You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta" Uncle Haroon ya ce "I'll do the same thing har sai ka ban amsa,
kasan da cikin Zahrah" Yaa Sheikh ya ce. "Eh" gabaɗaya suka kalli Yaa Sheikh Father
ya ɗaga hannu zai ɗauke Yaa Sheikh da mari daga bakin ƙofa aka ce.
"Kada ka kuskura hannunka ya sauka akan ɗana Engineer Aliyu" suka kalli bakin ƙofar
zumbur Mother ta miƙe tsaye tana nuna matar da hannun ƙirjinta na ɗagawa kamar zata
shiɗe ta ce
"Ummul-khairy!" Ummul tai murmushi hannunta riƙe da key ɗin mota, Abba Hakimi ya
kalli Ummul da kyau kaifi ya ce. "Ɗanki kuma?" Ta ƙarasa shigowa ta nemi waje ta
zauna ta ce.
"Na katse muku hanzari ko? Ku gama sai muyi magana daka baya" Father ya ce.
"Ni da ɗan dana haifa a cikina za kice ɗan ki?" Ummul ta girgiza kai kawai ta juya
kan Zahrah ta ce.
"Kin tuna magana ta? The day you slapped me, you insulted Aliyu's grandfather, nace
zan nuna miki ikona a lokacin da ki ka san wacece ni, In sha idan harni na haifi
Arɗo a yau zan baki divorce paper ya zauna da zaɓin zuciyar shi" Father ya miƙe
cikin faɗa da ɗaga murya ya ce.
"Ke awa? Ni nake da ikon saka Aliyu ya yi abin da nake so bake ba, ɗana ne
mallakina ne" Ummul ta juya ta kalli Mother ta ce
"Barrister Maryam me ya sa kika ɓoyewa mijinki, while I doesn't f****** care" ta
juya kan Father ta ce "Tunaninka me? Biyayya Yaa Sheikh ya yi maka, baka san cewa
kafin ya amince sai daya samu yarda ta ba? Na maka uzuri"
Abba Hakimi ya gaji da jin duk wannan maganganun ya ce.
"Zahrah ɗan waye a hannunki" cikin kuka ta ce "Yaa Sheikh" Jadda ta miƙe tare da
dungure kan Zahrah ta ce.
"Annamimiyya to Allah ya isan malam Alkur'an"
"Aliyu? Kin tabbatar ɗan Aliyu ne?" Ta jinjina kai ya ce "Ya akai kuma kika san
Aliyu bai da lafiya? Kuma yakai ɗan ya zama na Aliyu bayan mu'amala bata taɓa haɗa
ku ba" ta fashe da kuka sosai ta ce. "Don Allah Abba kayi mini alfarma idan na faɗa
maka gaskiya ba zaka bar Yaa Sheikh ya sakeni ba, don Allah Abba wallahi zan iya
mutuwa idan babu Aliyu nayi ladama" ya jinjina kai ya ce "Inaji" ta share idanuna
ta ce.
"Ba ɗan shi bane, lokacin da mukai aure ina da cikin wata huɗu" Jadda ta hangame
baki ta kasa cewa komai. Ta ɗora da faɗin. "Nayi ƙoƙarin ganin na samu mu'amala da
Yaa Sheikh domin na ɗora alhakin cikin akan shi amma ya rusa duk wata ƙofa, har
maganin sha'awa na zuba masa wanda na tabbatar ba zai iya jurewa ba sai ya keɓe da
mace,amma bai kulani ba, Ummul ke sanar dani ai bashi da cikakkiyar lafiyar ɗa
namiji sai na faɗawa Father" ta rushe da kuka sosai ta ce.
"Don Allah Ummul kada ki rabani da mijina don Allah Kiyi haƙuri" Ummul murmushi
kawai take. Father kunya ta mamaye shi, ya kasa haɗa idanu da kowa tashin hankalin
shi bai shige yadda Ummul ke iƙirarin Yaa Sheikh ba ɗan shi bane.
Abba Hakimi ya sauke numfashi ya ce.
"Aliyu ya akai Halisa ta zama ƙanwar El-bashir?" Yaa Sheikh ya yi shiru Ummul ta
ce.
"Bari kaga babbar hujja sai ka gasgata da idanunka" ta miƙe tare da fita, wata
iriyar zabura Mai martaba ya yi dashi da Umma A'isha lokacin da sassanyar muryarta
ta ratsa cikin parlourn....


Littafin kuɗi
₦500
08119237616
Mai son posting har weekend 1k[1/6, 7:18 PM] Abk: Ba iya su Mai martaba ba, hatta
Mother ta girgiza da ganin wacce ta shigo, wani abu yake shirin faruwa mai kama da
almara banda haka yaushe zasu ganta a daidai wannan lokacin?
Abba Hakimi ya sauke numfashi yana girgiza kansa da son tabbatar da abin da
idanunsa suke gane masa, da gaske ita ce. Har kawo lokacin Mai martaba bai gasgata
abin da ƙwayar idanunsa ke gane masa ba, ya ƙarasa gareta yana mai gyara Alkyabbar
jikinsa.
Idanu cikin idanu wato eyeballs to eyeballs.
"Fulani" Mai martaba ya furta cikin rawar murya yana riƙe hannunta, ta dai kalle
shi ta kasa cewa komai amma irin kallon da take masa yafi kama da kallon wanda ka
sani shekara da shekaru.
"Fulani ke nake gani, da gaske ke ce?" Farin cikinsa ya kasa ɓoyewa har bai san
lokacin daya rungometa ba a gaban mutanan ya ce.
"Allhamdulillah! Lallai Ubangiji ya yi gaskiya,duk wanda ya yarda da Allah to zai
isar masa, you're still alive. Zuciyata bata yaudareni ba da kullum take faɗa mini
kina raye saɓanin wasu da ki ka zama matacciya a idanunsa, Shukru ilaika Ya Allah"
Ya saketa a hankali har lokacin bata ce komai ba, kamar bata gama dawowa daidai ba,
duba da yanayin yadda take kallon mutane.
Umma A'isha ta ce
"Nana idanuna ke gane mini ikon Allah, da gaske ke ce Nana?" Gabaɗaya idanunta ya
cika da hawaye bata taɓa tunanin zata ƙara saka ƴarta a cikin idanunta ba, Wacce
ake ta magana a kanta sai binsu take da kallo zaka ɗauka bata taɓa saninsu ba sai
yanzu. "Besty"
Ta ce tana nufar inda Yaa Sheikh yake zaune shi ma yana binta da idanu, tana zuwa
ta zauna kusa da shi tana riƙe hannunsa ta ce.
"Besty where is my daughter, ina Danejona take?" Abba Hakimi ya yi murmushi mai
sauti ya ce "Idan duniya da gaske daman bai ci a manta Besty ba"
Sai a lokacin Ummul ta saki murmushi itama tana bin su da idanu kafin ta ce "Ta ya
ya zata manta wanda yake kula da ita da wanda ya reni yarinyarta?"
Uncle Haroon ya ce
"Na kasa fahimta, kuyi mini dalla-dalla, Khadijah ba cewa akai ta ɓata ba? Ina aka
sameta aure ta sake har ta samu yarinya kamar Halisa? Ya akai Yaa Sheikh ya san
inda take, kuma ya akai Aliyu ya auri Zahrah bayan yasan akwai cikin wani a
jikinta? Meye dalilin El-bashir na son kashe jininsa, Ya akai Yaa Sheikh ya zama
ɗan matar nan bayan gabaɗaya mun Shaida ɗan gidan Engineer Aliyu ne da Barrister
Maryam? A fitar da zuciyata daga cikin zullumi wallahi kai na kulle kamar wani
drama haka nake ganin abin" Ummul ta ce.
"You don't have to be worries, i think this is the right time daya dace gaskiya ta
kuri ƙarya, kowa kuma ya san abin da yake ɓoye, duk abin da zai je ya dawo ku ɗauka
tsararre ne daga Ubangiji, hukumu lillahi ya tsara komai a lokacin daya so, ya
kashe wanda ya so, ya kuma raya wanda ya so, kada muyi baƙin ciki, har abada ba zan
taɓa amsar Arɗo daga wajanku ba, ina son dai kuyi mini adalci akan abin da zan faɗa
muku" Ummul is an educated, beautiful, intelligent woman in the community.
Mother ta riƙe hannun Ummul cikin kuka ta ce
"Don Allah ki rufa mini asiri Ummul-khairy, Wallahi ina son Aliyu kada ki rabani
dashi, ina jinsa kamar ɗan dana haifa a cikina" Father baya gane karatun da ake
idan hankalin shi ya yi duba to ya tashi.
Ummul ta ce.
"Kada ki damu Barrister, kawai ina son nunawa Engineer ƙarshen shi da yake son
tirsasa Aliyu yin abin da bai niyya ba, nayi imani da Allah ko kai ne ka haifi
Aliyu to a wannan karan ba zai iya yi maka biyayya wajan sakin Halisa ba"
Tai shiru tana sauke numfashi ita kanta zuciyarta babu daɗi a hankali ta ce.
"Ka tuna lokacin da matarka ta haihu acikin asibitin Specialist Yola dake Jimeta?"
Father ya jinjina kai yana furta.
"I remember the day, we went to visit Yola"
Abba Hakimi kallon Ummul kawai yake sai yanzu ya lura gabaɗaya nutsuwarsu ɗaya da
Yaa Sheikh, har yarda take juyawa hannunta da yadda take son tankwashe ƙafa lokaci
zuwa lokaci kuma tana son girgiza kai musamman idan abu ya bata mmki, ko acikin
wayayyun mata masu tarin ilimi da wahala a samu kamar Ummul-khairy Abdullahi Abdul-
majeed.
Ummul ta miƙe tsaye sai kuma ta zauna ta ce.
"A wannan rana ni ma ina cikin Specialist Yola, lokacin ina ɗauke da cikin Aliyu
rayuwa ta mini zafi, bana da kowa mijina daya kasance Arɗo cikin Rugar Bello Allah
ya yi masa rasuwa, wanda kuma kashe shi akai akan wani cikar buri, iyayena sun yi
nesa dani, infact bana cikin Familynmu sbd fushin da mahaifinsa ya yi, baya son
Abou-Aliyu ni kuma na kafe shi nake so, ya ce naje idai auren Fulani ne zan gani,
lokacin da mukai aure da Abou-Aliyu Arɗon Rugar Bello ban sha wahala ba, mun rayu
cikin farin ciki walwala kwanciyar hankali da jin daɗi, ban taɓa ɓatan wata ba.
Rana tsaka Arɗo ya shigo gida da ciwon ciki a ranar bai kwana da rai ba, gari na
wayewa aka naɗa sabon Arɗo, a cikin satin ciki ya bayyana a jikinsa, na fara shiga
wata sabuwar rayuwa, nasha wahala da taimakon Ubangiji na raini cikin nan, ranar
haihuwa a daddafe naje asibitin Specialist Yola dake ina da file acan, aka amshe ni
ina shiga kuma aka shigo da Barrister Maryam itama tana naƙuda, mu duka mun sha
wahala mun ɗauka ba zamu kai labari ba, cikin ikon Allah Barrister Maryam ta haihu
kuma namiji amma ya zo babu rai, sakamakon duguwar naƙuda da ruwan da babyn ya sha
a ciki, tana Haihuwa ni ma na haihu, kyakkyawan jariri duk da wahalar rayuwar da
muka sha amma girman Aliyu ya bani tsoro, sumar kanshi har rufe ido take saboda
yawa, tun a lokacin sumar kan nashi kala biyu ne, nayi farin ciki amma na kasa
bayyana shi a fili, a lokacin tunanin yadda zan kula da shi kawai nake, na lumshe
jajayen idanuna zuciyata cike da zullumi a hankali na kalli Barrister Maryam na ce.
"Ina tunanin addu'a za mu yi da Ubangiji ya sauke mu lafiya, baƙin ciki bai kamace
mu ba" cikin kuka ta ce.
"Dole nayi kuka, baki san tsayin shekarun dana ɗauka ina addu'ar Ubangiji ya bani
ciki na haihu, saboda uwar mijina ta takura mini tana tunanin ni juya ce, gashi
Allah ya amshi addu'a ta kuma Ubangiji ya amshi abin dana haifa" Nayi murmushi
kawai ina sauke ajjiyar zuciya mai nauyi kafin na furta.
"Riƙe Babyna idan kina so bani naki wanda ya rasu" bisa mamakina sai naga Barrister
Maryam ta tsorata komai take tunani a lokacin ohu! Kamar na shiga ranta na ce.
"Kada kiyi kaddama, ki ɗauka ɗana Aliyu shi ne wanda zai kawo daidaito tsakanin ki
da uwar mijinki, mu duka muna cikin damuwa bani da hali bani da ikon kula da Aliyu,
bani da wadatacciyar cimar da zan samu ruwan nonon shayar da shi, wandon da zan
sakawa Aliyu bani dashi, ina da zuciyar nema da tawakkali amma a wannan karan na
gaza, na bar miki Aliyu duniya da lahira na bar miki shi, ki ɗauka shi ne ɗan da ki
ka haifa yanzu, ni kuma Ubangiji zai bani wani a lokacin da ya so" ni kai na nasan
na faɗi hakan ne, akan rashin mafitar da bani da ita, da kuma son nemawa Aliyu
kyakkyawar makoma, ilimi, nagarta, kyakkyawar tofa. Farin cikin Barrister Maryam ya
kasa ɓoyewa da sauri ta amshi Aliyu,ni kuma na ɗauki babynta, babu wanda yasan abin
nan sai mu uku, ni, ita, da kuma wacce ta amshi haihuwarmu" Ummul tai shiru tana
sauke numfashi idanunta ya yi jajir, ta ɗago kai taga kowa kallonta yake anyi shiru
ana sauraranta.
Yaa Sheikh kallon Ummul ɗinsa kawai yake wacce itama take kallon shi.
Khadijah Dada tana kusa da Yaa Sheikh taƙi matsawa, ƙuruciyar shekarun sun motsa
yadda take very close da Yaa Sheikh koda iyayenta Abba Hakimi Umma A'isha ba tayi,
sun tasu tun suna ƙanana.
Ummul ta ɗauki ruwa ta sha kafin ta ɗora da faɗin. "Ban san cewa kuskura nayi ba
wajan sadaukar da jinina ga wacce ban sani ba, kullum da soyayyar ɗana nake kwana
nake tashi, gabaɗaya jama'ar Rugar Bello sun ɗauka ɗana ya jima da rasuwa, ni kuma
nasan yana nan yana rayuwa a duniya, gidan da yake, da rayuwar da yake duk na sani"
tai shiru kafin ta ce.
"Babban kuskuren da ki kai Barrister Maryam barin address details naki a jikin
file, na amshi komai wajan Dr, ashe har photo taiwa Aliyu, ganin rayuwar da nake
ciki ba sauyi na fara tunanin komawa gidan iyayena, senato Abdullahi Abdul-majeed,
a lokacin ya sauka kan mulki, ban sha wahala ba, domin iyayena suna bala'in so na,
na tattara komai nawa na fara neman aikin police na samu, lokacin nasan halin da
Aliyu yake ciki, shekarar farko ta zaman Aliyu a Madina a shekarar nima na sauka na
haɗa plan da komai, naje masa matsayin ƴar aiki ya kuma ɗauke ni, shi kaɗai yake
rayuwa Umar-khan ke musu girki da komai, a zahiri plan ɗin El-bashir ne zuwana
gidan Aliyu,a baɗini kuma nawa plan ɗin ne domin na samu connection da ɗana, tun
kafin bayyanar komai haka kurum Aliyu zai sakani a gaba da kallo, sai nace masa
yaya? Sai kawai ya miƙe yabar wajan, wata rana na ce ko kana buƙatar wani abu, sai
naji ya ce.
A'a, ina ji kamar ke nake cikin barcina, nasan ƙwayar idanunki, kai tsaye na shaida
masa ni ce really mother ɗin shi biological. Ya kasa yarda ya ce mother ita ce
babar shi, nasan shi Dr ne a ɓoye a zahiri kuma Malami kuma lecture kuma kai D.N.A
test komai ya nuna ni ce babar shi, tun a lokacin Aliyu ya ɗauki ma'adanin ajjiye
sirrin shi saɓanin baya da yake da zuciyar shi, ni na bawa Aliyu shawarar kai Dada
Rugar Rome, a lokacin da akai mata kurciyya, Dada ta zauna wajan Abokin mijina,
yana da ɗa Yabi, suna zaune da matar shi Shatu, fitar Dada daga masarauta ya yi
daidai da bayyanar cikin jikinta, nan take aka Shaida mini ni kuma na faɗawa Aliyu,
duk sati sai yaje Rugar Rome, kaya kala-kala yake kaiwa Dada, lokacin da ya jima
bai ce ba, shi ne suka shiga mayuyacin hali, Aliyu da kan shi amshi haihuwar Danejo
ya gogeta da zaitun ya rungometa ya kuma raɗa mata suna Halisa ya ɗora da Danejo,
duk sanda zashi yana ɓoye kan shi baya bari aga fuskar shi, sunyi sabo da Halisa ya
goyata a bayan shi, yana mata waƙa wani lokacin ya ce _IDAN BA KE ba Aliyu_ har
takai shekaru biyar lokaci kuma Aliyu ya kwanta ciwo na tsayin shekaru, daga nan ne
bai ƙara waiwayar Rugar Rome ba, sai lokacin da za ai masa aure da Zahrah, rigima
sosai ya yi mini akan baya so, shi fa Halisa kawai zai rayu, na rasa soyayyar da
Aliyu ke mata,amma hakan baya rasa nasaba da soyayyar da ya kewa Khadijah, ba iya
Halisa ba son da Aliyu ya kewa El-bashir ya ɓaci, duk abin da El-bashir ke masa ya
sani, amma ya ce ba zai taɓa cin mutuncin jinin Besty ba"
Tai shiru tana ƙara ɗaukan ruwa ta sha kafin ta ce. "Auren Halisa da Yaa Sheikh ba
tsautsayi bane, everything that happens is a plan, Aliyu planned how to marry his
adopted daughter. I also supported him, na koma Rugar Bello da Aliyu kafin lokacin
nai musu bayani suka fahimta, nan take kuma ya maye gurbin Mahaifinsu na shugaban
Rugar, shi ne yasa a karɓe Naggen su Halisa daga wajan shugaban Rugar Rome, wannan
shi ne" jikin kowa ya yi sanyi ana zaton wuta a maƙera sai gata a masaƙa.
Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh ya ce.
"Malam ya akai kasan Inda Khadijah take bayan mun wayi gari ba ita cikin
Masarauta?" Kamar Yaa Sheikh ba zai magana ba sai ya gyara rawanin kansa yana
miƙewa tare da sauya waje, so yake ya yaki ce Dada daga gare shi tunda sirika take
wajan shi, ƴarta yake aure, bayan ya zauna ya ce.
"Abba na buɗe idanu a wajan Mother, Soyayya ta gaskiya ta nuna mini, ban san ya
akai na kasance wajanka ba, amma mother ta shaida yaye aka kawo ni wajan Umma
A'isha, lokacin shekarar Besty ɗaya a duniya, mun shaƙu sosai mun taso tare komai
tare, babu abin da nake sha'awa irin yadda Abba ke karatu tare da mutane tun ina
shekara goma na sauke Alkur'ani na shaddace Hadisai, a makaranta ɓangaren Islamic
nayi na samu abin da nake so, ina gamawa na juya fannin likitanci, lokacin da Mai
martaba ya nemi auren Besty ban damu ba, lokacin data bar gidan nan a Matsayin
Matar shi, dukkan wata walwala tawa ta ɗauke sai kuma a lokacin na gane ba Soyayya
ce ya shaƙuwa ba, abin yafi kama da wanda ka ke so ka rayu da shi irin ta har abada
ɗin nan, tun a satin farko na aurenta nake yawan mafarkinta tana kuka, bata cikin
kwanciyar hankali, kai tsaye na fahimci Aljani ne a jikinta wanda da bai bayyana
kan shi ba sai yanzu, baya ƙaunar kuma ta kasance a gidan mijinta, a wannan lokacin
kuma ta samu cikin El-bashir wanda ya ɗagawa wasu jama'ar dake cikin masarauta
hankali, bayan haihuwar El-bashir aka sakawa Besty idanu, Aljanin jikinta ya takura
mata, bayan shekaru huɗu da haihuwar El-bashir na saka Almajirai na saukar
Alkur'ani suka kwana suna yi, 10 a Sakoto tayi mini nasha wahala kafin Aljanin
yabar jikinta ta samu barci, sai dai tashin da tayi ta tashi da babbar ƙaddara ta
baza tare da fita daga cikin masarautar, komai take akan idanuna cikin sauri nabi
bayanta, da ƙyar na kamata zuwa mota na samu wani gida na ajjiyeta,naci gaba da
kula da ita tsayin shekaru 3 lokacin El-bashir yana sa shekaru 7. A lokacin kuma na
mayar da ita Rugar Rome, a shekara ta 8 da haihuwar El-bashir ta haifi Halisa,
wacce take shekaru 17 yanzu El-bashir kuma 25 suna da tazarar shekara 8, nasan El-
bashir yana mini kallon wanda na kashe masa mahaifiya ko na salwanta da rayuwarta,
wanda kuma bashi da wayo hakan ta faru akwai wanda ya zauna gina shi akan tubalin
ƙiyayya dani, Auren Zahrah kuma babu shi akai na domin ba a aure da ciki, na amince
zan aureta ne sbd hankalin Father ya kwanta dani kuma nayi masa biyayya kamar yadda
Ummul ta ce, na kuma rufa mata asiri, ya akai ta samu cikin ɗan waye ban sani ba,
amma nasan tana da dalilin aure na, na kuma san duk wanda ke farautar rayuwata"
"Ikon Allah, Al-hakkumu bowayi gagara misali!" Cewar Uncle Bashir.
Engineer kunya ta kama shi, tsoro da fargaba suka wanzu a zuciyar shi, tashin
hankalin shi ɗaya kada gasky tayi halinta akan shi.
"Sannu Aliyu, Sannunka kai da mahaifiyarka bamu da baki ko kalmar gode muku, kin
cancanci ki zama uwa ta gari" Abba Hakimi ya juya kan Zahrah ya ce.
"Ina da ikon da Malam, kuma nasan mahaifiyar shi zatai mini karar haka, nayi miki
al'ƙawarin da zarar ki ka faɗa mini gasky akan wannan jaririn to lashakka Malam zai
aureki a karo na biyu" kafin Zahrah ta ce komai wayar Yaa Sheikh ta ɗauki ƙara
ganin sunan Dr ya sanya ya ɗaga kiran.
"Hello Dr Ibrahim ke magana" Yaa Sheikh ya jinjina kai Dr ya ce.
"Mrs Yaa Sheikh Aliyu haydar ta farka daga suman da tayi, akwai babbar matsala muna
nemanka yanzu" Yaa Sheikh ya miƙe tsaye yana faɗin
"Gani nan" Ummul ta kalle shi sai ba tayi magana ba, Mother ce a sanyaye ta ce
"Aliyu ya dai?" Ba tare daya kalli kowa ba ya ce.
"Matar malam" duk suka kalle shi da rashin fahimta "Wace haka?" Cewar Mother sai a
lokacin ya fahimci mai ya yi ya ce "Ta farka kuma da matsala cewar Dr i think am
going.."
Abba Hakimi ya ce.
"Ɗan da kata, ina jinki Zahrah" Cikin kuka Zahrah kamar ranta zai fita ta ɗaga
hannu tare da nuna direction ɗin da Father yake zaune ta kasa cewa komai sai kuka
take tari na sarƙe numfashinta.
"Ɗan Father ne, shi ne ya yi mini cikin na rantse da Allah Abba.....

IDAN BA KE
Isn't free book is for sale, nrml grp 500 for Special grp 1k posting har weekend.
08119237616
[1/8, 7:03 PM] Abk: Cak Yaa Sheikh ya tsaya daga tafiyar da yake, tunda ake wannan
abun bai taɓa jin maganar data buge shi irin yanzu ba, ya kasa juyawa gani yake
kamar ba gasky bane, ji yake kamar ya nutse a wajan dan kunya, babu wacce yake jin
nauyi acikin wannan al'amarin kamar Mother, Father gumi kawai ke yanko masa idan ya
miƙe sai ya koma ya zauna
"Kin san me ki ke faɗa kowa? Kalamanki sunyi tsauri, tsaurin da ba ko wanne kunne
zai iya ɗauka ba" Zahrah ta ce
"Abba ina son Yaa Sheikh, akan soyayyar shi na yanke shawarar faɗa maka gaskiya,
wallahi Father shi ne Uban jaririn nan" da ƙarfi cikin ɗaga murya Father ya ce.
"Ƙarya ki ke, munafuka Algunguma ni zaki yaudara,ina matsayin abokin uban naki? Sbd
kuka ko muryarta baya fita ta dubi Father sai ta ɗauki wayarta tare da shiga vedio
ta play akan wani vedio tare da juya screen ɗin wayar zuwa ga father,
Kasancewar suna waje ɗaya da Abba Hakimi ne yasa shima yana daga zaune yanke hango
vedion.
"Amma ba zaka ka manta da vedion nan ba ko? Shi kaɗai ya isa ya zama shaida a
gareni?"
Jikin Father rawa kawai yake da ɓari. Su biyu ne a cikin vedion a ɗakin hotel
Zahrah na zaune Engineer Aliyu wanda aka fi sani da Father tsaye yana riƙe da waya
a hannu. Zahrah ta dube shi da kyau ta ce
"Na faɗa maka ina ɗauke ciki kuma naka baka yarda ba, ga Pregnancy Test ɗin da nayi
maybe zaka fahimta daidai" Father ya kalli Zahrah kafin ya karɓi result ɗin ya duba
ya ce.
"Kin tabbatar ciki na ne Zahrah?" Ta ce "Of course YES! Kada ka manta kai ne ka
amshi virgin ɗina" Ya yi murmushi ya ce.
"Ni ɗin? ni ki ke kira na amshi Virgin naki?" Ta miƙe tsaye ta ce "Oh! Ka manta
before hakan ya kasance nayi Virginity test?"
_The only way to know whether or not someone has had sex is to ask. There are no
physical examinations or tests that can reveal whether or not a person has had sex
before. No, not even so-called “virginity tests._
Ya ce "Ban manta ba, kawai nayi mmkin yadda cikin ya shiga ne, amma ya kamata a
zubar da shi kafin kowa ya sani" ta ce "Tab wai ba, ciki ɗaya, ciki biyu, ciki uku
duk kana sani subar dashi a wannan karan ba zan yi ganganci da rayuwata ba, kuma Dr
ya tabbatar cikin ba zai fita ba ka nemi mafita" Ya sauke numfashi ya ce.
"Ok shikenan, amma waye Deen da kuke mu'amala da shi kada kiyi mini ƙarya nasan
komai kina nufin shi bai isa ya ɗora miki ciki ba, ko shi ba namiji bane?" Yana
sauke magana ta ɗora da faɗin.
"Ya isa har ya kai, ba gwanda shi ba, tsakani na da Deen ya sauke mini sha'awata,
ta hanyar romance wani abu mai kama da sex bai taɓa shiga tsakanina da shi ba"
Father ya ce.
"Ki aure shi mana" da ƙarfi ta ce "I can't, cos I don't love him anymore ba zan
aure shi ba, idan kuma kana son Ubana ya san halin da ake ciki fine, Dady ne da
laifi daya sahale maka shiga gidan shi sama taka da sunan wayewa, sai yanzu nake
jin baƙin ciki da kuma taƙacin ilimin da nayi na shige ƙa'ida gabaɗaya wayewar
gidanmu bata amfane ni da komai ba" a rikice Father ya ce.
"Calm down please Beb, yanzu me ki ke so ayi?" Ta ce. "I want to marry your son
Aliyu" a firgice Father ya ce. "Kin san me ki k cewa, Aliyu fa? Kai ba zan iya ba"
ta ɗauki jaka ta ce. "Ok fine, zan sanar da Dady komai" ya yi saurin riƙota ya
rungome sosai ya ce.
"Is okey, na amince ki auri Aliyu kuma zan yi masa ta ƙarfi yadda dole sai ya
aureki, kuma ki ɗora alhakin cikin akan shi" Zahrah tai dry ta ce
"Gaskiya kai ɗan iska ne, ka ɗorawa ɗan ka cikin ka, to ɗan shi ne ko ƙanin shi?"
Father ya yi murmushi ya ce.
"I've no option, what ever yanzu muje ki ban kayan daɗi, banda ina mugun so da
ƙaunar Barrister wallahi da aurenki zan, amma inawa Barrister son da ba zan iya yi
mata kishiya ba" ta taɓa baki.
Cikin sauri Abba Hakimi ya ce. "Stop the video"
Ya faɗa yana runtse idanunsa ganin ana ƙoƙarin sake aikata zina ta vedion.
"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Uncle Haroon da Uncle Bashir suke ta
maimaitawa Jadda ta kece da kuka ta ce.
"Ashe dai ɗaga nono ya tabbata akan Ali, na haifi karuwi a cikina, na haifi ɗan
taure mai bin ƴan iskan mata, Allah ya saka mini Allah dai ya saka mini haihuwarka
da nayi, da nonona daka sha da tarbiyyar dana baka, wacce masifa ce wannan mutum
kamar wani Ayu!" Mai martaba ya yi ta jin abun banbara kwai, wai namiji da suna
Hajara, ganin abin yake kamar wani wasan kwaikwayo ko labarin littafan hausa da ake
faɗa..
"Ina jinki Zahrah"
A hankali ta ce "Tunda mukai haka da shi ya tafi ya fara neman hanyar da zai sanya
Yaa Sheikh ya aure ni, cikin haka aka samu matsalar daya sanya Yaa Sheikh dawowa
daga Madina ba shiri, lokacin da ya amince da aurena kafin ya faɗawa Dady ni ya
fara sanarwa, nasan da komai. kullum da fargabar yadda zan kasance da Yaa Sheikh, i
love him with all my heart and soul, ganin bani da mafita ya sa na nemi Deen da
ƙawata Surrayerh, ita ta bani shawarar neman yarinya...." Ta faɗa musu duk yadda
tsara plan na ɗaukan Halisa da yadda suka kai Dada asibiti, daɗin da ɗawa sun ƙara
yi mata asiri wanda ya yi tasiri

Please Login or Register in order to submit comment