You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hankali ya
bayyana a fuskar shi, Dattijo da Hajia suka kalli Yaa Sheikh ta ce.
"Mai gidana shigo mana kai tsaye" ya dai tsaya ta ƙara cewa "Lafiya dai?" Ya ƙara
yin shiru ta gyara zama ta ce "To kaci kan ka, wallahi nafi ƙarfinka sai dai uwarka
gata nan" Ummul dai tayi murmushi kuma bata kula Yaa Sheikh ba, alrdy Mother ta
sanar mata komai, hakan ya yi mata daɗi duk da abune mai wahala Halisa ta ce dole
sai ya rabu da ita, ya ƙarasu ciki ɗauke da Sallama kan akan cinyar Ummul ya gaida
kakannin na shi.
Shi bai magana ba Ummul ba tai ba, can ta ce "Ɗaga ne da na kawo maka lunch" ya
girgiza kai ya ce "Azumi" ta ce "To Allah ya bada lada" a hankali taji gabaɗaya
kan shi ya ɗauki zafi sosai ta taɓa kan ta ɗauke hannu ta ce "Baka da lafiya?" Ya
ce "Lafiya lou" tai ta kallon shi. Ta cire hiramin ta dinga shafa sumar kan shi
tana masa addu'a, a haka taji saukar numfashi shi ta leƙa taga ashe barci yake.
Wasa wasa sati guda ya shuɗe, na biyu ya shafe, na uku ya shige sati huɗu cif bai
sanya Halisa cikin idanunsa ba, ko gilmawar ta baya gani.
Halisa kuma sai ta fahimci baya gidan take fitowa parlourn suyi hira, da zarar taji
motsi ko ƙamshin turaren shi take barin wajan. Tana shan wahala amma haka take
jurewa cikin dare tayi ta kuka tana riƙe ƙafa, ta faɗa sbd buƙatar mijinta da take,
Yaa Sheikh baya bambance Alhamis da Litinin kullum cikin azumi yake,ya rame sai
fararen idanunsa da suka ƙara fitowa. Zahrah ce kwance gadon asibiti Jikinta na
rawa, na'urar room ɗin sai ƙara take, Surry ta riƙe ta riƙe Muhammad sosai, cikin
sauri Mimi da Dr suka shigo ganin ba zai iya ba, ya ƙara kiran wasu likitocin aka
nufi emergency da ita, da ƙyar suka shawo kan matsalar. Alhaji Farouk da Mimi suka
kalli Dr ta ce "Ban fahimta ba Dr mene ya samu yarinyata?" Ya gyara zama yana zame
Glasses ya ce "Bayan hawan jinin da take da shi, ciwon zuciya ya shige ta da ƙarfi,
bai kai matakin aiki ba, amma irin shi da wuri yake kisa, domin ganin yarinyar ku
ta ci-gaba da rayuwa a duniya ya zama dole ki bata abin da zuciyarta ke so" Kuka ya
ƙwacewa Mimi Alhaji Farouk ya ce "Me take so har haka? Idan kuɗi ne akwai komai
take so za a siya mata" Mimi tana kuka sosai ta ce "Abin da Zahrah ke so, kuɗi bai
isa ya siye shi ba, ko da zaka ƙarar da gabaɗaya dukiyarka ne, ba zaka sama mata
Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu ba" Alhaji Farouk ya miƙe ya ce "Dole naje na samu
mahaifiyar Yaa Sheikh da Abba Hakimi tun da mahaifin shi baya duniya ya zama dole"
Cikin dare wajan ƙarfe 3 Halisa na zaune a saman kujera hannunta riƙe da ice cream
wanda Maimoon ta siyo mata a Havilla, ta saka a freezer ya ƙara sanyi tare da
ƙanƙara. Ta lumshe idanu tare da siɗe ƙaramin cokalin da baki sanyi na ratsa ta
sosai, yana ƙara sanyata cikin wani hali feelings mai tsanani na ta so mata, ta
ajjiye ice cream tare da miƙewa tsaye daga ita sai Riga da wando na Pajamas white
colour Yaa Sheikh's favorite colour ta sanya Scuff faux-shearling slippers sai
ƙamshi take ƙirjinta ya ƙara cika, ta miƙe zata juya zuwa cikin bedroom kenan ta ji
an ɗaga ta cak tare da fara tafiya da ita...[1/18, 1:37 PM] Abk:
https://vm.tiktok.com/ZMYJCVDeF/

Ka shiga link ɗin ka faɗi kalma ɗaya mai kyau akan littafin idan ba ke👆🏾08119237616

Ko ba a faɗa ba, tasan shi kaɗai ne zai iya yi mata haka, ta shiga kokawa zata
ƙwace kanta amma ta kasa, ta daddage ta fasa ihu ta ce
"Wallahi zan maka ihun kwarto idan baka sauke ni ba" bai shirya tunan asirin da
take shirin yi masa ba, ya yi saurin dire ta ƙasa yana riƙe da hannayenta, kalmomin
da zai mata bayani yake ta harhaɗowa a bakinsa amma ya kasa samun cikakkiyar kalma
ko ɗaya, ganinta kusa da shi ba ƙaramin barazana bace ga zuciyar shi da kuma abin
da ke addabar shi tsayin satittika.
Ya numfasa yana riƙe kan shi gudun kada ya yi abin kunya a gaban ƴar ƙaramar
Yarinyar dake neman jan shi a ƙasa ya ce "Zawja ni ne kwarto?"
Ta kame fuska tare da ɗauke kai can, ganin yadda muryarta ke tasiri a zuciyar Yaa
Sheikh take saukar masa da nutsuwa yasa ta ƙara tsuke ɗan ƙaramin bakinta.
A raunace cikin wani sabon yanayi mai wahalar fassaruwa YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR
ALIYU ya furta.
"Zawja ƴar fillona come to your husband, why are you doing this to me, am I
stranger?" Cikin ƙarfin hali, da rashin nutsuwar Zuciya data gangar jiki ya furta
hakan.
Halisa ta ƙwace hannunta tana yin nesa da shi taƙi cewa komai, babu alamar tausayi
akan fuskarta... Taurin kan yarinyar ya bashi mamaki bai san lokacin data sauya ta
zama mai kafiya da naci haɗi da zafin zuciya ba. "Anya kina son rabauta da ribar
dake cikin zamantakewar aure Zawja? So ki ke na zama Ayuu!?"
Ya yi shiru da nufin ko zata tanka masa amma tai mursisi dole ya tsuguna ya lashe
aman da ya yi mai datti da wari, daman tabarmar kunya da hauka ake kwashe ta.
"Na yi miki al'ƙawarin idan akan taɓa jikin ki da nake ki ke wannan kumfar bakin,
to na haƙure zuwa lokacin da ranki zai fari, bana son ki ƙaura cewa Idanuna, IDAN
BA KE ba san ya nake b" sai lokacin ta kalle shi ta ce.
"YAA SHEIKH" Ganin kamar da gayya ta faɗi sunan na shi ya sa kawai ya bita da
Idanu, yanzu ta dai na bashi mamaki, kallon mara tausayi wacce bata amsar uzuri
yake mata.
Ta kalle shi ta ce "Ba jikina ne bana so ka taɓa ba, so nake ka haƙura dani na
tsayin shekarun da suka rage maka a rayuwa, ka yi zuciya ka bani takardar sakin
daka furta kuma ka ayyana a ranka YAA SHEIKH ALIYU" cikin rawar murya YAA SHEIKH ya
ce
"ƙarya na ke, iya laɓɓa kawai na furta haka, IDAN BA KE babu wata rayuwa da zan
iya" dariya ta so kama Halisa amma ta danne tana dafe ƙirji ta ce "Asstagafirullah,
Allah na tuba ka manta ƙarya haramun ce?" Bai ƙasa a gwiwa ba wajan furta.
"Ni ba Manzo ba, ni ba sahabi ba, ni bawa ne na Allah, a koda yaushe zan iya kauce
hanya!"
Ta ware hannunta irin "Anyway, is not problem"
Ya langwaɓe kai ya ce
"Kin yarda IDAN BA KE babu numfashin Aliyu" ta nuna shi da hannu ta ce
"Wallahi ba zan koma gidanka ba, idan har ni ce kwanciyar hankalinka to ka shirya
tafiya lahira da kwanan kabari" tana faɗin haka ta juya tana kaɗa masa ƙugu wanda
suke ƙara sanya YAA SHEIKH cikin wani hali wanda shi kan shi ba zai iya furta ko
fasalta yadda ya ke ji ba.
Ya zube akan kujera yana dafe kan shi, bakinsa ɗauke da addu'ar samun sassauci da
rahamar Ubangiji. Ya miƙe a sanyaye tare da nufar part ɗinsa yana zuwa ya nufi
bathroom ya sakarwa kan shi shower da ruwa mai sanyi, ya daɗe tsaye yana mayar da
numfashi. Ya ɗaura alwala yana fitowa ya saka Jallabiya Viridian green mai ƙaramin
hannu, ya ɗauki hirami ya ɗora a kan shi tare da ɗaukan prayer mat ya shimfiɗa.
Sallah ya yi raka'a biyu raka'ar farko ya karanta Fatiha da Surah Kafiroon, ta biyu
ya yi Fatiha da Surah Al Ikhlas. Cikin sujjadar ƙarshe ya shiga faɗin.
" ‫ َفِإ َّنَك َتْقِدُر َوال‬،‫ َوَأْسأُلَك ِمْن َفْضِلَك اْلَعِظيم‬،‫ َوأْسَتْقِدُرَك ِبُقْدَرِتَك‬،‫َالَّلُهَّم ِإِّني َأْسَتِخيُرَك ِبِعْلِمَك‬
‫َأ‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬
‫ الّلُهَّم ِإْن ُكْنَت َتْعَلُم َّن َهَذا ْال ْمَر‬،‫ َو ْنَت َعّالُم الُغيوِب‬،‫ َوَتْعَلُم َوال ْعَلم‬،‫ْقِدر‬
Idan zama da Halisa matsayin matata shi ne alheri
‫َو ْن ُكْنَت َتْعَل‬ ‫َأ‬ ‫َأ‬
‫ ِإ‬- ،‫ َعاِجِلِه َو ِجِلِه َفاْقُدْرُه ِلي َوَيِّسْرُه ِلي ُثَّم َباِرْك ِلي ِفيِه‬،‫َخْيٌر ِلي ِفي ِديِني َوَمَعاِشي َوَعاِقَبِة ْمِري‬
‫َح ْي ُث َكا َن ُث َّم َأ ْر ِض ِني ِب ِه‬ ‫ِل‬
‫ َفا ْص ِر ْف ُه َوا ْص ِر ْف ِني َع ْن ُه َوا ْق ُد ْر ي ا ْل َخ ْي َر‬،‫ َأ ْم ِري‬."
Bayan ya kammala Sallar Istihara ɗin ya jingina da jikin gado idanunsa rufe, barci
ya ƙaura cewa Idanunsa tare da yi masa hijira, ƙaramar yarinya na son Jan shi a
ƙasa ya zama kamar bita zai-zai, bai taɓa mafarkin zata ƙaurace masa har haka
ba,bai ɗauka bayan shi zata damu da ganin wasu nata ba, ya ɗauka iya shi ɗaya ya
ishe ta a rayuwa. Ya ɗauka ba zata nemi soyayya mai zafi daga gare shi ba, sai
gashi tunaninsa ya saɓa zaton shi. Har aka kira Assalatu yana zaune, rabon shi da
cin kyakkyawan abinci har ya manya. Ya miƙe yana ɗaukan casbawa tare da yin waje. A
harabar gidan yaci karo da Abba Hakimi da kuma Umar-khan da Ishaq-Hakim sun fito
zasu nufi Masjid. Suka jera ba tare da kowa ya yi magana ba,cikin takun shi mai
kama dana wahainiya, nutsuwa,kamala, kwarjini da tarin Ilhama dake kwance saman
fuskar YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU ya shiga wajan liman tare data kabbarar
harama, karatu ya fara a sanyaye cikin rashin sautin murya saɓanin da, gabaɗaya
suka rasa meke damun shi yana yi yana rafkanwa, bayan ya sallame ya yi sujjada
bayan sallama. (Sujjadar ba'adi). Wa'azi ya fara akan gudun duniya da duk wani
kayan kyale-kyale dake cikinta.
Misalin 10 na safe Abba Hakimi da Mother da kuma Umma A'isha na zaune saman kujera
Halisa fito sanye da ƙaton hijabi har ƙasa, ta durƙosa har ƙasa ta gaishe su.
"Matar ya ya akai ne?"
Ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Jon wuro makaranta nake son na koma Please" ya
daɗe yana kallonta yana jajanta lamarin kafin ya ce. "An shige ki da yawa, wanne
mataki ki ke kafin ku dawo?" Ta ce "Jss2 zan shiga" ya ce "Tab, yanzu Kinyi girma
sai dai a biya ki zana weac da neco, bana jin kuma zaki iya karatun University"
Da sauri ta ce "Zan iya Jon wuro, Allah ina da ƙoƙari ko karatun Alkur'anin da ka
ke mini haddace shi nake, gashi yanzu ina izu talatin da biyar" ya ce.
"Na gamsu, duk da ina mamakin kaifin tunaninki da basirar da Ubangiji ya baki
Halisa" Mother tai murmushi ta ce "Duk wanda ya zauna da YAA SHEIKH ai ba zai taɓa
zama daƙiƙi ba,balle kuma wanda ya rena" walwalar fuskar Halisa ta ɗauke ta ce "Ai
da ƙoƙarina Dada ta haifeni"
Mother ta ce "Haka fa" ita dai tai shiru
Abba Hakimi ya ce "Tambayi mijinki, shi ne zai baki iznin idan ya amince zan bawa
Umar-khan ya yi komai"
Tamkar zatai kuka ta ce
"Ni bani da wani miji, ka dai na haɗani da kowa don Allah Jon wuro" daga bakin ƙofa
aka ce.
"Anƙi ɗin, bayan duniya ta gama shaidawa Gadanga shi ne mijinki kuma shi ne
gatanki"
Jadda ta ƙarasa faɗa tana shigowa ciki, Maimoon ta biyo bayanta. Daga tsaye Jadda
ta ce "Halisa ki ke meye ne? Ke kam ba a nonon Khadijah ki sha wannan mugun halin
ba, uwarki ba haka take ba, ta san halarci ta san kuma wanda ya yi mata, tun wuri
ina baki shawara ki bi mijinki dau da ƙafa, kafin wata can tayi ciki tashi, ni
Alkur'an da zai aure mata uku ma da ya kyauta mini, ai lafinki ne da ki ka sake
masa jiki yana lugudan da ya yi niyya da shi, har ya banka miki ciki, waya faɗa
miki ana yi wa namiji haka? Ai basu da kunya ta wannan ɓangaren kuma tunda kuka
fara dole ku ƙare tare, balle namiji kamar Malam wanda ya karanta yaji komai a
Muslunci"
Wani takaici ya kama Halisa ta ce.
"To ya yi auren mana, ni daman ai bana son shi" Jadda ta dungure mata kai ta ce
"Laa! Ji tsinanniyar ƙarya, mai ƙarya a ƙona shi a wuta yasin, gashi nan kin cika
kin yi fam! Alamar kin son buƙatar mijinki mayya kema ɗin fitinanniyya ki yi ta
lalata ɗan jama'a yanzu ki guje shi" ta juya kan Abba Hakimi ta ce "Can fa naci
karo da shi, wallahi sai dana zubar masa da ƙwalla, ni na ɗauka ma da wani ɗan
ganyen nai karo kai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya, wai Malam ne soyayya ta
rugurguza shi haka, huhuhu! Ke kam ba zaki taɓa gamawa da duniya salamun ƙaulin ma
idan har baki rungomi mijinki da hannu bibbiyu ba, idan ba yara ki ke so kina samun
cikinsu akan titi ba" ba wanda ya kulata can ta nisa ta ce.
"A to meye ma ruwana, wannan rayuwar kowa yaji da abin da yake gaban shi, Allah ya
sa ba wata tsiyar na ce ba, amma dai ƴar mutan Rome kinci amanar malam" Umma A'isha
ta ce "Amana kam ta ci" Jadda ta muskuta ta ce
"To Ubangiji ya san yadda zai da lamarin, ko kuma kawai ya saki ƴar banza mai zubin
zabiya, ni da ƴata ce da tuni na haɗa mutin a gaban kowa zai ɗaga mata nono" ta
jinjina kai ta ce "Allah ya san yadda zai da lamarin" Halisa ta haɗe fuska sosai ta
ce
"Idan auren a hannunki yake yanzu ki sake mini shi, ko ki je ki sanya ya sake ni ki
ga idan zan mutu masifaffiyar mata kawai" Jadda tai mitsi mitsi da idanu ta ce
"Kiga masifa akan Mai rawani Wlh shi ne azababbe, meye nawa da zan raba haɗin
Allah?" Mother ta shiga cikin zan can ta ce.
"Rabo da Jadda kin ji daughter, gidan Aliyu ne ba zaki koma ba" Ta kalli Abba
Hakimi ta ce
"Jon wuro makarantar?" Ya numfasa ya ce "A'a, ba ruwana jeki nemi izini wajan
mijinki,kafin ya ce baƙin ciki nake masa"
Ta miƙe zuciyarta babu daɗi bata son duk abin da zai sanya ta shiga sabgar shi.
Bayan tafiyarta Jadda ta ce
"Maryam haƙuri nazo baki, ki daina gani na kamar tsohuwar banza nasan me nake,
Yaran da Ubangiji ya azurtaku dasu zaki duba, kada rayuwar su ta ƙare a haka"
Mother ta ce.
"Ayya Jadda kin yi mini adalci kuma ki fahimci ni, wallahi a yanzu bana son
Engineer ko kaɗan, zaman court kawai nake jira ya sawwaƙe mini kuma ya bani
ƴaƴana..." Mother ta dinga faɗa ta inda ta shiga bata nan take fita ba. Jadda ta
fashe da kuka ta ce.
"Azaba, daga nemen taimako sai zagi Maryam?" Dr A'isha data shigo yanzu ta ce.
"Babu batun zagi, Gasky ce kawai ya bata raguwar sakin ya je ya yi rayuwa da sauran
karuwai" Mother ta kalli Dr A'isha haka kurum kalmar ƙarshe ta ɓata marai har taji
zafin Dr A'isha ɗin. "Ya je ya yi rayuwar da sauran karuwai" hausawa sun yi gaskiya
da suka ce ba a shiga tsakanin miji da mata, duk lalacewar mijinki dole a kira shi
da uban ƴaƴanka, bare kuma _first love_
Jiki a sanyaye Jadda ta fito daga gidan, Engineer dake cikin mota gaban shi ya faɗi
ganin yadda mahaifiyar ta shi ta fito, gabaɗaya Ƴan-uwan shi suƙi saka baki cikin
matsalar.
Dr A'isha ta miƙe ganin Mother bata tanka ta ba, ta nufi bedroom ɗin Halisa ta
shiga bata kyakkyawan darasi akan ƊA-NAMIJI ta ɗora ta akan tubalin da zata ka Yaa
Sheikh hankali kwance duk ta nunawa Dr A'isha ita bata ra'ayin Yaa Sheikh yanzu,
karatu kawai take so. Ta rantse da abin da zai kasheta ba zata koma gidan shi ba,
balle auren shi.
Dr A'isha ta bata sabuwar waya mai kyau tare da sim, ta buɗe mata komai WhatsApp,
Arewabooks, wattpad. Ta nuna mata yadda ake karatun littafin duk ta iya Hausa harda
ɗan turanci. Kana ta sakata cikin wani shahararren group na MU MA MATA NE.
Ta ƙara yi mata gargaɗin kada ta kuskura ta ƙara barin Yaa Sheikh ya taɓa koda
hannunta ne.
Kiran Ummul a waya ya sanya Yaa Sheikh shiryawa cikin wata dakakkiyar shadda mai
kyau da ɗaukan idanu, fara tas ya ɗora hirami idanunsa maƙale cikin sirirn farin
Glasses photochronic and faɗawar da kwayar idanunsa tayi. Kasancewar ranar juma'a
ne ya ɗora Alkyabba mara nauyi, ya fito

Please Login or Register in order to submit comment