You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gidansu gidan boko ne
a waye suke gaba ɗaya, hakan yasa Zahrah keta aikata alfasha hankali kwance. "Kinzo
da mota ne?" Surayyerh na miƙewa tsaye ta ce "E, kefa?" Zahrah ta ce "A'a, ba zan
iya driving ba wannan cikin duk ya sauyani muje kiyi dropping nawa gida" "ok let's
go" Fita sukai Zahrah da Surayyerh aminai ne duk faɗan da za suyi har abada babu
mai ji, su gama fushi su shirya. Mota suka shiga Surayyerh na driving Zahrah na
gefe a haka suka bar cikin Abti America.

Da idanu Dada take bin kuɗin da Danejo take bata, a sanyaye ta ce "Duk wannan?" "E,
Dadana ɗan Almajirin mai yagaggun kaya ne yace mini aradu duk kindirmo ake siya
dasu, kuɗin da yawa" Dada ta jinjina kai ba tare da tace komai domin magana bai
dameta ba, tun bayan rasuwar Baffansu Danejo ta zama shiru-shiru sanadin hakan
ciwonta ya sake yin tsamari. "Dadana nawa ce wannan?" Danejo ta tambaya tana nunawa
Dada gudar dubu ɗaya, girgiza kai Dada tai bayan ta tsurawa dubu ɗayar idanu ta ce
"Ban san sunanta ba, ki bari Hamma Yabi ya zo sai ki tambayeshi ko?" Miƙewa Danejo
tai ta ce "Bari naje wajan Shatu na tayata irga Naggenmu" fita tai a hanya taci
karo da Hamma Yabi, da sauri Hamma Yabi ya kama hannun Danejo ya shiga duba Funa,
Fobbina, Wayla, Hirna. Ma'ana Gabas, Kudu, Arewa, da Yamma, ganin ba kowa yasa
Hamma Yabi faɗin "Mun shigesu Danejo, gobe ake bikin gasar wasa da maciji, wanda
Sarkin ruga yake sawa, kuma yau za'a zaɓi wanda za'ai wasan dashi" fararen idanunta
ta juya sosai cikin rashin damuwa ta ce "Hamma mene abin damuwa, ni Dadana kawai
nakeso ta samu lafiya ina ta mafarki wani kala" girgiza kai Hamma Yabi yai kaifn ya
kama Danejo sosai ya ce "Baka iya wasa da Mashiji ba Danejo, kuma Sarkin ruga zai
iya zaɓarki matsayin wacce zatai wasan, idan baki iya ba Mashijin zai iya saranki
ki mutu murus, ko baki mutu ba idan baki iya ba Sarkin ruga zai iya korar mutum
daga cikin Rugar Rome" cike da tsoro Danejo ta zaro idanu waje ta ce "Mi boni
Hamma Yabi yaya zanyi?" "Yanzu shai mu jira muga wa za'a zaɓa, kije ki ɗauki
kindirmo mai man shanu ki bawa Dada gobe zamu koma ashibiti" kai ta ɗaga alamar to
Hamma Yabi ya nufi cikin jejin nemo wani sassaƙen magani ita kuma ta nufi wajan
garke a nan ta samu Shatu ta kama bakinta a nonon Nagge tana ta sha hankali ƙwance.
Zama tai kan wani Leggal (Icce amma kututture) samun kanta tayi da tunani wanne
kalar Mashiji za'ai wasan dashi? Meyasa idan taje Birni take ganin wasu mutanan ba
irinsu ba komai nasu daban ne, meyesa birni ta banbanta da Rugar Rome?. Ajjiyar
zuciya ta sauke tana murza yatsun hannunta da sauri takai dubanta zuwa ga ƙadamin
yatsarta idanunta ya sauka akan zoben dake maƙale da yatsar da tsananin mamaki take
kallon hannu yaushe wannan abun ya zo hannunta? Mene sunansa ita bata taɓa ganin
abu mai kama da zobe ba sai yanzu, ga wani zane a tsakiyar zoben kamar tambarin abu
amma bata san ko mene ba, ƙoƙarin zare zoben take amma ta kasa hakan yasa dole ta
hqr. Suna zaune a garken suka ji ana shelar Sarkin ruga yana neman jama'ar Rugar
Rome baki ɗaya. Da Shatu da Halisa suka kalli juna zuciyarsu cike da zullumi amma
Danejo tai ta maza ta kama hannun Shatu suka nufi wajan. A tsaye suka samu mutane
wasu na sanye da fararen kaya na Fulani wasu kuma Kuraye yawancin su gaba ɗaya
farare ne, amma sam babu cikakken addini ga rashin tsafta. Sarkin ruga ya gyara
tsaiwa yana faɗin "Kamar yadda kowa ya sani, a gobe ne zamu gabatar da gasar wasan
Mashiji, za'a zaɓi mutum ɗaya ya buga wasa da ƙaton Mashiji kamar yadda muka saba,
idan mutum ya kashe Mashiji akwai kyautar Nagge da kuma ƙwayar nono guda hamsin,
idan Mashiji ya kashe mutum Shi kenan wasa ya zo ƙarhe, idan mutum bai mutu kuma
za'a kuresa daga Rugar Rome baki ɗaya, don haka yanzu zamu fito da alƙalin wasa ya
zo ya zamu wanda za'ai wasan da shi" Shatu ta ƙankame hannun Danejo ita ko kalmar
Mashijin bata so taji an faɗa balle ta gansa a gabanta. Dajeno kam shiru tai kanta
a ƙasa tunani fal ranta domin gaba ɗaya ma hankalinta baya wajan. Alƙalin wasa ya
fara zagaye mutane har ya shige kan Danejo gama dubawa yai sannan ya gyara murya ya
ce "Mun zaɓi Halisa Dajeno Rome a matsayin wacce zata fafata da ƙaton Mashijin mu a
gobe....

#Sarautar marubuta
#True life story
[1/3, 4:48 PM] Abk: *🌈 IDAN BA KE 🌈*

Nimcyluv sarauta
*_Arewabooks@Nimcyluv_*

3.
"Na shiga uku ta ya ya zan iya wasa da maciji? Wallahi kashe ni zai yi" Danejo ta
faɗa a fili cike da tsora wanda ya sanya har ta kusan sakin fitsari gaba ɗaya ta
firgita. Shatu ta ce "Ki faɗa masa ba zaki iya ba a zaɓi wata, idan Mashijin ya
kashe ki na shiga uku na lalashe aradu" da sauri Danejo ta fito tsakiyar fili
idanunta akan Alƙalin wasan muryarta na rawa ta ce "A yi mini afuwa Alƙalin wasan
ba zan iya wasa da maciji ba aradu sarata zai yi" Alƙalin wasan ya kalli Danejo
sosai, shi ya ɗan jima bai ganta ba, ta ƙara girma da wayo sosai ta zama ƴar
budurwa irin girman ƙauyen nan dai. Sai rashin tsafta da addini dake ɗawainiyya da
ita duk da ana ƙoƙarin ganin an magance hakan a cikin Rugar Rome. Murmushi alƙalin
wasan ya sake yi cikin kulawa ya ce "Zaki iya mana? Ai Baffanki ya ƙware wajan iya
sarrafa maciji, a wasan ƙarshe kuma macijin ya zama silar mutuwarsa, ki yi wasan ko
dan ƙarasa cikawa Baffanki burinsa na zama gwarzo a Rugar Rome. Tabbas zaki iya
Halisa Dajeno Rome" girgiza kai tai da sauri idanunta cike da hawaye ta ce "Ba zan
iya wasa da maciji ba, mene ya sa sai ni? Baffana daban ni daban kalleni ƙarama ga
maza nan da yawa a zaɓi wani daga ci" Sarkin rugar yai saurin faɗin "Ke aka zaɓa,
kuma dole kiyi domin ba zamu taɓa sauya ra'ayinmu ba, ya zame miki wajibi muddin
kina cikin Rugar Rome" a tsorace Shatu ta ce "Hande en boni, yau mun shiga uku"
kasa cewa komai Danejo tai domin gani take kamar ma ta mutu ne lokaci kawai take
jira.
Da sauri ta juya idanunta cike da hawaye ta nufi cikin bukkarsu zuciyarta cike da
zullumi da kuma fargabar abin da zai je ya dawo. A haka ta shiga cikin bukkar
Idanunta akan Dada wacce take kwance cikin halin ciwo, domin a kullum ciwon nata
ƙara tsanani yake. "Dada Alƙalin wasan ya zaɓi Danejo matsayin wacce zatai wasa da
maciji a gobe" da sauri Dada tana jan numfashi ta kalli Danejo cikin damuwa ta ce
"Mene ya sa baki cewa masa ba zaki iya ba?" Shatu tai saurin faɗin "Sarkin ruga ya
ce wai dole tayi domin cika muradin Baffanmu" Dada ta miƙawa Danejo hannunta cikin
kulawa ta ce "Waye yace muku Baffanku wasan maciji shi ne burinsa?" Danejo ta kasa
magana sai ajjiyar zuciya take saukewa Shatu ce tai ƙarfin halin cewa "Sarkin ruga
ne ya faɗa" Murmushin taƙaici Dada tai bata taɓa ganin zalunci irin haka ba, ta
rasa me suka tsarewa Sarkin ruga da yake shirin ƙarar dasu ta hanyar kashesu da
maciji wanda wasu suka tabbatar macijin tsafi ne. Cikin ƙonar zuci ta ce "Baffannku
bai taɓa sha'awar yin wasa maciji ba, halima babu wannan al'adar ta wasa da maciji
a Rugar Rome, daga baya Sarkin ruga ya samar da ita, bayan ya samar da ita ya zaɓi
Baffanku matsayin wanda za'ai wasan dashi" shiru tai sbd tarin daya sarƙe mata
numfashi, da sauri Shatu ta ɗauki ruwa ta bata, numfashi ta sauke kafin ta ce "Bisa
dole Baffanku ya amince, yasha wahala kafin ya kashe macijn bayan ya samu raunuka
wanda ya sa ya kwanta jinya, da shekara ta zagayo aka ƙara zaɓar Baffanku abin
mamaki shi ne babu bambanci tsakanin macijin shekarar data shige da kuma wanda aka
fito da shi, Baffanku ya tsorata, gashi idan ya ce ba zai ba to za'a kuresa daga
Rugar Rome, tun daga wannan shekarar Baffanku ke gabatar da wasan Maciji, har zuwa
shekarar da maciji ya kashe shi wanda kuma anyi hakan ne domin aga bayansa. a ruɗe
Danejo ta ce "Kenan kashe Baffa akai Dada?" Dada ta girgiza kai ta ce "Ba zance ba,
bani da hujja akan haka koma mene hukuncin na wajan Allah".

Danejo taja numfashi cike da raunin murya na rashin sanin mafita zuciyarta cike da
tarin zullumi ta kalli Dada ta Shatu ta ce "Dada ba zan iya ba, ina jin tsoro"
"Halisa idan ba kiyi korarki za su yi daga cikin Rugar Rome, ni kuma ba zan jure
hakan ba, Ubangiji na tare dake. Dole kiyi wasan imma ki mutu ko kiyi rai Kinji
ko?" Kafin Danejo tai magana Hamma Yabi ya shigo da sauri idanunsa akan Danejo
yana faɗin "Tashi mu tafi Danejo daman nasan bayanki suke son gani kamar yadda suka
kashe Baffa" kallo Hamma Yabi Danejo tai idanunta ya kumbura sbd kuka ta ce "Hamma
ina zamu?" Muryarsa na rawa ya ɗaga ta tsaye ya ce "Zanje na ɓoyeki sai an gama
wasan zaki dawo, zan nuna ban san idan kike ba" Dada tai saurin cewa "A'a Yabi,
kada ai haka kamar Halisa tare damu, idan ta tafi to Shatu ce zata maye gurbinta
kasan haka ai" zama yai sosai ya ce "Yanzu haka zamu zauna? Ke baki da lafiya ita
kuma muna kallo maciji ya kashe ta?" "Akwai Allah" Dada ta bashi amsa tana rufe
idanunta. Halisa kasa bacci tai ga yunwa ga tsoro can cikin dare ta tuna ai ha tayi
sallar issha ba, da sauri ta fito daga bukkar gaba ɗaya rugar shiru babu kowa sai
wutar da aka kunnawa ko wanne garke dake ci hankali. Can bayan bukkarsu ta nufa tai
tsari a wajan tai alwala babu ko shafar kai ta kwararan ruwan ta dawo. Sallar ma
dungure tai Fatiha kawai ta iya cikakkiyar babu gyara. Yadda taga rana haka dare,
dab da Asuba ta nufi garke tare da tatsar nono, tana gamawa ta Ajjiye. Gari na fara
haske bayan tai sallah ta kaɗa shannun zuwa cikin jeji. Har zuwa lokacin bata da
nutsuwa ita a yanzu ba wasan majin ya dameta ba, illar rashin lafiyar Dada idan har
macijin ya kasheta waye zaici gaba da kula da Dada? Zama tai a gefen wani dutse ta
shiga rusa kuka da iya ƙarfinta.

Commissioners Quarter's
Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi,
wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka
ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka
haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta
ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan.
A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana
latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman
t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga
kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta
ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin
rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta
wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta
sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time
table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba
tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching
akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a
jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa
hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta
kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki
Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce
"Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi
kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba,
wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki
Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri
Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki
saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan
idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta
kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina
game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin
Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa,
naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi
kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo
kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya
Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai"
Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi
lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta
ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok"
cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah
yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai
saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa
suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna"
marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san
familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da
aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky
Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai
ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace
wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta
kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai
soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we
getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci
sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce
"Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh
sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni
wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya
karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu
Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina
kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah".

Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan
wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana
mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu
kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana
kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da
fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza
kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance
mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na
fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa.
Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda
yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa
ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya
wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne?
Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar
Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon
Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi
tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan
ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma
rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya,
wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai
faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince
ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa
kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka
shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da
durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce
"Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk
wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan
yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince
yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa
kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya
zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar
gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai
yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje
daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya
jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka
bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin
maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar
Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani
maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa
dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai
wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi
kan juna.


Bala'i kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu ƙari👌🏾. Muje zuwa

#Sarautar marubuta
#True life story
[1/3, 4:48 PM] Abk: *🌈 IDAN BA KE 🌈*

Nimcyluv sarauta
_*Arewabooks@Nimcyluv*_

4.
A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne
maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya
macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana
fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse
macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya
buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya
sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar
zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin.

Sarkin ruga ya kalli tarin jama'ar da suke wajan hadda Shatu da Hamma Yabi, da
sauran mutanan rugar kafin ya numfasa ya ce "Lokaci ya yi ake a kawo mana Halisa
Dajeno Rome cikin fili, domin su fafata da maziji yau ranar tace" Wani mai suna
Giɗaɗo ya rusuna tare da faɗin "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya kalli Hamma
Yabi tare da faɗin "Maza jeka kawo ɗiyar taku, tana ɓata mana lokaci" Hamma Yabi ya
ce "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi bukkarsu tun daga
nesa ya hangeta kwance a bakin bukkar inda Prince ya kwantar da ita tana barci.
Cikin sassarfa ya ƙara yana faɗin "Assha Subuhanallahi barci a ƙasa Danejo" ya faɗa
yana ɗagota tare da jijjigata sosai, da sauri ya buɗe idanunta tana zabura "Hamma
Yabi yaushe na dawo nan?" Kallonta yai ya ce "Kina nufin baki san lokacin da kika
kwanta a nan ba?" Girgiza kai tai ta ce "Aradun Allah ban shina ba, kawai naji iska
mai daɗi ta lulluɓeni wani barci yazo mini daga nan ban san komai ba" Girgiza kai
yai yana kama Hannunta ya ce "Danejo ƙurushiya, maza muje sarkin ruga na jiranmu"
dafe ƙirji tai cike da tsoro ta ce "Na shiga uku na lalashe, Kur'ani na manta yanzu
hamma yabi shikenan mutuwa zan, zan mutu na bar Dada? Zan mutu banyi karatu na zama
babbar mace ba? Don Allah kada na mutu yanzu bana son wasan nan" rirriƙeta Hamma
Yabi yai sosai ya ce "Ma zaki mutu ba Danejo, sai na kai ki burni Kinyi karatu kin
zama babbar mace abar ƙwatance, sai kin zama mace ta farko wacce zata kawo sauyi
cikin Rugar Rome, ki daina kuka kinji" kai ta ɗaga masa kafin da sauri ta ce "Kuma
zan zama wannan mutumin na jikin bango?" Zare idanu Yabi yai kafin ya ce "Wannan
gwamna ne fa" murɗa baki tai cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai irinsa nake son zama"
Yabi ya dungure mata kai ya ce "Aradu ƙarya kike, ina zaki iya yin siyasa tayaya
zaki zama gwamna daman mata na zama gwamna ne?" Banza tai masa bai ƙara ce mata
komai ba ya jata zuwa filin da za'a gabatar da wasan.

Giɗaɗo dake tsaye shi da Sarkin ruga suna jiran zuwan Hamma Yabi da Danejo ya ce
"Me ya sa ka zaɓi Danejo kasan ba zata iya wasan ba" murmushi Sarkin ruga yai kafin
ya ce "Ina son ganin bayanta ne, kuma a hankali zan ƙarar da zuri'ar Manga a cikin
Rugar nan, wannan macijin na tsafi ne hatta mutuwar Manga ni na shiryarta"... "Amma
me Manga yai maka haka?" Cewar Giɗaɗo. Sarkin ruga ya ce "Sirri ne.." kaifin su
ƙara magana Hamma Yabi ya ƙaraso hannunsa riƙe da Danejo wacce ta ƙanƙamesa sosai
jikinta na rawa da ɓari.

Alƙalin wasan ya ce "Yawwa yanzu zamu fara, Danejo ta shigo cikin fili jama'a ku
buɗe idanunku da kyau yau za kuga wasa wanda baku taɓa ganin irinsa ba" Halisa
Dajeno Rome na tsakiyar fili ko kuka ta kasa a wannan lokacin ta tsaya ne kawai
tana jiran taga ta inda mutuwa zata zo mata, domin abune mai wahalar gaske ace yau
ta rayu ko ta tsira da ranta. Sarkin ruga ya bada umarnin a fito da Macijin, da
sauri Alƙalin wasan ya nufi bukkar da macijin yake. Yana kwance sharkaf yau lamo a
ƙasa tare da yin gammo da jikinsa, wani irin zabura yai tare da fasa kansa a
lokacin da alƙalin wasa ya shigo cikin bukkar, ƙuri yai masa da idanu yana ƙare
masa kallo. Ko me ya tuna Ohhu a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar ya koma
ya kwanta, shi kansa Alƙalin wasan ya tsorata jikinsa na rawa yasa hannu ya ɗauki
Macijin da ƙyar sbd nauyin da yake da shi.

Tun da Halisa Danejo Rome ta saka idanunta akan macijin taji gabanta ya faɗi,
jikinta ya ɗauki rawa hawaye suka fara sintiri a saman Fuskarta, bata taɓa ganin
maciji mai girman wannan ba, tama rasa wacce kalar addu'a zatai duk da ba wani abu
ta iya sosai ba. Alƙalin wasan ya ajjiye macijin nesa da Halisa, aka fara kallon
kallo tsakanin Danejo da Macijin, an shafe tsayin wasu daƙiƙo aka rasa waye zai
fara kaiwa wani hari tsakanin Danejo da Maciji Prince?. Zaro idanu tai waje ganin
ya fara warware tare da yin tsayi sululuuuu kuma ya nufo inda take, tana ja baya
yana biyota har ya ƙaraso dab da ƙafarta tare da tsorawa zoben hannunta idanu. Juya
tai tana neman inda zata gudu can idanunta ya sauka akan wani ƙaton dutse. Da sauri
ta ɗauka tare da riƙewa a hannunta, ganin haka yasa Macijin bin ƙafafuwanta suuu
haka ya dinga sufa a jikinta, har ya naɗeta ciff kansa daidai Fuskarta yana tsora
mata idanu tare da kallon cikin idanunta.

Jirkinta na ɓari ta ɗaga dutsen tare da kwaɗa masa a tsakiyar kansa, wani kalar
ihun azaba macijin yai yana fasa kai kamar zai sarata, sai kuma ya saki kansa tare
da ɗorasa saman ƙirjinsa gaba ɗaya naman Macijin rawar azaba yake, kansa tuni ya
fashe ya fara zubar da jini. Ganin nasarar da Halisa Danejo Rome ta fara samu yasa
Hamma Yabi da Shatu tare da sauran jama'ar Rugar Rome suka fasa ihun murna, Sarkin
ruga da Alƙalin wasan

Please Login or Register in order to submit comment