You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ko ya faɗa muku wani abun?" Father
ya yi dariyar baƙin ciki ya ce "Wannan ne zai magana? Ko ya yi bata da wani amfani
me zamu fahimta banda, A...Aaaa...ƙikkkk... Yeee gaba ɗaya Aliyu bashi da amfani a
rayuwarmu, naji baƙin cikin samunsa Matsayin ɗa namiji" wani baƙin ciki ya tukare
zuciyar Mother idanunta na cika da hawaye ta ce "Sai yanzu na fahimta larurar Aliyu
ta sanya kake ƙinsa? Ubangiji ya ɗora masa shi nake roƙa kuma ya ye masa" Abba
Hakimi ya numfasa kalam Father sun bashi mmki a haka ya share ya ce "kayi babban
kuskure Aliyu, kuma Sheikh abin Alfaharin duk wani ɗan Kano dama Najeriya ne,
muhimmancin bai tsaya iya ƙasar shi ba, har ƙasa mai tsarki.. Allah ya kyauta wata
rana zaka gane gaskiya lokacin da za kaji kunya" juyawa kan Mother yai ya ce "Akwai
abin da ya faɗa miki ne, ina son shigar da maganar zuwa court ne" Mother ta ce
"Yana cikin ƙoƙarin fahimtar dani suka taho wajanka ya faɗa mini bashi ya aikata
ba, kuma ni ma na shigar da ƙara ni zan tsaya masa tare da Barrister Zainab" wayar
Mother ce ta fara ringing ganin sunan Umar-khan ya sanya ta ɗauka cikin sauri ta
miƙe tana faɗin "Ohhh ok on our way" kashe wayar tayi idanunta akan Abba Hakimi ta
ce "Umar-khan ya ce muzo yanzu al'amarin ya shige tunani" da sauri ta nufi ɗaki
tare da ɗakko mayafi da key car.
Abba Hakimi da Mother suka nufi state c.i.d hankali a tashe Maimoon da Zeefa da
Fattoumah sai kuka suke a rayuwa suna ƙaunar yayan nasu duk da babu wata jituwa a
tsakaninsu. Ko abinci suka kasa ci sai sallah kawai da suke suna addu'ar Allah ya
kuɓutar da Sheikh ɗin. Hankali kwance Father yake zaune yana waya da babban
amininsa ko da wasa bai masa magana akan matsalar da suke ciki ba, duk da cewa
al'amarin ya gama zaga ko'ina a faɗin Nigeria.
A kiɗime Mother take bin su Saif-Wazir da kallo ganin yadda idanunshi ya yi jajur
alamar kuka suka sha. "Ina Babana ina Aliyu mai ya faru da shi?" Shiru Saif-Wazir
ya yi mata, ta juya kan Umar-khan ta riƙe wuyansa sosai cikin faɗa ta ce "Where's
my son Umar-khan? Ina Aliyuna?" Umar-khan ya yi ƙasa da idanun shi ba tare da ya ce
komai ba. Sakin Umar-khan tayi ta nufi wajan Ishaq-hakim ta ce "Ishaq-hakim faɗa
mini gsky ina Aliyu me akace yana da gsky ko? Ba aikata abin da ake zarginsa ba?"
Hannunsa ya ɗaga tare da nuna mata wani waje da sauri ta juya Idanunta ya sauka
akan Sheikh Aliyu Haydar Aliyu wanda aka cire masa Jallabiyar jikinsa aka ɗauresa
da Sarƙa tun daga wuyansa hannunsa zuwa ƙafarsa farar fatar jikinsa tayi jajir
bakin Ishaq-hakim na rawa ya ce "Mother Sheikh ya amsa laifin da ake zarginsa ya
tabbatar shi ne ya lalata ƴan matan hadda ciki.....


_*IDAN BA KE...* labari ne da kuka daɗe ba kuci karo da irinsa ba, ƙaddarar labarin
akan soyayya ne mai tsayawa a zuciya da saka shauƙi a zuƙatan masu karatu.....
Tsammaci abin da baka tsammani salo na musamman🫣💋 08119237616._
[1/3, 4:48 PM] Abk: *🌈 IDAN BA KE 🌈*

_*Zaku samu cikakken labarin a Arewabooks, kuyi searching sunan littafin ko
username Arewabooks@Nimcyluv*_

8....
Ihu da kururuwa Prince ya din ga yi, sbd tsananin azabar da Abba ya ganawa masa.
Cikin wata kakkausar murya wacce take nuna cewa ko a cikin Aljanu shi ɗin nada
banne, kuma taƙadiri ne. "Akan aurena dake kan Halisa banƙi na kashe kowa na illata
shi ba, daga ci hadda kai Abba, ba ruwana da kasancewar ka mahaifina, kada ka
rabani da Danejona zakai babban kuskure zanyi ɓarna a duniya" Bakin Abba na fitar
da hayaƙi kamar zai kunna wuta a ciki ya ɗaga hannunsa sama gaba ɗaya ya naɗe
Prince cikin wata sarƙa da yana bakinsa ɗauke da addu'ar neman samun nasara akan
Prince ɗin.
Duk ihun da yake bai hana Abba ya sarƙafesa cikin yanar ba idanunshi ya yi wata
kala. Cikin ɗaga murya mai amo! Ya ce "Na raba aurenka da Halisa, babu kai ba ita,
kuma a yanzu zan cire cikin dake jikinta mara imani mai muguwar zuciya" yana faɗin
haka ya yi girgiza tare da ɓatar da Prince ɗin baki ɗaya daga wajan. A hankali Abba
wanda Asalin sunansa ya kasance MURWAS ya sauke numfashi, tare da juyawa ya kalli
Halisa dake kwance a ƙasa tana barci, juyawa ya sakeyi ya kalli Safwan dake kwance
shi ma. Cikin nutsuwa wacce ba zata addabi dabbobin dajin ba ya yi Girgiza tare da
rikiɗewa ya koma suffar mutane sak. Hannuna ya ya ɗauki Halisa Dajeno Rome da sauri
ya nufi cikin Rugar Rome zuciyarsa fal farin ciki ganin yau ya raba ɗansa Bilal da
Bil-adam.
Babu kowa cikin rugar kamar an share hakan yasa ya fara bin bukkokin Rugar da kallo
kamar daga sama Hamma Yabi ya fito daga cikin ruga zufa na yanko masa hannunsa riƙe
da ƙwarya maganin gaba ɗaya tunaninsa ya yafi wani wajan bai lura da mutumin dake
tsaye yana binsa da kallo ba. "Jamɓanduna" Abba ya faɗa yana kallon Hamma Yabi dake
ƙoƙarin yin gaba, tsayawa ya yi yana duba mutumin da ya ce masa Ina kwana, cike da
mamaki ya ce "Jamni tawon" ma'ana lafiya. Abba ya jinjina kai ba tare da ya ce
komai ba, jikin Hamma Yabi na rawa ya amshi Danejo daga hannun Abba kafin ya ce
"Ikon Allah, ina kasa meta? Tsayin mako guda ta ɓace mana ba ita ba labarinta, shai
Allahamdulillah" Murmushi mai sanyi Abba ya yi cikin nutsuwa ya ce "Ayyah ni ma
yanzu ina iyu a cikin ruwan na ganta kwance gefen ruwan" cikin nuna jin daɗi da
manta halin da Dada ke ciki wanda duk rashin Danejo ya haifar da haka ya ce
"Shannu, wallahi shannunka kaji" kai kawai Abba ya ɗaga yana ƙarewa yanayin rugar
kallo kafin ya juya bayan sun yi Sallama da Hamma Yabi yabar wajan. Yana fita ya
ɓace a wajan baki ɗaya.

Dada na kwance bakinta na fitar da wani ruwa kamar dafara Shatu na gefe tana kuka
tamkar ranta zai fita. A cikin wannan halin Hamma Yabi ya shigo cikin bukkar
hannunsa ɗauke da Danejo wacce har yanzu take bacci. Jikin Shatu na rawa ta miƙe
fuskarta cike da hawayen halin da mahaifiyarsu ke ciki, amma hakan bai hana
Fuskarta baiyyanar da farin cikin da zuciyarta ke ciki ba na ganin Yayarta Danejo.
Bakinta na rawa ta ce "Hamma ina ka samu Danejo, da gaske ita ce yanzu Dada zata
tashi naji daɗi sosai" bai ce komai ba ya kwantar da Danejo gefen Dada idanunsa
akanta ya ce "Maza kawo mini ruwa" Shatu ta miƙe da sauri tare da nufar tulo ta
tsiyayi ruwan mai ɗan sanyi, tana bashi ya shiga shafawa Danejo yana kiran sunanta.
A hankali ta sauke ajjiyar zuciya tana buɗe ido a nutse. "Danejo"... "Halisa" Shatu
da Hamma suka kira sunanta lokaci guda,a sanyaye cikin sanyin jikinta kamar kullum
ta shiga binsu da idanu. "Kin farka?" Kalmar Hamma ta sanya ta lumshe idanunta kana
ta buɗe a hankali tana sake binsa da kallo kafin ta yunƙura zuwa zaune "Naga kuna
ta kallona kamar za a cini ɗaya?" Murmushi Hamma ya yi ya ce "Munji daɗin ganinki
Danejo, mako guda kenan mun rasaki kin ɓace daga idanunmu" da Mmki take kallonsa
ɓata? Mako guda? Taje ina? Ita gani tayi kamar barci take mai ɗauke da mafarkai
kala-kala. Shiru tayi tana ƙara sauke numfashi tare da fara tunanin maganar Hamma
Yabi. "Hankalinmu ya tashi, Kullum Dada cikin kiran sunanki take, gashi yanzu ko
buɗe ido ba tayi jikinta ya tashi ina tsoro kada mu rasa Dada kamar yadda muka rasa
Baffa" ambaton sunan Dada ya saka Danejo saurin juyawa zuwa gefenta manyan idanunta
ta buɗe "Dadata" ta furta a ruɗe ganin yadda Dada ta ƙanƙame jiki, idanunta na
kafewa kamar mai shirin mutuwa cikin muryar kuka ta ce "Na lalashe ni Danejo Dadata
kada ki barni kada ki mutu do Allah,Kada kibi Baffana" sai girgizata take amma ina
Dada ko motsi ba tayi.
Da sauri Hamma ya fita zuwa bakin hanya tare da samu abin hawa yana zuwa suka ɗauki
Dada a mota zuwa asibiti, asibitin babu jama'a sosai. Dr Hamza na zaune a Office
gabansa cike da kuɗi ya kalli Dr Iliya ya ce "Kawo maganin nan ya yi mana rawa
sosai, na ƙara tura saƙo zuwa ɓangaren lafiya akan magungunan da suka bayar ya
ƙare, sbd cututtukan da suke damun jama'ar rugar, ina saka ran cikin satin nan za a
kawo maganin" Dr Iliya ya numfasa yana jinjina kai kafin ya ce "That's good. Amma
da gaske maganin ya ƙare ne?".. "No ba wani ƙare wa da ya yi, har yanzu ban bawa ko
mutum ɗaya ba" cikin fahimta Dr Iliya ya kalli Dr Hamza yana faɗin "huh! za a kawo
maganin sauro kyauta ma a raba, sbd yawaitar Maleriya"

"Na samu Information ɗin hakan, amma idan an kawo gidan sauron, asibitin nan za a
Ajjiye mu zamu raba, so za a bawa Kowa akan 1500 each one" waro ido waje Dr Iliya
ya yi kafin ya ce "baka ganin zamu iya samun matsala, tunda kyauta gwamnati ta
bayar?" Ɗaga hannu Dr Hamza ya yi yana dakatar da Dr Iliya da faɗin "Hakan shi ne
ribarmu, ba za mu yi musu bauta ba kamar wasu bayi, they have to pay"
Kafin Iliya ya yi magana Hamma Yabi ya faɗo office ɗin da sauri cikin tsawa Dr
Hamza ya ce "Malam ya haka zaka faɗo kamar wani mahaukaci? Me ya sa duk fulanin nan
baku da ilimin zaman rayuwa ne, baku san yadda ake mu'amala ba?" Hamma baya gane
zancan nasu ya ce "Don Allah ka taimaki Dadarmu, kada ta mutu cikin wannan halin
ita kaɗai ta rage mana, sau wajan goma ina zuwa" "Idan munje kanta lafiya zamu bata
kenan? Ko zamu hanata mutuwa? Zan maka last warning Kada na sake ganin ƙafarka
cikin asibitin nan, na faɗa maka bamu da maganin ko ɗaya me kake so nayi maka? Haba
kuna yi mana adalci mu likitoci sai an bimu a hankali mai ya sa zan zuciyarku ya yi
yawa ne?" kasa magana Hamma yai sbd Hawayen daya cika masa idanu me ya sa su Fulani
ake musu kallon mahaukata wanda basu san me suke ba? Akwai wani bambanci a jikinsu
wanda ya bambanta su da sauran jama'a ne? Juyawa ya yi yana zuriyarsa babu daɗi.
Danejo na ganinsa ta ce "Hamma ya naga ka daɗe, numfashi Dadata zai gudu ka
taimaka, ina masu bada lafiya ɗin?" A hankali ya kama hannunta ya riƙe yana shafa
kanta dake ɗauke da suma mai kyau can ƙasa ya ce "Muje gida, ba zamu ƙara zuwa
asibitin nan ba, Allah ya a bamu Kuɗi mu kaita asibitin burni" shiru kawai tayi
tana kallonsa tare da son fahimtar abin da yake nufi a haka suka koma gida jiki
babu daɗi, kwana sukai ba su yi bacci ba, Shatu kawai ta runsta sbd ƙarancin
shekarunta. A daren Danejo ta sanyawa ranta zata sai da nono iya iyawarta ta tara
kuɗi masu yawa akai Dada asibiti. Hakan yasa ta tashi da asuba ta tatsi kindirmo a
ƙwayar gari na fara haske ta nufi cikin burni wajan Abti America.

Mother ce ke sakkowa daga upstairs kunnanta maƙale da waya idanunta sanye cikin
farin glasses ta fito a Barrister Maryam ɗinta sak. A hankali ta ce "Na riga nayi
reporting case ɗin, idan ba a samu good evedance ba akan wanda suka kawo ƙarar
Aliyuna, kai tsaye zan maka ko wacce ƴar banza a court dama kawai nake jira" daga
cikin wayar aka ja numfashi tace "Barrister Maryam kasa aje court,idan akaje to kin
bawa duniya damar zata fahimci halin da ake ciki,abi komai a sannu" ɓayayyiyar
ajjiyar zuciya Mother ta sauke idanunta na sauka akan Zeefa da Fattoumah "Ok za mu
yi magana bari naje wajansa Allah ya sa ya yi magana, al'amarin Sheikh na bani
tsoro yana bani mamaki" ƙara tattaunawa sukai kafin sukai sallama. "sannu da
sakkowa mother" idanunta akan Plasma ɗin da suke kallo ta ce "Fattoumah sau nawa
zan ce bana son kuna kallon zee world ne? Ashe ban isa daku ba ko?" A sanyaye
Fattoumah ta ce "We're sorry Mother ba zamu sake ba" zama tayi ta ce "Change the
channel immediately Mamana" Sauya channel Fattoumah ta yi zuwa Aljazeera tana faɗin
"Ok Mother" kallonsu ta yi sosai ta ce "Where's Maimoon and Auta?" Zeefa ta bata
amsa da "She's inside the kitchen, Auta barci take" Mother ta ce "Bana son barcin
yamma taso mini ita" tana faɗin ta miƙe tare da nufar kitchen daga bakin ƙofa ta
tsaya tana kallon Maimoon dake haɗa coffee ta ce "Ina Lunch ɗin Sheikh?"... "Gashi
a tray mother bari na kai masa" tsareta tayi da idanu ta ce "Bani nan" tray ɗin
lunch ta bawa Mother tana ci-gaba da aikin gabanta.
Haɗaɗɗan part ɗinsa ta nufa tun daga nesa ƙirar arar Sheikh Muhammad didat ta ratsa
cikin kunnuwanta da Mmkin fal fuskar Mother ganin ƙofar shiga parlournsa a buɗe.
Ƙamshin air-cod ya ratsa cikin hancinta. Tana shiga idanunta ya sauka akan Umar-
khan dake zaune gabansa ɗauke da system yana duba wani abu, ganin Mother ya sa
Umar-khan saurin miƙewa tsaye ya ce "Sannu da zuwa Mother" "Yawwa Umar-khan ina
Aliyun?" Hanyar da zata sadaka da bedroom ɗin Sheikh ya kalla yana faɗin "a Parlour
na samesa lokacin da nazo, ina fara yi masa magana akan wannan case ɗin ya tashi ya
shige bedroom har yanzu bai fito ba" jinjina kai tayi ta nufi bedroom ɗin, babu
abin da bedroom ɗin yake sai ƙamshin turarensa ROJA wanda ya a jima da kama ɗakin
duk da cewa bai fiye rayuwa a cikin gidan iyayen nasa ba, yafi rayuwa a Madina idan
yana ƙasa Nigeria kuma yafi rayuwa a gidan Hakimi. ba kowa nan ma a bedroom ɗin sai
tsarin ɗakin da Mother tabi da kallo wanda a kullum yake Sauya mata, komai na ɗakin
fari ne tas, ɓangaren clothes, shoes, perfumes. Komai daban yake. Juyawa tayi zuwa
parlourn tana faɗin "Umar-khan Aliyu baya nan fa? Ko dai ya tafi gidan Hakimi?"
Umar-khan yai shiru ya ce "Bashi da ikon fita, kamar kullum ƴan jaridu na waje ta
ko'ina maybe yana Library ɗinsa" sai a lokacin ta tuna da Library tana zuwa ciki ta
samesa zaune akan wata ƙyakkyawar kujera wacce take juya kanta da kanta ya rufe
idanunsa, sumar kansa ta ɗan bayyana sbd yanayin naɗin rawanin nasa wanda ya yi da
farin hirami. Hannunsa harɗe a ƙirji. Zama tayi kujerar dake kusa dashi tana kama
hannunsa ta ce "Abbana Babana" ajjiyar zuciya Sheikh Aliyu Haydar ya sauke sbd jin
sunan da Mother's ta kirasa da shi amma ya kasa buɗe idanunshi domin baya son ta
fahimci halin da idanunsa ke ciki wanda sune kaɗai suke fallasa raunin zuciyarsa.
"Buɗe idanunka mu yi magana Babana, ba zan taɓa bari kayi gidan yari ba, zan
tabbatar da kai a matsayin mai gsky ba zaka wulaƙanta ba" nan ma shiru ya yi mata
bai ce komai ba kamar yadda ta tsammata. Hawayen da take maƙalewa ne ya kwance mata
wanda ya zuba a tafin hannun Sheikh. Da sauri ya ƙankame hannunsu dake riƙe da nata
yana buɗe idanunsa a hankali wanda suka sauya daka rinewar da sukai. Fararen idanun
nasa ya ɗora akanta ganin hawaye a Fuskarta ya ƙara sashi cikin damuwa amma sam
hakan bai bayyana a garesa ba. "Kayi magana Babana rashin maganarka shike sawa a
dinga tunanin baka da gasky, zuciyata ba zata jure ganinka haka ba" Kallonta yake
har lokacin bai ce komai ba. Ganin bashi da niyyar magana yasa Mother fashewa da
kuka sosai tana miƙe tsaye da sauri ya riƙe hannunta gam! Yana miƙewa tsaye
jallabiya ce jikinsa mai kyau da tsada ga laushi da tsantsi. Kai ya fara Girgiza
mata yana matse hannunta sosai babu abin da Sheikh yake ƙauna sama da mahaifiyarsa
sai Father daga su Hakimi sune duniyarsa. Hannunsa mother ta riƙe ta ce "Try to
speak Sheikh ban damu ba nasan zan fahimce ka, zamu Court bani da wani proof da zan
kareka, mene gasky?" Riƙe hannun Mother Sheikh ya yi tare da fara buga ƙafa yana
ƙoƙarin buɗe bakinsa. Ganin haka yasa Mother taimaka masa wajan riƙe hannunsa tana
faɗin "Ahha say something, speak Babana, say it" hannunta duk biyun ya kama ya riƙe
yana runtse idanunsa sai buga ƙafa yake tuni hawaye ya fara cika idanunsa. "Yee...
Ƙaƙƙƙaaa... M...mmm" kai ta ɗaga masa tana shafa kansa a fisge bayan ya buga
ƙafarsa da ƙasa yana saka hannun Mother a bakinsa ya ce "Babbbban akaita ba, bbbb
ba zan taɓa yin yin yin haka ba mother" yana faɗin hakan yana ƙara saka hannun
Mother a bakinsa duk ya jiƙa mata hannu da yawunsa mai ƙamshi a ƙoƙarinsa na ganin
ya yi magana daidai waya baiwa ta Sheikh idan koyarwa zai yana samu maganarsa ta
fita yake fara karatu cikin sauri baya tsayawa sai ya gama yana gamawa baya ƙara
cewa komai yake fita daga hall. Wani irin rauni ya kama zuciyar Mother tausayi da
ƙaunar Sheikh ya ƙara wanzuwa a zuciyarta wacce irin larura ce haka wacce bata
barin har babban mutum? Zare hannunta ya yi domin har ransa bai san lokacin daya
saka hannunta a baki ba a hankali ya juya zai bar wajan da sauri mother tana goge
hawaye ta ce "Aliyu" cak ya tsaya tana ƙoƙarin magana Umar-khan ya shigo wajan da
sauri gaba ɗaya suka bisa da kallo Umar-khan ya ce "Sheikh na shirya mota a ƙofar
baya, yanzu zamu bar gidan nan jami'ai na hanyar zuwa nan zasu kamaka" ko motsawa
Sheikh bai ba shi dai ya san ba zai taɓa hana abin da Ubangiji ya tsara afkuwa ba.
"Jeka Aliyu ka bisu su fitar dakai Sheikh" Mother ta faɗa tana jan hannunsu ganin
haka yasa ya bita har zuwa bakin wata sabuwar mota shiga ya yi. Drivern yaja, Umar-
khan shima ya shiga mota, Saif-Wazir ya shiga wata motar. Motar ƙarshe kuma Ishaq-
hakim ya shiga kai tsaye suka nufi wata hanya ta daban. Sbd gujewa haɗuwa da
jami'an da kuma ƴan jaridu, kasancewar duk sunyi connecting wayoyinsu dana juna
yasa Umar-khan gyara bluetooth na kunansa ya ce "Saif-Wazir" Saif ya amsa da "Ina
kan layi" haka Ishaq-hakim da kuma Drivern Sheikh. Cikin jin daɗi Umar-khan ya ce
"Saif-Wazir idan mun isa Shatalelen gidan gwamna kabi hanyar Amado bello way" Saif-
Wazir ya ce "Noted bro" Umar-khan ya ce "Ishaq-hakim kabi hanyar Asibitin nasarawa,
Drivern Sheikh Kabi hanyar ƙofar nasarawa,ni kuma zanbi hanyar kasuwar tarauni,
gaba ɗaya hanyoyin zasu haɗamu a titin Dawaki roud zamu sauka gidan Hakimi.." haka
duk suka amince suna zuwa Shatalelen gidan gwamna ko wacce mota ta ɗauki hanyarta
suka ɗauke tunanin jami'an tsaron daka hanyar da zasu bi, Sheikh na bayan mota ya
zubawa ikon Allah idanu a haka suka ƙarasa Dawaki roud motocin suka haɗu waje guda
kai tsaye suka ƙarasa gidan Hakimi. Sheikh na fito da ƙafarsa waje aka riƙe hannuna
tare da saka masa sarƙa kamar daga sama yaji ance "You are under arrest.....

08119237616.
[1/3, 4:48 PM] Abk: *🌈 IDAN BA KE 🌈*

*_Arewabooks@Nimcyluv_*

10....
Kasa magana Mother tayi sai Ishaq-hakim da tabi da kallo tana son gasgata abin da
yake faɗa. "Ta ya ya Sheikh zai amsa laifi fyaɗe? Laifin da duk duniya ta san ba
zai iya aikatawa ba?" Ta faɗa a fili tana sakin wani raunataccen kuka mai tsayawa a
zuciya ba zata iya kallon Sheikh cikin sarƙa a ɗaure ba, kamar wani ɗan fashi ko
Kidnapper. Umar-khan ne ya kama Mother wacce take ƙoƙarin zubewa a wajan sbd kukan
da take idanunsu ya yi jajur ya ce "Ki daina kuka Mother, wata kila Sheikh ya amsa
laifin ne sbd rashin mafita, mu duka abin ya zo mana cikin wani sabon yanayi wanda
bamu taɓa riskar kanmu ciki ba, Ubangiji ka ɗai ya san gaskiya kuma shi muke roƙa
ya fidda Sheikh Aliyu daga cikin wannan jarrabawar" gaba ɗaya zuciyar Mother ta
karaya tunaninta ya tsaya cak duk inda take neman wata hujja ta kare ɗan nata babu.
Da hannu bibbiyu ta riƙe Umar-khan ta ce "Kai ne kake tare da Babana Umar-khan, ka
taimaka mini nasan kasan Aliyu ba zai iya aikata hakan ba, yana tsare imaninsa yana
amsar rayuwa a duk yadda ta zo masa" Umar-khan ya mayar da hawayen dake cika
idanunsa kafin ya zaunar da Mother ya ce "Be patient Mother, muyi addu'a kawai amma
da ace zan iya bada shaida, da iya abin da zan faɗa ya isa ya wanke Sheikh daga
cikin zargi"

"That's enough, this is not a place to make noise" Wani daga cikin jami'an tsaron
ya faɗa yana daka musu tsawa.
Sai a lokacin Abba Hakimi ya yi ajjiyar zuciya domin shi ma Al'amarin ya girgiza
shi fiye da tunanin kowa, zuciyarsa shi zafi take masa sosai. A nutse ya juya ya
kalli Ishaq-hakim ya ce "Ka mayar da Barrister Maryam gida yanzu, ka ce ina buƙatar
ganin Aliyu immediately" da girmamawa Ishaq-hakim ya amsawa mahaifin nasa,
idanunshi akan Mother yana jiran ta miƙe.
Cikin kuka ta kalli Abba Hakimi ta ce "Ina son nayi magana da Aliyu Please Hakimi"
Kafin Abba Hakimi ya bata amsa wani daga cikin Jami'an tsaron ya ce.
"No way Madam" tana share hawaye ta ce "Don girman ka bani 2 minutes nayi magana da
ɗa na, ina son tambayarsa, tare da kwantar da hankalin shi" cutting nata out ya yi
da faɗin. "Isn't necessary Maaah..." A ƙagauce Abba Hakimi ya ce "take her out
Ishaq-hakim" Mother na kuka sosai tana kiran sunan Sheikh Aliyu aka fitar da ita
waje, Aliyu shi ne rauninta ka kaf cikin yaranta tafi ƙaunarsa duk abin da Mother
ta mallaka daga cikin dukiyar iyayenta Aliyu ta bawa, She owned all her property
for him, Lands, houses, companies, all signed in the name of Aliyu's property.
Su Mother na fita Abba Hakimi ya kalli jami'an tsaron cikin murya mai taushi ya ce
"Kun samu hujja mai ƙarfi da kuka kama mini ɗa na?" Ɗaya ya sunkuyar da kai cikin
girmamawa ya ce "Har yanzu bamu da hujja, amma a duk bin ciken da mukai Sheikh ƙara
shiga ciki yake, yaƙi buɗe baki ya yi magana, gwamnatin Madina da universityn ƙasar
sun matsa akan kwana biyu suka bayar idan ƙasa Nigeria bata ɗauki mataki ba, zasu
ɗauka da kansu domin su irin wannan cases ɗin kai tsaye suke bincike kuma hukuncin
kisa ne" runtse idanu Abba Hakimi hukuncin kisan ya daki zuciyarsa ainun. Umar-khan
da bakinsa ke rawa tun ɗazo sbd masifa ya ce "Ita kanta gwamnatin Madinan idan bata
da hujja dole ta haƙura, ina masu kawo ƙarar? Daga ina wannan zan can ya fito? Ina
ƴan matan da akaiwa fyaɗen suke?"
"Stop raising your voice, we are working on our system, nan ba Court bace" Umar-
khan zai sake magana Abba Hakimi ya yi gyara murya kafin ya ce "Ka bari abu komai a
nutse, shi ya sa na mai da Barrister Maryam gida" Saif-Wazir dai na tsaye duk
yadda suka so a basu Sheikh su yi magana hanawa akai. Kuma a gobe za a kaisa court
domin fara gabatar da Shari'a tun da case ɗin ya zo da hargitsi. Haka suka komai
gida zuciyoyin kowa babu daɗi.
Sheikh na zaune daga shi sai single da wani farin trousers mai laushi tunda yake a
duniya babu wanda ya taɓa ganin tsari da zubin halittarsa sai yanzu, an tuzarta shi
tuzarcim daya har zuƙa kuturwar zuciyarsa, shi kaɗai sai tsuma yake shi da ko sauro
baya so baya ƙaunar yaga baiwar halittar da tsaraicin jikinsa, yana tsarkake
jikinsa domin sirrinsa ne, amma yau da wanda ya dace da wanda bai dace ko wanne tom
and jerry gani yake abin ya yi masa zafi ainun. Dalilin daya sanya ya amsa laifin
kenan ba tare daya shirya hakan ba.

Mother na komawa gida ta samu Fattoumah na zaune ita ɗaya a Parlour da sauri
Fattoumah ta ce "Mother ina Yaa Lee? Ba zai dawo ba?" Murmushi mother ta yi tana
ɓoye damuwar ranta ta ce "Ya dawo mana Manana, yan gidan Abba Hakimi where's your
sisters?" Da hannu ta nuna mata part ɗinsu, Mother ya kama hannunta suka shiga
ciki. Yaran duk suna zaune sanye da hijabi sunyi shiru bayan sunci kuka sun ƙoshi,
cikin faɗa ta ce "Maimoon, Zeefa what's this? Kuna da hankali zaku shigo ɗaki
kuyita kuka kamar anyi mutuwa, Depression kuke son ya kamaku ko mene?" Gaba ɗaya
suka miƙe tsaye jikinsu na rawa za su yi magana ta ɗaga musu hannu ta ce "Ku fita a
nan wajan, maza aje a kunna kallo ayi" fita gaba ɗaya sukai jiki babu ƙwari mother
ta bisu da kallo tausayin su na kamata tasan duk sanadin Aliyu Haydar suka shiga
wannan damuwar. Kuma ita idan har ƴar halak ce ba zata sake zuwa wajan Father ba
akan maganar Sheikh Aliyu ɗin ba.
Tana fitowa daga cikin bedroom ɗin upstairs ta haura zuwa nata bedroom ɗin wayarta
ta ɗauka ta shiga kiran Barrister Zainab akan gobe zasu shiga Court sun daɗe suna
waya kafin ta kira Yaya Halima anan ta kwantar mata da hankali ta ce ita ma ta nan
zuwa dan sunyi nisa ne. Har Mother ta miƙe da sauri kuma ta koma ta zauna domin
gaba ɗaya ta manta da batun Jadda cikin sauri ta danna numberta wayar ta jima tana
ringing kafin a ɗaga a fusace akace "Allah dai yai gutsi gutsi da duk wanda yake
addabata wannan masifar har ina, ba lallai mutum yaga Annabi ba" A hankali Mother
ta ce "Jadda ni ce Maryam" Jadda ta ce "Wata abace Maryam kuma? daga wacce duniya
mena haɗa dake?" Shiru Mother can kuma ta ce "Mahaifiyar Sheikh Aliyu" Jadda ta
zabga salati da

Please Login or Register in order to submit comment