You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dole in shiga inga halin da Abba yake ciki"

Da sauri ta wuce Lubna na biye da ita.

A falo taga 'yan gidan gaba d'aya.

"Karki sake ki k'araso nan''
Abba ya fad'a tare da mik'ewa tsaye.

Su Fauziyya da Mameey da Fahad ma duk suka mik'e.

" Abba karka yi min haka dan Allah kayi hak'uri"

"Idan baki bar min gida ba zan tsine miki Janan dama kina cikin fushina har yanzu"

Fauziyya ta taho da sauri gurinta Abba ya tsayar da ita cikin tsawa "idan kika je gurinta sai dai ki bita kema bazaki sake rab'ata ba"

Duk kansu kuka suke,idan ka d'auke Fahad da Abba suma dai kana ganinsu kasan suna cikin damuwa matuk'a.

"Bana k'aunar k'ara ganinki har k'arshen rayuwata Janan,kece sanadi kin take umarni na idan har na mutu to tabbas ke kika kasheni Janan domin ke kika yayo mana bala'in yaron nan baya ganin darajar ni mahaifinki ne ke kuma matarshi amma haka yake zagina nida mahaifiyarki ko kunya babu kin cuceni Janan"

Kukan ta ya fito fili ta fara fad'in "na shiga uku ni Janan Abba ka yafe min in har baka yafe min ba na san wuta zan shiga,Abba na cuci kaina na cuceku dan Allah kuyi hak'uri Mameey"


Duk tabi ta rud'e sosai,rik'e ta Lubna tayi itama tana basu hak'uri tana kuka.

Abba na k'ara cewa "babu yafiya tsakanina dake sai dai hisabi Janan,ki fita kawai bana son ganinki"

Da wannan kalaman suka fito daga gidan duk Kansu suna kuka har Lubna.

Gidansu Lubna suka nufa ta zauna tana ta bata hak'uri ita da ummansu amma kuka take k'ara yi.

Idonta yayi Jajir ta kalli Lubna tace "in har ni 'yar halak ce na bar auren Aliyu,na tsane shi bana son ko k'ara ganinshi Allah ya saka min zalunta ta da yayi,ko me Abba yayi wa. Aliyu bamu cancanci haka daga gareshi ba"

Hmmm "ba zuga ki nake ba Janan amma da kinji irin furucin da yayi wa Mameey a zama na k'arshe da saikin fi tsanarsa wallahi"

Ta goge hawayen idonta tace "ki fad'amin labarin Aliyu dan Allah ki fad'a min me Abba yayi masa?"

"Ki kad'ai kunnenki ki nutsu zan baki labarin Aliyu da kuma irin laifin da aka masa kamar yadda ya fad'a a kotu"

_*Shekarun baya da suka wuce....*_
_(Labarin Aliyu)_








*_Ku biyo ni kujiπŸ‘‚_*













_*Sadeey S Adam*_✍
[9/29, 8:17 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁




_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


_🎢Kin shiga raina kin samu guri kin zaunaaaa......zana rik'e ki hannu biyu alk'awari zan miki gataπŸ˜„_🎢
*_Taken naki ne Ayshat A Muh'd(Aunty)_*



πŸ’ƒπŸ’ƒ _...........🎢Soyayya ce,nayo dace ni nayo murna haushi ya gushe_🎢
_*in kana da masoya ka moreπŸ’ƒin kana da masoya kafi k'arfin wulak'anciπŸ’ƒin kana da masoya ba k'unciπŸ’ƒAllah ka barni da masoyana ka k'ara min Adadin su ka inganta min rayuwarsu ka sa fara'a dawwamammiya a zukatan su Ameen ya rabbil alaminπŸ™*_





22

_Shekarun baya da suka wuce_
_*(LABARIN ALIYU)*_

Haifaffan garin nan ne cikin unguwarnan lokacin bata shigo gari ba dan k'auye ne sosai sai an fita daga Kaduna a lokacin kafin a had'e shi da garin Kaduna ya dawo cikin gari sosai,a lokacin sunan shi _bad'ko village_ kafin ya dawo G.R.A.

Aliyu tun tasowarsu Fulani ne usur kuma kyawawan Fulani kamar yadda kika gani.

Mahaifinsa shahararren manomi ne kuma makiyayi.

'Ya'yanshi biyu da Aliyu da Sabira wadda ake kiranta da Ummi, haka zalika matanshi biyu Umma Saude sai Gwaggo Zaliha wadda bata tab'a haihuwa a gidan ba.

Gidansu Aliyu Family house ne an kewayeshi da dannin kara sai dai ko wane gini a ciki ginin jar k'asa ne saiya kewaye abinsa still daga ciki.

'Kannen babansa,baba Isa da baba Tanimu ko wanne da matansa a ciki.
Shi baba Isa matanshi uku yayinda baba taminu yake da mace d'aya sai 'ya'yansu birjik.

Sai kuma d'an wansu baba halliru dashi yake zaune a can _Cinai_ shima d'ansa nan gidan yazo ya kafa nashi d'akin ya cigaba da noma anan.

Kinsan idan aka ce miki an had'a abu na yawa dole ayi gulma amma duk da haka suna da had'in kai wajen cima,domin abinci idan anyi kowa sai an kasa an bashi.

Hafsa d'iyace ga autansu baba Rabe(mahaifin Aliyu),tun tasowarta a gidan su Aliyu ta tashi ta ganta domin tun tana 'yar shekara uku iyayenta suka rasu sanadin cutar shanu data kama su a k'auyen da suke mai suna _dawo_ ita Hafsa lokacin an kawota gidansu Aliyu ta d'an zauna sai Allah yasa cutar bata ritsa da ita ba,haka baba Rabe ya cigaba da rik'onta ta, ta kuma zauna a d'akin Zaliha tunda itace bata tab'a haihuwa ba.

Zaliha kuwa ta d'auki son duniya ta d'orawa Hafsa haka tayi ta tara kud'i tana yiwa Hafsa gata.

Aliyu kuwa dama baba Rabe ya jajirce a kansa saboda lokacin suna shigowa cikin Kaduna a k'afa suzo makaranta sai yaran k'auyen suke gudun karatu saboda wahala sunfi maida hankalinsu ga noma da kuma kiwo wanda shine al'adar 'yan garin.

Ganin Aliyu baya wasa da karatu yasa baba ya rik'a tara kud'i yana biya masa,a haka har ya shiga aji uku na secondary Jss3 kenan,a lokacin kuma baba ya siya masa keke yake zuwa dashi har ya gama sannan aka canza masa da wani tsohon Babur.

A yadda ya bayyana yace yasha wahala sosai saboda shekara uku yana nema admission daya samu sai a bawa 'ya'yan masu kud'i,a shekarata hud'u ne ya nema shima ya damu dan yaci duk wata jarabawa da aka yi amma sai akace sai ya kawo dubu d'ari biyu sannan zai samu gurbin karatu a jami'ar.

Baba kuwa yace ya hak'ura kawai,shi kuma ya dage yace yana so sai baba yace to Indai haka ne sai dai ya nemo kud'i da kansa domin shi kud'in da yake tarawa nasu ne wanda zasu inganta rayuwarsu ko bayan ransa baya so su wulak'anta.

A haka ya shiga tunanin mafita,kuma lokacin ne aka saka bikinsu da Hafsa wanda dama suna son junansu.

Ganin ba yadda za'ai ya samu kud'in yasa yace ya hak'ura kawai ya koma gona ya cigaba da shuka da kuma taya baba kiwon shanuwansu.

Tun aurensu da Hafsa gidansu ya fara lalacewa domin gwaggo Zaliha Sam bata k'aunar auren Hafsa da Aliyu dan ita tafiso ta aurar da ita a birni yarinyar da ko primary batayi ba dan ko zo bata sani da turanci ba.

Kullum fad'a da tsegumi a gidan,goggo Zaliha bata da magana sai ta fad'in an asirce ta an hanata haihuwa d'iyar da take iko da ita an aurar da ita ga mutumin da ko gidan kansa baya dashi sai d'an kewaye a gidan ubansa tun abin baya damun Aliyu har yazo yana damunsa daga lokacin kuma ya fara Neman mafita.


Birnin ya shiga yaje gidan wani abokinsa da sukayi secondary school tare dan ya nema masa koda gadi ne a birni dan shi ya gaji da gori.

"Zaka samu abinda yafi gadi idan har ka daure" Usman ya fad'a lokacin da Aliyu yaje masa da k'orafi.

"Wane aiki kenan?" Aliyu ya tambaya.

"Aikine mara wahala amma kuma yana da had'ari sannan aikin bana ragwaye bane zaka iya?"

"Ka sakani a duhu Usman kamin bayani"

"Karka damu Haidar zanzo gobe muje in kaiwa oga kayan dana kawo, a cikin Abuja yake, sannan in had'a ka dashi kaima ka samu kasonka ai daga ranar abokina ka zama Alhaji dan zaka samu a k'alla dubu d'ari biyar idan har ka kawo kaya lafiya"

"Bazan iya sata ko yankan kai ba Usman na hak'ura kawai"

"Dalla Abokina karka damu magunguna ne zaka shigo dasu kawai,ai wallahi wannan tsohon mashin d'in ma babu kai babu shi"

"Kai fa baka da mutumci abin harda zagi da ai keke gareni yaushe nayi Babur d'inma"

"Mazaaa! ina gaya maka karka damu ba wata matsala"

A haka Aliyu ya dawo k'auyen cike da murna,yana tsara yadda zaiyi da kud'in idan ya samu.

Yana shiga gida ya tarar da malam zaune kan tabarma a k'asan darbejiya dake can k'arshen gidan.

Da sauri Aliyu ya k'arasa wajen yace "sannu da hutawa baba"

"Yawwa haidar dama dawowarka nake jira dan yaune nayi niyya fad'a maka wani sirri zo ka zauna"

Zama yayi kusa da baba,cikin rad'a baba yake fad'in "ka san ina da manyan gonaki guda hud'u Wanda duk Wanda ke shuka a gidan nan a ciki yake yi ko?"

"Eh" Aliyu ya amsa

"To inada manyan filaye guda uku Kasan su?"

"Na san guda d'aya dai"

"To zanje dakai in nuna maka sauran biyun,amma kafinnan ina son sanar da kai cewa takardun filayen dana gonakin dana gidan nan duk suna k'asan bishiyarnan nayi rami mai zurfi na saka a cikin tukunya dan karsu lalace,Aliyu na ajje muku ne domin zai muku amfani kaida k'anwarka bayan raina"

Jikin Aliyu yayi sanyi,a take sukaje baba ya nuna masa sauran filayen suka dawo.

Matarsa ya tarar kwance tana ta juyi,tsohon cikine da ita a lokacin.

Ganin bata jin dad'i sosai yasa ya kasa fita ko ina ya zauna suna ta hira yana kwantar mata da hankali dan tana mugun tsoron haihuwa ga wani lokacin cikin yana wahalar da ita.

Da dare bayan sallahr magariba suna zauna ta gama abinci kenan ta zubo sai ga laure 'yar gidan Malam Isa ta shigo kewayen "Yaya Haidar kazo kayi bak'o a mota"

Kallonta yayi yace "waye kuma haka har a mota?"

"Yace dai kai yake nema"

Tunda ta fara magana Hafsa ta tsaya kawai tana kallonta,ta shi yayi yana shirin fita tace "ah'ah ga abinci kuma na zubo mana"

"Ki fara ci kafin na dawo"
"A'a kaje ka dawo kawai" ta fad'a

Yana fita ya tarar da Usman tsaye jikin motarsa,bayan sun gaisa yace "lafiya kuwa na ganka a daren nan?"

Usman yace "wallahi wajen wani malami zanje nan bayan garinku kuma mota bazata shiga ba saboda gonaki ga kuma yashi,shine nazo neman alfarmar ka aramin Babur d'inka inyi sauri inje in dawo"

Aliyu bai kawo komai a ranshi ba ya shiga ya fito masa da babur d'in sannan ya bashi mukulli yace "Allah ya dawo da kai lafiya"

Shima Usman ya bashi mukullin motar yace "idan na dawo sai in karb'a"

"A'a ka rik'e a gurin ka"

"A'a ka ajje min"

Haka sukayi dashi ya tafi.

Aliyu ya dawo gida suka fara cin abinci da matarshi hankali kwance.

Tafiyar Usman batafi da minti 30 ba kawai sukaji ana harbe harbe ga kuma jiniya ta motocin 'yan sanda.

Kafin su fito waje tuni 'yan sanda sun shigo gidan wasu kuma suna waje sun wa gidan k'awanya dan kar wani ya sid'ad'e ya gudu.

Salati su baba da baba Tanimu ke tayi kasancewar sunga bak'on abu dan sun san zuwan 'yan sanda ba alkhairi bane.

"Lafiya me muka yi muku?" Aliyu yake tambayarsu.

"Ina mukullin motar dake waje?" d'aya daga cikin 'yan sanda ya tambayeshi.

"Mai motar ya tafi da mukullinsa taya zai barshi anan?"

Mari ya kifa masa ya sake tambayar mukullin motar,shi kuma Aliyu a tunaninsa ko wani ne a k'auyen yaje yace an kawo masa mota ko kuma tunaninsa ana zargin motar sata ce shiyasa ya kafe yace babu mukullin a hannunsa.

'Dan sandan ya bawa sauran umarni da su shiga su duba ko ina,bayan an cajeshi babu mukullin a jikinsa.

Ba'a wani sha wuyar ganinsa ba dan ba b'oyeshi yayi ba.

"Wannan kuma na wace motarne?" d'an sandan ya d'aga mukullin yana tambaya yana kallon Aliyu.

"Yallab'ai wallahi ba nawa bane ajiya aka bani"

Fita sukayi suka bud'e motar,wasu manya-manyan kwalaye aka fito dasu guda uku sai bindiga 'yar k'arama.

Suna bud'e kwalin suka fara fiddo da cocaine d'in suna d'agawa,dukkanin mutane an taru sosai.

Juyowa yayi ya kalli Aliyu yace "muna zarginka da shigowa da hodar iblis"

"Hodar iblis kuma?"

"Eh miyagun k'wayoyi sannan meya kawo bindiga motarka?"

Ganin ana neman zura masa ankwane yasa yace "wallahi ba mota ta bace ta abokina ce,ya ari Babur d'ina Ku jira yanzu zai dawo"

Mari d'an sandan ya sake kifa masa yace "mu zaka rainawa hankali?taya mutumin da yake da mota zai karb'i Babur?meyasa ka karb'i motar baka san meke cikinta ba,shima nemasa muke kuma kaine abokin hark'allarsa"

"Allah ya isa tsakanina da kai da ka saka Hafsa ta aureka har da ciki,ashe mugun haline dakai,'yallab'ai Ku tafi dashi dan tun da ya rik'e bindiga wata rana muzai kashe ai halin uwarsa gareshi bak'ar zuciya ba" Gwaggo Zaliha ta fad'a,Aliyu na kallonta yana kuka yana fad'in "kin san halina gwaggo kinsan bazan aikata haka ba"

"Haba Haidar dama ai son zuciya b'acin ta kana da son zuciya fa"

Ganin za'a tafi dashi ne ya saka Umma da sauran 'yan gidan keta kuka.

Da sauri baba ya ruga ya rik'e su yana fad'in "d'ana kamili ne bazai tab'a aikata haka ba,na san wace irin tarbiyya na masa dan Allah Ku sake shi Ku kama Wanda ya muku laifi" wani hanb'ara da wani d'an sanda yayi masa ne ya sa ya fad'i k'asa abinka da tsohon mutum kuma ga wahalar k'auye jiki ba k'wari, Aliyu yana kallo amma ba damar ya tsaya dan janshi kawai ake yana kuka.

Duka 'yan gidan suka durk'usa aka d'ago baba ana ta kuka,a lokacin numfashinsa ne kad'ai zaka gani ka gane yana da rai.

Hafsa kuwa tashi tayi da sauri ta k'arsa gaban d'an sanda ta d'auki kara ta rad'a masa dan taji zafin yadda taga mijinta da baba basuji ba basu gani ba.

Shi kuwa yana juyowa a kufule ya mareta sannan yasa kulki ya daki cikinta.

Wani wawan k'ara da tayi ne yasa suka juyo kanta.

Jini ne shatata yake bin k'afarta babu abinda kowa ke fad'a sai "inna lillahi wa inna ilaihi raji'un"

Aikuwa Aliyu sai daya fuzgi kansa ya k'arasa gareta kallonshi kawai take bata cewa komai,sai da 'yan sandan suka d'aga shi sannan a hankali ta samu damar cewa "Haidar Allah ya saka mana,Haidar ka yafe min"

Aka tafi dashi aka maka a cell baiji ba bai gani ba.

Washe gari aka fito dashi da safe yaga an sakashi mota an nufi hanyar k'auyen nasu sai yayi tunanin ko Usman ya dawo ya fad'i gaskiya,suna zuwa yaga k'ofar gidan mak'il da mutane aikuwa ya fara hawaye dan ya san idan ba baba ne ya mutu ba to Hafsa ce.

Aikuwa ko gidan ba'a bari ya shiga ba,akan tabarma ya zauna baba Isa yazo yana ta bashi hak'uri ya sanar masa da Hafsa ta rasu.

Sai da yayi k'aramin hauka a gurin dan har gidan da ba'a barshi ba sai da ya shiga,baba ma babu lafiya bai ma san wake kanshi ba,haka aka d'auki Aliyu aka maida cell tamkar zararre.

A ranar da yamma aka kaishi gurin commissioner Abba kenan shi kuma lokacin suna meeting sai yace a tafi dashi zai nemeshi idan ya gama bincike.

Shekaru takwas ya kwashe a prison sannan wani wanda yayi zaman shekara 10 dan yazo da shekara 2 aka kawo Aliyu to tare suke shi dama hukunci aka yanke mai na shekara goma to ranar da zai fita bayan yaji labarin Aliyu yace masa zai je har wajen commissioner in Allah yasa ya samu ganinsa zai masa bayani.

Watan mutumin 4 da tafiya aka saki Aliyu,yana zuwa unguwarsu yaga ta zama gari sosai dan kuwa gashi duk a ciki muke kuma bamusan sunyi rayuwa anan ba dan babu alamun an tab'a ginin k'asa a nan,dan nan d'in ma sai da yasha wahala aka gane ta aka kawoshi,kuma yana zuwa ya tarar da gidanku shine gidannan nasu,yace sai da ya shekara biyu yana bara yana kwana a kango yana neman iyayenshi da 'yan uwanshi sannan ya samesu sanadin wata Zuhra.

Lokacin daya tambayi mamanshi ya akai suka dawo nan sai ta bashi labari ai tun bayan rasuwar Hafsa da kwana 5 Baba ma ya rasu,tun daga lokacin 'yan gidan kowa ya fara zamewa yana cewa shi bazai zauna dasu ba.

A haka kowa ya baje,hatta shanuwai da ragunan baba duk an sace babu su,to sai baba halliru yace su dawo kangire su zauna,tace shekarsu uku a kangire shima ya rasu,sai d'ansa habu daya mallaki gidan yace ya bar musu shi kyauta.

Tun daga lokacin yace sai ya d'auki fansa a gurin Abba,Usman da gwaggo Zaliha wadda ita bama asan inda take ba.


Ajiyar zuciya Janan tayi ta kalli Lubna da idanunta da suka gama rinewa tace "Lubna dani dake tare muka taso tare mukayi primary school tare iyayenmu sukayi deciding na dawowa unguwarnan shin kin tab'a jin ance Abba na da wani mummunan hali?meye laifin Abba?laifinsa shine ya barshi yayi shekara takwas a prison amma ai d'an adam ajizine"

"Yace wai Abba ne yasa akayi masa wannan cin mutumcin sannan dukiyarsu tana gidanku"

"Lubna taya Abba zai sa ayi masa wannan cin mutumcin?shi Abba ai baisan komai ba an kawo masa case kawai bama zaice ga Haidar d'in da akama laifi ba in ba yanzu ba"

"Shima haka Abba yace lokacin da mutumin yazo ya bashi labari kasa runtsawa yayi dan ya manta da case d'in,amma a lokacin ya fara bincike sosai ya gani gaskiya sannan yace a saki Aliyu a kuma bashi hak'uri sannan yasa a nemo Usman wanda har yanzu ba'a ganshi ba,kuma yace d'an sandan da aka ce ya daki matarsa ta mutu! Abba ya sallameshi daga aiki dan yazo kotun shima ya amsa laifinsa yace baima san ta mutu ba,Aliyu baiyi bincike ba shiyasa nake jin haushinsa duk da labarinsa abin tausayine"

"Wallahi Abba baya da laifi,bana tausayin Aliyu saboda ya wulak'anta min iyaye,sai yanzu nake dana sanin saninsa a rayuwata"

"Yanzu shine ake ta bincike a gidanku dan ba'asan inda bishiyar take ba an sare ta amma ranar Wednesday za'a cigaba da shari'a".

" to yanzu ya kike ganin shari'ar?wa ake bawa gaskiya?"

"Kowa Aliyu yake tausayi yana masa kuka dan Abba daya fad'i uzurinsa ma cewa sukayi k'aryane kawai inji lawyern Aliyu"

Kuka sosai Janan take tace " kimin Alfarma na zauna a gidanku zuwa ranar laraba dan Allah Lubna"

"Bazai tab'a yuwuwa mu zauna da masu bak'in hali a gidannan ba"

Dukkansu suka juya dan ganin ko waye ke maganar.










*Ku biyo SaNaz dan jin ko waye???πŸ“*











_Sadeey S Adam_✍
[9/29, 8:17 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁


_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```




23

Daddy suka gani tsaye jikin k'ofa ransa a b'ace tamkar bai tab'ayin fara'a ba.

"Meya kawo ta gidannan?"

"Daddy Janan ce fa"

"Tun kafin kiyi wayo na san Janan dan haka ki tattara ta ta bar min gida yanzun nan sannan na datse alak'arki da ita kamar yadda na datse tawa data mahaifinta dan bazamu zauna da azzalumai ba"

"Daddy kayi hak'uri dan Allah,Abba yace ta bar masa gida kaima in ka koreta ina zataje?"

"Gidan uwaki" ya cilla mata dak'uwa ransa a b'ace ya cigaba da fad'in "ubanta ya koreta sai nine zan rik'e ta?tun kafin raina ya gama b'aci ki nuna mata hanya ta fita ta bar min gida"

Hawaye sharkaf a idon Janan haka ta tashi jikinta sai rawa yake ta rab'a ta jikin k'ofar ta wuce,da sauri Lubna ta saka mayafi zata bita daddy ya tsawatar mata yace ta zauna.

A falo Janan ta tarar da Umman Lubna a tsaye.
Kafad'arta ta dafa tace "Janan kiyi hak'uri kinji ki d'auki k'addara a duk yadda tazo miki Allah ya shige miki gaba"

Da k'yar ta iya cewa "ameen" ta wuce kawai.

Cikin kuka Lubna ke fad'in "Daddy tun tasowa ta nake tare da Janan baka tab'a rabamu ba sai yau rana d'aya zaka rabani da ita,daddy na san dani ce a halin da Janan ke ciki wallahi bazata tab'a min haka ba"

"Ki rufamin baki kafin in miki duka a gidan nan,ni bazaki fi k'arfina ba wallahi ni ba sakaran uba bane sakarai kawai" Jan k'ofar yayi ya fita ita kuma ta cigaba da kuka.

Napep ta tara ta shiga ya kaita har k'ofar gidan Aliyu,bata ga kowa a k'ofar gidan ba hakan ne ya bata damar fad'awa gidan Asabe.

A hankali tayi sallama dan kar su Umma su jita.
"Ah ah Amarya ce a gidan namu shigo bismilla"

Duk da tasha kuka ta k'oshi amma hakan bai hanata b'oye damuwarta ba wajen k'irk'iro murmushi,d'akin suka shiga bayan sun gaisa ta kawo mata ruwa.

Cikin jindad'i tace "nagode" Jakarta ta bud'e ta fiddo dubu biyu ta mik'a mata.

Karb'a tayi tana fad'in "me za'ayi dasu?"

"Kyauta ce na baki"

Baki bud'e Asabe tace "Jaka goma fa?ina zan kaisu? a'a wallahi sunyi yawa Amarya"

"Kin cancanci fiye da haka,wallahi naso ace ma siyayya na miki amma ban samu damar haka ba,kinga tun da aka kawoni nake ajje da dubu hud'u banyi komai dasu ba sai yau ne ma na kashe 500 nayi kud'in mota ki ajje kyayi wani abu dasu karki damu"

"To nagode Allah ya Saka da alkhairi,amma idan babu damuwa zan tambayeki dan Allah"

"Karki damu indai na san amsa zan fad'a miki"

"Kowa ya ganki ya san ke 'Yar manya ce dan Allah shin auren soyayya kukayi da Aliyu?"

"Tabbas auren soyayya mukayi"

Shiru tayi kafin tace "amma idan haka ne meyasa yake dukanki koda yaushe?sannan kowa a k'auyen nan yana son Aliyu tun sanda yazo garin nan saboda kirki,hak'uri da kawaici irin nasa amma akwai wata magana da naji d'azu wadda ta d'aure min kai"

Murmushi Janan tayi tace "karki damu bara na shiga gida dan ina dawowa nan nayo" tayi haka ne dan ta kawar da maganar.

Tashi tayi da sauri ta fito,Asabe ta biyota tana sake mata godiya.
***
Kwance ta ganshi kan katifa yana Waya,kallon daya bita dashi ne yasa tasha jinin jikinta.

Cire hijabin tayi tana k'ok'arin ajje jaka taji ya wullo mata wata tambaya "daga ina kike?"
Juyowa tayi ta kalleshi tace "kamarya?amma ai Kasan na tafi makaranta ko?"

"Sai kika biya gidan wa daga nan?"

"Ni babu inda na biya"

Cikin tsawa yace "kada ki yarda kiyi wasa da hankalina Janan"

Shiru tayi ba tare da tace komai ba,ganin yana neman ya rufeta da fad'a ne ta juya zata fita taji ya finciko ta.

Sai daya fara zabzabga mata mari sannan yayi ball da ita ta fad'i k'asa.
"Bance karki je gidanku ba?"

Kukan da ta fara ne yasa Umma da Ummi saurin shigowa kewayen dan bama su san ta dawo ba.

"Iyeee munafukar Ashe kin dawo?"

"Sai yanzu taga damar dawowa ba basarakiya"

"Umma gidansu taje dana ce karta biya ko ina"

"Ai ga irinta nan wayace ka barta taje makarantar ai sai da nace kar tayi tunda kaima bakayi ba"

"Wallahi bazata k'ara fita daga k'auyen nan ba sai ranar dana bata takardar sallama"

Umma tayi dariya tace "ai ranar tazo daga k'arshen satin nan ne in Allah ya kaimu,ai so nake a kasa ganeta amma har yanzu naga da sauranki,dalla tashi ki samo mana ruwa kuma minti biyar na baki ki dawo"

Kuka kawai take zuciyarta cike da fargaba.

"Bazaki tashi ba sai na sake miki sabon duka?" Aliyu ya fad'a.

Da sauri ta tashi jikinta na b'ari ta d'auki gyalenta dake kan tabarmar ta yafa ta fita tsakar gidan.

Fanteka ta d'auka ta fita tana goge hawaye.

Zuciyarta kawai ta raya mata ta tafi rafi ta fad'a ta mutu kowa ma ya huta da takaicinta dan gani take ita ta jefa iyayenta da kanta a wannan ibtila'in.

Tafiya kawai take zuciyarta a cunkushe da damuwa.

Tsaye take bakin rafin babu kowa kasancewar rana tayi yawa,zama tayi a gefen rafin ta zuba k'afafun a cikin ruwan tana ta addu'o'in neman gafarar Allah kafin ta fad'a kawai taji an dafa kafad'arta.

A tsorace ta juyo ta kalleshi.

"Hey" ya fad'a lokacin da yake zare bak'in glass d'in dake fuskarsa.

"Sannu" ta fad'a a tsorace.

"Nazo wuce wa na hangoki a nan,pls ko zaki iya min wani taimako?"

"Na me?"

"Calm down ba cutar ki zanyi ba naga duk kin tsorata"

Bata ce komai ba illa tsoron kawai da yake bata.

"Mom d'ina ce babu lafiya so tana son fitowa tayi amai kafin ta fito har tayi a mota so shine nake so in babu damuwa kid'an taimaka min tun da naga ke macece"

"Babu damuwa" ta fad'a a sanyaye shi kuma ya bita da kallo yana mamakin yadda 'yan k'auye ke irin wannan wahalalliyar rayuwar dan ko dressing basu iya ba.
a zuciyarsa yake fad'a yayinda ya kafa mata ido tana d'ebo ruwa a fantekar.

"Muje ko" ta masa magana bayan ta d'ebo ruwan,gaba yayi tana binsa a baya a zuciyarta tace.

_abinda zan aikata haramun ne Allah yana sona da rahama shiyasa ya turo bawanshi ya hanani fad'awa ga halaka._

Yadda taga Maman nashi a galabaice ta tausaya mata dan haka bayan ta wanke mata jiki da inda ta b'ata da amai kawai ta d'auki gorar ruwan da ta gani a gefe ta kunce zaninta,guntun maganin da Asabe ta bata ne ta zuba a ciki ta jijjiga sannan tace "Idan kika sha wannan da yardar Allah zaki samu sauk'i"

Ta kafa mata gorar tana sha kawai taji anyi baya da ita.

Da sauri ya karb'i gorar ya d'aga hannu ya kifa mata mari.

"Daga cewa ki taimaka mana sai ki bata wannan k'azantar taku,Ku matsalarku

Please Login or Register in order to submit comment