You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yaran gidan ne da suka taso da ga lesson wadda takanas aka dauki malamin da zai zo har gida yana musu bita, yasa ta tashi musamman da 'karamar cikinsu ta fada kanta tana fadin, "Mami yaushe kika dawo?"

"Khairat kin san yadda na gaji!" Ta 'daga ta, tana cewa "Ina Yaya Jawad?"

"Ya na lafiya, ya ce duk yana gaishe ku"

Ta sake cewa, "Mami bai ba da komai ki bani ba?"

Daga Sumayya har Sa'adah dariya suka yi yadda Khairat din ta yi.

Jakarta ta bude ta dauko wani dan abu a nade da wrapping paper ta ce, "ga shi nan ni kaina sai da ya ro'ke ni kar na bude tunda ban san ma ya saba, ya dai ce mini zan ga abin Khairat don Allah kar na bude."

Yayansu Ayman wanda shi ma yana da yayu Abba da Khalifa suna Egypt suna karatu, ta nufa tana cewa, "Bude mini yaya!" Nan da nan ko ya hau warwarewa sai ga Lush Cookies Biscuit har guda biyar sai Teddy Bear 🧸 'yar 'karama mai kyau da yar 'karamar takarda an rubuta little Khairat.

Da murna soasai tace "Yaushe to zai dawo Mami?"

Anis ne ya ce, "Sai nan da 6 weeks."

Ta galla mishi harara, "Na tambaye ka ne?" Da yake sa'kuwar shi ce ba su cika jituwa ba. Ta juya ga yayansu,"Yaya Ayman kwana nawa ne a 6 weeks?"

Kai tsaye ya ce mata, "42 days." Da sauri ta ce, "Gobe zan samo stones 42, kullum na dinga minus, ranar da suka 'kare to ranar zai dawo saboda na soya mishi wainar fulawa."
Dukkan su dariya ta ba su, amma Sa'adah mamakin wayonta take, tana kallon Anis tana tuna daidai lokacin haihuwar sa ta shiga matsaloli masu yawa da Malam.

Shekarunta biyar a duniya amma wayonta da azancinta ya zarce na 'yan shekaru bakwai.
mutumiyar Jawad ce sosai ta fi shiri da shi fiye da yayyenta.

Shi ma kuma haka yake ji da ita musamman da shi ba shi da 'kani ko 'kanwa sai ya tattara dukkan 'kaunar da yaya yake yi wa 'kanwarshi a kanta.


*Bayan kwanaki uku*

" Iya Iya dai, na san tabbas daga shigarki ba za ki ce mini wai har kin yi barci mai nauyin da za ki kasa jin kuwwar da wayar ke faman yi ba."

Da kanta ta tashi ta leka, ganinta ta yi tana kwance ta 'kudundune ta rufe fuskarta da dukkan hannayenta,
"Kin san Allah? Idan kika bari na shigo ba ki tashi ba sai na ci mutuncinki, ai na san sarai kina ji na"

Tashin ta yi tana murtsika idanuwanta "Ni fa Inna barci nake yi!" Kafin Innar ta yi magana wayar ta sake daukan ruri a karo na uku dan haka ta kafeta da idanuwa, akan dole Sa'adah ta sa hannu ta amsa wayar.

Sannan Inna ta juya ta fita tana fadin, "Shashasha haka ki ke tunanin za mu bar ki ki yi ta zama? Ai tunda kin gama karatun to kuwa wallahi sai dai ki fito da miji cikin jerin wadanda suke son ki dan ba zan yarda da wannan zaman ba. Haka kawai kowa ya zo ki ce bai yi miki ba, kowa bai miki ba, wanda ya yi mikin kuma bai shirya sake zama dake ba. Amma kin kasa gane gaskiya, kin kasa gane ita mace lokacin ta 'kan'kani ne! Bari Baffan naku ya dawo na gaji da halinki!"

Sa'adah kuwa da alatilas ta dauki wayar Alh. Mamman wanda dan majalisar tarayya ne mai ci a yanzu, ya so ta tun tana budurwa, a lokacin yana dan majalisar dokoki na jaha, shi ne har yau yake ta bibiya, tun lokacin budurcinta ta san komai game da shi.

Mutum ne mai yawan kyauta da kyautatawa, ta tabbatar da hakan, ita kanta ta san ya mata 'barin kudi. Tun a lokacin yana da mata biyu da yara takwas wanda wannan dalilin yana cikin dalilin da ya sa ba tayi marmarin ma auren shi ba, Illa dan ta sami rabonta kawai, to yanzu kuma amaryar ce ta rasu shekaru biyu da suka wuce a wurin haihuwa, shi ne yake ta bin kanta ta maye mishi gurbinta, tunda ya riga ya saba da mace biyu ga kuma tsananin 'kaunarta da yake.

A nata bangaren kuwa ba ta fatan 'kaddara ta 'kaddaro ya zamo miji a gareta shi yasa tun watanni shida da suka shude ta yakice shi a dukkan lamarinta, tunda dai kam ai ta riga da samun rabonta🤔.

Ta yi amfani da alfarmar shi ta cimma burinta, da kuma mallakar kayan 'kawa na alfarma, idan ko hakane dole ta yi gaggawan wullar da shi tun kafin reshe ya juye da mujiya.

Uzirin tana aiki ta ba shi akan za ta 'kira shi anjima, murmushi ya yi ya ce, "Ranar da na ga 'kiran ki a wayata Sa'adah tabbas rana ce mai muhimmanci a raina!"

Ya'ke ta yi tare da fadin, "Aiko idan hakane zan baka mamaki, ka saurare ni zuwa anjima"..

Ba ta jira cewar shi ba ta daste kiran, ta yi wulli da wayar ta na neman tsari da 'kaddarar da za ta hada su zaman aure da wannan mai tulelen ciki.

Kanta ta ji ya cushe musamman yadda Inna ta fara matsa mata a cikin kwanakin nan akan lalle sai ta tsayar da miji cikin manemanta, har zuwa yanzu ba ta jin akwai wani da za ta yi zaman aure da shi kamar Mukhtar Kabir Bichi.

Amma ko shi da ta tabbatar da abu 'daya, ta ha'kura da shi ba dan ba ta so ba sai dan ha'kurin shi yafi.

Ta kuma gamsu ita ke da laifi da kaso mai yawa na 'kaddarar rabuwar su da Abban Jawad, ta tabbatar ya so ta, son da ba algus amma *HALIN YAU* da rudin 'kawaye ya jefa ta cikin kogin nadama.
Irin wanda ake cewa tsalle daya mai jefa mutum rijiya, ya yi dubu bai fito ba! A hankali ta koma ta kwanta tana tariyo rayuwar ta, ta baya, tun kafin haduwarta da Mk Bichi. haduwarsu, aurensu, rabuwarsu, har zuwa yau da take jin duniyar ta yi mata daurin goro.

Ashe 'dan Adam baya rabuwa da matsala? Ashe duk matsalar da mace za ta fuskanta indai tana zaune a dakin aurenta matsalar da sauki, akan matsalar rashin auren, da rabuwa da 'ya'yanta? Wanne tabbas mace keda shi a wannan halin na yau, za ta sake samun damar aure a karo na biyu? Idan ta samu din ma ba za ta kauce wa matsalar *HALIN YAU* ba, ko kuma ta tabbata tana aure-aure.

Ta nisa ta tuna wata maganar gyara kayanka, da fasihiyar marubuciya, Fadila lamido inda take fadin, *"Uwa da sadaukarwa aka san ta, domin rayuwarta da ta 'ya'yanta, ta inganta.*'

To shin ita me ta yi ne dan ganin ta SADAUKAR da komi dan inganta kanta da tilo 'danta? Tabbas ba ta yi ko mai ba, sai rusa farincikin kanta dana 'danta Jawad! Ta yi dalilin da yake rayuwa ba a tsakanin uwa da uba ba, hawaye ya gangaro mata na takaici da kaico iri iri.

Ta tuna wani darensu a Abuja, ya dinga rarrashinta akan ta kwantar da hankalinta su zauna lafiya, komai take so zai dinga yi mata a hankali, a lokacin ita kuma tana ganin tamkar idan ba ita, ba zai iya rayuwa ba, saboda yadda yake tsananin sonta da kulafacin son zama da ita, duk yadda take ganin aibun su Halima, a yanzu da take fuskantar NADAMAR biyewa Halayyar yau, ta fi ganin aibun kanta da kanta, tabbas zuciyarta da tunanin ta basu mata adalci ba, domin tunda ta taso take jin ana azanci da cewa idan mafa'din magana wawane majiyinta ba zai zama wawa ba, amma ita sai ta zama mahaukaciya ma.

Zuciyarta ta sake ba'ki wani irin numfarfashi take yi tamkar mai fama da cutar Asma, hakanan hawayen ba'kin ciki ya kwace mata tamkar mai yin Takaba.




```Alkalamin
SURAYYA DAHIRU ```✍🏼✍🏼


🌺 *HALIN YAU*! 🌺





https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/


*SADAUKARWA GA*
*SADIQ ABUBAKAR*.




7-8





HAWAYEN nadama marar amfani ya ci gaba da zuba da ga kyawawan idanuwanta ba 'ka'kkautawa, a hankali ta koma ta kwanta, zuciya na suya, rabon da ta shiga irin wannan yanayin tun shekarun baya da suka shude.

Shekarun da suka fi kowanne tsauri da tsanani a rayuwarta, a lokacin da ta dinga yun'kurin gyara kuskurenta amma MK bai ba ta wannan damar ba.

Duk da ta san ita ke da kaso mai yawa na lalacewar aurensu, tunda ba irin 'kabali da ba'adin da bai mata ba, ba kalar rarrashin da bai yi mata ba. amma tasa hannu har da 'kafafu ta tankwabar da dukkan ha'kurinsa, ta tabbatar akan dole ya rabu da ita, ita kanta ta shaida hakan.

Tissue tasa ta goge hawayen da ya 'ki yankewa, take kuma zuciyarta ta yi tsalle ta hasko mata irin kyaun da ya yi cikin tufafin da take matu'kar son ganin sa a ciki wato farin kaya, sam ba ya girma, ba wanda zai kalle shi yace ya kai shekaru arba'in har da biyu.

Dan kuwa idan ya ce bai yi auren fari ba, ba wanda zai 'karyata shi, Ubangiji ya mishi kyakkawan jiki matu'ka gaya.

Murmushi mai hade da hawaye take yi lokaci guda, saboda yadda ta ji a ranta da zuciyarta domin ita ya yi shigar tare da fatan ko Allah zai sa su hadu, a hankali ta fara jin sau'kin 'kullewar da 'kirjinta ya yi yana raguwa, a dalilin tabbacin da ta sake samu na har yau shi ma yana son ta, dama idan akwai abin data yarda dashi to son da ya ke mata ne. Amma kuma me yasa bai yarda da ita ba?

Nan da nan 'kuncin 'kirjinta da ya fara warwarewa ya dawo ya 'kulle fiye da farko idan akwai abin da yake 'daga mata hankali bai wuce rashin amincin daya jefe ta da shi ba, alhalin shine mutum na farko daya kamata ya shede ta,
ta kuma zama amintacciya a idonsa, kuka ya 'kwace mata sosai, da sauri tasa hannu ta rufe bakinta dan kar Inna ta jiyo.

Haka ta danna kanta a pillow ta yi kuka mai nuna tsantsar bakin ciki da takaicin da mai yinsa ke ciki, duk yadda zuciyarta ta yi zafi, kanta take 'kalubalanta, ta san ko mai Malam ya yi ko ya ce mata, ba shakka ita ce sila, ita ta janyo.

Istigifari ta dinga ambato dan ta sami sau'kin zuciyarta, tsawon lokaci kafin ta ji ta fara samun nutsuwa sai ajiyar zuciya take saukewa.

Wayarta ta dauko tana nazarin shin a littafi zata rubuta ne ko a waya? A littafin tafi gamusuwa da ta rubuta tarihin rayuwarta dan ya zama izna ga sauran mata. Idan ta sami halin buga shi, za ta buga dan ya zama gargadi ga duk wacce son zuciya da *HALIN YAU* ke dawainiya da ita.

Mi'kewa ta yi tana laluben littafi da biro a cikin jakar karatunta, amma cikin rashin sa'a ba ta samu ba, kowanne ta yi rubutu mai yawa a ciki.

Tsaki ta ja, ta rike 'kugu kafin ta yi wani yun'kurin abin yi, ta ji sallamar almajirinsu yana fadin na dawo.

Da sauri ta iso ga katifarta, ta 'daga pillow ta dauki gudar dari biyar ta fita ta ba shi, ya siyo mata littafi na rubutu mai shafi tamanin (80 leaves).

Daga nan ba ta dawo dakin ba, buta ta dauka dan tayi alwalar la'asar tunda yan mintina ka'dan ne su ka rage.

*****

Kwance ya ke kan sofa a dakin barcinsa, ya lumshe ido tamkar mai barci amma a zahiri ba barcin yake yi ba.

Tun ranar da ya ga Sa'adah nutsuwa ta masa tutsu duk yadda ya kai ga daurewa har abin ya bayyana a fuskarsa da gangar jikinsa gaba'daya.

Wata irin nutsuwa ya gani a tare da ita, wadda bai taba gani a tare da ita ba, gaba'daya ta canja, ilimi da hankali sun matu'kar ratsa ta. ba kamar lokacin da suka rayu tare ba. ko dan ya dauki lokaci mai yawa bai ganta ba ne?

Farida ce ta shiga dakin, kusa da 'kafafuwansa ta zauna tana mai jan yatsun 'kafarshi, a hankali cikin sanyin murya da halittarta ce, ta 'kira shi "Abban Jawad!"

Bai amsa ba, amma ya bude idanuwanshi da suka yi ja alamun ko barci bai ishe su ba ko kuma ana cikin damuwa.

Ta sake nazartar shi a hankali ta ce, "Tunda ka dawo na kasa gane maka, na san akwai abin da ke damun ka amma ka'ki fada mini, ni kuma na san matsalar! Idan na yi rantsuwa cewar Sa'adah ke da ala'ka da wannan damuwar da kake ciki ba zan yi kaffara ba, mai yasa ba za ka yafe mata ba, mai yasa ba zaka daina wahalar da zukatanku ba, me yasa kake gudun gaskiya da gangan? Ni dai na san ', kullaci, da rashin yafiya ba halayyarka ba ce!

Ban san me yasa ka aro ka yafa akan Sa'adah ba! yau shekaru kusan bakwai kana ta wahalar da zukatanku, sai yaushe za ka hutar da ku? ko makaho ya ji halin da kake ciki yasan kana sonta, balle ni da nake tare da kai, na ro'ke ka ka gaggauta gyara tsakaninku, tun kawaicina bai 'kare ba, tun ban fara kishi da ita kamar yadda take yi dani ba, na tabbatar idan hakan ta faru ba zaka samu nutsuwa ba!"

Sai a lokacin ya bu'de baki murya ba amo ya ce, "Kece kike ganin haka duk yadda kike tunanin lamarin ba haka ba ne, kinsan kuma ban taba 'karyar ba zan dawo da ita ba, saboda Ubangiji ne ke jujjuya lamura, idan ya 'kaddara sake zama a tsakaninmu zan dawo da ita."

"Zuwa yaushe za ka dawo da ita din? Ka fi shekaru uku kana wannan maganar, ba irin girman kanta da ba ta ajiye ta baka ha'kuri ba, ni kaina na sha ganin ta tsugunne a gabanka. haba Abban Jawad! Wanne irin abu ne haka da ba zai wuce ba?"
Ta fada muryar ta na karyewa.

Shi kansa bai san mai yasa ya shiga ru'du a dalilin halin ko in kular da Sa'adah ta mishi ba, da kuma yadda ta daki 'dansa a gabansa, alhalin kuma tun tuni ta san baya son ta masa haka a gabansa. Amma saboda da ta nuna masa ba shi da sauran gurbi a zuciyarta, ba shi da mutunci a idonta ta rufe Jawad da duka akan idonsa.

Sannan a gaban jama'a ya tsaya dan ya taimake su amma ta wula'kanta shi, ta nuna masa iyakarsa, idan ya tuna wadannan abubuwan sai ya ji har zazzabi ne ke neman kama shi, hakan na nufin Sa'adah ta daina son sa, ta ha'kura da shi ke nan? Zuciyarsa na bugawa idan ta hasaso masa cewar ta samu wanda take so, ko kuma za ta sabunta soyayyarta da Khalil Ibrahim wanda yake jin komai na iya faruwa da shi idan hakan ta faru.

Ya nisa ya ce, "Ke fa duk yadda kike tunanin lamarin Sa'adah ya kerewa tunaninki, yanzu bata so na, ba ta da burin sake zama da ni"

A yadda ya yi maganar ta san akwai abin da ya gani a tare da ita da ya jefa shi cikin wannan yanayin.

Wata'kila ta gaji da bin kansa, ta tattara ta jefa shi a kwandon shara, kamar yadda ya mata, shine kuma dan son kai irin na namiji zai ji an masa rashin kyautatawa, su dai sun fi son mace ta yi ta bin su, suna jan ta a 'kasa.

"A hankali cikin son 'karfafa masa guiwa ta ce, "To ina ruwanka da soyayyarta? Ina tabbatar maka son da kake mata ya isa ya ri'ke auranku, muhimmin da za ka damu da shi mutuncinka a idonta, balle ma nasan nan duniya ba namijin da take so sama da kai, ba kuma wanda zai zarce ka a gunta. Wata'kila ta gaji da yadda kake tamaula da ita ne, ko ba ta ci albarkacin so ba, taci albarkacin Jawad! ko ka san Jawad, komai zan yi masa ba zai gamsu ba, matu'kar ba uwarshi ya gani a tare da kai ba"

Idonta ya dan ciko, ta dan tsahirta sannan ta ci gaba da magana, "nan gaba Jawad zai tattara dukkan tsana ya dora mini, zai ga saboda ni ka 'ki zama da uwarsa, kai ma kasan tunda muka dawo 'kasar nan ya canja, na ro'keka dear kar ka ruguza farinciki da kwanciyar hankalinka da na 'danka"

Janyo ta jikinsa sosai ya yi, ya ri'ke hannunta ya kalleta sosai ya ce ,"Farida ke din mai kirki ce, mai ha'kuri ce, mai sanin ya kamata ce, kina sona kina son kwanciyar hankalina, ina yaba miki, ina kuma fatan Allah ya fi ni yabawa, Allah ya ba mu zuria dayyiba!"

Hawayen da take ma'kalewa ya zubo a kan fuskarta ta ce, "Ni da ban da lafiya ne zan haihu?"

Cikin kulawa mai yawa ya ce, "To menene ya gagari Ubangiji? Son da nake miki wallahi ko ban taba haihuwa ba, zan zauna dake a haka domin ke nake so ba wani abin da zan samu a gareki ba, sannan rashin haihuwarki kullum ke sa na ji son ki da tausayinki na sake cika mini dukkan zuciyata, ina son ki da ke da dukkan lalurarki Farida!"

Sai kawai ta fada jikinsa tasa mishi kuka, shi kuma yana dan bubbuga bayanta, yana jin ina ma zai iya bude mata 'kirjinsa dan taga 'kololuwar matsayinta a zuciyarsa?.

Ya tabbatar bata san yadda yake jin ta a Zuciyarsa ba ne.


```Alkalamin
SURAYYA DAHIRU```✍🏼✍🏼


[5/14, 11:03] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```

```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________

https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•


_GAISUWAR GIRMA GA_
*HAJ HAFSAT SODANGI*
_(MIJIN TACE)_


9-10.


Tsawon lokaci suna wannan halin har ya samu nasarar dawo mata da walwalarta,
"To kawo mini abincin nan mu ci don nasan ke ma ba ki ci ba".

Ta yun'kura tana cewa, "Ina zan iya ci alhalin mijina bai ci ba!" Kicin ta nufa ta hada komi a kan faranti ta kinkima ta yi dakin nashi kamar yadda ya ba ta umarni, Sai da ta shimfida ledar cin abinci sannan ta zuba musu abincin a faffadan plate, shinkafa da miyar kifi ne, sai hadin Salad, gefe kuma zobo ne wanda ta sarrafa da tsurar sugar da cocomber sai flavour.
Ba ka jin komai sai karo tsakanin cokali da plate kasancewar shi ba ya magana idan yana cin abinci.

Suna gamawa ta kwashe komai ta gyara wajen sannan ta hada masa ruwan wanka ya shiga. Ta fice zuwa nata dakin, ta fito falo sukayi kicibus da shi, ya fito cikin lallausan yadi mai kalar sararin samaniya,(Skye blue) bai dora hula ba, amma ya taje sumar nan da ta cika kan fam! Ya dora farin glass a idanuwanshi, sai tsadden kamshin turaren Versace ne ke tashi a jikinsa.

Kugu ta rike ta zuba mishi ido tana murmushi ta ce, "Na san mijina gwanin iya wanka ne, amma irin wannan kwalliya haka da La'asariyar nan! Sai ina? ko wurin Iya Basiru za a?"

Ya fashe da dariyar tuna baya, sai ya ce, "Kinsan fa har yau fadanta na nan lalle idan ta ji wannan sunan kin san 'yan kallo zaku kwasa."

Ita ma cikin dariya sosai ta ce, "Ai na san yanzu ta girma da fada, ka san me?"

Ya girgiza kanshi, "Ada idan mun hadu sai na faki idon mutane naga ba kowa, sai na ce mata Sa'ade ko na ce Iya Basiru, sai na ga ta fara sababi, kawai sai na sulale na bar ta a wajen."

Ya sake sakin dariya "Ashe ke ce kike tsokanar ta duk mu hadu a ba ta rashin gaskiya?"

"E to ai haushi nake a lokacin, ta dauke maka hankali, har sai da ta kwace mini kai!"

Ya nuna ta da yatsa, "ke ko! kin san irin su Sa'adah suna dadewa kafin a gane cutar su da ake yi, saboda hayaniyarsu sai sun dade kafin a gane a fahimci gaskiyarsu. yau kwana biyu ban je gidan Hajiya ba can na nufa idan kuma za ki dauko mayafinki, Bismillah".

Kai ta girgiza alamar a'a tare da cewa, "Na fi son na je na wuni, ka gaishe ta da kyau!"
Ya fice ita kuma ta bi shi da addu'ar dawowa lafiya.

Da sallama ya shiga gidan, a tsakar gidan ya same ta zaune kan tabarma tana jin radio, kusa da ita ya zauna. suka gaisa tana tambayar Farida, daga nan kuma tayi shiru da bakinta.

"Hajiya wai har yau fishin rashin zuwanki wurin Jawad din ne? Ni ma fa ban ji da wuri ba, ina Bauchi ya yi mini waya daga can na zarce amma ki yi mini uziri, kiyi hakuri."

"Ni abin da ya dame ni, ba a kai masa abinci da 'yar miya ba!"

Dariya ya yi sannan ya ce, "Ai yanzu ba a barin su su tafi da shi hostel, iya wanda suka ci a wajen shike nan, saboda kwalara sannan kuma a can na tarar da uwarshi ta je masa da abincin".

Shiru Hajiyar ta yi tana jin takaici rashin Sa'adah cikin ahalinta, ba karamar asara ba ce. Tunda ita kam a iya zamanta da yarinyar ba za ta ce ga ta'kamaiman laifinta ba, sai yan 'kananun kura-kurai da ko 'danka na cikinka wani lokacin zai yi maka.

Duk artabun da ake yi tsakanin uwar miji da surukan zamani ita ba ta san shi a zamanin zaman Sa'adah ba, yarinyar ta iya zama da manya.

Komin fa'da da rashin ha'kurinta, ita dai ba ta ganin su, tunda dai mafi yawa akan kishi take fadan. duk mace kuwa ba a raba ta da kishi, sai dai wata ta iya dannewa wata kuma nata mai zafi ne.

Sannan abu mafi dadi a halayen Sa'adah yadda ta yarda ta isa da ita, duk yadda ta murde, da zarar tasa baki za ta ha'kura ta bar maganar. Amma ga shi nan, shi da ta haifa ta kasa sarrafa shi, akan komen yarinyar, shi yasa take jin kunyarta, take jin nauyin iyayenta, duk da aure rai ne da shi, Ubangiji idan ya 'karar da zama ba yadda za ayi.

Ta kalle shi, "Kuma kun gaisa da ita?"

Tausayin uwarsa ya tsirga mishi ya san babban burinta Sa'adah ta sake zama surukarta a karo na biyu, ya yi 'dan murmushi "Hajiya ai da ma muna gaisawa"

Harara ta galla mishi tare da cewa, "Ina ce nan da ta zo duba Jawad akan idona ba ku gaisa ba?"

"An yi haka Hajiya amma ai ba ni zan gaishe ta ba ko?"

"Kai ne namiji, Kai ne zaka fara magana tunda gidanku ta zo, kuma uwar dan ka ce!"

"To ni Hajiya ba uban 'dan nata ba ne?"

Kwafa ta yi, "Wallahi ba ka ta ba bata mini rai na ji zafinka sosai ba sai akan Sa'adatu."

Kai tsaye ya ce, "Na ba ki ha'kuri Hajiya! yanzu ma shi zan ba ki, ki yi ha'kuri ki yi mana adddu'a."

"To tun yaushe nake adduar?" Niyya ce dai da ba ka yi ba!"

Ya katse mata fadan nata ta hanyar cewa, "Da kyar fa Jawad ya sa ta gaishe ni, kuma na taho a hanya na ga motarsu ta lalace, wai ni da abin arziki, na tsaya na ce su zo mu taho amma yarinyar nan a gaban jama'a ta tsinka ni! Ko kallon tsiya ba ta mini ba, bare na arziki."

Ya nisa sannan ya ci gaba da fadin, "Amma kullum sai ki yi ta dora mini laifi, ki yi ta ganin ni ne marar kirki, alhalin tsiyarta tafi ta tsohuwar mota. Inda tana son sake zama da ni ai lallaba ni za ta ci gaba da yi, tunda dai ta san ba na son rashin kunya."

Tunda ya fara magana ta zuba masa ido tana nazarta shi, tsawon shekaru bakwai da rabuwarsu, yau ne ya bude baki yake magana mai tsayi a kanta. Ta kuma lura da sassauci da afuwa mai yawa akan lamuranta a yau, ta tuno farkon rabuwarsu da ta nuna iko irin na uwa, akan sai ya mayar da ita tilas, yasa mata kuka riris lamarin da yasa ta janye

Please Login or Register in order to submit comment