You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

breakfast baki ba, ita kuma tayi
tazo inda nake ta gaishe ki, kefa? Ko ina kwana babu" Ta ɗauke kai ta ce "Amma ina
da niyyar gaisheka" kafin ya yi magana Halisa ta ƙwalla masa kira ta ce "Ɗan babyna
Abbana Yaa Sheikh banga zumar ba"
Ya miƙe tsaye tare da ajjiye wayar shi ya nufi upstairs, yana zuwa ya sameta
durƙoshe gaban freezer yana zuwa ya saka ƙafa ya zungureta bata kallesa ba ta ce
"Ina take" a hankali ya ce
"Stand up" ta miƙe da ƙyar kafaɗarta ta sake tayi saurin shigewa jikinsa tana
"Wayyo Abbana" ya riƙo ƙugunta tare da binta da kallo ya ce "Zaki iya haifar yara
20 anya?" Ta zare ido ta ce "Tab ai na gama daga wannan"
"Kidding" ya furta domin shi da gaske zuri'a yake son mai yawa tunda familynsa basu
da yawa. Ta ce "Sakeni to" ya kalli ƙirjinta ya kalli bakinta ya ɗauketa ya ɗora
saman freezer kafin tayi aune ya fara bata wani cikakken sumbata yana birkitata,
yana shafa duk inda yaso baya son yi abin kunya inda yaji abu ya yi masa sai ya
fara faɗin..
"Yasubuhanallah! Ya Allah Ma sha Allah" cikin ƙaramin lokaci ya ɗorata akan network
duk tana cewa bata so suka hargitse juna, ƙarar da taji yasa tayi saurin dubawa ta
zare idanu ganin ya kusa yaga mata gaban riga. Ta sakkowa da sauri yana shirin
kamota tayi waje tana maida numfashi, a hanya sukaci karo da Zahrah da take da
wayar Yaa Sheikh da ake kira, ta bita da kallo kishi ya mamaye zuciyarta fal!
Tana shiga ta samu Yaa Sheikh ya kifa kansa da jikin freezer ta ce "Ana kira" yana
yin magana zai fallasa halin da yake ciki, ya miƙe tare da juya mata baya "Are you
already?" Ta faɗa tana shirin dawowa gabansa ya yi saurin ɗaga Jallabiyar shi yana
shigewa bathroom.... Misalin 5 na yamma motar Yaa Sheikh tayi parking a harabar
gidan Abba Hakimi, ya fito yana gyara zaman babbar rigar jikinsa, Halisa ta buɗe
ƙofa ta fito sanye cikin duguwar riga kamar kullum ta zumbula hijab, ga liƙab a
fuska hadda safar hannu, tana fitowa ta ɗage liƙab ɗin tana haɗe fuska tare da tura
baki ya yi murmushi mai sauti cikin kamala ya ce
"Yanzu ki ka amsa sunan Matar Malam" Tayi gaba sbd haushin hijabin take ji ga cikin
daya fara takura ta, duk ta damu kanta ya kuma ƙara fuskarta ƙiba tayi wata ƙatuwa,
ita ta fara shiga cikin gidan bakinta ɗauke da sallama, Abba Hakimi da shigowar shi
kenan ya ce "A'a wa nake gani kamar matar?" Ta nemi waje kusa da shi ta zauna ta ce
"Ni ce Jon wuro ina yini" ya dinga ya ce "Ma sha Allah,sannu kinji Allah ya bada
lafiya" Umma A'isha ta ce
"A'a tashi daga nan kada ki danne mini miji, jibi yadda ki ka zama narkekiyya ni
ƴar nan" Ta juya tana amsa sallamar Yaa Sheikh ya zauna saman kujera cikin tarin
nutsuwar nan na shi ya gaida su. Umma A'isha ta ce "Me kake bata ne? Wannan ƙibar
ai ta shige ta hankali" Halisa ta ce "Soyayya yake bani, ke kam matar nan mene
damuwarki da ƙiba ta ne?" Abba Hakimi ya ce
"Kishi take baki da ita" Mother ta fito ita da Dr A'isha cikin farin ciki ta ce
"Oyoyo ga Daughter ma sha Allah, aure ya karɓe ki" ta zauna Halisa ta gaida ita ta
ce
"Mother wai baki koma gidan Father bane?" Kai tsaye ta ce "Eh, Aku"
Tayi murmushi kawai ta ce "Allah sarki Farther tausayi kuke bani ne" Dr A'isha tayi
mmkin yadda Halisa taƙi ko kallonta balle ta gaisheta.
Abba Hakimi ya ce
"A'isha ta samu matsala da mijinta, harta dawo gida" Ya juya ya kalleta fuska haɗe
ya ce
"Ɗauki tarkacanki ki koma" cewar Yaa Sheikh. Ta ɓata fuska amma sosai taji daɗin
jin muryarsa ya buga mata wata gigitacciyar tsawa ya ce "Out immediately"
Ta fashe da kuka sosai tare da jan mayafi tayi waje. "Me ya sa?"
Yaa Sheikh ya kalli Abba Hakimi rai ɓace ya ce
"Shirme tayi, bayan ita ce bata haihuwa ya rufa mata asiri...

08119237616
[2/9, 7:03 PM] Abk: Duka suka bishi da kallo, Mother ta ce "Idan har haka Dr A'isha
ta yaudari kanta" Abba Hakimi ya kasa magana, sbd a iya saninsu babu wata hujja
data nuna cewa Dr A'isha ce bata haihuwa, a kullum mijinta take nunawa matsayin
wanda ke kawo naƙasu kuma likitoci sun ƙara tabbatar da hakan. "Amma a ko wanne
lokaci Likitoci sune suke bada tabbaci akan mijinta shi ne baya haihuwa, ya akai
reshe ya juye zuwa mujiya?"
Umma A'isha ta ƙare tana kallon Yaa Sheikh da alama suna jiran su ji ta bakinsa ne
kuma yaja baki ya rufe yaƙi cewa komai, suna da tabbacin kuma ba zai ce komai ɗin
ba, na bayan ma daya furta ta kaishi ƙarshe ne.
Halisa ta kalli Mother ta ce "Ni dai wallahi yunwa na keji" sai a lokacin Yaa
Sheikh ya ɗaga fararen idanunsa tare da kallonta, abincin da taci kafin su taho har
mamaki yake, amma yanzu har tana neman wani?.
Mother ta ce "Shi yasa gaki nan kamar an zuba yis tubarkallah, me zaki ci" Halisa
ta sakko ƙasan carpet tana miƙar da ƙafarta wacce ta kumbura, a nutse ba tare da
kowa ya lura ba ya dinga kallon ƙafar dole akwai dalilin kumburin. Ta buɗe baki
cikin takurawa irin ta masu juna biyu ta ce
"Kawai ni duk abinda kuke da shi a bani zanci"
Umma A'isha ta kada baki cikin zulaya ta ce
"Bafa Abbanki Yaa Sheikh ke bamu kuɗin cefane ba" kamar jira take ta bata martani
da
"Mijina bashi da rowa, idan ku kai mini rowa na haifi ɗana haka zaku haɗu da shi"
"Da waye zamu haɗu?" Umma A'isha ta sake faɗa, domin Halisa jikar ta ce shi ya sa
bata damuwa da sakin zan can nata. "Gwarzon mijina ba irin tsohu na kujera" Sai a
lokacin Mother ta sake cewa
"Yanzu kuma kan Ubana kika dawo" Ta juya kan Yaa Sheikh ta ce
"Malam ka ɗauke matarka duk ta Ishemu" Yaa Sheikh ya ɗan faɗaɗa fuskarsa yana mai
yin baya kaɗan ya ce
"Wajan Ummul zamu, taci a can" Mother ta riƙe baki ta ce "Kana son faɗa mana Ummul
tafi kula maka da Matarka ko?" Ya miƙe tsaye yana shafa fuska zuwa gemunsa, Halisa
ta kama jikin kujera ta miƙe tana faɗin "Ai wallahi tafi so na, shi ya sa nake son
ɗanta kamar hauka I love you Abbana so much love" tuni ya yi waje ta zura hijabi
tana cewa
"Kuma ba zan dawo ba sai na haihu" Umma A'isha ta kada baki ta ce
"Allah ya raba lafiya, mu ai haka muke so" Abba Hakimi da addu'ar fatan alheri da
samun farin ciki na har abada ya bisu, Halisa macace tana son Abbanta bayan kallon
miji da take masa, tana masa kallon komai nata shi ya sanya bata riƙe kanta akan
soyayyar shi, tana da kaifin baki kamar reza tunaninta kullum kaifafa yak. Yaa
Sheikh yana riƙe kansa sbd bai saba ba, kuma halinsa ne haka baya iya bayyana yadda
yake ji sai dai ya nuna shi a aikace, jajir tacce ne, ya gode Allah da son da ya
kewa Halisa bai rufe masa idanu ya kasa nuna mata kuskurenta a duk sanda tayi ba
daidai ba.
Yaa Sheikh na fita ya tsaya jingine da jikin motar shi yana shaƙar iskar dake
wajan, tafiya yake son yi mai muhimmanci amma baya son barin baya da ƙura, Halisa
nada ciki tana tsananin buƙatarsa Zahrah na cikin damuwa da muradin jinsa a
jikinta, ya kuma abinda ke faruwa babu wata cikakkiyar fahimta da fuskantar juna
tsakanin matan nashi guda biyu! Laifin waye? Nasa? Ko Halisa da take ƙarama kuma
uwar gida? Ko kuma Zahrah mai zuwan yanzu data kasance Amarya kuma gaba da Halisa a
shekaru.
Horn ɗin mota ya dawo da shi cikin tunaninsa ya ware idanun yaci karo da motar
Father dake shigowa cikin gidan lokacin kuma Halisa ta fito hannunta riƙe da jakar
da Mother ta bata, Yaa Sheikh ya ɗauke idanu yana daidaita kansa da kyau tare da
juyawa ya miƙawa Halisa hannu ta kama ya dawo da ita kusa da shi yana amsar liƙab
ɗin hannunta zai saka mata ta ce
"Modibbo ka barni kamar zan faɗi nake ji" ya riƙeta da sosai ya ɗaura mata daidai
kunnenta cikin lallashi ya ce
"Dole ki saba Zawja"
Mother ta ce "Kinga na manta na baki wannan....," Maganarta ya tsaya lokacin da
sukai idanu biyu da Father ya fito daga mota shi da Maimoon, Auta sama sai Zeefa da
kuma Jaddada. aka shiga kallon kallo, Father ya yi baƙi ya lalace ya fita
hayyacinsa kamar ba mijin nan nata ɗan gayo ba, Jadda baki ya mutu sbd halin da ɗan
ta ke ciki, babu jimawa kuma wata motar ta sake shigowa Uncle Haroon da Uncle
Bashir ne a ciki. Yaa Sheikh ya juya zai shiga mota Uncle Haroon ya ce
"Malam Aliyu ai da ka tsaya ko?" Ya saki hannu motar tare da harɗe hannunsa yana
rufe idanu. Mother ta kalli Maimoon da Idanunta ya yi jajir sosai, ta ce.
"Are you sick?" Maimoon ta kasa magana ta fashe da kuka tana zubewa a ƙasa tare da
riƙe ƙafar Mother, Zeefa da Auta Fattoumah ma sukai elxty what Maimoon did.
Kuka suke sosai gwanin ban tausayi, a raunace Father ma ya tsuguna ya ce "Maryama
na sani, wallahi na sani kuma hakkinki dana Yaa Sheikh ke bibiyar rayuwata, ban
cancanci ki tausayi mini ba idan nayi kamar na haƙura dake sai naji babu wacce nake
buƙata a cikin rayuwata sai ke ɗin nan, wallahi Barrister IDAN BA KE na tabbatar
rayuwata zata iya salwanta, babbar isharar da Ubangiji ya nuna mini yadda ƴata ga
cikina Fattoumah take cewa ta tsaneni, wacce kalar jarrabawa ce wannan" Ya fashe da
kuka ganin yadda Mahaifinsu ke kuka ya sanya gabaɗaya ya ran suka sake fashewa da
kuka sosai. Ya ƙara riƙe ƙafarta ya ce
"I made a mistake, a mistake I can't fix,But let's take this as the determination
of the existence of Muhammad,
Destiny is the cause, be patient and forgive me for the blessings of God and our
children"
Tausayi ya kama Mother irin tausayin _Mata zuwa ga mijinta_
Uwa uba yaranta da rayuwarsu ta fara lalacewa. Jadda ta matse hawaye ta ce "Harfa
cewa nayi zan ɗaga mishi nono, gashi tun ban ɗaga ba rayuwarsa tana gantali
tsakanin duniya da lahira, ni dai an fitar mini zakka a cikin yarana naga Nahwu
naga aya akan Aliyu, amma hannunka ba zai taɓa ruɓewa ka yanke ka yar ba, kiji
tausayinsa ko ɗan mitsitsi ne ki yafe masa kana ki koma gidansa ku rungumi yaranku"
ta kece da kuka sosai ta ce
"Wallahi gorin duniya nake jiye musu, a dinga nuna su da baki ana babansu ya yi wa
wata cikin shege harta haihuwa"
Uncle Haroon ya kada baki ya ce "Sai haƙuri fa"
"To ba ya zama dole ba? Haka fa Ubanku ya yi daman ance shi hali ɗan akene ya mutu
tare da bar masa mugun gado"
Uncle Haroon ya yi shiru
Jadda ta ce "Naga duk kun tsare ni da idanu? Ku ɗin nan Ubangiji ne ya taƙaita da
kuma ƙarfin addu'a kwarankwasa da a shegu za kuzo duniya, muta ta addu'a kullum ina
kuka cikin dare sbd Ubangiji yafi duba zuciyarta har ya shiryu, shi ya sa duk
abinda zaka aikata a duniya ka tuna cewa zaka haifa, idan baka haifa ba za'a haifa
maka, gado kuma jini yake bi gashi nan Ali ya kwashe Iskancin da ubanku ya yi"
"Yanzu ai ba wannan maganar ake ba"
Ta kalli Uncle Bashir ta ce "To ita nayi niyya babu ruwanka dani" Engineer Aliyu
dai yana tsugune ya ƙara cewa "Ki rungumi ƙaddara ki dawo gareni don Allah, wallahi
wallahi Ina son ki IDAN BA KE I can't be..."
"Ya Isa, Allah ya yafe mana baki ɗaya" cewar Mother. Ta ɗago Auta Fattoumah ta
rungome Idanunta ya yi jajir, Jadda ta ce "A'a bana son mugun abu irin naku na
lauyuyi cewa zaki na yafe maka Ali kuma zan koma gidanka" kai tsaye ta ce
"Zan koma Albarkacin yarana" Father ya saki Ajjiyar zuciya. Zeefa ta ce "Father ka
tashi Mother ta yafe maka" ya miƙe ya dubi Yaa Sheikh ya ce "Ka yafe mini kai ma
Aliyu don Allah" Yaa Sheikh ya jinjina kansa kawai yana buɗe ƙofa zai shiga mota.
Jadda ta zabga Salati ta ce "Muhammadur Rasulullah s.a.w wa nake gani haka kamar
ƴar Fulani wacce aka ce ta sai da nono"
"Ni ce" Halisa ta sauke Glasses tana faɗar haka, Jadda ta ce "To baki da lafiya ne
naga kin kumbura?" Tayi shiru sai kuma ta ce "Allahamdulillah"
"A'a wallahi da sauƙi, ina lafiya a wannan ƙibar kamar anyi miki fanfo, koda yake
ai ga Malam nan yasin da ban gane shi ba, kalli yadda kumatu ya zazzago"Halisa ta
kai da su Uncle Haroon, Maimoon ta gaida Halisa. Kana Yaa Sheikh ya shiga mota tare
da yin key bakinsa ɗauke da tasbihi ya nufi hanyar zuwa wajan Ummul, yana fita
motar Umar-khan na shigowa daga wajan aiki bankin Yaa Sheikh. Driving yake a nutse
duk da bai wani saba da tuƙan na shi ba, amma ba zai jure ana driving matansa ba.
Halisa ta juya ta kalle shi ta ce
"Kayi haƙuri Habibi ƙalbi"
Ya saka hannu ya kamo nata tare da ɗora a fuskarsa, bai ce komai ba. Ta ce "Ina da
kishi bana son ko wacce ta raɓeka Habibi, amma banwa kai na adalci na amince da
ƙaddara ko zan mutu don kishi kada ka damu, ina neman alfarma ka bawa Zahrah ƴan
cinta na Matarka"
Ya sauke numfashi cikin nutsuwa ya ce
"Allhamdulillah" ta kalle shi tana jan gemu ta ce "For?" Ya sha corner ya ce "Zawja
tayi hankali" tayi kicin-kicin da fuska tana zame hannunta ta ce "Oh da mahaukaciya
ka aura" Ya juya ya kalleta sai kawai ya girgiza kai ba tare da ya ce komai ba.
Gatekeeper ya buɗe masa gate ya dinga zubawa Yaa Sheikh addu'a neman zama lafiya.
Ya shafa Aljanu sai bai ji kuɗi ba, ya amshi jakar hannunta ya buɗe ya ɗakko kuɗi
ya bashi. Jakar ya bata ta ce "Kai Habibi ka riƙe mini mana" yana riƙe hannunta
zuwa cikin gidan ya ce "Ba mijin novels bane ni"
A kusan tare muryarsu ta ratsa parlourn dattijo ya amsa shi da Hajia halisa ta
gaishe su ta ce
"Wannan tsofaffin kamar tattabaru kullum kuna tare" Dattijo ya ce
"Matar Malam gidanku" tayi dariya. Yaa Sheikh ya miƙe tare da nufar part ɗin Ummul,
ya yi sallama ta amsa tare da bashi izini tsaye ya sameta gaban wardrobe tana gyara
clothes ɗin ta, ya nufeta ta rungume shi sbd baya girma a Idanunta. *Yaa Sheikh
Aliyu haydar Aliyu* baya jin kan nashi matsayin babba a gareta.
Ya tsuguna ya gaidata ya nemi waje ya zauna, kallon da yake tayi mata ne ya sanya
ta lura akwai wani abu ta ce
"Arɗona ya akai?" A taushashe ya ce "Ki bani labarin Abbi" tayi shiru sai kuma ta
zauna ta ce
"Na faɗa maka, me kake son ji kuma" Ya kalleta ba tare daya amsa ba ta ce.
"Mahaifinka samun kamar shi za a jima, kamar yadda kake cewa Matarka *IDAN BA KE*
ba zan iya rayuwa ba, haka yake duban cikin idanuna ya ce "Ummul-khairy kina da
haƙuri, Ubangiji ya biya ki, *IDAN BA KE* zan yi rashin wani sashe daga cikin
rayuwata" tayi shiru alamar tana jin zafin abin sosai amma ta jure ta ce
"Bayan kasancewar shi Arɗon Rugar Bello, shi ɗin ma'abocin shiga jeji ne, har aka
yi rashin sa a ya faɗa gidan tururuwa, tunda daga wannan lokacin yake jinya sosai,
ya fara gane-gane amma bai faɗa mini ba, daga ƙarshe ko yana gida sai ace an ganshi
waje kaza, na share duk ban damu ba, ashe a faɗawa gidan tururuwa da ya yi, ya samu
matsala Aljanu suka ratsa jikinsa wanda lokacin daya yana iya fahimta ko jin abinda
ba ko zai ji ba, idan na damu sai ya ce meye ne ƴar matana akwai wanda zai maye
gurbinki gareni, yana nan zaki samu, wani lokacin cikin dare zai ta shi ya fita
jeji babu jimawa sai ya dawo, da safe na sake gani ya dawo mutum biyu kenan, sai ya
ce kada na wani damu, mahaifinka har magunguna yake bayarwa ya ɓoye wata laya acan
Rugar Bello ya ce kada a taɓa fito da ita sai lokacin da wani jininsa ya ɓukaci jin
wani abu daga cikin rayuwarsa" ta goge hawayen idanunta ta ce "Magana ta Gasky ban
taɓa ganin mutum kamar mahaifinka ba, nagartar shi ta kai, yana da zafi ƙwarai amma
yana da sauƙin kai baya ɗaukan duniya ta zafi, idan na kalleka sai naji kawai shi
nake gani baka ɗauki komai nawa ba, baka ari wani abu daga wajena ba amma babu
abinda ka bari na Mahaifinka everything"
Ya saka hannu ya goge mata hawayen idanunta ya ce "Allah ya yi masa rahama, ina son
Abbi kamar yadda nake son Ummul" ta ja hancinsa ta ce "ina tunanin lokaci zuwa
Rugar Bello ya yi a fito da layar a duba mene cikinta" Kafin ya yi magana suka ji
muryar Halisa Ummul ta ce "Shigo" tana shigowa ta juya zata fita ganin uwa da ɗana
zaune saman gado Yaa Sheikh sai narkewa Ummul yake. Ummul ta miƙe ta ce
"A'a dawo mana ni tashi zan yi" Halisa ta ce
"A'a daman kawai yunwa nake ji" Ummul ta kalli Yaa Sheikh ta ce
"Bata ci abinci ba kuka taho?" Yaa Sheikh ya kwanta gadon Ummul yana sauke numfashi
ya ce "Ita take cinye abincin gidan fa, ni da Fatymerh bamu da ci" Halisa ta haɗe
fuska taƙi cewa komai sbd ganin idanun Ummul, ta ce "Shige ya danna miki wannan
ƙafar bari na kawo abinci" ta fita ita kuma ta shigo bedroom ɗin tana zama ya jawo
ƙafar ya dinga danna mata, idan ya kalli ƙafar sai ya kalli fuskarta shi kaɗai ya
saki murmushi ta ce "Wai Habibi me ka kewa dariya" ya ce "Kalli hancin ki Zawja
kamar fanke, Asstagafirullah" ta ɗauki pillow ta cilla masa ya cafe ta ƙara ɗaukan
wani ta cilla masa sai kawai ta fashe da kuka ta ce "To waye ya jawo mini idan ba
kai ba" ya rungumeta bakiɗaya ya ce "Sorry zo nayi miki waƙa".... Misalin 9 na dare
ya shiga sakkowa daga kan upstairs ya nufi part ɗin Zahrah yi mata sai da safe, ya
sameta kwance Idanunta yana kallon gefe ɗaya wayarta can nesa da ita, Ya yi sallama
ta amsa a hankali tana tashi zaune ya jima tsaye yana kallonta kafin ya zauna kusa
da ita cikin taushin murya ya ce "Lafiya"
Tayi murmushi kanta ƙasa ta ce "Ya Ummul? jikin Halisa su Abba Hakimi" ya tsora
mata idanu yana son gano meke damunta, ganin yaƙi magana ta ce
"Nayi abinci ban sani ba ko zaku iya ci" nan ma bai magana ba sai can ya ce "Ina ki
ka iya?" Ta ce "Nayi searching by Google" ya jinjina kai ya ce "Come" Ta kalle shi
ta ce "Halisa" bai magana ba ya saka hannu ya jawota jikinsa ya rungometa, a
tsakanin nan ya lura Zahrah nada haƙuri, kuna da alama haƙurinta shi ne zai
taimaketa Allah baya taɓa mutum da mugwayen abubuwa dole ya baka wani abu wanda za
ai misali da shi, tabbas tana da haƙuri ya kuma ji tausayinta Halisa kuma zafi
gareta ta iya masifa amma tana da saurin yafiya. Ya ƙara rungometa jin ta sauke
numfashi a kunnenta ya ce "Fatymerh Zahrah" tayi murmushi sai taga bata damu ta
neman komai wajansa ba, a karo na farko wani abu mai kama da SO ya gilma a
zuciyarsa game da ita ɗin. Ya ɗago kanta duk ta rame amma tana da kyau sosai itama
babu zato taji ya ce...
[2/10, 1:34 PM] Abk: *_Arewabooks@Nimcyluv75_*
Ransa ya ji ya ɓaci for no reason ya sauketa daga jikinsa yana miƙewa tsaye
hannunsa zube cikin aljihu, slowly ya sauke numfashi trying to control his anger,
cikin nutsuwar nan tasa mai jan hankalin mutane gare shi ya shafa kai a hankali ya
ce.
"Da kin huta, munci abinci" tayi murmushi ta ce "To babu damuwa sai a zubar, daman
ba lallai ku iya ci ba" bai kalleta ba ya nufi waje yana faɗin.
"Ba kyau albazaranci, ki fito da abinci za a bayar" kai tsaye ya buɗe ƙofa ya yi
waje, not too long ya dawo ya sameta a parlour hannunta riƙe da warmer ta miƙa masa
ya amsa tare da sake fita, ta na nan tsaye ya ƙara dawowa ya saka key ya rufe
gidan.
Tayi ta kallonsa jin kamar idanu na yawo a kansa, gently ya juya yana zuba mata
idanunsa da yake rufewa sbd tsananin gajiya da son yaji ya samu kansa cikin hutu ko
ya yi barci ishasshe. "Need something?" Ta yi ƙasa da kai sbd kwarjinin da ya yi
mata, yau ɗin sai ta ganshi yafi kullum cikar zati ta ce
"Karatun? Ina nufin wankan da kai magana" ya ƙarasa kamar zai tsaya inda take sai
ya dubeta da kyau cikin kulawa ya ce "Zuwa safe, ki kula"
"Okey good night sweetheart" tayi part ɗinta, shi kuma ya yi addu'a ya shiga tofawa
a ko wanne lungu na parlourn, kafin ya kashe hasken ɗakin.
Direct wajanta ya nufa, tun tuni zuciya da gangar jikinsa ke jansa zuwa gare ta,
ƙofar a buɗe take ya buɗe bata parlour ya shige bedroom bakinsa ɗauke da sallama
cikin sanyin murya.
"Wasalamu Alaika Yaa Sheikh" ta faɗa tana miƙewa da ƙyar frm head to toe yake binta
da kallo. "Me ciki"
Ya faɗa cikin sigar wasa ta ɓata fuska ta ce "Ai dai daga wannan Shikenan, matarka
ta haifa maka" Ya saka hannu ya ɗagata yana murmushi ba sosai ba ya ɗorata a gadon
ya ce "Lallai yarinya"
Ta ce "Abba"
Ya kalleta bai amsa ba ta ce "Me ya sa ka ke son ce mini yarinyar bayan kasan yanzu
nima uwa zan zama"
Sunna ne zama da matarka kayi hira koda baka da ra'ayi ko baka da surutu hakan yasa
ya ce "A sbd ke yarinyar ce" ta ɓata fuska sosai ganin haka ya lumshe idanunsa ta
ce "Tashi ni yau na yafe kowa ya kwana a bedroom ɗin shi, wlh takura ni ka ke Abba"
Ya maƙale kafaɗa yana shafa sumar kansa tare da kwanciya saman cinyar ta ya ce
"Ni ba inda zani kawai ki barni ina nan, ina gadinki da killata kuma sannan, na
baki kula idan akwai buƙata kenan" ta saki baki jin babban malami kamar Yaa Sheikh
yana zage yana rera mata waƙa kafin ta ce komai ya riƙe kumatunta yana girgizawa ya
ce
"Ko na tafi sai na dawo, sadakin ki sai na kawo zuciya ya nai mini zillo....," Ta
tuntsire da dry sosai ta ce "Wow What a nice voice, Habibi kafi mawaƙin murya mai
daɗi" bai kulata ba ta ce "Daman ka iya waƙa? Malami guda?" A taƙaice ya ce
"Malami Sahabi ne? Ba gashi kin yi dry ba"
"Don Allah sake mini kaji." Ya miƙe zaune ya ɗauki ƙafarta ya ɗora saman cinyarsa
ya shiga danna mata, yana tsananin jin tausayin mace mai ciki, bare Ƴar fillonsa
kuma gudan jininsa.
"Tab Yaa Sheikh da waƙa!" Ya kame kansa da kyau ya ce "Ki kula, kada a barbaɗi baki
mara saiti"
"An gama jarumin, gwarzona mijina aljannata kuma ubana duniyata, I love you so much
Modibbona" ya girgiza kai kawai. Ta ƙara cewa
"Ina son ka" yaji kalmar har ƙasan zuciyar shi, tsigar jikinsa ta tashi wani abu na
fisgar shi musamman da cikin Jikinta ya ƙara sanyawa ta dawo kamar ba ita ba,
jikinsa ya saki ya yi baya ya kwanta itama ta kwanta tana ɗora kanta a ƙirjinsa ta
danne masa ƙafa da ƙafarta ta ce "Yau ba darasi ne?" A hankali ya ce "Ayu ki ka
maidani?" Taja hancinsa ta ce "Kawai na san ɗan Ummul da zalama akan darasin auren,
baka da haƙuri" neman magana take da abinda za a fara yi masa surutu akai har ya yi
shiru sai ya ce
"To nace ki huta yau" Ta ce "Ni kuma ina buƙatar ka yau ɗin nan yanzu ma" Mamakin
ƴar rainonsa ya gama cika shi ba ko wacce mace ke tarar mijinta kai tsaye ta ce
tana buƙatar shi ba, sbd jan aji da iyayi irin na mata, bayan aure zama ne na
dindindin, a koda yaushe miji yana cewa yana buƙatar matarsa rana ɗaya zaki iya
warewa ki nemasa koda shi ɗin bai nema ba, hakan zai sanya ya ƙara jin son matarsa
ƙwarai da gaske a ran shi.
"Baki jin kunya?" Tayi fari da fararen idanunta ta ce "Mene abin kunya, kai da ka
ke nema kunya kaji? Kullum kazo da ƴar murya, sai ni zanji nauyi? Kenan na cutar da
kai na ko bayan kai mijina ne ni kuma matarka ce" ya fahimci dai shi ɗin take
buƙata, daman shima tausayinta ya keji nan da nan ya farke rigar barci tare da
cilli da ita, wannan lokacin Halisa ta nunawa *Yana Sheikh* Abbanta ita ma macace
ta san kan duniya, ta shayar da shi mamaki yana riƙe kansa amma sai da taso sashi
yin abin kunya da zarar yaji bakinsa ya buɗe zai ce "Yasubuhanallah Allahu Akbar".
Bayan komai ya daidaita ya rungumeta ya ce "Allah ya yi miki Albarka".
Da Subhi kusan tare suka tashi ya yi alwala ya sanya Arabian jallabiya da farar
hula kansa, abin mamaki yana zuwa ya samu Zahrah zaune saman ladduma tana kallon
sama, suna haɗa idanu ya jinjina mata kai tare da rufe ƙofar ya nufi masjid.
Misalin 11:00 Zahrah ta fito kusan a tare kuma

Please Login or Register in order to submit comment