You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gina a gidan Adnan.

A haka har bacci ya kwasheta,k'arfe uku na dare alarm ya tasheta ta shiga toilet tayi alwallah ta fito ta kalli su Lubna dake ta bacci ta d'ala mata duka zubur ta bud'e ido.

Dariya Janan tayi tace "a rage baccin asara a tashi ayi nafila"

"Dalla malama mene haka kin san Allah zan tashi su kausar da duk 'yan matannan in har baki barni ba"

"A'a suna baccinsu a takurasu shikenan dai kema koma".

Dariya kawai tayi ta juya kwanciyarta data baby.


*********

Dubban mutane ne suka shaida Auren Janan da Adnan,Alh Ibrahim shine ya zamo waliyyinta.

Tana zaune ita da su kausar taji ana rangad'a gud'a.

Jinkinta yayi sanyi lokaci guda ta tsinci kanta a wani yanayi da bazata musalta shi ba.

Fauziyya da Bilkisu ne suka shigo d'akin suna rangad'a gud'a Janan tayi saurin rufe fuska.

" to Hajiyata an d'aura fa Salman ya zama na Janan" Fauziyya ta fad'a tana dariya.

Ita dai batace komai ba bayan farin cikin da ya mamaye ta.

Lubna ce ta shigo da gudu tare da zama gefenta tace "Umm auren masoya ya tabbata wallahi an d'aura yanzu Adnan d'in ya kirani suna wajen lunch na d'aurin yanzu zasu dawo ki shirya za'ayi pix fa.

Pictures kuwa anyi su kala-kala sai kusan k'arfe biyu 'yan d'aurin Aure suka fara shirin tafiya Abuja da yake tun 11am aka d'aura auren ita kuma Amarya da yamma za'a kaita da dare kuma za'ayi fitacciyar dinner ta friends kawai ba iyaye.

A waya Adnan ya kirata ya sanar da ita sun bar Kaduna yanzu amma da sun sauka zai kirata dan haka karta yi nisa da wayarta.

"Allah ya saukeka lafiya mijina ka kulamin da kanka"

"Ameen matata kema ki kulamin da kanki"

"Insha Allahu".


*_2hours later_*

Gida cike yake da mutane ana ta hada-hada.

Janan tana gidan su bilkisu ita da k'awayenta dan har ta sake yin wanka ta saka wani tsadaddan lace ga alkyabbarta a cikin closet d'in haj Mariya dan an fara shirye-shiryen tafiya kai Amarya,sai za'a kaita sannan za'a saka mata alkyabba.

Fauziyya ce ta shigo tare da jan hannunta tace "kizo inji Mameey"

Murmushi tayi tace "ya Fauzah ba dai har an kawo motoci ba?"

"A'a cewa dai tayi na kira ki"

"To"

"Lubna muje ki rakata"

"To Yaya Fauzah" har sun fito farfajiyar gidan Fauziyya na rik'e da hannun Janan wayarta ta fara ringing,d'agawa tayi ta kara a kunne tace "gashinan mun taho da Janan d'in fa?"

Daga d'ayan b'angaren Mameey tayi magana ba dai suji me tace ba sai Fauziyya kawai tace "to shikenan"

Katse wayar tayi tace "wai muje falon baffa(Alhaji Ibrahim) shine yake nemanki itama Mameey yanzu zata shigo.

" wai meya faru ne Yaya Fauzah nifa gabana fad'uwa yake "

"Babu abinda ya faru wa'azi dai kinsan dole a miki fad'uwar gaba kuwa dama ta zama dole ga kowace Amarya kafin a kaita"

A falon suka tarar da Baffa da wani abokinsa,Haj Mariya sai Momma da Yaya Musahin.

Suna yin sallama duk suka d'ago kai suka kallesu, gaidasu sukayi sannan suka zauna a gefe,Janan kanta a k'asa ta kasa had'a ido da kowa.

Fauziyya ta rik'e hannun sosai.

Momma ce ta tashi ta koma gabanta ta zauna "Janan kinci abinci?"

Kai ta d'aga alamar eh.

"Kin tabbatar kinci kin k'oshi ko zaki k'ara?" Haj Mariya ma ta jefo tata tambayar.

"Alhamdulillah" ta fad'a har lokacin kanta a k'asa.

"Janan d'ago ki kalleni" Alhaji Ibrahim yayi maganar.

"Na'am" kawai tace ta kasa d'ago kan.

"Kin tsinci kanki a jarabobi masu yawa na rayuwa kuma kin fawwalawa Allah hakane?"

"Hakane baffa" ta fad'a lokacin da taji bugun zuciyarta ya k'aru.

Ya d'an yi shiru sannan ya cigaba da fad'in "Janan ina son ki k'ara juriya ki zama jajartacciya mai tawakkali kinji"

"To"

"Duk abinda kikaga ya samu bawa muk'addarine daga ubangiji kuma kowa da tashi Jarabawar"

Nan kuma shiru tayi d'akin yayi tsit.

Alhaji Ibrahim yafi minti biyu kafin ya sake cewa "zaku shirya ku tafi Abuja dake da Mamanki damu,mijinki Allah ya k'addara musu sunyi accident a hanyarsu ta komawa yanzu haka suna asibiti acan Abuja"

Tun kafin ya k'arasa magana ta mik'e tsaye.

Da k'yar Momma ta zaunar da ita.

Kusan seconds goma bata ce komai ba babu hawaye a idonta.

Lokaci guda ta zunduma salati sannan ta rungume Momma "na shiga uku,na shiga uku meyasa rayuwa ke wahalar damu"

"Janan kiyi hak'uri ai da sauk'i jikin nashi"

"Momma na shiga uku wallahi na shiga uk......" Daganan basu sake jin motsin ta ba.

"Janan! Janan!!" Sunanta suke kira suna jijjagata amma ina.

Fauzah da Lubna ma kukan kawai suke.


_30 Minutes later_

Tana bud'e ido taga Mameey rik'e da hannun ta.

Da sauri ta tashi ta sake fashewa da kuka "Mameey d'azu muka gama waya da zasu tafi fa wannan wace irin k'addarace ranar aurena"

Rungumeta Mameey tayi tana rarrashi.

"Na shiga uku"

"Baki shiga uku ba Janan Addu'a zaki masa ki tashi ku tafi kar dare yayi,an had'a miki kaya a trolley saboda ke zakiyi jinyar mijinki Allah ya bashi lafiya"

Wani sabon kuka ta fashe dashi.

Mameey ta kalli Fauziyya tace "ku tafi keda Lubna idan yaso sai ku dawo tare dasu Baffa ko?"

"To Mameey"

Mota biyu akayi,Momma, Fauzah, Lubna da Janan a d'aya.

Sai d'ayar kuma "Alhaji Ibrahim,Sagir Muhasin da Fahad.

Janan har suka isa tana kuka fuskarta tayi jajir idanunta ma haka sunyi jajir sun sake juyewa ga fatar idon ta kumbura.

A k'ofar asibitin aka jagorancesu har zuwa inda su Mommy suke dan har lokacin su kansu basu samu damar ganin shi ba,ga 'yan sanda a tsaitsaye.

Mommy idonta yayi jajir itama lokaci zuwa lokaci tana goge hawaye.

Abba k'arami yana ganin Janan ya ruga ya rungumeta yana fad'in " Ammi oyoyo".

Sun gaisa da Mommy ta janyo Janan tare da d'ora kanta a cinyar Janan d'in "kukan ya isa haka 'yata kiyi addu'a kinji"

"Ance sauran sun rasu?"

"Mommy ta kalli Momma tace "Motar da ta kara musu mutum biyu sun rasu motar su Adnan kam shi kad'ai ne ya rayu shima d'in baki ganshi ba" ta sake goge hawaye sannan tace "abindai sai godiya ga Allah sauran ukun ma har an tafi dasu gida za'ayi jana'iza,shi kansa Adnan d'in bai san inda kanshi yake ba har yanzu muma ba mu samu ganin shi ba tukun"

Adam dake tsaye yayi ajiyar zuciya yace "Allah kenan mota d'aya fa muka shiga a zuwa amma a dawowa yace bazai shiga motana ba saboda ina mahaukacin driving kawai dai Allah ya k'addara hakan zata faru dashi ne"

"Allah ya bashi lafiya"

"Ameen".







_Sadeey S Adam_✍
🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁



_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„




```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```




51

Anyi komai na shagalin biki tamkar na budurwa,Kamu,dinner, gala,da duk sauran occasions da ba'ayi ba lokacin bikinta da Aliyu sai da aka yi yanzu,duk da bata da wasu k'awaye a Kaduna amma 'ya'yan 'yan uwa da abokan Fauzah duk sun zo,Humaira da Zee kuma suna a gaba,Momma dama da ita aka fara biki Muhasin sai ranar d'aurin Aure zaizo,Mammy ma cewa tayi ranar d'aurin Aure zata zo Ja'afar zai kawota sai su Kausar Jidda da laila ne sukazo ,Raihan bata zo ba amma Lubna da ita aka yi komai dama tun wancan zuwan bata koma ba,Umman Lubna kuwa bata hanata komai ba dan itama tana zuwa ayi aiki anan ne take fad'awa Janan d'in cewa daddyn Lubna na tayasu murna da fatan alkhairi dan bazai samu zuwa ba yana jin nauyin iyalan Abba.

Haka Maman Raihan ma tazo amma bata fad'i dalilin rashin zuwan Raihan ba itama kuma Janan d'in bata tambaya ba.

Gidan dai cike yake da bak'i kala-kala.

Yau ma a gajiye ta dawo tana shiga d'aki ta cire kaya ta saka na bacci sannan ta zube kan gado tare da lumshe ido.

Lubna ta d'aleta "Lallai yarinyar nan me kike nufi?"

Ta d'an bud'e ido d'aya tace "ke wallahi bacci nake ji na gaji"

"Allah tashi zakiyi mu fita mu kama wani aikin gobe fa d'aurin aure"

Rufe idon nata tayi tace "babu inda zani wallahi a gajiye nake ga wayata nan Adnan ma ce masa nayi kada ya kira sai sun sauka saboda bacci yayi min yawa a ido idan ya kira ki tasheni"

"Cab kin raina min hankali fa wato ni zan jire miki kiran Adnan ba?"

"Haba kawata kinsan nifa Amarya ce sai da lallab'a"

"Lallai kam,sannu amarya ke d'in zan lallab'a?zaki bushe kuwa"

"Ni dai komai zaki ce baccina zanyi" ta juya mata baya.

Lubna tayi dariya ta fita kawai.

Kamar daga sama taji wayarta na ringing ta lalubo da hannu ta d'aga sannan ta kara a kunne.

"Har kun isa?"

"Itace sallamar?"

"Oh salamu alaikum da fatan kunje gida lafiya ya gajiyan dinner?"

Murmushi yayi tamkar tana gabansa yace "Alhamdulillah kinga yanzu muka sauka ko fita daga mota banyi ba nace sai na kira gimbiyata naji ya take"

Hamma tayi tare da yin mik'a sannan tace "wallahi har na fara bacci"

"Tun yanzu"

"Eh wallahi kasan tunda aka fara biki ban samu nayi baccin cikakken awa biyu fa"

"Meyasa?"

"Hayaniya mana ga kasan dai taro dole sai an gama ake samun nutsuwa"

"Hakane kam ai bayan biki a gaba zan sakaki ki rik'a yin bacci har sai na tabbatar kin huta kin rama baccin ki"

Dariya tayi cikin jindad'i tace "office d'in fa?"

"Ai hutu zan d'auka na wata uku inci amarcina dani dake babu mai takura mana in riritaki tamkar kwai"

Dariya ta sake yi tare da fad'in "wow kace na zama 'yar gatan Adnan"

"Sosaima"

"To yanzu kasan abinda za'ayi?"

"Sai kin fad'a"

"Kaje kayi wanka kaci abinci sannan ka kwanta kayi bacci dan ka huta kafa kashe wayarka kada ma Adam(amininsa) ya damar min kai da kira,ka kular min da kanka"

"Karki damu gimbiyata angama duk abinda kikace ai shi za'ayi"

"Yawwa na manta ban fad'i wani abu ba?"

"To ina jinki"

"Kayi mafarkina kaji,ina Sonka sosai" bata jira me zai ce ba ta katse wayar ta kasheta gaba d'aya saboda kunya taji, murmushin jindad'i tayi ta fara tunanin irin soyayyar da zata gina a gidan Adnan.

A haka har bacci ya kwasheta,k'arfe uku na dare alarm ya tasheta ta shiga toilet tayi alwallah ta fito ta kalli su Lubna dake ta bacci ta d'ala mata duka zubur ta bud'e ido.

Dariya Janan tayi tace "a rage baccin asara a tashi ayi nafila"

"Dalla malama mene haka kin san Allah zan tashi su kausar da duk 'yan matannan in har baki barni ba"

"A'a suna baccinsu a takurasu shikenan dai kema koma".

Dariya kawai tayi ta juya kwanciyarta data baby.


*********

Dubban mutane ne suka shaida Auren Janan da Adnan,Alh Ibrahim shine ya zamo waliyyinta.

Tana zaune ita da su kausar taji ana rangad'a gud'a.

Jinkinta yayi sanyi lokaci guda ta tsinci kanta a wani yanayi da bazata musalta shi ba.

Fauziyya da Bilkisu ne suka shigo d'akin suna rangad'a gud'a Janan tayi saurin rufe fuska.

" to Hajiyata an d'aura fa Salman ya zama na Janan" Fauziyya ta fad'a tana dariya.

Ita dai batace komai ba bayan farin cikin da ya mamaye ta.

Lubna ce ta shigo da gudu tare da zama gefenta tace "Umm auren masoya ya tabbata wallahi an d'aura yanzu Adnan d'in ya kirani suna wajen lunch na d'aurin yanzu zasu dawo ki shirya za'ayi pix fa.

Pictures kuwa anyi su kala-kala sai kusan k'arfe biyu 'yan d'aurin Aure suka fara shirin tafiya Abuja da yake tun 11am aka d'aura auren ita kuma Amarya da yamma za'a kaita da dare kuma za'ayi fitacciyar dinner ta friends kawai ba iyaye.

A waya Adnan ya kirata ya sanar da ita sun bar Kaduna yanzu amma da sun sauka zai kirata dan haka karta yi nisa da wayarta.

"Allah ya saukeka lafiya mijina ka kulamin da kanka"

"Ameen matata kema ki kulamin da kanki"

"Insha Allahu".


*_2hours later_*

Gida cike yake da mutane ana ta hada-hada.

Janan tana gidan su bilkisu ita da k'awayenta dan har ta sake yin wanka ta saka wani tsadaddan lace ga alkyabbarta a cikin closet d'in haj Mariya dan an fara shirye-shiryen tafiya kai Amarya,sai za'a kaita sannan za'a saka mata alkyabba.

Fauziyya ce ta shigo tare da jan hannunta tace "kizo inji Mameey"

Murmushi tayi tace "ya Fauzah ba dai har an kawo motoci ba?"

"A'a cewa dai tayi na kira ki"

"To"

"Lubna muje ki rakata"

"To Yaya Fauzah" har sun fito farfajiyar gidan Fauziyya na rik'e da hannun Janan wayarta ta fara ringing,d'agawa tayi ta kara a kunne tace "gashinan mun taho da Janan d'in fa?"

Daga d'ayan b'angaren Mameey tayi magana ba dai suji me tace ba sai Fauziyya kawai tace "to shikenan"

Katse wayar tayi tace "wai muje falon baffa(Alhaji Ibrahim) shine yake nemanki itama Mameey yanzu zata shigo.

" wai meya faru ne Yaya Fauzah nifa gabana fad'uwa yake "

"Babu abinda ya faru wa'azi dai kinsan dole a miki fad'uwar gaba kuwa dama ta zama dole ga kowace Amarya kafin a kaita"

A falon suka tarar da Baffa da wani abokinsa,Haj Mariya sai Momma da Yaya Musahin.

Suna yin sallama duk suka d'ago kai suka kallesu, gaidasu sukayi sannan suka zauna a gefe,Janan kanta a k'asa ta kasa had'a ido da kowa.

Fauziyya ta rik'e hannun sosai.

Momma ce ta tashi ta koma gabanta ta zauna "Janan kinci abinci?"

Kai ta d'aga alamar eh.

"Kin tabbatar kinci kin k'oshi ko zaki k'ara?" Haj Mariya ma ta jefo tata tambayar.

"Alhamdulillah" ta fad'a har lokacin kanta a k'asa.

"Janan d'ago ki kalleni" Alhaji Ibrahim yayi maganar.

"Na'am" kawai tace ta kasa d'ago kan.

"Kin tsinci kanki a jarabobi masu yawa na rayuwa kuma kin fawwalawa Allah hakane?"

"Hakane baffa" ta fad'a lokacin da taji bugun zuciyarta ya k'aru.

Ya d'an yi shiru sannan ya cigaba da fad'in "Janan ina son ki k'ara juriya ki zama jajartacciya mai tawakkali kinji"

"To"

"Duk abinda kikaga ya samu bawa muk'addarine daga ubangiji kuma kowa da tashi Jarabawar"

Nan kuma shiru tayi d'akin yayi tsit.

Alhaji Ibrahim yafi minti biyu kafin ya sake cewa "zaku shirya ku tafi Abuja dake da Mamanki damu,mijinki Allah ya k'addara musu sunyi accident a hanyarsu ta komawa yanzu haka suna asibiti acan Abuja"

Tun kafin ya k'arasa magana ta mik'e tsaye.

Da k'yar Momma ta zaunar da ita.

Kusan seconds goma bata ce komai ba babu hawaye a idonta.

Lokaci guda ta zunduma salati sannan ta rungume Momma "na shiga uku,na shiga uku meyasa rayuwa ke wahalar damu"

"Janan kiyi hak'uri ai da sauk'i jikin nashi"

"Momma na shiga uku wallahi na shiga uk......" Daganan basu sake jin motsin ta ba.

"Janan! Janan!!" Sunanta suke kira suna jijjagata amma ina.

Fauzah da Lubna ma kukan kawai suke.


_30 Minutes later_

Tana bud'e ido taga Mameey rik'e da hannun ta.

Da sauri ta tashi ta sake fashewa da kuka "Mameey d'azu muka gama waya da zasu tafi fa wannan wace irin k'addarace ranar aurena"

Rungumeta Mameey tayi tana rarrashi.

"Na shiga uku"

"Baki shiga uku ba Janan Addu'a zaki masa ki tashi ku tafi kar dare yayi,an had'a miki kaya a trolley saboda ke zakiyi jinyar mijinki Allah ya bashi lafiya"

Wani sabon kuka ta fashe dashi.

Mameey ta kalli Fauziyya tace "ku tafi keda Lubna idan yaso sai ku dawo tare dasu Baffa ko?"

"To Mameey"

Mota biyu akayi,Momma, Fauzah, Lubna da Janan a d'aya.

Sai d'ayar kuma "Alhaji Ibrahim,Sagir Muhasin da Fahad.

Janan har suka isa tana kuka fuskarta tayi jajir idanunta ma haka sunyi jajir sun sake juyewa ga fatar idon ta kumbura.

A k'ofar asibitin aka jagorancesu har zuwa inda su Mommy suke dan har lokacin su kansu basu samu damar ganin shi ba,ga 'yan sanda a tsaitsaye.

Mommy idonta yayi jajir itama lokaci zuwa lokaci tana goge hawaye.

Abba k'arami yana ganin Janan ya ruga ya rungumeta yana fad'in " Ammi oyoyo".

Sun gaisa da Mommy ta janyo Janan tare da d'ora kanta a cinyar Janan d'in "kukan ya isa haka 'yata kiyi addu'a kinji"

"Ance sauran sun rasu?"

"Mommy ta kalli Momma tace "Motar da ta kara musu mutum biyu sun rasu motar su Adnan kam shi kad'ai ne ya rayu shima d'in baki ganshi ba" ta sake goge hawaye sannan tace "abindai sai godiya ga Allah sauran ukun ma har an tafi dasu gida za'ayi jana'iza,shi kansa Adnan d'in bai san inda kanshi yake ba har yanzu muma ba mu samu ganin shi ba tukun"

Adam dake tsaye yayi ajiyar zuciya yace "Allah kenan mota d'aya fa muka shiga a zuwa amma a dawowa yace bazai shiga motana ba saboda ina mahaukacin driving kawai dai Allah ya k'addara hakan zata faru dashi ne"

"Allah ya bashi lafiya"

"Ameen".







_Sadeey S Adam_✍
🍁🍁🍁
*DIREBAN GIDANMU*
🍁🍁🍁



_*by SaNaz deeyah*_πŸ‘„



```Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv```


_Wannan shafin sadaukarwa ne gareki sister Ramlat,tnx 4 d luv & support😍._




52

Har su Mammy da Fauzah suka juya ba'a fito da Adnan ba.

Sun tafi ne da niyyar washe gari su dawo.

Sai gab da sallar isha'i sannan suka suma ganinsa.

Suma Janan tayi lokacin da ta ganshi dan ta tsorata ainun,guri kad'an ne a jikinshi ba bandeji da fulasta.

Kuka sosai take lokacin da ta tsinci kanta a kwance a gadon asibiti.

Tashi tayi da sauri ta koma d'akin Adnan d'in lokacin Mommy waya take Adam na rik'e da hannunsa.

"Sannu Janan" shine abinda ta fad'a bayan ta ajje wayar.

Janyota tayi jikinta tana rarrashi tare da cewa "ba kuka zakiyi ba addu'a zakiyi kinji".

Kai ta d'aga alamar to.

"Ga Jalal ma hankalinsa ya tashi sosai yace a satin nan zai samu yazo"

"Wlh kuwa Adam nima na ce masa yayi zamansa tunda koda yazo d'inma dubiya ce kawai amma yace a'a"

"Dole sai yazo d'in Mommy ai bazai iya hak'uri ba dan koni bazan ce karya zo ba"

"Allah ya kawo shi lafiya"

"Ameen"

Mommy babu yacce batayi ba akan Janan su tafi gida amma tace ita babu inda zataje ita zatayi jinyarshi.

Haka Mommy ta hak'ura suka tafi aka bar Janan d'in ita kad'ai.

Hannunsa ta rik'e sosai tana kuka.

Daga dare zuwa safiya nurses sunzo dubashi yafi a k'irga.

'K'arfe biyu ta tashi ta fara nafiloli na nemawa mijinta lafiya wajen ubangiji.

Da asuba kuwa yanayin sallah ta shiga toilet d'in tayi wanka saboda mutane zasu fara zuwa da gari yayi haske.

Mai kawai ta shafa a jikinta ta fesa turare,ko kwalli bata saka ba idanunma duk sun kumbura.

Material ta saka doguwar Riga mara nauyi sannan ta ajje gyakenta a gefe ta kalli inda Adnan yake kwance kamar gawa.

Komawa tayi ta kulle k'ofar d'akin da key sannan ta dawo tayi masa bed bath.

Ta gama sannan ta shafa masa turaruka ta zura masa kaya cikin dubara da k'ok'ari da jajircewa takeyin komai.

Tsura masa ido tayi bayan ta gama shiryashi,ta goge kwallar idonta tace "kaman ba kai ba Adnan lokaci guda kamaninka sun canza"

Ta zauna kan kujera tare da rik'o hannunsa tace "karka mutu dan Allah Adnan,ina buk'atarka a raye saboda mu cika burinmu na rayuwa ina son ka dan Allah ka tashi"

Sunkuyar da kai tayi ta cigaba da kuka a wannan kukan bacci ya d'auketa.

Ji tayi an d'an bubbugi kafad'arta,ta bud'e ido a hankali ta kalli nurse d'in.

"Bacci kika samu?"
Murmushi tayi tare da cewa "ban ma san ya d'aukeni ba"

"Kiyi hak'uri sister Addu'a zaki cigaba da yi kinji,duk da dai munji ance jiya aka d'aura auren ku lallai dole ki shiga tashin hankali amma dai addu'a itace magani"

Kai kawai ta d'aga.

"Ga wannan k'arfe takwas likita zaizo za'aje lab a k'arbo jini sannan za'ayi test da yamma"

"To" tace tare da karb'ar takardar.

Nurses d'in suna fita suka fara gulmar yana da HIV a test d'in da aka yi sun gani.

'Dayar tace "kika sani ko itama tana dashi"

"K'ila kuwa gashi a haka kamar masu lafiya"

"To suna bin k'a'idoji kuma kinga ai musu kud'ine"

"Hakane kuma"

"Uhm kinga muyi abinda zai fishshemu"

Tafiya sukayi ba tare da sun sake magana ba.


'Karfe bakwai Mommy tazo itama kwantar mata da hankali ta cigaba da yi duk da cewar itama cikin damuwar take.

Su Mameey sunzo sun yi dubiya haka 'yan biki yawanci duk anzo an dubashi.

Cikin kwana biyu Janan ta sake zugewa ta rame tamkar ba ita ba,kasancewar yadda taga jikin Adnan na sake rud'ewa da an saka masa jini yake k'onewa hankalinsu ya kai k'ololuwar tashi.

Kwananshi hud'u a asibiti Jalal ya diro k'asar k'arfe 12 na dare.

Ko gida baije ba tun daga airport da direban gidansu yazo d'aukanshi yace su wuce asibiti.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shine abinda ya fad'a lokacin da yaga Adnan d'in.

Jin yadda ya rangad'a salati ba k'aramin d'aga wa Janan hankali yayi ba.
Aikuwa hawaye dama k'iris suke jira sai gasu shar a idanunta.

Juyowa yayi ya kalleta jikinshi a sanyaye yace "Janan ko kema baki da lafiyar ne?"

Kai ta girgiza alamar a'a.

"Gaskiya bazai yuwu a bar Adnan anan ba sai dai a tafi dashi can outside gurin k'wararrun likitoci"

Ita dai shiru tayi tana k'ara goge hawayen idonta.

Ya kai dubansa ga leb'ensa wanda yayi bak'i k'irin yace "Kamar ba kai ba Allah ya baka lafiya"

"Ameen" ta amsa a sanyaye

Juyawa yayi ya kai duba ga direban yace "Malam Hassan ka tafi gida kawai dan ni ina nan ka sanarwa Mommy haka da safe"

"Okay Allah ya k'ara masa lafiya kaikuma Allah ya huta gajiya"

"Ameen" ya amsa.

Yana gefen gado rik'e da hannun Adnan wanda a lokacin ma jini aka saka ita kuma Janan tana zaune kan kujera hannunta rik'e da al Qur'an tana karantawa.

'Karfe biyu ta shiga toilet ta d'oro alwallah ta dawo ta tada sallah,ganin haka ne yasa Jalal shima ya shiga yayi akwallah ya fito ya tada sallah.

Da Asuba kuwa yana fita masallaci tayi sauri ta shiga tayi wanka sannan ta saka kaya bata ma tsaya fesa turare da shafa mai ba kawai ta d'ebo ruwa tayiwa Adnan bed bath sannan ta shiryashi tana cikin shafa mai Jalal ya shigo.

"Ya mai jiki?"

"Da sauk'i ina kwana"

"Lafiya k'alau sannu da k'ok'ari Janan"

Murmushi kawai tayi.

"Bara naje gida nayi wanka sai na dawo"

"To ba damuwa".


***********

Yarinyar da suka yiwa fyad'e kwance take cikin jini tana jujjuya kai.

Faisal da yazo gareta ya durk'usa kusa da ita a hankali ta rik'o hannunsa bakinta na fidda jini da k'yar tace "mamana ni kad'ai take da ita dan Allah ku kaini gurin iyayena kar nayi mutuwar wulak'anci"


Wasu hawaye ne suka fito a idonsa sau biyu yanayin nadama meyasa bazai mik'a kansa gurin 'yan sanda ba.

"Ka kaini gurin Abbu dan Allah"

"Ya sunanki?"

"A...Amal"

Ganin tana mimmik'ewa yasa shi d'aukarta da sauri ya saka a mota ya shiga da ita cikin garin Abuja.

Yayi tunanin kiran ogan nasu sai yayi tunanin akwai matsala.

Dad'insa d'aya ba sosai suka fiya sato 'yan mata a Abuja suna lalatawa ba sundai fi yi a kano dan haka kai tsaye ya wuce private hospital d'in daya sani.

Da gudu ya shiga ya yi bayani aka fito da sauri aka d'auketa aka yi cikin da ita.

Yana k'ok'arin binsu ya hango Jalal tsaye yana waya da sauri ya k'arasa gurinshi yace "d'an uwa dan Allah kayi min taimako"

"Na me?"

Janyo hannunsa yayi suka zagaya sannan yayi masa bayanin irin abubuwan da aka yiwa yarinyar baisan kowa nata ba a hanya suka had'u da ogansa motarta ta lalace shine ogannasu yace bara ya rage mata hanya daga nan suka amfani da hoda suka gusar da tunaninta.

"Subhanallah to a wane unguwa take?"

"Ban sani ba tace min sunan ta Amal amma naji tana kiran Abbu maybe babanta ne,kada kace tsintarta kayi ka zamo d'an uwa a gareta in har Allah ya tashi kafad'unta zata sanar da kai komai ni yanzu kaduna zan tafi zan zartar da wani abu sannan in kai kaina ga 'yan sanda bana so a kamani yanzu ba tare dana isa Kaduna ba"

"Amma meyasa sai ni meyasa zaka ce saini taya ban san yarinyar ba........."


"Kayi hak'uri d'an uwa" da gudu Faisal ya shiga motarsa ya bar Jalal tsaye.

Yafi minti biyar kafin ya shiga ya tambaya inda take.

"Kaine ka kawota?"
"Eh nine" ya fada a sanyaye.

"To gaskiya bazamu tab'a ta ba sai kayi reporting ma police"

"taya zaka ce inyi reporting ma police bayan kana gani yadda jini ke duba a jikinta"

Dafa kafad'arsa doctor yayi yace "tsarin ko wane asibiti a garinnan kenan case na fyad'e bama karb'a har sai an kira 'yan sanda saboda gudun kar abin ya zamar mana matsala"

Janan da ta fito zata je lab ta hangosa tsaye a gurin da sauri ta k'arasa ganin itace kar ta fad'i abinda zaisa a tuhumesa yayi saurin cewa "Kinga yadda Amal ta koma na rasa ya zanyi fyad'e aka mata kuma suna ik'rarin sai mun kirawo police sannan su tab'a ta"

Fuskarta d'auke da mamaki amma ganin yadda ya rikice ne yasa ta danna number Ja'afar ta kirashi tayi masa bayani dsame abinda ya faru da Ummi but wannan 'yar uwar Jalal ce ta santa ma(tayi masa k'aryar hakan).

Cewa yayi a bawa doctor waya,bayani yayi masa sosai tare da fad'in ayiwa yarinyar komai zasu k'araso cikin awa uku.

Ana shiga da ita suka had'a ido

Please Login or Register in order to submit comment