da ita, matu'kar ta ce ba za ta zauna da ke ba, ke ko ba zan iya rabuwa da ke akan ta ba"

Sai kawai ta saki kukan da take ta haniniya da shi akan kar ya zubo, ya 'dago ta ya shiga lashe hawayen nata, wanda na tsananin murnar maganganunsa ne ko da ba haka ba ne a zuciyarsa ya nuna mata girmamawa tare da karramawa, ta kuma gamsu yana son ta sosai.

"Ubangiji Ya sanya alheri ya zaunar da mu lafiya, Allah ya 'kara maka lafiya, da bu'din arziki ya kuma hore maka ikon yin adalci"

Amin ya ke ta fa'di tare da jin ba abu mai dadi a duniya irin mace ta gari, mai fahimta, mai kuma ilimi da aiki da shi, don sau tari shedanun matan masu ilimin ne, kawai aiki da shi ne ba sa yi. A fili ya ce, "Ubangiji Ya miki albarka My Feri-Feri, Allah Ya ba ki rabo mai amfani."

Zuciyarta ta yi fes ta na jin dadin wannan addu'ar da yake yawaita yi mata na albarka da samun zuri'a mai albarka.

Suna haka har aka kira La'asar sannan suka mike shi ya yi Alwala ya yi masallaci ita kuma ta yi a 'dakinta.

Bayan ya dawo Masallaci bai shiga gidan ba a 'kofar gidan ya samu gefe ya zauna ya ciro wayarshi ya fara lalubo lambarta, karon farko bayan shudewar lokaci mai yawa, daf da za ta tsinke ya ji ta dauka, Sallama ta yi, ya amsa, sai kuma ta ja bakinta ta tsuke, shi kansa sai al'amarin ya zo mishi a bai bai, cikin 'karfin halin da aka san namiji da shi ya ce, "Ke ba ki iya gaisuwa ba ne?"

Cike da son ta nuna mishi ba shi da sauran matsayi a zuciyarta ta ce, "Waye?"
Bai yi mamaki ba, dan haka sai ya nufin 'kunsa mata takaici shima.

"Wadda ki ke ta sallar dare ne akansa".

Yana rufe baki ta ce, "Babu wannan halittar"
tare da kashe wayarta.

Zuciyarta na bugawa wai yau mafarki take ne ko kuwa da gaske Malam ne ya kira ta taka nas? Wacce iriin sa'a yau ta tashi da ita? tana tuna kalaminshi na 'karshen maganar su a wani lokaci da ya shu'de, sai ta ji murnarta ta koma ciki, ba za ta saurare shi ba har sai ya janye kalamunshi, da kallon da yake mata, idan ko ba haka ba, to tabbas ba za ta sake mu'amala da shi ba, bare babbar mu'amala irin ta aure, ko da hakan na nufin mutuwarta ne.








Al'kalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼✍🏼
[5/16, 13:26] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺


*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•



*SADAUKARWA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*



*Fatan Alheri ga*
_DANDALIN MUM KHADY_.
🤝🏽




15-16



Mamakin ta ne ya yi matu'kar kama shi wai yau shi ta kashe ma waya? Anya Sa'adah za ta canja hali kuwa?

Sake 'kiran ta ya yi a karo na biyu, amma ga mamakin sa har 'kiran ya katse ba ta 'daga ba.

Ya ri'ke wayar ya yi jim cikin sanyin jiki da tunani iri iri.
Ya san kirkinta ya fi sharrinta yawa, har yau kuma, shi dai a idanuwanshi bai ga wacce ta iya tsara kwalliya da gayu irin Sa'adah ba, ma'abociyar son 'kyale-'kyale ce, kusan wannan dabi'ar tata na son kayan 'kawa masu tsadar gaske ya taimaka wurin sake jefa aurensu cikin garari.

Lambar amininshi ya lalubo Dr. Mahmoud Karfi, ba ta dade tana dokawa ba, ya ji an 'dauka, tare da sallama, kai tsaye MK ya ce, "Kana Ina?" Daga can bangaren ya amsa da cewa, "Ina makaranta, lafiya?"

"Lafiya Lau jira ni gani nan zuwa"

Ya katse wayar ya mi'ke ya shiga gida, ya dauki mukullin motarshi, tare da yi wa matarshi sallamar ya fita, ta bi shi da addu'ar dawowa lafiya.


"Kai tsaye sabuwar Jami'ar Bayaro ya nufa, bai bi takan ofishin saba, ya zarce ofis din Dr. Mahmoud Karfi.
Da sallama ya shiga shi ka'dai ya tarar yana dakon isowarsa, musabaha suka yi, Dr. Karfi ya dube shi, "Ka sa ni tunani iri iri fa"

Jim MK ya yi tare da cewa, "Wallahi ru'dani na shiga, ka san Hajiya ta matsa akan maganar na dawo da yarinyar nan, to dai yanzu na amsa mata akan na amince bayan na yi addua na kuma ji na aminta da lamarin. Wai yau na 'kira ta a waya da farko ce mini ta yi waye?"

Dariya ta so subuce wa Dr. 'Karfi, amma ya kirne, shi kuma ya zarce da cewa,
"Karshe kuma sai ta kashe mini waya"

"Alhamdulillah!"

'Karfi ya furta a fili tare da cewa "Ni na da'de ina ji a jikina idan dai ba mutuwa ce ta sure dayanku ba, to kuwa za ku sake ha'dewa. Shi yasa na kyale ka ka sami nutsuwa, ka san dai Sa'adah ta bi ka iyakar bi akan ka yafe mata, amma ba ka yi ba, ka zo ka yi aure dole ta gaji ta yi fishi, amma na san fishin ba mai yawa ba ne, tunda tana son ka."

A sanyaye ya ce, "Anya kuwa? ba ku san ta ba ne, a makarantar su Jawad fa baka ga iya shegen da ta mini a bainar nasi ba"

Dariyar da Dr. 'Karfi ya ke ri'kewa ta subuce, ya hau yi sosai, har ta sha'kar da MK, don haka sai ya mike ya ce, "Na gode"

Da sauri 'Karfi ya ruko shi ya na fadin, "Yi hakuri ka zauna ai ba mu gama ba"

Cikin fushi ya ce, "Ya zan zo maka da matsalar da ta dame ni, ka sani gaba kana mini dariya ka mayar da ni mahauka ci!"

"Wane ni Allah ya huci zuciyarka zauna mu gama"
'Karfi ya fada bayan ya shanye dariyarshi. Komawa ya yi ya zauna amma fuskar nan a ha'de.
"Yanzu ka san me? Zan je na same ta mu yi magana, idan ya so sai mu koma tare, daga nan kuma shike nan sanda za ka je ma ba zan sani ba"

Cikin cin magani ya ce "Ni wallahi bazan ta zarya a wajenta ta na mini iya shege ba, yanzun ma Hajiya ce ta matsa amma banda haka ta je can ta 'karaci tsiyarta"

Mahmoud ya ce, "Yanzu ma damuwar da na gani a fuskarka, akan ta kashe maka waya, Hajiya ce ta matsa ka fada mini?"

Tsaki ya ja, ya san sha'kiyanci zai masa, tunda idan akwai wanda ya san yadda yake son Sa'adah to kuwa Mahmoud ne.

Sai kawai ya mi'ke ya fice yana fadin, "Sai ka yi kai ka'dai."

Shi kuwa ya ci gaba da dariyar shi a sake yadda yake so.

Ta idar da sallar Maghrib ke nan tana zaune tana tasbihi, zuciyarta cike da farin cikin fara gyaruwar al'amuranta, wayarta ta hau kuwwa, ganin sunan Baban dady yasa ta jin wani farin ciki ya 'kara kama ta, ba ta yi azarbabin 'dagawa ba har ta katse.

Kafin ta yi wani yun'kurin, ya sake 'kira, haka ta gama yau'kinta, ta dauka hadi da yin sallama,"Ranki ya dade ai na zaci ba za ki dauka ba ne"

'Yar dariya ta yi, "Akan me? Sallah na idar."

"Ya mutanen gidan to?" Ya tambaya, ta amsa mishi da, "Duka lafiya Lau"

"Ina son ganin ki wanne lokaci zan same ki?"

sanin mutuncinsa da karamcinsa ya sa ta fadin ko yaushe "Ina gida!"

"To ki saurare ni anjima kadan zan iso."

"Sai ka zo." Ta fada tana jin wani irin nisha'di na tsirga mata.

Wanka ta shiga ta fito ta shirya cikin lallausan yadi ruwan hoda, mai shegen tsada ba shi da adon komai haka yake plane sai yauki yake da 'daukar ido. Doguwar riga ne aka 'kawata da shudin stones masu sheki matu'ka, don haka ta yane jikinta da matsakaicin mayafi blue,
mai da roll on kawai ta shafa, kasancewar turarukanta sun kama kayanta sosai kuma ma'abociyar yin turaren kaya ne irin na barebari (garam). Duk da dare ne, sai da ta shafa powder ta kuma zagaye le'banta da jan baki ruwan hoda.

Yanayin jikinta irin tauraruwar wasan kwaikwayon nan ce Hafsat Barauniya, duk da Hafsar ta fi ta shekaru, ta kuma fita hasken fata, kasancewar Sa'adah mai duhu ce, ba kuma ta yarda ta shafa man da zai canja mata launin kalarta ba,
illa tana 'batar da kud'a'de masu yawa wurin siyan tsadadden man dake fitowa da ainihin kalarta, ta goge ta yi tas da ita, ta yadda ko mace sai kin yi sha'awar launinta shi yasa idan akwai tambayar da a rana ana mata ya kai sau biyar, ita ce wanne mai ki ke shafawa, wanne mai ki ke amfani da shi? wani lokacin ta fa'da, wani lokacin kuma ta yi murmushi wushiryarta ta sake 'kawata ta tace "Vaseline"

Tana tsaye jikin Shoe Rack (ma'adanar takalman)ta ta fito da wani Tom's blue, Innarta ta shigo ta kalle ta ta ce, "To 'dawisu sarkin ado a wannan daren kike wannan kwallliyar anya Iya baza ki rage wannan 'kyale-'kyalen ba? Shi yasa ai da yawa mazan suna son zuwa gunki amma gani suke kin fi 'karfin su"

"Inna tunda ba ni na fa'da ba ai shi kenan, idan mutum da gaske son nawa yake ya zo mana idan mun daidaita ai zan aure shi ne"

"Yanzun kuma mai za ki yi da takalmi, da na ga kina gogewa? Na san dabi'ar ki ce ca'ba kwalliya ba sai za ki fita ba, amma wannan takalmi ai na fita ne, kuma kin san ba inda za ki a wannan daren"

"Kai Inna don Allah!" Ta fa'da cike da shagwaba, "Ni fa ba fita zan yi ba, ba'ko zan yi"

"Kin fa'da wa Baffanku za ki yi Ba'ko?"

Kai tsaye ta ce, "Na fada masa kafin ya tafi sallar Isha"

"Shi kenan amma don Allah Iya ki daina bata wa mutum lokaci kina kuma karbe mishi abin hannunsa alhalin kin san ba auren sa za ki yi ba,
yaudara ba kyau. Alhaji Mamman din nan ni ban ga laifinsa ba, mutum mai mutunci mai nagarta ga shi babba ne ya mallaki hankalinsa amma kina tasa 'kafa kina shure shi, kuma kina kar'be mai dukiya"

"In sha Allah, Inna ko mai ya kusa zuwa 'karshe, ki 'kara 'kaimi wurin yi mini addua"

Dadi ya kama uwar tata kusan yau ne Sa'adah ta bude baki ta yi magana mai kyau akan aure.

Nan da nan ta hau fa'din,
"Addu'a kam ai kullum yin ta nake, mantawa na ke da ko mai sai ke idan ina addu'a, Allah ya miki zabin alheri"

Ta fita tana sake cewa, "Ba abin da ke raina irin in gan ki a 'dakinki kin nutsu wuri daya"

Har sai da ta yi sallar Isha sannan ya mata waya ya iso. Fararen kujerun da ta tanada saboda zuwan wanda tabawa izini, ta 'diba ta fita dasu zauren gidan nasu da ke da yalwar fili, tana zuwa shi ma yana 'karasa shigowa, da sauri ya karbe kujerun yana cewa "Ai da kin sani kin jira na zo na 'debo, wannan ba aikin uwargidanmu ba ne"

Dariya ta yi, "Za ka fara ko?"
Shi ma dariyar ya yi, "Zan fara fa'din gaskiya ba"

komawa ta yi ta ha'do mishi ruwa (pure water) da kuma kunun ayan da Inna ke yi akan faranti tare da Tumbler, ta ajiye mishi tare da cewa "Ga ruwa"

Ya yi godiya ita kuma ta hau gaishe shi tare da tambayar iyalinshi, ya ba ta amsa da cewa, "Ai ta yi fishi da ke tace rabon da ki taka mata tun barkan haihuwar Kausar,
ga Kausar tana gudu ko Ina."

Ta ce, "Hidimar makaranta ce ta 'boye ni amma yanzu kam na gama za ta gan ni, a ba ta ha'kuri"

Sai da ya bude ruwa ya sha sannan ya yi gyaran murya ya ce, "Zuwan fa na mussaman ne, tare da albishir din abin da muka dade muna nema ya samu, takanas MK ya same ni ya ce mini ya kira ki, amma kin kashe mishi waya haka ne?"

Kai tsaye ta ce "E ai ban san shi ba ne"

"Ban gane ba ki san shi ba ne"?

"To bai gabatar da kansa ba,
ya fara maganganun da ban fahimce su ba".

Shiru ya yi tare da cewa
"Amma ba ki da lambarsa ne?"

"Ban da ita"

"Ba ki da ita?" Ya tambaye ta cike da mamaki.

"E!" Kawai tace ta ja bakinta ta tsuke.

Kamar zai bar maganar sai kuma ya ce, "Amma aikin haddace a kanki"

Nan ma ta ce, "Na manta"

Ya yi dariya, "Sa'adah wai yaushe kika cire mu a ranki har haka ne?"

Murmushi ta yi ta ce, "A lokacin da na fahimci ba komai ne idan ka rasa yake dawo maka ba, ba kuma komai ne kake so yake zama alheri ba"

Da sauri Dr. 'Karfi ya ce, "To mu dai alheri ne kuma mun dawo mu sake daukar ki a karo na biyu."

"Amma bai kama ta, ya manta cewar aure ya 'kare a tsakanin mu ba?"

Ta fa'da cikin 'daure fuska.






Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼


🌺 *HALIN YAU*! 🌺



•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•


17-18.




" A a ban sani ba bai kuma fa'da mini ba."

'Karfi ya fa'da cikin yanayi na rashin gamsuwa, tare da zuba mata ido yana ta a uziya saboda yadda shaidan ke 'kawata mishi ita, ya riga ya binne wannan abin a ransa har abada ba zai yi tarayya da MK akan mace ba, macen da ya tabbatar amininshi yana mata son da bai yi wa kansa ba.

Ya numfasa ya 'kira sunanta,
"Sa'adah karki wahalar da ku, da ke da Mukhtar kuna son junanku, nan duniya ba abin da zai kankare wannan son, dole za a sami matsala a cikin zamantakewar aure, muhimmi shine ayi afuwa, a yafe, a kuma manta, amma ba za a iya kaucewa matsalar ba. ko wani sabon auren kipka yi komai jin da'din da za ki riska sai kin tarar da matsala"

Ya nisa sannan ya sake fa'din,
"Ina tabbatar miki kuma a yanzu ne ya fi dacewa ki koma dakinki, ba a wancan lokacin da ke kadai kike son komawar ba, yanzu da shi ya bukaci hakan da kansa za ki fi 'kima, ki fi daraja"

Sunkuyar da kai 'kasa ta yi hawaye na cika idonta, amma ba ta ce komai ba, ganin yadda jikinta ya yi sanyi, hakan ya 'kwarara guiwar 'Karfi.

Ya sake kur'bar ruwa ya ce, "Kar ki bari wannan damar ta kubuce miki, ina tabbatar miki, MK bai so wata mace kamar ki ba, kar ki bari rudin 'kawaye da zuciya su sake rudar ki a karo na biyu, wai ya yi aure, ko kaza da kaza, da duk abin da zai sake dagula miki lissafi.
Ki sa a ranki cewar ko kuna tare zai auri Farida! tunda an rubuta a cikin littafin 'kaddararshi cewar matarshi ce, mu gode Allah da ya kasance rabuwa ku ka yi, ba mutuwa kika yi ba, kin san akwai rabon da ke kashe mutum".

Hawayen da ta ke tattalawa ya zubo akan lallausar fuskarta, ta ce, "Ai ni sai daga baya na gano dama auren ya 'kallafa rai zai yi shi yasa ya yi ta zungurata, komai 'kankantar laifi sai ya juya shi ya zama garma, ashe dama akwai abin da ya 'kudure, to ya aureta hankalinshi ya kwanta, ni ma kuma ai bai jini a gadon asibitin mahaukata ba, bai kuma ji labarin auren nashi ya zama ajalina ba"

Kuka ya so kubuce mata saboda haka ta yi shiru sai rishin kukan kawai. Sai da ta nisa sannan ta sake dorawa da cewa, "Ni kuma nan duniya ban ga mai zai mini na ga farin shi ba"

Ta fada cikin dakewa da shanye kukan dake son kunyata ta. Jikin Mahmoud ya sake yin sanyi, ya yi shiru cikin rashin abin cewa.

Tsawon mintuna biyar kowa ya yi shiru a tsakaninsu sai fama suke da tunanin zuci.

Shudewar yan mintuna kafin ya ce, "Ni fa ba tone-tone za mu yi da ke ba, dukkanku, kowa da irin nashi laifin amma kin sani, laifin ki ya fi yawa"

Cikin takaici ta ce, "Baban Dadi tunda laifina yafi yawa, ai ya sake ni ya auro wacce ba za ta yi kuskure ba, wacce son da ake mata zai sa ayi ta mata uzirin ri'ke igiyar aurenta da kyau, sai dai a nuna mata kurenta cikin ladaftarwar da shari'a ta tanadar, shi yasa ni ma da na gane ba son nawa ake ba, kuma duk ni ce mai laifin sai na dau hukuncin da macen da ta san ciwon kanta za ta dauka don ta tsira daga ba'kin cikin namiji".

Shiru Mahmoud ya yi mata ya lura kishin Farida ne ya ke cinta shi yasa take ta furzar da magana, don haka ya 'kyale ta, at least dai za ta sami sau'kin ciwon dake addabar zuciyarta.

Sai da ta yi shiru don kanta, sannan yace"Ki yi ha'kuri, ki bi komai a sannu, ban hana ki nuna bacin ranki ba, amma kar ki wuce gona da iri, saboda kin san kema kin mishi laifin da sai da ya yi jinya bayan rabuwarku, tunda har ya sau'ko, to fa kar ki wuce makadi, ina fada miki wannan maganar ne a matsayin yayanki"

Ya dan numfasa, kana ya zarce da fadin, "Lamarin aure yanzu sai ha'kuri ba Perfect Marriage, kowanne aure da irin nashi 'kalubalen, duk abin da aka ce ibada ne, to fa sai an yi hakuri".

Ya mi'ke yana cewa, "Zan wuce, ki saurari zuwanmu!"

Hannu yasa a aljihunsa ya fito da yan dari biyar guda ashirin ya zuba kan kujerar daya tashi, da sauri ta ce, "Don Allah ka bar su, kullum a cikin hidima kake "

Murmushi ya yi yana cewa,
"Wannan kudin zance ne, ina fatan dai za a karbe mu da dukkannin raunin mu, kasancewar mu Malaman makaranta masu sadaukarwa, ba ma su satar kudin jama'a ba"

Ta san sarai inda maganar shi ta dosa, da Alhaji Mamman ya ke, tunda ya sha ganin ta da shi, wanda 'karara yake taya amininsa kishi.

Dariya ta yi tana kuma godiya amma ta ci alwashin bashi ya ci, dole sai an baje maganar nan ai ya san tun farko ta zabe su tabar Alhaji Mamman din da dukkan abin da yake da shi.

Tun a mota yake 'kiran lambar MK amma bai dauka ba, har ya gaji ya mayar da wayarshi caji a jikin motar. Mintuna kusan ashirin har ya shiga layin gidansa yaji 'karan wayar shi, ganin sunan MK yasa shi dauka da sauri, tare da cewa, "Wai ina ka shiga ne?"

Daga can ya amsa mishi da cewa, "Wallahi ina tare da Farida ne ba zan so ka yi mini maganar Sa'adah a gabanta ba"

Shiru Dr Mahmoud ya yi yana jin shi kam bai san wani namiji da ke gudun 'bata wa matarshi da gangan irin MK ba, ya tuna lokaci da dama da yake zaunar dashi yana caccakar shi akan tsoron Sa'adah ya ke yi, ashe ba tsoro ba ne tunda ga Farida ma hakan ya ke mata.

Mutum ne mai martaba abin da yake so, ko wadda yake son sa, ya sake tuna ko a abotarsu, MK ke ha'kuri da shi, shi ke masa hidima ba tare da tunanin ai yasan yawan albashinsu 'daya ba, samun irin Mukhtar Kabir Bichi zai yi wuya a wannan lokacin.

Amma duk da hakan sai da ya tsokane shi da cewa, "Dadi na da kai mijin ta ce ne kai, ni ban san me ya sa kake jin tsoron mata ba, ai na 'dauka Sa'adah ce kawai dodon taka, ashe wa lnnan alankosar ma murza ka take yi".

Shi ma cikin 'kosawa da shakiyancin da ba ya gajiya da mishi ya ce, "Kai ai ba za ka gane karatun ba ne ni kadai na san mai suke jiyar da ni, ka ga kuwa ai dole na yi tattalin farincikinsu, kar ni ma a hana ni nawa farin cikin"

Dariya sosai 'Karfi yake yi yana cewa, "Ashe haka karatun yake ganewa ne ban yi ba? amma da dukkan alamu karatun naka na daban ne"

"Idan kagama iya shegen naka, ina sauraranka don waje na fito, idan kuma ba ka gama ba, to zan koma, ma hadu gobe"

'Karfi ya gintse dariyarsa hadi da cewa, "Kai MK wallahi da alama 'yar darun taka, ta shiryawa daru kala-kala, amma dai na san kishi ke 'dawainiya da ita, ka san tunda ka yi auren nan bata bude baki ta ce 'kala ba, yana ta cin ranta, na ga soyayyarka mai yawa a idanuwanta duk da bakinta na 'kirarin rashin son"

Shiru MK ya yi har Mahmoud ya yi tsammanin ko wayar ce ta katse. Amma da ya ce,
"Kana ji na kuwa?"

MK ya amsa da cewa
"Ina jin ka. Mamakin ta ne ya ke ta kama ni".

"Ai ba mamaki a lamarin mace." A cewar 'Karfi.

"Ka shirya gobe muje mu same ta, kada Hajiya ta tambaya ta ji ba ka fara kafa tubalin kome ba ta yi fishi"
Ya 'karasa maganar cikin zolaya.

"Hmmm!" Kawai MK ya yi tare da cewa "Na gode sosai sai mun hadu gobe idan Allah yaso"

*

Sa'adah tana shiga a dakin mahaifiyarta ta ci burki, "Inna na dawo"

"Zo ki zauna magana zamu yi"

Ba ta musa ba ta shiga ta zauna daf da ita,"Waye ya zo?"

"Ba wani daban ba ne Baban Dadi ne"

Tabe baki ta yi tare da cewa "Waye hakan, kar ki ce mini Mahmoud abokin Muutar?
Cikin shagwaba ta rungumo uwar tata ta ce "Shi fa mene ne Inna?"

Ture ta ta yi tana cewa
"Ashe baki daina bibiyar yaron nan ba ko? 'dazu amsar da ki ka bani na komai ya kusan 'karewa akan maganar aure, ashe kina nan kina zawarcin Muutar ne? Wannan shi ne al'kawarin da ki ka mini?
Tunda kin zabi son ranki sama da nawa to ki je ki ta yi,
amma ki sani ba da yawuna ba, ba kuma da son raina ba, sai don kin fi 'karfina, don kin san zaki samu goyon bayan mahaifin ki ne"

Ta nisa sannan ta ci gaba da cewa, "Tunda na ga kina ta hanzarin shiryawa tare da 'doki na tabbatar ba kowa kike wa wannan rawan jikin ba sai shi"

"Inna ba fa yadda kike zaton lamarin ba ne wallahi ban karya al'kawarinmu ba, amma don Allah ki yi hakuri ki gafarce ni ba na son kina damun kan ki akan wannan maganar"

"Ai dole na damu tunda na gane ke da Baffanku, ba ku da burin da ya wuce ki koma gidan Muutar, ni kadai na san ba'kin ciki da wahalar da na sha kafin na samo ki a dalilinsa. kuma yanzu da komai ya wuce sai ya lallabo ya sake dama miki lissafi, saboda ya mai da ke marar zuciya, wacce ba ta san ciwon kanta ba"

Cike da tausasa murya Sa'adah ta ce, "In sha Allah Inna ba zan sake shiga halin da kike jin tsoro ba, ni ma nasan abin da kike guje mini, tuni na cire shi a raina."

"To idan dai haka ne ki ba wa Alh Mamman ko yaron nan Anwar dama wani cikinsu ya fito, ki yi aurenki idan ba haka ba, hankalina ba zai kwanta ba."
Ta fada tana goge hawaye da hannun zaninta.

Jikin Sa'adah ya yi sanyi ashe dai da gaske Inna take akan ba za ta

Please Login or Register in order to submit comment