You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

'yan k'auye Jahilci ya muku yawa babu wayewa ko kad'an a tare daku"

Kallonshi kawai take lokacin da wani hawayen ke k'ara tsiyaya a idanunta.

"Sai an zageku ku hau kuka sai kace Ku kukafi kowa hawaye,dalla matsa"
Ya fad'a yana kwantar da mamanshi sannan ya shiga motar ya jata da k'arfi.

Motar ta bi da ido wani sabbin hawayen na zuba a idonta.

Tafi taji daga bayanta a hankali ta juya hannunta rik'e da kuncinta.

"Shiyasa na biyoki dan inga me kike aikatawa nan ne gurin d'ibar ruwan ko?"

Girgiza kai tayi tana kuka tace "Aliyu wallahi taimakonsa yace nayi ma........" A d'ayan kuncin ya sake marinta sannan yasa k'afa ya tad'iyeta yana fad'in "ni zaki ha'inta?k'arya kike wallahi kuma ki dawo gidan zaki sameni"

Bai kula ba da halin da take ciki ya barta anan kwance gefen titi cikin jini.

**********

A b'angaren wannan matar kuwa sai yamma lik'is ta bud'e idonta daga baccin data samu.

Kasala kawai taji amma ciwon k'irjin da bugun zuciyar da yake damunta babu ko kad'an.

Babban abinda yafi bata mamaki shine yadda suke ta kashe kud'i daga wannan asibitin zuwa wancan amma tamkar ana k'ara mata azabar ciwo ne,sai gashi lokaci guda duk wani ciwo da take ji babu shi.

Kallon d'an nata take da yake driving tace "Muhasin mu koma wannan k'auyen"

Sai da ya juyo ya kalleta sannan ya cigaba da driving yana fad'in "momma kece kike magana haka?"

"K'warai kuwa kuma yarinyar daka mara maganin data bani shine silar warkewa ta, dan haka mu koma ka nemi yafiyarta sannan mu mata godiya"

"Momma mun kusa katsina fa,taya zamu koma wannan k'auyen sannan mu dawo mu sake d'aukar hanyar yola bayan tafiyar da mukasha tun daga Abuja pls momma kiyi hak'uri" ya fad'a,dan shi a tunaninsa maganin da tasha a Abuja ne yayi tasiri dan sam bai yarda da maganin hausa ba.

"Muhasin ina magana kana musawa?kada kaima kace kabi hanyar da 'yan uwanka suka bi karkace kaima ka fara gajiya dani"

Parking yayi sannan ya juyo ya kalleta a tsanake yace "momma taya zan gaji dake bayan ke kika kawoni duniya,bana fatan kome na zama a rayuwa ace waini na gaji dake Allah kiyaye"

"To indai ba haka bane ina son mu koma ka bata hak'uri"

"Wallahi ko mun koma ba lallai mu ganta ba,a bakin ruwa na ganta fa taje d'iba kuma ban san ko sunanta ba ta ina zan ganta tunda babu gida a wajen?"

"Amma ai a k'auyen kusa da nan take ko?"

"Momma babu tabbas amma na san ko mun koma bazamu ganta ba"

"Indai kana bin umarni na to mu koma"

_wama ya sani ko maganin asiri ne ta bata,aini ko yanzu muka had'u da yarinyarnan in dai ba a gaban momma bane saina sake mata warning kawai zata halaka uwata da maganin k'auye yadda nake tsantsaninsu amma harta d'auki abu ta bawa uwata tasha._

"Magana nake maka Muhasin" ta katse masa tunanin.










_Sadeey S Adam_✍
[9/29, 8:17 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁


_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„


```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


24

"Momma ina jinki"
"Oh shine kayi shiru?"
"A'a k'ok'arin juyawa nake"
"Cewa nayi mu tafi yolan amma fa zamu dawo neman yarinyar ka yarda?"
"Eh na yarda" ya fad'a cike da jindad'in bazasu koma ba.

********

A hankali ta bud'e idonta ta fara kallon d'akin,ta fara ware idonta tana k'arewa d'akin kallo.

Wani irin nauyi da ciwo taji kanta nayi,ta saka hannu ta dafe kan kawai taji bandage sai a lokacin ne hankalinta ya gama dawowa jikinta ta kuma tuna duk abinda ya faru.

Da sauri ta tashi zaune ta kalli drip d'in da bai gama zuba ba,yana d'isa a hankali.

_ina ne nan waye ya taimaki rayuwata?_ tayi tambayar a zuciyarta.

Shiru tana zaune a d'akin ita kad'ai ta jingina da fuskar gadon dan bama ta san wane yanayi bane safiya,rana ko dare,d'akin labuye sun rufe ko ina sai hasken fararen lights da suka haske d'akin.

Ta shafe kusan awa guda tana tunani kala-kala akan irin halin da ta tsinci kanta a yanzu.

Jin ana bud'e k'ofa ne ya saka ta k'urawa k'ofar ido,ana turo k'ofar ta kalli wanda ya shigo sai da tayi mugun zabura har ta kusa b'alle drip d'in da aka jona mata.

Murmushi kawai yayi sannan ya k'araso jikin gadon ya tsaya.

"Meya kawo ni nan?" Ta fad'a bakinta na rawa.

"Oh baki ma sani ba?" Ya bata amsa ba tare daya damu da irin tsoratar da tayi ba.

"Na shiga uku"

"Bazaki tab'a shiga uku ba indai ina raye Janan"

"Jalal ina Aliyu wallahi na san dukana zaiyi in har na koma yanzu"

"Duka kuma?" Yayi tambayar cike da mamaki.

Sai a lokacin ta san tayi katob'ara sai kuma tayi saurin cewa "zai min fad'a ne"

Murmushi ya sake yi tare da zama gefen gadon "meyasa zaki b'oye min matsalarki?ko kina gani kamar bazan iya taimakarki ba?"

"Idan kika saka wannan a ranki baki min adalci ba"

Wani gumi daya tsatssafo mata a fuska tasa hannu ta goge,hakan ne yasa ya gane cewa lallai akwai abinda ke damunta take b'oyewa.

"Meke damunki Janan?"

Idanunta tuni ya fara fitar da hawaye "dan Allah ka mayar dani gidan miji na kar in samu matsala"

Ajiyar zuciya yayi ya dafe kan shi da hannunsa yana kallon yadda take kuka tamkar yace zai yanka ta.

A sanyaye ya fara fad'in "ban tab'a tunanin cutar da wani a rayuwata ba bare ke Janan,amma yau ni ne kike buyewa damuwarki ni dama tun da naga yanayinki a skul na san akwai abinda ke damunki amma duk kanku kun b'oye min"

Hannu tasa tana goge hawaye tace "kar ka damu idan kayi addu'a ma ya wadatar amma kayi hak'uri damuwa ta tana da tarin yawa bazan iya fad'a maka ba"

"Shike nan Allah ya shige miki gaba a duk al'amuranki"

"Ameen" ta fad'a lokacin da wasu sabbin hawayen suke fita daga idonta.

Tashi yayi ya fita ya bar ta dan a tunanin sa ganinshi ne yake saka ta kuka.

Ya kwashi kusan awa d'aya yana tunanin wane irin miji Janan ta aura?wace irin wahalace ta mayar da ita haka duk sirantarta amma ta sake raguwa gashi duk ta canza kamar ba ita ba,ya rasa ta ina zai fara taimaka mata tunda bai san meke damunta ba.

Tashi yayi ya d'auki ledar da yayi mata takeaway ya kai mata,tana zauna tana kuka ko gajiya batayi a haka ya tarar da ita.

Ajjewa yayi a gabanta yace "ga abinci nan na san kina jin yunwa" da ido kawai ta bishi lokacin yana k'ok'arin fita.
"Nagode" yaji ta fad'a.
Ya d'an juyo yana murmushi yace "karki damu"

Sai da taci abinci sosai tasha yoghurt da ruwa sauran kayan kuwa bata tab'a ba.

Tayi lamo a kwance tana ta tunanin irin azabar da zata sha idan ta koma gidan Aliyu amma ta san dole ne ta koma saboda in ta zauna anan zata jawa Jalal matsala da zargi.

Jin an turo k'ofar ne yasa tayi saurin tashi zaune.

Shi da likita suka shigo ya kalli drip d'in yace "ai ya k'are har ya fara jan jininta.

Ita ma da sauri ta kalli gurin,likitan ya cire sannan ya duba ta.

Kallon Jalal yayi yace " jinin ya sauka"
"To Alhamdulillah"
"Yanzu sai dai a kula da ita tana shan magungunan akan lokacin"
"Insha Allah"

Sallama suka yi ya rakashi har mota ya tafi sannan ya dawo.

A tsaye ya ganta jikin k'ofar "lafiya?" ya tambayeta.

"Zan tafi gida"
"Gida?"
"Eh"
"A wannan daren gaskiya ki hak'ura da safe na maidaki,yanzu dare yayi sosai fa"
"A'a ni dai tafiya zanyi kawai ka barshi nagode"
"Okay Allah ya bamu alkhairi"
Jin haka ne ya saka ta saurin kallonshi tace "ka bud'e min k'ofa dan Allah"
"K'ofa a bud'e take sai dai masu gadi zance su bud'e miki daga waje"
Jikinta a sanyaye ta fita shi kuma ya bita da fad'in "ki gaida Aliyu"

Tun da ta fita a gate taji garin shiru babu kowa sai street light sai kukan karnuka da take jiyowa daga neighbors d'insa.

_a ina zan samu napep?ina da kud'i a gida idan ya kaini sai in bashi_. Ta fad'a a zuciyarta tana ta fargaba.

A haka har ta fita daga layin ta shiga wani.
A lokacin ta fara tunanin ko dai dare yayi sosai kamar yadda Jalal ya fad'a gashi babu agogonta a hannunta bata san ya akayi yayi missing ba,bare taga time.

A tunanin nan har ta isa babban titi,ta tsaya cak tana tunanin Allah yasa ta samu abin hawa.

Motocin dake wucewa akan titin jefi-jefi babu wanda ya kula da itama.

Ta d'ebi kusan minti talatin sannan wata mota tazo,har ta wuce sai kuma tayo baya,a hankali aka fara zuge glass d'in baya sannan aka kunna wutar motar.

Samari ne har su uku a bayan motar sai d'aya a gaba da kuma wanda ke driving d'in.

" 'yan mata ina zuwa?" Wani mugun fad'uwar gaba ta cigaba dayi jikinta na tsuma tace
"C....ci....cikin....gari"

'Daya ya kalli d'ayan sukayi murmushi "ki shigo sai mu rage miki hanya"

Girgiza kai tayi alamar a'a.

Bud'e k'ofar suka yi ita kuma ganin hakane yasa ta yanki layi ta shiga da gudu suka bita, ta bar layin har ta shiga wani suka rutsata.
Ganin sun finciko ta ne yasa ta k'walla k'ara,suka toshe bakinta suna janta taji an funciketa ta baya.

Suma da sauri suka saketa tare da rufe fuskarsu yanda baza'a gane su wane ba,hijabin jikinta kuwa sun yaga mata shi.

Ganin Jalal ne yasa tayi saurin rungumeshi tana kuka tace "ka taimakeni karsu lalata min mutuncina"

Shima rik'eta yayi sosai a jikinsa ganin sunyo kansa gadan-gadan suna fad'in "ka bamu ita ko mu fasa maka kai da bindiga"

Jin haka ne yasa Janan tayi saurin runtse idonta jikinta sai karkarwa yake.

Murmushi Jalal yayi ganin bindigar dake hannunsu ta wasa ce suke amfani da ita wajen tsorata mutane.

Hannu yasa ya zaro bindigarsa ya nuna musu yace "duk wadda ya cika d'an iska ya k'araso nan"

'Daya daga cikin su yayi dariya mai k'arfi yace "mu zaka yiwa barazana da bindigar wasa?lallai yau sunanka matacce"

"Wayyo Allah Mameey ki taimakeni zan mutu"ta fad'a tana kuka tare da k'ara k'ank'ame Jalal tamkar zata shiga jikinsa.

Jalal ya d'aga bindigar ya harbi sama dan su tabbatar ba bindigar wasa bace.

Wani k'ara da Janan ta saki bata sake motsawa ba.

Su kuwa tuni sun tsorata sun d'aga hannu suna fad'in "kayi mana rai yallab'ai"
"Oh ku 'yan iskan k'arya ne ashe,ku b'ace min da gani anan kafin in fasa kan naku kafin ku fasa nawa"

Da gudu suka bar gurin,ya kalleta yace "Janan tashi mu tafi sun tafi"
Jin tayi shiru ne yasa ya d'agota yaga tana neman fad'uwa.

Sai a lokacin ne taji wani abu ya tsarga jikinsa,da sauri ya karanto addu'ar neman tsari daga shad'an.

"Janan" ya kira sunanta yana sa hannunsa a hancinta dan ya tabbatar tana numfashi.

Ganin ta suma ne yasa ya d'ago ta a kafad'a ya nufi gida.

A kan gado ya direta har lokacin a sume take.

Da sauri ya nufi fridge ya d'ebo ruwa ya shafa mata a fuska.

Zubur ta mik'e tana neman gudu yayi saurin rik'e ta "Janan nine fa"

Kallonshi tayi jikinta na rawa tace "na shiga uku Jalal meke faruwa dani ne?ko dai nayiwa Allah laifi ban sani ba?"

"Ki nutsu Janan babu abinda kika ma Allah,kiyi ta istigfari kinji"

'Daga kai tayi alamar to ,ta cigaba da kuka.

"Shiyasa na hanaki tafiya kika k'i dama fa babu wanda zaki samu k'arfe 1 na dare"

Ita dai bata ce komai ba har ya gama surutansa ya tashi ya ja mata k'ofa.

Ranar bai runtsa ba dan tunanin abinda ya faru tsakaninsu kawai yake,wani sonta ne ya fara ratsa jikinsa tun da yake bai tab'a jin son wata 'ya mace ba sai a kanta.

Da sauri ya tashi yayi alwallah yana jero nafilfili tare da addu'oin kub'uta daga halaka.


_*Washe gari*_

Sai k'arfe goma yayi mata knocking sannan ya shiga,zaune ya ganta kan sallaya ta zuba uban tagumi idanunta sun kunbura sosai kana kallonta kasan bata runtsa ba.

"Kar dai ace bakiyi barci ba?"

"Ina kwana" ta fad'a a sanyaye dan ita kunyar abinda ya faru jiya take.

"Lafiya lau ya k'arfin jikin?"
"Alhamdulillah"

Ajje ledar hannunsa yayi akan gado yace "ga kaya nan ki shiga bathroom kiyi wanka sai ki saka in kin gama ina falo ki fito kiyi break na maidake gida"

"Nagode" ta sake fad'a sannan ya fita.

Bayan ta fito daga wanka ta bud'e ledar,mayuka ne masu tsada da turare a ciki sai doguwar riga blue black had'e da mayafi babba shima blue black ne.

_Allah sarki Jalal,kamar ba kaine wanda na tsana ba amma yanzu babu mai kyautata min kamarka Allah ya saka maka da alkhairi._

Bayan ta gama shiryawa ta fita falon,a zaune ta ganshi yana waya yana dariya,yana ganinta yace "bara anjima zan kiraka" ya katse wayar yana kallonta.

"Ga abinci kan dinning table"
Jikinta a sanyaye taje ta zauna,ta fara ci kawai taji ya fita a ranta tunanin yadda shari'ar Abba da Aliyu zata kaya take.

"Na gama?" ta fad'a tana mik'ewa
"Kina nufin har kin k'oshi?"
"Eh bani jin yunwa"

Bai matsa mata ba key kawai ya d'auka ya fita ta bishi.

Ita ta rik'a nuna masa hanya har suka kai k'ofar gidan.
"Anan kike rayuwa Janan?" Ya fad'a cike da mamaki.

"Eh" ta bashi amsa a tak'aice,kallonta kawai yake cike da tausayinta.

Yara duk sun rufe motar suna kallo,tana shirin fita kawai ta hangi Aliyu da Nura a can bakin wani icce suma idonsu akan motar.

Gabanta yayi mummunan fad'uwa ta kalli Yarima Jalal tace "na shiga uku kaga Aliyu can, dan Allah ka taimaka muje kayi masa bayani"

Mamakinta kawai yake yanda yaga duk tabi ta rud'e "zamuje amma fa ki sani dole ki rage damuwa da tsoro saboda lafiyarki" kai kawai ta gyad'a suka fita tare.

Kafin ma su k'arasa inda Aliyu yake tuni su sun taho.

"Daga gidan ubanwa kike?" Yayi tambayar ransa a had'e,sai a lokacin Jalal ya k'ara tsinkewa da lamarin amma da yake miskiline sai yak'i cewa komai.

"Gidan ubanwa kika kwana" ya fad'a tare da tsinka mata mari.

Da sauri Jalal ya kallesa "akan me zaka daketa ko dan kana tak'ama kana aurenta kai baka da imani ne ko bakaga ciwo ne a goshinta ba"

"Dalla Malam dakata da matata nake ba da kai ba"

"Oh mata! dan kana tak'amar matanka ne shine zaka nemi ka zubda mata mutumci,Ku dama 'yan k'auye baku iya cin arzik'i ba"

Kallonshi Aliyu yayi yace "mutuncinta wanne ne bai zube ba tunda har zata iya zuwa ta kwana a gidanka,sannan cin arzik'i kuwa ita ce tayi dan ita tace tana sona bani ba"

Ya juya ya kalleta cikin tsawa yace "har ta kai ki kwana a gidan maza sannan k'ato ya kawoki"

Girgiza kai take tana kuka,ya matso daf da ita kamar zai mata magana ya k'ara wanka mata mari a karo na biyu.

Cikin zafin nama Jalal ya d'aga hannu ya mareshi.

Aikuwa yara sai ihu suke mutane duk an firfito waje.

Ya d'aga hannu zai rama Janan tayi saurin rik'ewa,ya fuzge har sai da ta kusa fad'uwa.

Ta kalli Jalal dake tsaye cak yak'i matsawa tace "kayi hak'uri Jalal na san ni na jawo maka dan Allah ka tafi ka tafi ka bar nan p.........."

Da k'arfi taji an fuzgeta ta juya taga Umma ce.

Bata saketa ba sai a tsakar gidan.

Juyowa tayi ta kalli Ummi tace d'akko min Razer.

"Dan Allah kiyi hak'uri Umma Ku barni haka dan girman Allah" Janan ta fad'a tana kuka.

"Yau saina yanka k'afar naga da wacce zaki sake fita yawon karuwanci"

A daidai lokacin Ummi ta mik'owa Umma Razer.

"Yanka min k'afarta sosai"

Kallonta tayi kawai taji bazata iya ba. "Umma ki mata hak'uri"

"Me?"
"Umma da tausayi fa gaskiya bazan iya ba"
"Wannan yarinya baki da hali,mik'o min Razer ki kuma kawo min gishiri"

Zare ido Ummi tayi tana mamakin yadda Umma ke shirya mugunta.

"Ba magana nake miki ba"

A firgice ta ruga ta d'akko gishirin ta kawo mata.

Idon Janan a rufe tana ta kicin kicin na k'wace kanta amma yadda Umma ta matseta yasa ta kasa.

Yadda taji an yanki k'afarta tun daga babban yatsa har zuwa gwiwarta,wani azababben zafi daya tsarga mata daga babban yatsan har zuwa k'wak'walwarta ne yasa ta zunduma uban ihu,cikin zafin nama Umma ta watsa mata gishirin wanda ya saka Janan k'ara runtuma ihu tamkar zautacciya.

Ummi tayi saurin runtse ido ganin yadda jini ke zuba a k'afar.

Nura da wasu mata guda biyu tare da Asabe har rege-regen shigowa gidan su ke dan ganin abinda ke faruwa.















_Sadeey S Adam_✍
[9/29, 8:17 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁


_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


*_Wagga shafi naki ne kyauta Mom Haidar😍,ki daure ki karanta banso ki tafi strike shiyasa nasa dole Aliyu ya rangad'awa Janan saki ukuπŸ€ͺ_*


25

*inna lillahi wa inna ilaihi raji'un* shine abinda ko wannensu ke fad'a.

Wata harara Umma ta zabga musu tare da fad'in "munafukan banza kawai salatin me kuke?"

Nura ne ya kalleta yace "meya faru da ita haka Umma?"

"Kai baka ga abinda tayi ba,da namiji ta dawo gidan nan fa"

Sum-Sum ya fice ya bar gidan dan yaga ran Umma ya b'aci sosai.

Asabe da Yabi suka durk'usa gabanta har lokacin kuka take a fili yanda take jin azabar ciwon na sake shigarta.

Ummi ba shiri ta shiga d'aki, tunda take bata tab'a tausayin Janan kamar yau ba.

" 'Dagata mu tafi da ita gidanmu sai dai kome Haidar zaiyi yayi"

"A'a mu kaita chemist" Asabe tayi maganar.

"Ina mukaga wani chemist a k'auyen nan muje kawai gidan Malam Ayuba ya bata magani"

Haka kuwa sukayi suka d'agata tana kuka ta kasa ajje ko k'afar,har a lokacin jini zuba yake a k'afarta haka suka isa har gidan malamin.

Sai daya shafa mata man alayyadi a k'afar sannan yayi mata addu'oi kuma ya bata maganin da zata rik'a shafawa a gurin.

Suna fitowa daga gidan malamin cikin kuka tace "dan Allah ku kaini gidanmu"

"Ai bamu san gidanku ba Janan" Asabe tayi maganar.

Cikin kuka tace "zan nuna muku dan Allah ku muje bakin titi mu samu abin hawa"
*
Tun a k'ofar gate d'in su Yabi suka rik'a mamakin yadda Janan ta auri Aliyu bayan ta fito daga wannan tafkeken gida.

A babban falo babu kowa dan haka tace suje k'aramin falon.

Suna shiga suka tarar da Mameey da Fauziyya ne kad'ai a zaune a falon.

Da gudu fauziyya ta k'araso ta rungumeta suka fara sabon kuka.

Mameey tashi tayi ta k'araso gabanta ta rik'eta tana kallon k'afarta da har ta kumbura tayi jajir.

Gaisawa sukayi da su Asabe sannan tace su zauna.

Janan na zaune kusa da Mameey tana kuka tana fad'a mata irin azabar da ake gana mata a gidan Aliyu.

Duk kansu kuka suke hatta Asabe sai da ta koka,'yan aiki suka kawo masu ruwa da lemo.

A lokacin Fauziyya take kuka tana fad'a mata irin shari'ar da ake gudanarwa sannan Abba yace kar a fad'awa kowa har ita.

Kuka sosai Janan take gani take k'ila laifi tayiwa Allah yake jarabtarta da hakan amma wannan tsanar da Abba yayi mata tayi yawa.

Kallon Mameey tayi taga itama hawaye take,da sauri ta saka hannu tana goge mata "Mameey kiyi hak'uri karki k'ara tsinka min zuciya dan Allah" ta fad'a tana hawaye.

"Meya kawo Janan gidana?" Suka ji muryar Abba.

Da sauri Janan ta mik'e tsaye sai kuma ta zauna saboda zafin k'afarta tama manta da ciwon.

"Bance bana son ganinki tare damu ba,na yanke alak'armu dake na sallamaki a matsayin 'yata dan haka ki bar gidan nan yanzu-yanzu"

"Yallab'ai baka da lafiya fa amma har ka jiyo muryar Janan ka fito"

"Saboda tayi min mummunan tabo shiyasa ko guri tazo sai naji jikina ba dad'i"

"Abba kayi hak'uri dan Allah, wallahi idan kana fad'in haka ji nake kamar ana sokamin wuk'a,Abba ka duba halin da nake ciki ka tausaya min"

Tari-tari yake yana fad'in "kina son kashe ni ko Janan?bana son ganinki ki daina zuwa wallahi idan na sake ganin k'afarki a gidan nan ban yafe miki ba,na haramta miki zuwa gidana"

Sunkuyawa yayi k'asa yana tari yana nunata da yatsa yana fad'in ta fita.

Kuka take tamkar zuciyarta zata tsinke haka ta bar gidan ita dasu Asabe da suka mata jagora.

***********

Yana zaune akan lafiyayyar kujerar ya zuba duka hannayensa ya rik'e hab'arsa.

Mommy sai fad'a take ta inda take shiga bata nan take fita ba,ya zuba ido kawai yana kallonta,ga tarin damuwa na damunsa ga fad'an Mommy ya rasa da wanne zaiji.

Maganar da tayi ne ya sashi saurin cire hannayen ya kalleta a d'an tsorace.

"Ko me zakayi saika kiramin Janan a Waya yau sai na k'ure k'aryarka,ka samu wata ka bata waya dan a tsarani ko?"

"Mommy wallahi ba k'arya nake miki ba?"

"Shiyasa nace ka kiramin ita a waya naji dalilin dayasa tace zata zo bata zo ba"

"Mommy bata k'asar an fita da ita waje bata da lafiya"

Hmmm "Jalal kenan ni zaka maida yarinya?to shima d'an uwan naka na bashi nan da wata d'aya ya dawo gida kuma ya samo mata acan inda yake karb'ar magani na gaji da ganinku a haka,ko so kuke sai na mutu banga jikokina ba"

Ajiyar zuciya yayi sannan yace "Mommy please kiyi hak'uri zaki ga jikokin ki harda 'ya'yansu insha Allah"

Hmmm "kamar da gaske"

"Dagaske nake Mommy ki kwantar da hankalinki"

"Okay ina dai jira ka kawo min Janan"

"Amma Mommy ya kamata a samo wata 'Yar aikin dan gani nake kamar aiki yayiwa inna Abu yawa" ya kawar da maganar

"Ai ina tayata da wasu abubuwa,to me za'a kawo bayan duk kun gujeni kai ka tafi Kaduna shi ya tafi waje,Asaben ce abokiyar hira kawai"

"Mun kusa dawowa fa"

"Allah yasa".

Ranar Mommy ta tsokano masa inda yake masa ciwo dan wuni yayi yana rik'e da agogon Janan yana tunanin ko yanzu a wane hali take?oho!.

*********
A k'ofar gidan ta sake goge hawayen fuskarta ta kalli Asabe " bazan shiga ba kasheni zasuyi"

"Babu abinda zasu yi miki mu shiga in kaiki"

Girgiza kai tayi tana fad'in "wlh kashe ni suke son yi"

"To ko gidanmu zata?" Yabi tayi maganar.
"Haba Yabi taya zataje gidanki bayan da mijinta,haba kinsan k'auyennan yanzu sai abin ya zama surutu"

Da k'yar suka lallab'ata ta shiga gidan.

Gidan shiru kamar babu kowa haka d'akin ma da sukaje ba kowa.

Akan katifar suka kwantar da ita sannan suka zauna suna hira saboda su mantar da ita damuwarta.

Sai la'asar lik'is suka bar gidan dan abinci ma Fura Asabe ta siyo suka dama kuma har a lokacin Aliyu bai shigo gidan ba.

Haka in zatayi alwalla kamar zatayi kuka saboda zafin ciwon in ta saka masa ruwa.

Ranar haka ta sake kwana ba tare da ta runtsa ba,ga k'afar sam ta hanata bacci Aliyu kuwa bai kwana a gidan ba dan bata ganshi ba.

Da Asuba a daddafe tayi sallah sai a lokacin bacci mai nauyi ya d'auketa.

Maganganun da taji ne ya saka ta bud'e idonta.

Ganin Aliyu tayi tare da wasu maza guda uku wanda tayi imani cewa ma'aikata ne.

Da sauri ta tashi taja mayafinta ta rufe jikinta.
Abin har ya kai Aliyu ya shigo mata d'aki da maza saboda baya kishinta.

"Yawwa ta tashi ma" Aliyu ya fad'a yana kallonta.

Kanta na k'asa dan bata san dalilin zuwan nasu ba,ji tayi ance mik'a mata takardu tare da fad'in "gashi kiyi signing"

"Signing akan me?" Tayi maganar cikin sanyin murya tana kallon Aliyun.

"A'a naga kina kallona ko baza kiyi bane?"

"Ai ban san ko na mene ba"

"Daga kotu muke,zakiyi signing sannan ki rubata Account number da Account name d'inki"

Kallon mamaki kawai ta bisu dashi,hannunta na shaking ta karb'i takardar ta rubuta tayi signing.

"Dukiyata ta dawo hannu na"
Ya fad'a yana dariya yana kallon ta.

_kenan kud'in account d'inmu za'a bashi?,Dana san haka ne wallahi na wancan account d'in zan rubuta shine mai dubu 70 kacal a ciki._ tayi maganar a zuciyarta

Fita sukayi ta zauna kawai tana zulumi tana tunanin ko meya faru a kotu yau?,ita dai gabanta fad'uwa yake.

********

Suna fitowa daga kotu Abba ya zube.

Da sauri suka rufar masa duka suna kuka,da k'yar suka sakashi a mota zuwa asibiti.

Kai tsaye emergency aka nufa dashi dan ya fita hayyacinsa tamkar ya mutu.

Cikin ikon Allah likitoci suka samo kanshi.

*_6 hours later_*

Yana kwance akan gadon idonsa na kallon silin,Mameey na zaune gefen gadon yayinda Fahad da Fauziyya ke tsaye a jikin gadon.

Har lokacin suna cikin damuwa Fauziyya kuwa kuka kawai take.

Kallonsu yayi cikin k'arfin hali yace "karku damu akwai Allah kuma yana kallon duk abinda ke faruwa kuma ya sani ban zalunci kowa ba amma an zalunceni,duka gidana da nashi an had'a an bashi saboda kawai ba'a ga inda aka binne dukiyarsu ba sai ace komai bamu an basu, sannan an dakatar dani daga aiki ba tare da hak'k'ina ba duk irin ruk'on aikina amma ace wai ban san aikina ba"

Tari ne ya sark'e masa,Fahad ya rik'oshi yana fad'in "Abba dan Allah ka cire komai

Please Login or Register in order to submit comment