You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nayi mata yaya lokaci ban jira amsawan ta ba nace.
Parents din mu ne suka shigo duba jikin hajiya naga ya dace su gaisa da ita shine na zo fada mata.
Sai ta danyin jimmm a wurin nace zaki iya masu biyayya koda bakiso saboda martaban yarki da take jinin su hakan zai sa su soku sosai a jiki.
Ina fadin haka na bar wurin ba tare da tsayawa in saurari amsan da zata ban ba don irin kallon da take min a lokacin gashi da gani tasha kuka don idanuwan ta da suka nuna alaman hakan.
Dakin na koma inda na samu su mamu sun shigo suna zaune saman kujera ga abinda aka kawo masu ba wanda ya taba a cikin su.
Sai fadi suke su zasu tafi nace haba maman ikilima tun yanzu zaku tafi tace yaya na iya da wanan mai alkunyan wai da ita ba zata shigo dakin ba tace.
Mumu na kalla ina fadin ba zaku bari har a dan jima ba hjy maryam da sai kallon manyar jakkunan dake zube daga can gefen gadona ta juyo tana fadin Alh ne kawai a gida sai murja da Nafisa suma yanzu da mun koma zasu fitone sukace.
Muryan merry ce dake shigowa ya hana kowa wani magana merry ta shigo tana saye da wani bakin dogon riga a jikin ta mara hannu rigan sai gurin hannun da akaiwa dan tattara kamar kwalliya.
Gaida su ta fara tana tsaye suna binta da kallo hjy maryam da mamu suna tambayanta ina Amina saini ce suna tambayan Queen ce don haka suke kiranta nan.
Ta ce tana waje da sauran yaran a falo tun dazun bata tsaya ba kawai ta juya ta fita daga dakin tana mai jin zafin su a ranta don gaba daya kowa a wurin ta mai laifi ne gare ta.
Don sune suka jawo mata bacin ran da take ciki a yanzu wanda auren mu da yaya yayi take ganin da hadin bakin duka yan uwan shine akayi shi.
Basu dade ba suka fito har mama hadiye sai Amma ce da zata tsaya damu har aya umar din ya dawo gida .
Sai da suka biya dakin hjy sukai mata sallama kafin mu rakasu har waje nida maria ina fadin sai mun shigo suka tafi.
Ban koma daki ba kitchen na hada ma hjy abinci mara nauyi nakai masu dakin nan muka tsaya muka bata tare da matan kafin in fito na bata magani tasha.
Dakina na koma na samu har Amma tayi barci yasani fitowa zuwa wurin maria a nan na dan zauna don kada mu tayar da Amma danaga ta samu barci sosai a lokacin.
Daga dakin na yara na tskayi sallaman su murja na fito da sauri na tare su muka dunguma zuwa dakin hjyn da a yanzu zaune muka sameta tana zufa nace su kunna Ac sanyi ya gauraye dakin tukunna zata fi jin dadi.

A haka har muka share kwanaki a gidan ba ruwan wani da wani a cikin a na zamane kawai a tsakanin mu kowa yana jin kansa.
Kwatsan da wani safiya nake jin dan hayaniyar yaya da merry tun suna rigima a hankali har aka fara jin muryoyin su .
Nidai ina dakina ban fito ba sai wani tsawon lokaci da maria ta shigo take fada min wai taga merry ta fita tana ganin kamar tafiyan ke nan tayi don da kayan su suka tafi.
Sai zuwa yamma kuma muka ganta ta dawo a rikice wai bataga Queen ba inda sukaje shiga jirgi.
Gaba daya hankalin mu gidan ya tashi sosai da wanan labarin batan Queen daya riskemu a lokaci daya.
Duk abin nan da akeyi amaryan yaya tana part din ta ta kure shiyanta da sauti gamu sai faman buga waya akeyi ko ina tun munayi mu kadai har abu ya karde unguwa ga baki daya security suka zo sai lokacin ne baba balarabe ya shiga yai fada sosai kan abinda ta aikata din ya fito yana fada sosai har saida merry dake tsaye a gefena ta jingina da jikina don kukan dayaci karfin ta.
Babu mai iya kama wani a cikin mu a lokacin duk hankali tashe muke a gidan gaba dayan mu ga baki daya .
Naga karfin halin wanan samiran don har mukaci muka sude muka koma ciki wanan matar bata ko leko mu ba kowa na fita da ita a baki a gidan.
Sai can cikin dare muna zaune a falon mu zugun zugun merry duk ta fice a yanayi ta sai ga su yaya Aliyu sun dawo da yarinyar wai a nan cikin airport aka sunce ta ta samu wuri ta boye don bata son bin mahaifiyan ta zata zauna da yan uwanta a nan.
Shi umar ma a lokacin bai garin yayi tafiya kasan south Africa wani business shida Nasir sai ta waya muke communicating dashi kawai.
Merry data gigice lokacin da aka shigo da yarinyar sai zubewa tayi sumay a lokaci daya kafirci baiyi ba wallahi.
Ranan munga tabara a wurin merry irun na kafirai da basu san Allah ba mahaifiyar ta ko ta kira yafi a kirga a ranan.
Sai lokacin muka samu kwanciyar hankali kama yarinyar nayi naje nayi mata wanka na bata tea mai kauri tasha sai barci.
Wayewan gari tun karfe shidda gidan namu a cike yakw da mutane yan barka da arziki da Allah ya kiyayye wanda ya nuna hadun kai ga musulmai gare ta.
Har wani kungiya na kirstan aka turo muna gidan wai daga kungiyar su na kiristoci na kasa da kasa sukazo sun so tafiya da merry din da yarta kawu balarabe yayi tsaye ya hana hakan.
Kuma sai abin yaso ya koma wani rikici a lokacin don sunyi tsaye sai abasu su su wuce dasu kawu balarabe yai tsaye sai uban yarinya ya dawo ya yanke hukunci da kanshi.
Dole ba yarda zasuyi suka barta suka tafi don kawu balarabe fitananen mutum ne sosai kowa yasan shi da fitina.
A wanan lokacin ne na zama kamar nice yar uwan merry din ko da yaushe muna tare ina bata magana duk ta fita cikin hayacin ta saboda fargaban data shiga na yar nata.
Kwanan yaya biyu ya juyo ya dawo saboda halin da yarsata shiga na bata hankalin shi yayi kololuwan tashi a can duk da an fada mai anga yarinyar saidai bai yarda da hakan ba.
Dawowan shi yasa mutane suka fara tururuwan zuwa masa jajen abinda ya faru da yartasa daga ciki kuwa har samira da mahaifiyar ta dako leke basu leko yiwa kowa barka da arziki ba da farko.
Ance abin duniya baya boyuwa don dai basuyi sa, an zuwa gidan ba saboda sun samu Amma da mama hadiye da tun faruwan abin suna gidan basu koma gida ba don tare muke dasu a gidan.
Gaisuwa suka fara sai jajen batar yar da suka fara mai a lokacin mama hadiye tace wai mamaki hajiya sabuwa wai me yasa kuke daukan mutane wasu iri kamar kunfi kowa dabarane ?
Kallon mama kowa dake falon yayi har da bakin dake nan a lokacin hjy sabuwa daba kyale ba tace akan me zaki fada muna haka hadiye ?
Dole in fada maki do naga kuna son mayar da kowa wawa a gidan nan saboda kunyi na farko ga hjy kunji dadi.
Ina nan ake kururuwan batar yar nan a gidan nan har wanda bamu sani ba ya shigo gidan nan taya mu bakin cikin abinda ya faru damu.
Amma yarki tana gidan nan bata leko kowa ba a gidan nan karshe ma sai kidan farin ciki data saka muna a gida sai yaya balarabe ne ya shiga ya tsawata mata.
Hakan baisa ta tako zuwa wurin uwar yar nan ta nuna bakin cikin ta ba gare ta ai na dauka ko akuyan muce ta bata yanzu tunda samira tana karshin inuwar shi tare da ita za ai zaman bakin cikin nan.
Yanzu kuzo don ganin ido saboda kunga umar ya dawo wai kunzo taya mutane bakin cikin abinda ya faru ko kunya babu don kun mayar damu bamu san abinda mukeyi ba ko mai ?
Hadiye akwaiki da wani magana yarshi ce ta tabata don haka shi muka zo yiwa tanzanko ba wani ba .
Wurin wa kike son muzone da wurin kishiya ko wa zamu zo din bamu gaji dukawa kishiya ba kema kin sani balle yar cikina ta tabi kishiya don son suna.
A take falon ya dauki hayaniya a wurin inda yan uwan hjyn su yaya suka karbe zancen ya zama nasu sai hayaniya ya tashi a falon .
Mikewa yaya yayi dauke da Abbana dake jikin shi yana rike da hannun Queen da sauran yaran dake biye dashi bayan shi suka fice daga falon.
Hayaniyar da yai yawa a falon yasa merry ta juyo inda nake zaune a kusa da ita tana tambayana meke faruwa ne wai na fara mata bayani abinda kowa ya fada a gurin.
Tace thank you mama da cewa wa mama hadiye da tai magana sun dauka kowa baida hankali da wayau sai su, .
Sun dauka zasu iya dumping din kowa a yadda suke son yi kome wanan matar ita da yar is devils they are very weaked in action.
Ba a daiyi ta da dadi ba a ranan don rayuka sun baci sosai a gurin samira tana taya uwar ta fadawa yan uwan hjy dake falon magana mai zafi.
Ga merry ta matsa min da tambayan me ake fada dole na koma hankalina ya kasu gida biyu a lokacin.
Sai bayan sun fitane sun koma part din su hjy sabuwa kecewa samira bance ki dagawa duk dan iskan dayaso ya kawo maki gani gani a gidan nan ba kaf.
Don basu da yadda zasuyi dake sai gani sai hange gida daine baki barin sa koshi dan iskan mai akidan turawa zai dawo haya bada dadewa ba zamu kamashi a hannu dumu dumu ya gama duk kwanaye kwanaye shi muna nan zai sake ki zakice na fada maki wanan maganan ai.
Amma umma baki ganin hakan da mukeyi duk da bai magana zai iya zama muna matsala tunda ba duka muka gama rufe bakin su ba jifa yanzu wanan gwaggon nasa data kawo wanan maganan a gaban sa.
Kyale yar iska idan na koma gidan boka zan bada sunan ta tunda tana ganin ita takai a yanzu.
Gaba dayan su sai nagama dasu kaf wallahi dani suke wasa basu san sabuwa ba jina sukeyi kawai.
Umma ni abinda yafi damuna a yanzu shine wanan matar tashi Fatima don ko ita kafiran kamar wanan fatiman ta shige mata a gaba a gurin shi.
Nima nayi wanan tunanen a yadda na ganta ta kara zama wata hamshakiya shegiya sai wani kyau da haske take karawa kamar itace mai dukiyan.
Yo yar banza dole ta haska tun yanzu ta cika mai gida da yan yayaye haka masu zubin turawa ko larabawa dasu can jifa ko hausa yaran nake ganin basaji.
Itama dole a satin nan mu kaita a sakarwa yar iska warin jaba kyauta da suran da take takama dashi duk ya tashi a banza yaji ya tsaneta ga baki daya.
Wanan maganan yaiwa samira din dadi sosai tace mama ko nawa ne indai har hakan zai faru da ita zan bada don a shirye nake inyi komai kan wanan yar iskan yarinyar .
Tunda tazo garin nan nake a cikin fargaba da tsoro daduk nayi arba ds ita wallahi sai naji gabana ya fadi uku uku ban san meke sa ina jin hakan ba a kanta da duk naga wanan yarinyar.
Wata rana kece zata koma tsoro ai uwarta ba sheri ta iya ba jummai ta samu sakarai ta kasa natsuwa ta juya yan banza yadda takeso sai kishin hauka da girman kai irin nata.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:22 - 🤐🤐🤐: Yaya umar tun fitan shi gidan su ya nufa tare da yaran shi da suke tare a lokacin , part din kawu suka nufa don yanzu sai suke jin gidan babu dadi gare su idan sun shigo.
Tun bayan barin hjyn su gidan na yan wani watannin dasuka shude gaba dayan su, gidan babu dadin zuwa gare su hakan kesa da sun shigo sai su nufi part din Amma sai wani lokaci sukan dan leka su mamu a part dinsu su gaisa.
Tunda ya shigo ya zauna suka gaisa da kawu bai kara magana ba yana zaune yaran nata dan surutu a tsakanin su sai can kawu ya dago kai ya kalle shi tare da fadin lafiya kake na ganka haka yau.
Dan murmushin yake ya sakarwa kawu tare da fadin babu komai daddy yana kara lumshe idanuwan shi a hankali.
Ko har yanzu zancen bacewar yarinyar ne ka saka a ranka ko kana zaton wasune suka dauketa da niyyah yin hakan.
No ba abinda nake wa tunane ke nan ba Amma wanan fitinar dai da mama ta dauko min a gidanane ya fara damuna .
Fitinan me ke nan saudaki kake nufi ta jawo maka a gida kuma bayan wanan zancen batar yar taka ?
Ya gyara zama tare da hade hannayen shi ya dan furzo da iska daga bakin shi yana fadin wanan yarinyar da ke zama a gidana .
Yanzun haka na barsu ita da uwarta a gidan suna masifa dasu gwago hadiye tana kokatin tara min mutane a gida.
Dan murmushi manya kawu yayiwa dan nasa yana fadin umar ke nan ai dama duk wanda ya sai lariya yasan zatai yoyo .
Ka taba ganin inda irin wanan hadin na mata zallah yai albarka abin son raine fa aka hada ba don Allah akayi shi ba.
Amma yanzu duk me ya kawo wanan zancen har suke wanan fitinan suna kokarin tayar maka da hankali kaida gidan ka.
Nan dai ya koro mashi abinda ya faru har fitina ya kaure a tsakanin su kawu yace ban san har sai yaushe wa yan nan mutanen zasu gane talala na sakar masu a gidan ka.
Wanan iya shegen shi jummai take son in barta tanayi a gidan nan sun dauka hakan wani wayewa ne ko burgewa a idon jama, a.
Basu san hakan zubarwa mutum kima da ajinshi yake ga duk wanda yaga suna aikata irin wanan rayuwan .
Ina dadi wai ace mahaifiya taje gidan yarta tana wanan sayar da halin haka kamar ba wa yanda suka samu irin tarbiyan mu ba a nan.
Na dauka hakan daya faru a tsakanin su da ita jimmai zai sa nadama da natsuwa yazo masu a rayuwan su sai dai ashe su a wurin su ba haka abin yake ba.
Daddy wa yan nan mutanen babu nadama a tare dasu abinda sukaiwa hjy sam su ko a jikin su ma don ko gaida ita sai wanan taga dama take shigowa ta dubata .
Gaba daya iyalina babu wanda ta sanda yazo a gidan balle harta kalle su da idon mutunci sai fadan nan nasu dasu mama na gane komai da takeyi da sanin mahaifiyarta take yin sa.
Don kalaman ds mahaifiyar ta jefawa su mama cikin zancen nasu ya nuna itace ke dora yarinyar a hanya ma.
Gashi gurin raba su fada da marry har hjy ta fado ta fama ciwon jikin ta tun ranan bamu gane kanta ba na kira likita mu mayar da ita asibitin yace ko mun koma da ita can babu abinda zasu iya mata a yanzu.
Allah ya taimaka zuwan Zahran nan kasan tun ranan da ta sauka ta rubuta magani da allura tare da bata taimakon daya dace muka fara ganin sauki sosai a gare ta.
Kawu dake kasa zaune yana wasa da Abbana daya rarafa zuwa wirin shi da sauri ya dago kai yana fadin madallah.
Al,amarin Allah ke nan yau yarinyar nan fatima ce maiba jimmai taimako har ta yarda ta karba daga gareta din.
Yarinyar da jimmai ta tsana har bata iya boye hakan a gaban kowa lalai lamarin ubangiji baida kadan.
Ko yanzu bukatana ya biya don ubangiji ya wankeni ga abinda nake son jimmai ta gane akan rayuwa.
Shi da na kowane balle mutum baka san a inda Allah zai turo ya taimake ka ba kaga yanzu sam babu wanda ya taba kawo hakan mu saman ma ita jimmai din data dauki duniya da girma takw ganin kaskancin yarinyar akoda yaushe.
Gashi yau wa yanda take ganin su din ne wata tsiya a wurin ta sun kasa taimaka mata dako sannu balle kallon arziki.
Dama irin haka yakan kasance sai Allah ya jarabe ka ta yarda zai nunawa mutane irin hikiman shi a ko yaushe.
Sai yanzu umar da yai shiru yana sauraren zancen mahaifin nasa ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin .
Ni kaina daddy ranan na dade ina irin wanan tunanen wanda ita kanta hjy naga alaman nadama a fuskanta lokacin da zahra ke rungume da ita tana bata abincin.
Murmushi sosai kawu yayi a fuskan shi yana fadi kuma a fili Allah yasa hakan ne a zuciyar ta .
Yanzu ina son ka kara kwantar da hankalin ka kan zancen batar yarinyar nan kada ka zargi kowa a kan hakan don a bakin yarinyar cikin hikima zakaji komai da ya faru da ita ba sai an saka zargin kowa ba.
Sai zancen wa yan nan mutanen naga abin nasu ba zancen nadama a cikin shi don haka duk hukuncin da kaga ta dace zaka iya dauka a kansu sai dai ina mai kara baka shara ka kara hakuri har gaskiya ya gama baiyana kanshi kowa ya fahinci manufan mu kan hakan.
Insha Allahu ya furta a sanyayaye ba tare da ya dago kanshi ya kalli mahaifin nasa ba in a son ranshine yaso wanan karon ayita ta kare a tsakanin shi da wa yan nan mutanen.
Saidai a yanzu dole yabi ra, ayin mahaifen nasa kan hakan daya bukata a wurin shi yanzu.
Bai fita gidan ba bayan yabar wurin kawu din saida ya biya da yaran part din su mamu suka gaisa ya dan jima a wurin mamu suka dan taba hiran batan Queen da tayi.
Ya dawo gida babu kowa a falo ga yaran dake a takure don sun ki cin abincin da kawu yasa a kawo masu da suka zo wurin shi .
Na idar da sallah azahar ke nan na dan kwanta in huta don merry bata barni kwanakin nan na samu natsuwa ba da tabaran ta irin na kafirai idan masifa ys yasame su.
Yaron ya shigo ya shimfide a kusa dani yana fadin gashi yayi barci kuma akwai yunwa a cikin sa.
Yanzu jan sai ya falka kuma ai tunda naga barcin nasa yayi nisa sosai abawa sauran suci kada suma suyi barci a hakan.
Yana kai kofa ya juyo yana fadin merry dazun take fada min irin kokarin da kikai mata lokacin da wanan abin ya faru da Queen.
Kai haba ai dole mu rausaya mata son bata san kowa ba a nan bayan mu idan duk muka juya mata baya da wanne zataji a ranta.
Dan murmushi kamar yadda yake ga al,adan shi ya sake yana murda kofan dakin y fita nema sauke ajiyanzuciya nayi na sauko ina gyarawa yaron kwancia kafin in fito daga dalin .

Kula sosai nake ba hjy kuma alhamdullahi tana samun a banci a kai dakai sai hakan ya kara taimala mata wurin jin sauki .
Bayan kwana biyu ne merry ta kara zancen tafiyan ta sai dai yaya ya nuna mata bai yarda ta koma mai da yar shi ba wanan shine kuma sabuwar fitinan daya kara kunnu kai a gidan namu kuma.
Ashe tun wancan ranan da mukaji suna fitina akan hakan ne har yakai yar taji uban na fadin ba za, a tafi da ita ba ta bar mashi yarsa a nan.
Shine dalilin da har Queen din taga zasu bar kasan nan tare da mahaifiyar ta ta gudu ta boye a ban daki akai ta neman ta taki fitowa.
Sai gashi kuma a yanzu din kuma wanan irin rikicin ya kara aukuwa a tsakanin su haka yasa ya dauke Queen bada sanin kowa ba ya turata Abuja gidan habbib dan uwan shi.
Merry na falkawane bata ga yarta ba ta tayar damu da kururuwa da tashin hankali dole kowa na gidan ya fito don jin abinda ke faruwa.
Banda ya umar da bai leko falon ba inda merry ke birgima da ihu dauke mata ya da akayi wanda tasan aikin umar din ne hakan.
Nice dai na koma mai kaunar nata a yanzu don haka na shiga dakin yaya din don ganin halin da yake ciki bai fito ba.
Samun shi nayi yana shiryawa hankalin shi kwance yana kuma waya a lokacin.
Jin motsin shigowan mutum ya tsaya yana kallona bai kuma daina wayan nasa ba a lokacin.
Maganan da yayi ne yasa na fahinci yasan inda yarinyar take a lokacin wayan ya kashe ya juyo yana tambayana lafiya ?
Queen ce kuma wai ba, a gani ba yanzu ihun uwarta ya tayar damu daga barci nake fada mashi.
Tana gurin na kawai ya fada a takaice tsayawa nayi ina kallon shi da mamaki ganin babu fuska kan hakan na juya na fita daga dakin zuwa falo.
Nan na samu merry tana kira a waya haka ya bani daman nufar dakin hjy don in duba su da kwana.
A zaune na sake su dakin suna magana duk yanayin su baya a cikin dadi a lokacin kara sallama nayi na shiga dakin .
Mun gaisa nake mata ya karfin jikin nata ta amsa min a kasalance da sauki bari na dan dawo yanzu sai sha magani.
Wanan karon Asabe ce tayi magana tana fadin mun tashi da zancen shan maganin sai ga kururuwan wanan matar ya tayar muna da hankali.
Dan murmushi nayi ina fadin mama kin san tsakanin da da mahaifi dolene hankalin uwar ya tashi haka .
Wanan dalilin yasa bata son zuwa da yar kasan nan don kada ta san kowa daga bangaren mahaifinta take nisanta ta da kowa nasa.
Ashe kuma bata tsira da hakan ba don yar ta nace sai a kasan nan zata zauna yanzu tare da yan uwanta.
Ni wanan abinda mai ya kama fitinan matar nan tunda tazo ya isheni a gidan nan babu kwanciyan hankali sam ga zuwan nata.
Sai yanzu nake hango gaskiyan Alh daya nace kan sai umar

Please Login or Register in order to submit comment