You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da aure.
"Ko bazaka iya bin umarni na bane?"
Umma ta katseshi.
"A'a ina tunanin yadda Zuhra da iyayenta zasu kalleni"

"Karka damu zuhra itace matarka ta dindindin in har ina raye,ita waccan ai da mun karb'i hak'k'inmu zamu kad'ata"

A haka dai ta tsara masa komai duk wani abinda ya dace yayi.

***********

Tana kwance tana chatting Fauzah ta shigo.
Bata yi yunk'urin tashi ba bayan ta amsa mata sallama kawai ta cigaba da chatting d'inta.

"Ko na miki laifi ne naga baki fara'a nazo wajenki"

"Bakomai naga kema tunda aka baki mota kike shareni"

Murmushi tayi tare da fad'in "wallahi ba haka bane kiyi hak'uri k'anwata"

Murmushi tayi tare da cewa "ya wuce"

"Zuwa nayi neman alfarma"

"Tame?"
Ta fad'a tare da ajje wayar.

"Drivern ki nake son ki aramin zai kaini gidan biki"

"To ke mezai hana kiyi driving da kanki?"

"Na gaji da driving sis"

"Wani na nema ke kina kin gaji"

"Ni dai ki aramin shi pls"

"Sai kace wani kaya kije kiyi masa magana mana"

"A'a nafi son ki masa magana da kanki saboda bani son ya raina ni"

"Nima haka"
Janan ta bata amsa.

"Aike drivern ki ne janan"

"Nifa na tsani guy d'in nan haushinsa nakeji wallahi dan saboda shi yau nak'i zuwa skul"

"Taimaka min ni dai pls"

Ranta bayaso haka ta tashi ta fita farfajiyar gidan.

A can kan bencin maigadi ta hangoshi shi kad'ai yana latsa wayarshi k'irar NOKIA X(RK) wadda tasha ado da kyaure(lol).

K'arasawa tayi bata ko yi sallama ba tace zaka kai Yaya Fauzah unguwa yanzu.

Tayi sauri ta juya zata tafi kawai taji yace "kinyi kyau"

Da sauri ta juyo dan ta tabbatar da ita d'in yake,tana juyowa suka had'a ido taga yana murmushi.

"Dama ke kyakkyawa ce kuma kwalliyar da kikayi ya sake fito da kyawunki ko sarauniyar kyau dole ta Sara miki,kyanta dake za'aje wannan unguwar saboda zanso ace har muje mu dawo ina kallon wannan kyakkyawar fuskar"

Jikinta gaba d'aya a sanye yake,ji take kamar a mafarki ne Aliyu yake fad'a mata haka.

Ta gabanta yazo zai wuce yace "kicewa yayarmu ina jiranta bara na d'akko motar"

Tafi seconds 30 a gurin kafin ta waiga sai take ganin kamar securities d'in gidan duk ita suke kallo,Murmushi ta d'anyi sannan ta ja k'afarta da tagama yin sanyi ta koma ciki,a tsaye ta tarar da Fauzah a falo.

"Lafiya naga kin dad'e kuma kin dawo a sanyaye"

murmushi tayi tace "Yace yana jiranki"
"Okay"
"Yaya Fauzah in shirya mu tafi tare?"
"Gaskiya sauri nake bazan Iya jiranki ba"
"Mayafi kawai zan d'auka"
"A'a ki bari maje wani lokacin gidansu zubaida zanje zamuyi wata magana ne"
"Amma da kika ce gidan biki"
"Na fasa gidansu zuby zani akwai maganar da zamuyi"
"Okay a dawo lafiya"

Fauziyya na barin gurin ta bi k'ofar da kallo.

_Ashe akwai ranar da zata zo inji ina son Aliyu?direba na ko dai asiri aka min?wannan wane irin sone na lokaci guda haka?_
Murmushi tayi tare da fad'in "lubna batayi k'arya ba.







_Alk'alamin Sadeey_✍
[9/29, 8:14 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁


*_by SaNaz deeyah_*πŸ‘„


```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```



05

A bangaren Fauziyya kuwa tunda ta fita ta sauya tafiya,sai wani irin taunar chewing gum take irin na tacaccun 'yan bariki.
Shi kanshi Ali yayi mamakin yanda take behaving a lokacin tamkar sabuwar kilaki.

Yayi sauri zai bud'e mata k'ofar baya ta dakatar dashi.
"Ban saka ka ba" ta furta tare da bud'e gaba ta zauna.

Shima zagayawa yayi ya zauna ba tare da yace komai ba.

Sun fara tafiya ne ya tambayeta ina zasu
"Park" ta bashi amsa
"Wanne"
"Duk wanda ya maka"
Maganar yaji ta wani iri dan haka kawai ya k'udiri niyyar zai ta tafiya koda zasu bar garin in har bata ce su tsaya ba.

Yanayin abubuwan da take yi ne yasa shi b'aro jirginta amma sai ya nuna baima damu ba.

Tana gani suna ta tafiya amma bata yi yink'urin tsayar dashi ba,daga tayi mik'a sai ta zame mayafinta daga jikinta kai duk wani abu da tasan zai ja ra'ayinsa haka ta rik'a yi har ya gaji yayi parking "naga mun tsaya?"
"Ina son ki fad'a min inda zan kaiki" ya furta ba tare daya kalleta ba.

Shiru tayi tsayin Rabin minti sannan tayi dariya tace "kayi kyau wallahi ka had'u"


Kallo ya bita dashi na _ban fahimci me kike nufi ba_
'Daga gira d'aya tayi ta sake fad'in "kayi min Aliyu tun ranar da aka kawoka gidanmu nake sonka"

"So kuma?" Ya fad'a a d'an razane.
"Eh so,kasan me?"
"Sai kin fad'a" kawai ya tsinci kanshi a mai bata amsa kai tsaye"
"Ina so muyi wani sirri amma ba yanzu ba ka bani number ka zan nemeka dan maganar bada rana zamuyi ta ba"

_ko dai Janan ta fad'a mata komai?_ ya tambayi zuciyarshi ba tare da ta bashi amsa ba.

"Yah kayi shiru" ta katse tunaninsa

"Yaushe zamuyi maganar?"

"Ka bani number ka sai na kiraka idan na saka time"

Babu musu ya bata numbershi,tayi masa umarni da su koma gida kawai.

*******

Tana kwance akan gado tana juyi tunani kala-kala take a cikin zuciyarta...

_ki kalli kanki a mirrow zaki tabbatar da cewa ke d'in kyakkyawa ce ajin farko_

Maganar Salman ta fad'o mata lokacin daya fara furta mata kalmar so.

Da sauri ta tashi ta nufi jikin mirrow ta kalli fuskarta,wani murmushi ta saki na jindad'i sai take ganin kamar a lokacin ne yake fad'a mata.

_zan tafi bazan sake dawowa garinku ba dan bazan iya jurar ganinki a matsayin matar wani bani ba,k'addara ta raba mu dake,amma nasan bazan tab'a samun kamarki ba har k'arshen rayuwata_

Zubewa tayi a k'asa lokacin da ta tuno maganarsu ta k'arshe da Salman,tun a wannan lokacin bata sake jin labarinsa ba sai labarin rasuwarsa da Abbanta ya kawo mata.

"Allah yaji k'anka Salman ya yafe maka laifukanka" ta fad'a tana zubda hawaye,a dai-dai lokacin Mameey ta shigo.

"Oh dama kin shirya shine kika zauna direba na can na jiranki kin kirashi kusan awa d'aya ko kin fasa zuwa skul d'in?"

Bata bata amsa ba kawai ta cigaba da goge hawayenta.
"Janan"
"Na'am" ta amsa a sanyaye.
"Kukan me kike?"
Nan ma shiru tayi.

Kusa da ita ta k'arasa ta tallabo hab'arta
"Nace kukan me kike?"
"Bakomai"
"Oh dama anayin kukan dad'i?"
Tayi shiru
"Tambayarki nake"
"Mameey Salman na tuna"
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil,Janan meyesa bakya jin maganar iyayenki?wace nasihace mahaifinki baya miki ita akan Salman?idan kin tuno shi meyasa bazaki masa addu'a ba"

"Ina yi masa"
"To ba kuka yake so ba addu'arki yake buk'ata oyaa tashi ki saka gyalenki ki tafi skul"

Jikinta a sanyaye ta tashi ta zura hijab ta d'auki handbag d'inta.

Tana fita ta hango Aliyu tsaye jikin motar shi kam tun daya ga fitowarta yake murmushi.

Wani zugi taji kanta nayi ganin fuskar Aliyu take tamkar ta Salman.
A take ta zube a gurin a sume.

"Subhanallah" wasu daga cikin securities d'in gidan suka furta.

Da sauri d'aya daga cikinsu ya nufi cikin gidan dan sanarwa dasu mameey.

Aliyu ma a rud'e yazo gabanta ya tsaya a dai dai lokacin da mameey da Abba suka fito a tare.

"Me aka mata ne?"
"Fad'uwa kawai tayi bamu San dalili ba" Ali ya bashi amsa.

A kafad'a Abba ya sab'eta sukayi cikin gida.


_2hrs ago_

Fad'a sosai Abba yake yi ita kam tana jingine da fuskar gado tana kuka.

Fauzah da Fahad suna tsaye yayinda Mameey ke zaune gefen gadon.

Ganin Abba yak'i daina fad'an sai maimaita Abu d'aya yake yasa mameey cewa "fad'an nan fa bashi zai saka ta nutsu ba"

"Kamar ya kenan? Duk ba laifin ki bane,ina amfanin yarinya k'arama kamar Janan ace namiji ya shiga ranta haka,ki gaya min dalilin dayasa ta fara soyayya da Salman ba tare da iznina ba???"

"Me kake nufi da hakan?kana nufin kace Janan bata isa aure ba ko kuma bata isa soyayya bane?"

"She's just 18 me ta sani game da wannan?"

"Ko ka so ko karka so gaba d'aya yaranka sun isa aure"

"Ni kuma bazan tab'a aurar da 'ya'yana ba ba tare da sun gama karatu ba"

"Shi kuma Fahad da yake aiki fa?meyasa ka hanashi ya fito da yarinyar da yake so ka aurar dashi ba?"

"Hadiza mu bar wannan maganar na san lokacin daya dace ko wanne na aurar dashi"

"Nima ina da right d'in bawa 'ya'yana zab'i"

"Oh haka kika ce?"

"K'warai ma kuwa"

"Mu zuba mu gani"
Ya fad'a a fusace sannan ya fita ya bar d'akin,mameey tabi k'ofar da kallo ranta a b'ace.

Ranar haka kowa ya yini a gidan da b'acin rai.









_Sadeey_πŸ’«βœ
[9/29, 8:14 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁


_*by SaNaz deeyah*_


```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```



06

Sanye take cikin doguwar riga ta atamfa,tayi rolling ta d'an k'aramin veil,idanunta d'auke da farin glass hannunta rik'e da wani d'an k'aramin novel.

A tak'aice tayi kyau matuk'a.
Tun daya hangota ransa ya b'aci,a zuciyarsa ya furta

_wannan kyawun naki nan bada dad'ewa ba zai zama muni sai nayi watsi da duk wani farin cikin zuri'arku_

smiling yayi itama ta mayar masa dan yanzu idan ta ganshi ji take tamkar an tsundumata a aljanna"

Tana k'arasawa gabansa ta saki murmushi wanda har ya bayyana hak'oranta.

"Barka da zuwa sarauniyar kyawawa"

Wani farin ciki ne ya mamaye zuciyarta ta bud'e baki zatayi magana taji muryar Fauzah a bayansu.

"Ku tsaya ku saukeni a skul"
Duk Kansu suka jiyo suka kalleta.

A hankali ta k'arasa jikinta sanye da wata fitted gown nylon wadda tabi jikinta.

Janan kawai kallonta take rai a b'ace.

Bata sake masu magana ba kawai ta bud'e seat d'in gaba ta zauna.

Janan ta bud'e k'ofar baya ta shiga ta zauna.

Yana driving a nutse yayinda duk kanninsu suke latsa wayarsu.

"Kayi kyau sosai Aliyu" kamar daga sama sukaji maganar.

Duk kansu suka kalleta,ta maze tamkar bata ma San sunayi ba,ta sake fad'in "ko dan dama ai kai kyakkyawane"

Shiru yayi baice komai ba,Janan ji tayi zuciyarta na tafasa tamkar an watsa mata garwashi a ciki.

"Malam kayi sauri ka saukeni karna makara"
Shi kanshi yayi mamakin yadda ta masa magana a tsawace.

Nan ma bai tanka ba ya san ranta ne ya b'aci saboda furucin Fauzah.

Suna zuwa bakin gate tace ya tsaya.
A fusace ta sauka ranta a b'ace.

***********

Ya kirata yafi a k'irga batayi picking wayarshi ba,da ta gaji ma kawai ta kashe wayar.

"Waye haka ya dameki har kike kashe Waya?"

"Aliyu ne bayan ya b'atan rai kuma yake kirana komai zai ce min oho"

"Aliyu kuma,wanne kenan?"
"Wanne kika Sani?"

"Ni ban san kina da wani Aliyu ba bayan direbanki"

"To shi nake nufi"
"Ta fad'a tana kallon gefe da ban"

"Karfa maganar lubna ta zama gaskiya"
"Tama zama"
"Kamarya?"
"Kamar yadda nake soyayya dashi har muna shirin yin aure"
"Direbanki"
"Ya isa haka Raihan karki saka raina ya b'aci"
"Haba Janan wlh nayi tunanin duk wasa kike amma ina ke ina direba"

"Mu tsaya a nan dan wlh raina ya gama b'aci,na kawo Salman ance baya da asali shi kuma Aliyu ai kinsan asalinsa ko?"

Jakarta ta d'auka ta bar gurin,Raihan ta bita da kallon mamaki.


Tafiya take gaba d'aya ranta a b'ace ta nutsa sosai cikin makarantar inda take ma ba mutane sosai hanyar clinic ne,kawai taji ta gabza karo da mutum,wasu stars ta gani na azaba,ta d'ago dan ta bawa mutumin hak'uri kawai taji ruwan mari har uku kafin ma ta shaida ko waye.

Ta dad'e idonta rufe kafin ta bud'e shi ta dirar dashi kan kyakykyawan saurayin.

"Hannu ta d'aga zata rama taji an rik'e ta tare da hankad'ar da ita k'asa,dariya suka hau yi sauran samari uku"

Shi kuma ya d'urk'usa k'asa saitin fuskarta yace "Janan Hashim,yarinya mara kunya,duk rashin kunyarki baza kiyi dani ba ko kuwa baki tab'a sanin waye ni a cikin polytechnic?kije ki tambaya waye yarima"
Mik'ewa yayi tsaye yana murmushi yace "kije ki tambayi ko waye ni bani da wasa musamman da talaka kamarki"

Gaba d'aya sauran mazan suka saka dariya.
"Guys muje" sun fara tafiya tayi saurin cewa "idan ka isa kai namiji ne ka fad'a min cikakken sunanka"

Juyowa yayi yana dariya ya girgiza kai kawai ya wuce.

Tashi tayi tana kad'ai kayanta sai a lokacin taji wasu zafafan hawaye na fita a idanunta.

**********

Tana kwance tana juyi gaba d'aya hankalinta a tashe yake,ga abinda ya faru a makaranta ga rashin sanin tak'a mai-mai inda Aliyu ya tafi domin Mameey tace tunda ya fita kaita makaranta bai dawo ba,ta kira numbershi yafi sau ashirin bai d'aga ba tana tunanin ko ramuwa yayi,bata yi tunanin kiran Fauzah ba dan bata kawo suna tare ba.

Haka ta zauna cikin k'unci ga rashin sanin sunan wannan guy d'in wanda ya wulak'anta ta a skul.




A b'angaren Ali direba kuwa bayan ya dire Janan a skul ya juya zai yi hanyar skul d'in su Fauziyya tayi saurin dakatar dashi.
"A'a Aliyu Najman hotel zaka kaini"

Yayi saurin juyowa ya kalle ta,tayi saurin zuge jakarta ta fiddo sark'ok'in gwal dasu bangles tace zan Kaiwa wata mata kayan saidawa ne,tazo daga lagos so anan hotel d'in ta sauna"

Kai tsaye ya nufi wannan katafaren hotel d'in.

Bayan yayi parking ta kalleshi ta marairaice tace "please Aliyu ka rakani bani son a min kallon banza dan Allah ka rakani muje mu fito"

"Amma idan muka shiga tare ai shine za'a miki wannan kallon"

"A'a please ni dai tsoro nake saboda ban tab'a shiga hotel ba"

"Ba damuwa muje" ya kashe motar ya bita.

Kai tsaye yaga tana tafiya ba tare data kira wayar kowa ba koda matar da tace tazo gurinta.

Sun hau bene kusan hawa uku kafin su isa d'akin kasancewar hotel d'in babba ne.

Ganin ta fito da key daga Jakarta yasa abin yayi matuk'ar bashi mamaki.

"Kika ce gurin wata kika zo naga kina k'ok'arin bud'e d'akin da kanki
" taje ta dawo shine ta bada key a kaimin"

Murmushi kawai yayi dan ya san k'arya take.

Suna shiga d'akin kuwa ta rufe da key,cire mayafinta tayi sannan ta cire bands da d'ankunnenta ta baza gashinta ta fad'a kan gado"

Murmushi tayi ta kalleshi "na mallaka maka duk kanin kaina kayi yadda kaga dama dani"

"Subhanalla kin san kuwa me kike fad'a"

"K'warai ma kuwa domin son ka ya rufe min ido"

"Wannan ba so bane"
"Wannan kuwa shine so" ta fad'a tare ta tashi zaune.

"Kaji tausayina Aliyu nayi maka alk'awarin babu wanda zaiji sirrinnan zamu rik'a zuwa nan muna biyawa junanmu buk'ata batare da kowa ya sani ba"

"Bazan iya ba,bazan tab'a aikata zina ba"

"Nima ban tab'a ba sai yanzu nake son farawa saboda na kasa b'oye feelings d'ina"

"Tunda kin san haka ai sai kiyi aure gudun fad'awa halaka"

"Abba bazai mana aure ba sai lokacin da ko wacce a cikinmu ta kammala masters ta fara aiki"

"Sai ki fad'a masa ke bazaki iya ba"

Duro wa tayi daga kan gadon ta k'araso gabansa ido cikin ido tace "kasan halin Abba yana da tsauri,Janan data fara soyayya haka ya rabasu yace shi ba zai bawa mai k'aramin k'arfi auren 'yar shi ba,sannan uwa uba baya da asali daga shi sai mamansa suke rayuwa a garin,tun lokacin daya rabamu ya hanamu kula kowa har sai mun gama masters sannan zai zab'a mana mijin daya dace damu"

"Baki da hujja,ki bud'e min k'ofa na fita"

"Aliyu pls"
"Ki bud'e nace" ya fad'a a tsawace"












_Sadeey S Adam_✍
[9/29, 8:14 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁



_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


07

Tsayawa tayi tana masa kallon mamaki yadda har yau yake mata shouting dan ta buk'aci taimako daga gurinsa.

"Kin tsareni da ido baza ki bud'e ba saina kirawo Abba"

Dariya ta k'yal'k'yale da ita tana tafa hannu "ka kirawo Abba kaga yadda zan maka sharrin da sai kayi dana sanin zama direban gidanmu"

_Aliyu kayi a hankali ka kuji sharrin mace dan tana da had'ari sosai_

Maganar mahaifiyarshi ya tuna lokacin daya fara soyayyar k'arya da Janan.

"Aliyu da yanzu munyi abinda zamuyi mun tafi saboda kaga lokaci na tafiya har munci awa d'aya da wani abin anan"

_ban tab'a aikata zina ba bazan fara a kanki ba,da ace ni mazina cine da yau kinga k'ask'anci da daga yau baza ki k'ara sha'awar wani d'a namiji ba,yadda na tsaneku haka zanyi fata fata dake in barki cikin nadama._

"Kai nake jira"
Ta haye kan gadon ta kwanta tare da lumshe ido "wallahi ko zamu kwana anan bazan bud'e ba sai ka biya min buk'ata ta"

Zama yayi kan kujerar dake jikin mirrow yana kallon ikon Allah,abin yana matuk'ar bashi mamaki wai mace ce ke nemansa.

Sun shafe awoyi sama da 8 dan anan yayi sallahr Azhar da la'asar,yana gani itama tazo tayi.

"Aliyu na fara jin yunwa ya kamata muyi abinda ya kaw........." Mari ya d'auketa dashi wanda ya hanata k'arasa maganar.

"Ni ka Mara?"
"Ki bud'e min k'ofa"
"Wayyo Allah zai kashe ni" ta fad'a da k'arfi tare da kama rigarta ta yaga har zuwa k'irjinta"

Janyo waya tayi ta danna kira "Cikin kuka da kururuwa tace " kuzo Najman hotel zai kasheni dan Allah ku ceceni" d'if ta kashe wayar.

Baiyi wani yunk'uri ba dan mamaki ya sandarar dashi a tsaye.

"Zan nuna maka ni cikakkiyar makira ce"

Suna tsaye taji jiniya alamar su Abba sun iso,tayi saurin yace bedsheet d'in ta rufe jikinta ta wullah masa key d'in ta Shiga toilet ta rufe.

Kusan minti 20 basu zo d'akinta tasan k'ila ana duba each and every room tunda bata fad'i d'akin da take ba.

Kamar daga sama taji ana fad'in " 'yata kina d'akin nan?"

Da Sauri ta bud'e ta fito tana kuka ta rungume Abba tana matsanancin kuka.

"Naga motar Janan a waje ina Aliyu?waye ya kawoki nan dan ya keta miki haddi?"

"Abba Aliyu ne"
"Yana ina?" Ya fad'a ransa a b'ace.

"Yana ganin shigowarku ya gudu"

"Arrest him" ya fad'awa 'yan sandan da suke tsaye a gurin,da sauri suka fita.

Suka duba ko ina a cikin hotel da wajenshi basu ga Aliyu ba sai dai motar Janan.


_(Kun san ya akai Aliyu ya gudu)?_

Tana wurgo masa key lokacin data shiga toilet shi kuma ya bud'e k'ofa ya fita,kasancewar hotel d'in yana da steps ta ko wane side shiyasa ya rik'a bi yana b'uya daga securities d'in Abba da k'yar ya samu ya fita dan an baza 'yan sanda ko ina,amma bai samu damar d'aukar mota ba.


A gigice ya ya hau napep ya kaishi gidansu.

"Yaya lafiya?"
"Ina umma?"
Tana d'aki.

Da sauri ya wuce zuwa d'akin,zaune ya tarar da umma tana goge hawaye.
"Umma lafiya"
Kallonshi tayi yadda ta ganshi a birkice ta tsorata da hakan.

"Bakomai ina tunawa da mahaifinka da 'yar uwarka da suka rasu ta hanyar Muggayen mutanennan"

"Umma ina cikin tashin hankali"
"Na me?"

Labarin duk abinda ya faru ya sanar da ita,tashin hankalin da ta shiga a lokacin ba na wasa ba.

"Akan wane dalili zaka bita ku shiga cikin hotel?kenan maganganun da nake fad'a maka duk sun tashi a banza?"

Kuka ta fara sosai,Ummi ta shigo ta rik'e ta "ka rugaza duk wani shirinmu Aliyu,ka cucemu"

Furucinta ba k'aramin d'agawa Aliyu hankali yayi ba.

"Umma karki ce haka ki gafarceni,nayi alk'awarin k'wato mana hak'k'inmu kota wane hali"

"Ta wane hali kenan?Auren yarinyar ne kad'ai mafita,kana tunanin wani mahaifine zai d'auki 'yarsa ya bawa fasik'i"

A gigice ya kalli umma yace "kina nufin kin yarda umma zan Iya aikata zina?ni d'anki ne na halak dan Allah ki daina jifana da wannan kalamai"

"Bance kai mazina ci bane amma kana tunanin akwai wanda zai yarda a cikinsu cewar baka aikata ba bayan kun shafe kusan awa takwas Ku biyu a d'akin?"

Kai ya dafe yana nadamar binta ciki da yayi,bai tab'a tunanin zata mai sharri haka ba.

"Yanzu meye mafita"

"Anjima zan je gidan saboda makullin motar janan ma yana hannuna"

"Inaso ka tafi yanzu Dan bana so ace an maimaita abinda ya faru a shekarun baya da suka wuce"

Jikinsa a sanyaye ya tashi ya fita.

Ummi na kuka ta bishi "Yaya bana son abinda ya faru damu ya sake faruwa dan Allah karka je"
Dafa kanta yayi yana murmushin k'arfin hali yace "karki damu zan dawo lafiya lau insha Allahu"

********
A bangaren su Fauziyya kuwa sai da Abba ya kaita asibiti aka tabbatar masa da lafiyarta k'alau sannan suka wuce gida,idanunta sun kad'a sunyi jajir kya kyace da gaske duk abinda ta fad'awa Abba gaskiya ne.

Mameey,Janan da Fahad duk suna falo hankalinsu a tashe suna jiran zuwan su Abba.

Aikuwa suna jin horn duk kansu suka fito.

Sunyi cirko-cirko Mameey ce ta k'arasa gurin Fauziyyar ta ruk'ota.

Falo suka koma duk suka zauna.
"Wai meya faru da fauziyya ne?"

Ajiyar zuciya yayi yace "Allah dai ya tak'aita amma daya lalata mata rayuwa"

"Waye wannan?"
Suka fad'a a tare.

"Wannan yaron Aliyu mana,ai na saka amin arresting nashi duk inda yake"

Tuni janan ta mik'e tsaye "wane Aliyu Abba?"

"Direban gidan nan mana,wai yaron nan ni zaici amana dubi duk abinda nake masa amma baya godiya,har ya yaga mata riga yana nemanta ta k'arfi sai shiga tayi ta kulle kanta a band'aki"

"Ai dama mutum ba abin yarda bane dan wa zaiyi tunanin Aliyu zaiyi haka" Mameey ta fad'a.

Janan kuwa ta sandare ta rasa me zata ce ma,kallon Fauzah kawai take.

"Abba kayi masa hukunci mai zafi" Fahad ya fad'a.

A hankali ta furta "bai aikata ba,bazan tab'a yadda ace Aliyu zaiyi haka ba"

Da gudu ta shiga d'akinta tana kuka.
"Meyasa haka?meke faruwa dani ne?"


"Ki jini da yarinyar nan"
"Bakaji me kace ba kaima,yarinya ai yarinyarce"
"A hakan kike cewa zasu iya zaman aure"
"Mu bar wannan maganar yanzu"
"A to"







_Sadeey S Adam_πŸ‘„
[9/29, 8:13 AM] Aishat A Muha'd: 🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁



_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


_ohhni Safnah shiru babu ita babu labarinta,pls dan Allah ina cigiyar Safeenah writer d'in *Sunyi Sake* dan kaf numbers d'inta switched off Allah yasa dai lafiya AmeenπŸ™_



08

Tana zaune a d'aki tana ta kuka dan ta rasa mafita shikenan a karo na biyu ta rasa masoyi,ta san Abba bazai tab'a yarda ya bata shi ba tunda har haka ta faru kuma dama soyayyar a b'oye suke yinta dan ta san babu yadda za'ayi Abba ya aura mata direbanta cikin sauk'i.

Tana cikin yanayin nan taji muryar Abba yana fad'in "Arrest him" a tsawace.

Da sauri ta tashi ta fita falo,idanunta suka sauka akan Aliyu yana fad'in "Abba Ku tsaya ku fahimceni wallahi ita ta nemeni"

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Janan ta fad'a tana kuka,da sauri ta k'arasa gabanshi "meyasa ta bugo waya tana neman taimako? kuma kace ita ta nemeka"

Kallonta yayi idonshi jajir yace "wallahi bani na nemeta ta ba ita tace na rakata hotel zata kaiwa wata mata kaya kuma tace bazata iya shiga ita kad........"
Abba ya wankeshi da mari "Rufamin baki"

Janan ta juyo ta kalli Abba tace "bai aikata ba Abba"

"Janan baki da hankali ne?"

"Mameey da hankali na ku duba ku gani,akwai kissar wani malami da yake cewa duk macen da tace an mata fyad'e a duba a gani da takalmi ta shiga d'akin ko kuma babu,idan da takalminta ta shiga to tabbas ita ta kai kanta idan kuwa babu takalmi to da k'arfi aka jata,sannan kuma tayaya Aliyu ya kai Yaya Fauzah hotel?idan ta k'arfi yayi mata babu yadda za'ayi su shiga saboda ma'aikatan ciki ai ba mahaukata bane,sannan meyasa tabi Aliyu bayan tana da motarta Aliyu baya da kud'in kama d'aki a katafaren hotel kamar Najman sannan rigar Yaya Fauzah ta gaba ta yage bata baya ba kinga kuwa duk zancenta k'arya ne koda ace Aliyu yana nemanta to tabbas ta amince ta kuma yarda sannan ita ta kama musu d'aki a wannan hotel"

"Abba k'arya take wallahi" Fauziyya ta fad'a tana kuka.

"Ki rufa min baki munafuka" fahad ya fad'a yana huci
"Abba tabbas akwai duba a maganar Janan"
"Kin cuceni Fauziyya ban yi miki wannan tarbiyyar ba" Mameey ta fad'a tana kuka

Abba da kanshi ya fara dukan Aliyu sannan ya bada umarni akaishi cell har sai ya nemeshi a kuma bashi abinci sau d'aya a rana sannan kar a yarda da belin.

"Abba"
"yi min shiru Janan".


Aliyu ya Ciro key daga aljihunsa ya mik'awa fahad "ga key d'in motarku"

Juyowa yayi ya kallesu d'aya bayan d'aya a lokacin ya k'ara k'udirar cewar sai ya shayar dasu ruwan bak'in ciki Wanda basu tab'a tsammani ba.

Suna fita dashi janan ta durk'ushe tana kuka.

"Na dawo kanki Fauziyya" a gigice ta d'ago kai ta kalleshi
"Ni kike neman zubda wa daraja da k'ima ko?"

Kai ta girgiza tana kuka "wallahi k'arya yake Abba,shine yace idan banje ba zai kasheni yaje ya wurga gawata inda baza'a tab'a gani na ba shiyasa na yarda na bishi" rufamin baki manufuka.

Fahad ya kalla yace "ka kulle min Fauziyya a d'aki kar ka yarda ko falo ta fito duk abinda take buk'ata a kai mata d'akin a k'wace system d'inta da wayarta har sai na gama bincike a Kansu"

Mameey dai kallonsu kawai take tana hawaye dan ta san duk abinda ya faru da 'ya'yanta laifin mahaifinsu ne.

*********

Umma kuwa ganin har dare yayi Ali bai dawo ba ta San tabbas akwai Matsala.

Kallon Ummi tayi tace "ko dai zaki bi Aliyu

Please Login or Register in order to submit comment