You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanayin kafin ya ce.
"Na amince, zan aureki"
Ta saki murmushi while hawaye na zuba ta ce
"Na gode Allah ya saka da alheri Ubangiji ya ƙara girma" Ya jinjina kai sukai shiru
ta kalle shi ta ce "Nasan takura maka akai, ko tausaya mini kayi ba dan kana so na
ba ko?" Ya nuna mata pillow ya ce
"Huta, barci" ta ce
"Nayi barci har na gaji, yanzu bani da wani damuwa daman kai ne damuwata" sai yaji
tausayinta, sai yanzu ne yake gane cewa duk wanda yake hauka akan SO! To kawai a
rabu da shi, so babban abu ne da kan iya tarwatsa zuciyar mutum murus ya lalata
masa rayuwa ya ɗauke masa farin ciki yanzu ya shaida haka.
"Matarka? zata amince dani, na maka al'ƙawarin ba zan taɓa janta da faɗa ba ko tayi
zan haƙura domin tayi mini komai datai mini halarci har ta amince ka aureni, wlh
idan ni ce ita ba zan iya barinka ba, balle ka auri wata ina maka son da Ubangiji
kaɗai ya sani kuma shi ne zai zama shaida, kana da kima kwarjini tarin da haiba
wacce ba kowa zai iya Fuskantarka da wani shirme, nasan zaka zauna sani bisa takura
kayi haƙuri,kai mini adalci ba laifina bane"
Ya girgiza mata kai a taushashe cike da kulawa ya ce
"Ba takura, ki nutsu zamu zauna gida ɗaya tare"
tai murmushi tana ɗan riƙe ƙirjinta. Ya taimaka mata ta kwanta ta ce
"Kada ka tafi don Allah"
Ya jinjina kai yana tsaye kanta tana kallon shi tare riƙe hannunsa har barci ya
ɗauke ta.
Fita ya yi, zuwa office ɗin Dr. Dr ya ce "Ko iyayenta basu san tana ɗauke da Cancer
ba, wanda kuma munyi scanning yaci ƙarfinta abu ne mai wahala ta tsallake wata
biyar a raye a duniya" Yaa Sheikh ya ce "Subuhanallah!" Dr ya ce "Yana da kyau ta
ƙare watanni biyar ɗin nan da farin ciki, kada ita kanta tasan cewa akwai Cancer
Jikinta hakan zai ƙara taimakawa wajan murmurewar Jikinta"
"Ba wani aiki?" Dr ya ce
"For now babu, domin taje ƙarshe sai dai fatan samun sauƙi wajan Ubangiji" ya miƙe
yana godiya. Daga nan sukai sallama Yaa Sheikh ya nufi Rugar Bello a hanya ya kira
Abba Hakimi sukai magana mai ɗan tsayi kana ya kira Ummul daga nan ya ajjiye wayar.
Halisa na zaune tana azkar Idanunta ya kumbura sbd kwana tayi tana kuka sai dab da
Subhi barci ya ɗauke ta, kasancewar ta saba ta shi yin Sallah ya sa bata makara ba
Ta miƙe da ƙyar tana dafe kanta Idanunta na lumshewa sbd barci ga wani irin
matsanancin feelings dake damunta ta rasa yadda zatai da rayuwarta, harta mata
tsayin lokacin data ɗauka ba tare da Yaa Sheikh ba, she miss his torch, his kiss,
his body his everything daya shafe shi amma zafin ranta ya kasa bari ta yarda tai
kewar, tana ƙoƙarin kwanciya mother ta buɗe ƙofa ta shigo lokacin wasu masallatan
nata sallah ta ce "Barka da safiya Mother" bata amsa ba ta ce "Kije, ki haɗa mana
breakfast, ga wanke-wanken ma da mopping" a raunace ta ce "Ina maid ɗin? Bana jin
daɗi" ta ce "Allah ya sauwaƙa mai aiki kuma mun sallameta ke zaki koma yin komai"
Kamar zatai kuka ta ce
"Bari gari ya yi haske to"
"Yanzu na ce, kafin Abba Hakimi su tafi kai kuɗin Auren Zahrah" kamar an caka mata
wuƙa a zuciya haka taji hawaye ya sakko mata, mother tai waje. Ita kaɗai ta dinga
kuka babu mai rarrashi
wayarta ta ɗauka da niyyar yiwa Maimoon ko Dr A'isha magana a online sai taga anyi
mata magana da prvt number, kamar ba zata shiga ba sai kuma ta buɗe abin data gani
ya yi mugun tayar mata da hankali ta dafe cikinta da sauri wanda ya murɗa fitsari
ya taho mata, tai downloading picture ɗin Yaa Sheikh ta gani rungome da Zahrah a
ɗakin asibiti a ƙasa kuma aka ce. "Mun gode sosai Halisa da shirmanki ya bawa
ƙawata damar samun cikar burinta, yanzu Yaa Sheikh na Zahrah ne har abada ki fara
kokawar neman mijinki domin yanzu wutsiyyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa, ke da Yaa
Sheikh har abada.....," Bata ƙarasa karantawa ba ta nemi ganinta ta rasa ta kuma
kasa fahimtar komai ta fasa wata ƙara tana faɗin..
[1/24, 7:40 AM] Abk: "Wallahi ƙarya ki ke, baki isa ki auri abin da na fiso a
duniya ba, dole ki rasa kamar yadda ki ka rasa" gabaɗaya Jikinta rawa yake har ya
gaza ɗaukan ƙafafuwanta ta sulale ƙasa tare da yin zaman ƴan bori.
Wani irin kuka take mai tarwatsa zuciya da sanya mutum cikin damuwa, duk wanda ya
ganta sai ya tausaya mata, hannunta na rawa ta ɗauki wayarta tare da kiran Dr
A'isha. Ringing ɗin farko aka ɗauki wayar tare da faɗin.
"Hello!"
Halisa ta ce "Adda A'isha na shiga uku, ba zan iya ba" Dr A'isha tai murmushi tana
kallon ɗaya wayar hannunta kafin ta fita daga inda take ciki, ta nemi bakin gado ta
zauna ta ce
"Shiga uku dame Halisa?" Cikin shassheƙar kuka murya bata fita sosai ta ce
"Da gaske Abbana aure zai yi wallahi, kuma Zahrah zai aura ba zan iya jurewa ba,
ina jin kamar zuciyata zatai bindiga" Dr A'isha ta kaɗa ƙafa ta ce
"Meye abin damuwa? You need a divorce paper, and you got it, I think you will be
happy". Halisa ta dafe ƙirji ta ce "I love my husband, ina son mijina kin san ban
tsane shi ba, ba kuma zan iya barin wata ta aure shi ba, yanzu ya zan?"
Dr A'isha ta runtse idanunta tana jin kamar wuta Halisa ta watsa mata a ƙirji da ta
ce _She loves her husband_ ta kasa cewa Halisa komai ta shiga dannar zuciyarta sbd
zafin da tayi..
"Na zama shasha, na rasa meke damuna" Dr A'isha ta ce "It's over, kin yi sake when
all is gone, yanzu sai da kibi hanyar da zaki hana Yaa Sheikh ya auri Zahrah, idan
ba haka ba kina kallo zai haɗa shimfiɗa da ita"
Ta sauke numfashi ta ce
"Kin san saki uku ya yi miki, ke da Yaa Sheikh har abada domin rama abin da ya yi
miki, shi ne hana shi auren Zahrah"
Halisa ta goge idanunta ta ce "Bana jin Abbana zai mini saki har uku, kuma anƙi
faɗa mini saki nawa ya yi mini"
"Kira ki tambaye shi mana?" Ta girgiza kamar Dr A'isha na gabanta.
Jin tayi shiru ya sa Dr A'isha ta ce "Ko ki je inda yake" sai a lokacin ta ce
"Ya yi tafiya"
"Zuwa ina? Yaushe zai dawo?" Cewar Dr A'isha.
A raunace wasu hawayen na biyu mata zuwa saman kuncinta ta ce
"Ban sani ba, bani da labarin yaushe zai dawo"
Dr A'isha tayi murmushi Idanunta akan mijinta wanda ya shigo daga masallaci kallo
ɗaya tayi masa ta ɗauke kai.
A hankali ta ce "Ask Abba Hakimi, you'll get the information Catch you later" tai
hanging up na kiran. Idanunta kan waya
Abubakar ya ce
"Sweetheart waya da Subhi yau babu ko azkar?" Ta yi masa kai ka ɗauka bada ita yake
ba.
Ya ƙara cewa "Dr na"
"Abubakar" ya buɗe baki da hanci yana kallonta ɗauke da mamakin yadda ta kira sunan
na shi babu ko risinawa ta ce "Dr kin san me ki ke cewa?" Ta ɗago idanunta fes akan
shi ta ce.
"Nasan kana da labarin ban taɓa yin hauka ba ko?" Ya jinjina mata kai ya ce "Elxty,
The way you called my name surprised me"
"To, Allahamdulillah tunda sunanka ne Abubakar ɗin" ya ce
"Meke damunki ne Dr?"
Idanunta ya sauya kala ta ce "Kai ne damuwata Abubakar, domin ka hana ni abin da
nake buƙata tsayin shekaru bayan a koda yaushe ina iya mutuwa,ko kafi so na mutum
ban bar masu yi mini addu'a ba? Burinka kenan nasan cewa kai ne baka haihuwa fa"
Da damuwa ya ce
"Ina tauhidinki ya tafi A'isha? Ni zan baki haihuwa?" Ta ce
"In a capital letters YES! ka duba Halisa matar malam, shekaru nawa na mata?
Gabaɗaya yaushe sukai aure amma yanzu cike ne da ita haihuwa take shirin yi, ni
kuma ina zaune a tutar babu"
Ya kai hannu zai riƙe ta domin wallahi gani yake kamar wacce Aljanu suka shafa ko
wacce kwakwalwarta ta taɓo
"Ras nake Abubakar, ina son faɗa maka cewa na gaji ne kawai I'm tired"
"Tired of what, Dr?"
A fusace cike da kallon wulaƙanci ta ce
"Your married, na gaji, na gaji, na gaji wallahi ka sake ni, naje na auri wanda
zuciyata ta rayu da son shi, daman aurenka is my destiny i know tun ba yau ba"
Ya dafe kai ya ce
"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, ni ki ke faɗawa haka Dr? Kin san abin da
kalamanki zasu iya jefani? Kin san tasirunsu cikin zuciyata, kin san son da nake
miki,
Kada kiyi amfani da jarabtar da muka tsinci kanmu ki cutar da rayuwata, haihuwa da
rashinta daga Allah suke, ta yiwu yaran ba alheri bane a garemu shi ya sa Ubangiji
bai azurtamu da su ba, shi da kan shi yana cewa yana jin tsananin kunyar wanda bai
azurta su da haihuwa ba, ki riƙe ƙaddara ki kuma yarda da ita shi ne cikar
imaninki"
"Shut up your mouth Abubakar Tijjani Asase, ka haifeni ne? ko malami ka zama da
zaka zauna kana faɗa mini Allah ya ce Annabi ya ce, tunaninki ni daƙiƙiyya ce ko?
Lemme repeat myself I'm tired I need my divorce paper immediately!"
"Wallahi Allah, ba zan sake ki ba, sbd ina son ki IDAN BA KE ki ɗauka rayuwata ta
zo ƙarshe ne, ki sani matata ce ke igiyar aurena ke yawo akan ki, da alama baki son
rabauta da aljanna ki koma wajan ɗan uwanki Yaa Sheikh ya yi miki darasin dake
cikin aure A'isha"
Yana kawowa nan ya fice daga cikin bedroom ɗin zuciyar shi babu daɗi.
Halisa tunda suka gama waya da Dr A'isha take zube a ƙasa tana auna maganganunta,
Hawayen fuskarta yaƙi tsayawa.
Ta miƙe da ƙyar jiki a sanyaye ta nufi Main parlour sanye da hijabi
Kitchen ta nufa aikin data tarar dai da gabanta ya faɗi, ta ta shi akan wahala
aiki koma ba sabon abu bane wajanta, tun a rugar Rome.
Zata kunce nagge duk yawansu ta tafi kiwo, ta tatsi nono ta tafi talla ta dawo tayi
aikin gidan, amma ƴan watannin da tayi tare da Abbanta Yaa Sheikh Aliyu haydar
Aliyu
Ya sangarta ta, ya bata farin ciki, ya bata tarbiyya, ya kula da ita bata aikin
fari dana baƙi sai ɗaukan darasin zazzafar soyayyar shi
da karatun da yake mata,
ita kanta bata san ya take jin kanta ba, ta manta ita ce Halisa Danejo Rome. Ta
dawo amsa sunan Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu, yanzu kuma data dawo Princess shi
ne za a haɗata da aiki har haka wanda ta mance yadda ake yin shi.
Lallai aure rahama ne, cikar ƙimar mace gidan mijinta. "Mena aikatawa kai na ni
Danejo?"
Ta yi ta surutu ita ɗaya taci kuka ta ƙoshi she just missed, amma me?
Shi ne abin da bata sani ba, tana buƙatar Mentoring kanta a cushe yake. A hankali
ta fara wanke-wanken ta gama tas, kana ta gyara kitchen ɗin.
Kasancewar an gyara wanke ta saka a inji malkaɗe ta malkaɗa. Gefe guda ta kunna gas
ta ɗora ruwan kunnun shinkafa. Ruwa ta zuba cikin pot ɗin ta kawo kwakwa wacce ta
goga ta zuba cikin ruwan, kafin ruwan ya rafasa ta koma wajan kullin ƙosan ta haɗa
shi. Ta ɗora kasko ta zuba mai daidai yadda zai sha kan ƙosan, ta zuba albasa cikin
man ta barshi ya yi zafi sosai.
Daidai lokacin ruwan data zuba ya tafaso tare da kwakwa, ta kawo haɗin kullin
shinkafar tare da muciya a nutse take zubawa tana damawa har ya yi kauri yadda take
so. Ganin bata gama ba ya sanya ta rage gudun gas ɗin man data ɗora, tana gama haɗa
kunnun shinkafar ta juye a wani babban flas. Ta goge wajan daya ɓaci ta ajjiye flas
ɗin gefe.
Ta dawo kan man data ɗora, ta haɗa ƙosan wanda ya sha kayan ƙamshi da ƙwai da
tafarnuwa.
Is taking long kafin ta gama soya ƙosan, ta ɗauki paper ta saka ƙasan flas sbd
gudun gumi ya lalata shi,ta juye tas ta ƙara ɗaukan wata paper ɗin ta rufe saman
shi. Ta ajjiye gefe guda.
Ta ta fasa tea da ginger da tafarnuwa da sauran kyan ƙamshi da barkono kaɗan. Shi
ma ta juye cikin mug ta goge wajan tas, tana gamawa ta koma Main parlour ta share
tai mopping ta kunna boner ta saka turare mai ƙamshi sosai ta fesa air-con.
Nan da nan parlourn ya ɗauki ƙamshi, a lokacin gabaɗaya Jikinta ciwo yake da ƙyar
take buɗe ido ga damuwar zuciya, ga feelings ɗin dake damunta har tsoro abin ke
bata, nan da nan za ta jita a jiƙe. Ta shirya breakfast ɗin lokacin goma saura
minti biyar cif. Mother ta fito cikin wata green ɗin atamfa ciganvi ɗinkin doguwar
riga. Tausayin Halisa ya kamata amma ta share ta ce "Sai yanzu ki ka gama?" Kallon
mother kawai tayi ta kasa cewa komai, ta ɗaga ƙafa da ƙyar ta nufi bedroom ɗinta.
ko hijabin Jikinta bata cire ba ta kwanta kan gado tare da jan pillow ta rungome,
ta rufe idanu sai suffar Yaa Sheikh ta dinga zama kamar magic a Idanunta, ta tuna
rungumar da ya yi mata ta ƙarshe sai ta matse ƙafa da ƙyar barci ya ɗauke ta.
Wajan azahar barcinta ya yi nisa taji kamar ana motsi a ɗakinta, ta kasa buɗe ido
sama-sama kuma wani ƙamshi ke ratsa hancinta yana sauka har ƙasan zuciyarta,
ƙamshin da ba zata taɓa manta irin shi ba, idan tai kamar zata farka sai a hura
mata iska taji an rungometa tsam a ƙirji, ɗumi na rasata. Ta saki jiki cikin
magagin barci ta ce
"Abbana" aka shafa kanta ana manna mata baki a wuyanta tare da sakar mata wasu
lafiyayyun kisses cikin wata murya mai rauni da shauƙi aka ce
"Madadin Abbanki ne" baki ya kai da niyyar kissing nata ta buɗe ido da sauri tana
cewa
"Modibbo!" Ɓat! Kamar gilmawar walƙiyya ya ɓaci daga cikin bedroom ɗin sai ƙamshin
turaren Roja daya bari, cike da zullumi ta miƙe tana kunna hasken ɗakin, abin
mamakin bai huce yadda ta ganta naked babu kaya ta juya zuwa kan bed taga kayanta
ya she zube a ƙasa.
Ta shiga tattaɓa Jikinta da sauri ta ɗauki hijabi ta saka har ƙasa ta saka wani
skert tai waje da gudu tana sakin ajjiyar zuciya,sam bata lura da tarin mutanan da
suke parlourn ba, kai tsaye tai wajan mother ta ce.
"Abbana ya zo?" Mother tai mata kallon baki da hankali ta ce "Waye kuma Abba?"
Halisa tai shiru. "Oh! Tsohun mijinki Yaa Sheikh wai?" Ta ɗaga kai da sauri ita
burinta ta ji ya zo ɗin.
Mother ta ce "Ikon Allah ko shirman naki har kwakwalwarki ya taɓa ne Halisa? Banda
haka ina za muga Yaa Sheikh yanzu bayan ya yi tafiya kuma ha yanzu zai dawo ba"
Halisa ta ce.
"Na ganshi yanzu a bedroom ɗina, na tabbatar shi ne, naji ƙamshin turaren shi har
na ce masa Abbana sai kuma ya gudu"
Mother ta ce "Ah, ta tabbata kin zauce tsanar shi ce tasa ki ka fara mafarki da
shi?" Ta tura baki ta ce "Koma mene ai Abbana ne, ko ya sakeni ai baby zan haifa
masa" Umma A'isha ta ce
"Haka ne, kuma babyn mai sunan Ummul da Mother" Halisa ta taɓa rai ta ce "Ai na
rasa Mother farin ciki take da Abba ya sakeni" Mother ta ƙara sawa ranta cewa
Halisa akwai wauta da ƙuruciya a kanta tana son mijinta sosai abu ne kawai ke yawo
a kanta.
"To ai ni ke nake tayawa murna, farin cikin ki shi ne nawa fa" ta juya kan Umma
A'isha ta ce
"Ke kaɗai zaki faɗa mini gasky, amma wallahi Modibbo na gani" Ummul dake zaune ita
da hajja da Dada da kuma Fulani Atine, da Fulani Balaraba sai Dr A'isha da Yaya
Halima da Maimoon da Zeefa. Ummul ta kalli Halisa ta ce "Arɗo ki ka gani, anya ta
ya ya?" Ta faɗa tana son tabbatar da abin da take zargi ta ce "Da gaske Ummul naji
ƙamshin shi" Ummul a ranta ta ce "Wato ya tuna da layyar zanar shi kenan? Yanzu
mata a suffa mai wahalar ganewa" a fili ta ce.
"Ki nutsu, gizau ne da saka abu a rai"
"Ba kiga kayan lefen Zahrah ba ne?" Sai a lokacin Halisa ta lura da wasu mayan set
ɗin akwatuna har set biyar different colours ta dinga kallon kayan, abin ka da
wacce ke shirin kaɗan ga damuwa da tai mata yawa, kowa ya juya mata baya, ga rashin
cin abinci. Ta runtse idanu bata fahimci baya tayi zata faɗi ba sai taji an kamata
an zaunar tare da bata ruwa ta gane cewa suman wani lokacin tayi, kanta a ƙasa ta
dinga goge hawaye a takaice. Daga ƙarshe ta miƙe tare da barin wajan.
Tana barin wajan Ummul ta ce "Mai ya sa kuke son wahalar da ita, why not a faɗa
mata Gasky she's still his wife, look at her condition ba ita ɗaya bace, don't
think wani abu zai iya affecting health ɗinsu?"
Mother ta ce "Wannan kada ki ji tausayinta ko kaɗan, barta kawai ba abin da zai
sameta"
Fulani Atine ta ce
"Allah sarki akwai ƙuruciya fa, na lura bata kula da Dadarta ba, balle mu" Dada tai
murmushi kawai amma yadda taga Danejo ta koma sai duk Jikinta ya yi sanyi.
"Sannu da ƙoƙari Ummul, kaya sun yi ma sha Allah Halisa anyi ƙoshi" Yaya Halima ta
ce "Wallahi sai son barka, hadda key ɗin mota, ki duba gold necklace ɗin da suke
ciki da rings, an narka dukiya" Dr A'isha ta ce "Yanzu an fasa haɗa na wajan
Barrister?" Yaya Halima ta ce "Lefen da Barrister ta haɗawa Halisa daban, wannan
kuma daga mijinta Aliyu ne kamar yadda Abba Hakimi ya buƙata" Dr A'isha ta jinjina
tana son fahimtar mai ya sa Abba Hakimi ya nuna mata an saki Halisa?...

08119237616
IDAN BA KE
₦500
[1/25, 7:24 AM] Abk: "Excuse me?" Ummul ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da nufar
bedroom ɗin da Halisa ta shiga, Dr A'isha ta bita da kallo tana son fahimtar abin
da Ummul take son yi.
Ummul na shiga ta samu Halisa zaune bakin gado Idanunta ya yi jajir hannunta ɗaya
riƙe da mararta dake mata mahaukacin ciwo,ganin Ummul ya sanya ta saki yanayin
fuskar domin Allah ya gani tana son Ummul sosai har cikin ranta.
"Ummul da gaske kayan lefen Zahrah ne?" Ummul ta ɓalle murfin gorar data shigo da
shi mai ɗan sanyi ta bata ta ce.
"Drink" ba tai mata musu ba, domin tana buƙatar ruwan sbd bushewar da maƙoshinta ya
yi. Sai da ta shanye fiye da rabi kafin ta ajjiye, ta tura mata plate ɗin wainar
fulawa wanda tasa Maimoon ta soya mata, aka saka Attahiru ciki sbd yajin da take
so, with egg aka soya da manja.
"Eat" Ummul ta furta cikin kulawa sai a lokacin ta ce "Bana jin yunwa Ummul, komai
a ƙirji yake tsaya mini"
"See you, you can do it maza cinye kiji wani abu" badan ranta ya so ba, ta fara cin
wainar fulawar ranta cinye tas ta ƙara shan watermelon juice.
Bayan ta dawo nutsuwarta Ummul ta kama hannunta ta ce
"Meke damunki Halisa? Mene a ranki share all your feelings with me kinji
daughterna"
Halisa ta kasa magana sai haɗiyar zuciya, idanunta suka ƙara rikicewa Ummul ta ƙara
yarda mugun mugun zafin zuciya ne da Halisa, taurin kai, tare da kafiya da naci.
"Talk" hawaye ya shiga silalowa Ummul ta ce "Ok don't cry my dear, take a deep
breath".
A hankali yaja numfashi kamar yadda Ummul ta ce "breathing down"
nan ma ta ƙara saukewa, kamar ƴa da uwa haka Ummul ta jata Jikinta ta rungome, ta
fashe da wani matsanancin kuka wanda bata taɓa irinsa ba, ta ƙanƙame Ummul tana
shassheƙa Jikinta na rawa, tausayinta ya kama Ummul ta rungometa very tight a
Jikinta, ta fahimci Halisa ba soyayyar miji ta rasa ba, hadda ta uwa, da wanda zai
zauna da ita yaji ainahin damuwarta, ta rasa soyayyar miji, ta rasa kulawar uwa, ga
batun kishiya, ga cikin dake Jikinta ga abubuwan da suke yawo a kanta tare da
gurɓata tunaninta.
"Ya isa daina kuka haka"
Ta ɗagota tana share mata hawayen ta ce
"Ya akai?" Cikin rawar murya ta ce "No one's love me, no one's care about me duka
sun tsaneni Ummul, ban san meke damuna ba, am a bad gril Ummul"
Ummul ta kama hannunta ta ce
"Listen, Halisa." Ta nisa kaɗan ta ce "If someone hate you tunani zaki dan me ya sa
ya tsaneki? Mene laifinki mai ki ka aikata har ya tsaneki? Idan ki ka fahimta, sai
ki fara ta yaya zaki Correcting mistakes naki? By apologies? Or by thinking your
future, idan yafiya zaki nema, at anytime zaki iya making mistakes na rayuwa wanda
kowa na yi, idan kuma zaki kalli rayuwarki ta gaba dake jiranki, to zaki fara
tunanin tayaya zaki kare kanki daga ƙara aikata wannan lafin da ki kai a baya? faɗa
mini wanne option ki ka ɗauka?"
Halisa was speechless da ƙyar ta ce "Zan yi tunanin gaba" Ummul ta ce "That's my
daughter, amma faɗa mini ke ki ka aikata har aka tsaneki ake Publishing naki haka?"
Ta marairaice ta ce "Nace bana son Abbana ya sakeni" Ummul ta girgiza kai, tana
kallon zallar ƙuruciya duk mai kunya a gaban uwa mahaifiyya ai ba zai ce baya son
ɗan data haifa ba, amma ita ko a Jikinta.
"Saboda me bakya son Abbanki?" Ta ce
"Ummul duk laifin shi ne fa, ya hanani zuwa wajan dangina, kuma ya furta kalmar
rabuwa dani ba tare da sanin yadda kalmar zatai tasiri a zuciyata, na yanke
shawarar na rama gwargwadon zafin da naji a zuciyata a kan shi, shi ne nace kawai
ya sakeni bana son shi, ban san meke damuna ba a lokacin amma komai ƙanƙantar abu
zafin shi nake ji a raina, cikin ƙaramin lokaci zuciyata take fusata, amma duk da
haka ya sakeni yaje zai auri wata to don Allah Ummul ba dole naji haushi na daina
cin abinci ba, na daina dariya da fara'a kuma kullum bana iya barci"
Ta jinjina kai irin abin ya ɓata mata ɗin nan ta ce "Duk dare abin ya yi ta yi mini
yawo a jiki, marata ta kumbura naji kamar akwai abin da nake so, naji ƙirjina yana
ta ƙaiƙayi, sai nayi kuka nake jin daɗin"
Ummul understand!
Tas ta gane me Halisa ke ji, ba Abin da take buƙata da kewa kamar mijinta ta kuma
kasa gane shi kan shi feelings ɗin.
Ta gyara zama domin Mentoring nata take son yi da kyau ta ce.
"Ki manta ni na haifi Yaa Sheikh, kiyi tunanin ni ce Dadarki shawara zan baki irin
ta ƴar da uwa"
Ta ɗaga kanta a hankali Ummul ta ce
"Kina son Aliyu ko baki son shi da gaske?" Halisa ta sunkuyar da kanta ƙasa kunya
ta kamata, tayi abubuwa da yawa wanda Idanunta ya rufe har bata san ta aikata ba,
yanzu kuma da wahala ta iya sarrafa kanta akan soyayyar tsohon mijin nata.
"Faɗi abin da yake ranki, kada kiyi wasa da damarki daughter" tai ƙasa da kanta
taƙi magana, Ummul ta miƙe tsaye ta ce "Ok fine bari naje kada muyi late zuwa Yola"
ta faɗa tana yin waje. "To ai ya sakani ko da ina son shi" ta faɗa a sanyaye
Idanunta na zubar da hawaye.
Ummul ta juya ta kalli Halisa sai ta dawo ta zauna, kafin suyi magana Dr A'isha ta
shigo ta nemi waje ta zauna, ba tare da Ummul ta kalli Dr A'isha ba ta ce "The you
need something?"
Dr A'isha ta girgiza kai ta ce "just to rest"
"Ok, am sorry zaki iya bamu waje, You can using the other room"
Rai ɓace ta miƙe ta fita, Ummul ta kalli Halisa ta ce "Ba ruwanki daya sake ki,
amsa zaki bani"
"Ina son shi, yadda nake son Abbana ko Mai martaba bana jinsa haka a raina, yanzu
ya manta dani" Ummul tai murmushi ta ce "Your father is your father, matsayin kowa
da ban, idan ki kai mini al'ƙawarin zaki sauya na miki al'ƙawarin zan saka Aliyu ya
ƙara aurenki ina nufin ya dawo dake"
"Ai wallahi nama sauya, ina son Abbana ina son zama da shi fa, da yana nan zai ta
rarrashina har nayi barci, kuma ya goya...," Ummul ta katse ta da faɗin.
"Enough, sirrine haka zaki zauna da Zahrah kina faɗa mata anything daya ke faruwa
matar malam?" Ta ɓata fuska jin sunan Zahrah ta ce
"To na daina, amma dai ai mijina ne" ba wasa a fuskar Ummul ta ce
"Haka ne, amma aure sirri ne! Ki nemi yafiyar Yaa Sheikh domin bashi kaɗai ba Allah
da mala'ikunsa suna fushi dake, kije ki zauna da abokiyar zamanki babu tashin
hankali ki nuna kema kina son mijinki duk abin da zai faruwa kada ki yarda tasan
faɗa kuke, ko kuna fushi, yanzu kije ki kira shi"
Ta marairaice ta ce
"Ai bani da number shi, ban san inda yake ba"
Ummul pretend! Ta zaro ido ta ce "Au kema? Ai babu wanda ya san duniyar da Yaa
Sheikh yake babu wanda yake da number shi, Innalillahi Allah ya sa ba wani abune ya
faru ba"
Halisa ta gigice ta miƙe zatai waje Ummul ta riƙeta sosai ta ce
"Ki bari Abba Hakimi ya dawo, nasan zaki samu wajan shi, da ga yau kada ki kuskura
ki ƙara faɗawa wani abin da yake faruwa" ta ce
"Adda A'isha kawai nake faɗawa ita take so na, take bani shawarar kada na sake bari
Abbana ya taɓa ni" murmushi kawai Ummul tayi tana ganin criminal take ganewa balle
ita da take police

Please Login or Register in order to submit comment