You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dansanda ya tsaya yayi kafin ya mike yanawa saurayin godiya tare da fatan samun sauki ya fito ya leka a dakin da yaya yake kwance.
Bayan tafiyan dansandane kowa ke fadin albarkacin bakin shi kan abinda saurayin dake muna wanki ya fada wanda daga kauye ya shigo gari neman kudi dama nasir ya dauke shi aiki a gidan.
Ban furta komai ba don magana yana dan fara dauko kamahin gaskiya sai nake jin ko a can gidan mu da yaran suke zaune kamar basu tsira ba a hannun makiyan.
Don zasu iya cin masu can su dauke su tunda sunyi niyar yin hakan a kan yaran nawa haka ya jawo hankalina kasuwa gida biyu a gurin tunane yanzu.
Zuwan mamu da kawu ne ya dan kwantar min da hankalun don sun samu labarin abinda mai wankin mu ya fada tun suna gida.
Kawu ne yakw fadin in kwantar da hankalina tunda har Allah yasa mi sanin gane wani abu mara kyau yana shirin faruwa da yaran naji a jikina kuma har hakan ya faru .
Sai in godewa Allah in dage dayin addua don addua itace takobin mumuni Allah ya kara tsarewa insha Allahu Allah zaibawa yaya lafiya ya tashi da yardan ubanginji.
Wanan kamar kina nunawa ubangiji rashin godiyane yau da ace wanan abin ya zama sanadin rasa umar fa ?
Ashe ba zaki zamo mai tawakkali ga jarabawan ubangijin ki ba fatima ?
Jin kalamin kawu yasa na dago kai ina kallin shi tare da kokarin share hawayen dake zubo min a lokacin.
Bayan kawu ya mike don shiga yaga dan nasa ya rage wurin dani da mamu sai Amma dake lazumi tana sauraren mu .
A hankali nace mamu yaran basu damun ki ko a can don nasan su da fitina idan basu ganin dayan mu tare dasu.
Saida mamu ta sauke ajiyan zuciya take fadin basu fitinan komai tunda ga sadiya nan da maria suna gani yau daine ita yar fitinan ta matsa da kiran mummy mummy ina jin maria tana lalashin ta itama kanta maria ai abin ya bugeta sosai don bata a cikin dadin rai duk yinin yau din.
Sai lokacin Amma data shafa addua take fadin yo ina zataji dadi wanda kake tare dashi yana a cikin wani hali haka mara kyau.
Mamu n fada maku ni zuciyana tafi karkata gun merry din nan don yarta da yaya ya karbe a hannun ta yanzu.
Kada kice haka sayadi don zato zunubine koda ya zama gaskiya don haka ki daina wanan zargin.
Sai ya kasance ita bata ma san da wanan zancen ba sai wani ya taka sawunta yai wanan aikin .
Abin ne da kama ai dole yar nan tayi zargin hakan don biri yai kama da mutum gashi an nemeta an rasa a garin nan tun jiya.
Wata kila tsoron taji kamar yadda habbib ya fada ai ana kan bincike dai insha Allahu gaskiya zata baiyana komai daren dadewa.
Fatan mu dai Allah ya tayar da kafadan shi ya bashi lafiya yasa hakan ya zamo mashi kaffara a yanzu.
To Amin Amma ta fada tana kawar da kai tare da fadin ni dama auren sadauki da kafiran nan bai taba kwanta min a rai ba sai ace ranon yar nan daine kawai ya kaishi ga auren ta .
Amma wanan ai ba macen nunawa tsara bane a fage don banga wani abinda yaja shi gareta ba.
Aurene gwaggo Allah ya kaddaro akwai aure a tsakanin su da rabon yar nan da kika fada yanzu.
Idan ba wani abuba ai sai ya bata yar ta karata can da ita ta bar dan nan ya zauna lafiya Ammake fadan hakan.
Amma wai kin san sai da wanan matar ta saka aka kwace wa yaya komai a can da farko kamar zasu rabo dashi sai gasu kuma sun kara dinkewa daga bayan nan.
Ke yar nan ki bar wanan zancen aka kwace mashi dukiya kuma yake zaune tare da ita ?
Kwarai Amma don kawai kara aurena da yayi daga bayan nan taimakon yaya guda shine tun farko sunyi alkawari a rubuce cewa ga addinin shi ya yarde mashi ya kara aure .
Kuma ta amince da hakan saidai lokacin da tasan da zancen aurena dashi ta kaishi kara kotu dole kotu ga al,adansu nacan ta raba dukiyan sa biyu ta bata rabi.
Bata san da yana dabaran turo arzikin shi gida ba daga bayan nan kuma da ta sani ta biyo shi har kasan nan da jidali wai a cewan ta tare da ita suka samu arziki don me zai munafunce ta yayi hakan ba tare da sanin ta ba.
Rikincin gangan ke nan wanan ta zama Sarka mai rikucin gangan arziki nasa sun hada karfi ne tare da ita ?
Gwaggo kin san su ga al,adan su ai haka abin yake na miji baida halin yin wani abin ba tare da sanin matar shi ba irin namu na nan.
Yau ina mahaukaciyar uwar shi tazo taji wace tafita famkama da abin danta ita da da anyi zance zatace ni uwar maza ne masu arziki kuma ?
Yoni wanan jahilci ko hauka za a kirawa jimmai yau dai idan umar ya fadi ya mutu ke A ruwa kin fita kaso a cikin abinda ya bari shine kawai bakin ciki da hassadan jummai dama dake.
Amma ni ban taba tunanen irin wanan ba a rayuwana idan za a barmin shi yafi a bar min tarin arzikin da hjy ke hange.
Affa ke kika san wanan Aruwa rikicin jummai ai ba sai da dalili ba abin ya zake mata a jiki don ita bata bar kowa ba.
Duk da wanan abinda ya sameta baisa jummai yin nadama ba don dazun nan kuna ciki wurin yaron nan take fadin wai dama ana son ya tafi a mamaye abinda ya tara.
Har abin yaso zama masu fada da hadiye shine dalilin dana tura hadiye gida dazun .
Don ba zamu taru anan ana sayar da hali ba mutane suna tafiya damu a baki.
Kai halin hjy sai ita duk da bawan Allah nan yana cikin wanan halin bautan ubagiji zukatan mutane baya a kwance take wanan furcin.
Mamu ne ke fadin wanan magana tana kada kai taci gaba da fadin wa take zargin ya aikata hakan yanzu gareshi ?
Na nisa tare da fadin ni zancen hjy bai taba damuna a yanzu matar da taje neman wace zata kifar da mutuncina a gidan yaya don kawai kiyayya irin nata.
Mai kuma zatayi ko ta fada a kaina yanzu inji zafin shi a kwance take amma zuciyar ta na cike da sheri.
Kawai lamarin hjy sai addua a gareta idan tana da rabon shiryuwa Allah ya gyara halin ta.
Na dauka wanan abin da ta sameta a yanzu zai sa ta yin nadama sai gashi har yanzu zuciyar hjy bai saduda ba ga yawan aikata sheri gana tare da ita .
Kafin wanan abin ya faru na fito da safe na samu mama asabe waje tana kuka nake tambayan ta.
Da farko bata so fada min ba saidana matsa da nuna mata damuwa na take fada min ita ta gaji da halin hjy.
Don duk dawainiyar da take da ita bata ganin haka wai jiya don tace a kiran in duba ta take fadin ta fahinci akwai makircin da muke kokarin kulla mata nida ita.
Don taga yadda take shige mun idan na shigo tana wani yabona to ta sani duk kilibibin da nake kallona kawai take don ta gane nufinmu a kanta.
So nake kawai na karasa nakasata sai nace mata haba hjy wanan wani irin magana ne yarinyar nan fa itace fa silar samuwan saukin ki a yanzu.
Sai cewa tayi dani koda banzo ba idan Allah ya nufa zata warke ne ta tsani ki ta tsani duk wani ahalin ki jin hakan da nayi nace .
Wa,iyazu billahi hjy mai yai zafi hakan uwar jikokin kine fa kike aibantawa hakan.
Nice shedaniya kike nufi da kike kore min shedan komai to bari kiji indai a kan wanan yarinyar da tayi sanadiyar barina dakin aurena kike kokarin karata a gaba ki sani bani bake asabe.
Dama nasan ba don Allah kike min abinda kike min ba don wani manufa takine kawai don da ba zaki goyi bayan yarinyar nan ba haka alhalin kin san irin kuntata min da sukeyi da ita da uwarta.
Mama asabe ta kare da fadin yanzu FFatima ya dace duk irin kokarin da nake da hjy tace min wai ba don Allah nake kulata ba .
Don haka ni na gaji wallahi tafiyata zanyi ba zan iya wanan abin ba gaskiya jiya sai abinda hjy ta manta bata fada min ba.
Nace mama don Allah kiyi hakkuri kada kice zaki tafi don yaranta yadda suka daukeki bazasu ji dadin hakan ba idan kin tafi.
Hjy halinta sai ita wallahi ya kamata ace iyanzu kin saba da wanan halin nata ita da kanta zata dawo ta nemeki ai .
Tunda ba zata iya yiwa kanta wani laluran ba dole sai an taimaka mata bamu rufe baki ba mukaji muryan ta tana kiran mama asaben.
Amma tace ke ki duba min wanan abin mamakin don Allah wai mutum na kokari da kai kake masa wanan bala,in haka don wani dalilin naka can.
Ganin su kawu sun mike daga inda muke iya hangen su a zaune suna magana sunyi cikin dakin da yaya yake kwance da sauri.
Saurin mikewa mukayi lokaci guda don bamu san abunda yake faruwa ba a dakin suka mike zuwa dakin nasa.
Kusan nice a gaba wurin shiga dakin a tsartsaye na samu su kawu suna gaida yaya din da yake kwance yana bin kowa da idanuwan shi.
Sai dai duk gaisuwan da suke mashi bai amsa ba sai binsu yake da idanuwan shi kamar wanda bai karkare farfadowa ba a lokacin.
Zuwan mu kusa dashi yayi daidai da karasowan su hjy gurin hjy tana ririke a hannun yan uwanta.
Ganin su yasa muka dan tsaya a bayansu kada sai gaidashi da jiki sukeyi mai ina gefe tare da mamu da Amma sai hamdala nake ga ubangijin talikai daya rufa muna asiri yaya ya samu lafiya.
Ganin ba za,a sarara ba a lokacin yasa na karasa bakin gadon na fara fadin yaya sannu ya jikin ?
Sai lokacin ya dan juya kanshi yana kura min ido kafin yayi kokarin budan bakin shi yana son yin magana.
Sai dai ya kasa sai kuma ya lumshe idanuwan shi a hankali ganin hakan da yayi ne wani kuka ya kubce min lokaci guda.
Bani kadai ba kusan matan dake dakin hawaye suke a lokacin Amma na fadin saudaki sannu ya jikin kuma tana share hawaye .
Jin muryan Amma din yasa ya kara bude idanun shi a hankali yana kallon mu ya kara dago ido ya kalleni a karo na biyu.
Kuka nake yayin da iyayyen mu maza ke fada dani akan in daina kukan sai ya dan saki dan murmushi kadan ya lumshe idanuwan shi.
Muryan likitan shine ya shigo yana fadin haba a rage yawa a dakin don ba,a son a dameshi da yawa hakan zai iya kara jefa shi cikin wani damuwa.
Jin yadda nake kuka yasa likitan dago kai yana fadin why doctor fatima kin san aikin ki kece kiba da muhinmiyar rawa wurin taimaka muna kan maigidan naki har muka kai ga nasara.
Dakin yayi tsit yayin da wasu matan suke ragewa kamar yadda likitan da kawu balarabe suka umurta.
17/11/2021, 07:26 - 🤐🤐🤐: Dan juyo kanshi yayi kadan tare da kokarin mika hannayen shi gare ni lokaci guda sai kuma ya kasa yin hakan don jikin shi da yayi mai tsami a lokacin.
Ganin hakan kawu sani ya fara fadin Alhamdullahi da alama aiki yayi kyau ke nan tunda har ya iya sheda matar shi a yanzu.
Jin hakan hjy ta fara kiran sunan shi da babawo ya jikin naka ya kake ji yanzu ?
Kawu yana ganin hakan ya gane mai hjy take nufi yasa ya bar dakin ta hanyar yiwa matan shi dake wurin nuni da kofa ba bata lokaci suka bi bayan shi suna Allah ya sauwaka tare da adduan kara samun lafiya gareshi.
Dakin ya saura daga ni sai hjy da yan uwanta a tsaye mun zuba mai ido duk da ba magana yake iya yiba a lokacin sai numfashin da yake mayarwa a hankali.
Ganin yadda suke basu ko nuna alaman cewa sun san dani a wurin ba yasa na yanke shawaran fita daga dakin lokaci guda duk da ina son kara duba yadda jikin nasa yake a lokacin.
Wurin Amma na koma na zauna basu fito ba saida nurse tazo tayi masu magana suka bar dakin duk muna zaune a inda muke tare da Amma sai kara kwantar min hankali da takeyi.
Shigan likitan ne ya sa a kirani nazo da sauri yake fadin mara lafiya ne yace a kira mashini ina shiga hjy da suke daga gefen mu suka taso sai dai likitan ya rufe kofan babu halin shiga gare su.
Banji dadin yadda na samu yaya ba a wanan shigar don numfashin shi ba kamar dazun ba da muka barshi.
Isa nayi bakin gadon da yake kwance hankalina a tashe na kai hannuna saman goshin shi lokacin ne ya bude idanuwan shi a hankali yana kallona.
Ido ya dan kura min kamar bai ganeni ba sai kuma naga ya sakar min murmushi a cikkn karfin hali da daurewa na kara matsawa kusa dashi.
Hannuna dake saman goshin shi yake kokarin lalaba a hankali gane hakan da nayi yasa na kai hannuna da sauri na kama nasa.
Ji nayi ya rike hannun nawa sosai ya furta zahra na amsa da hawayen dake zuba a fuskana.
Stop crying yace min a daidai lokacin da likitan ya budewa yaya habbib da Aliyu kofan suka shigo.
Zahra zan tafi in barki da dawainiyar yaran mu ke kadai kiyi hakkuri da hakan zahra haka Allah ya nufa da ra, , , sai ya dan fara shakuwa.
Gaba daya rudewa sukayi Aliyu kan kasa zama a dakin yayi ya fito yana kuka wanda hakan ne ya jawo hankalin sauran mutanen dake waje.
Saida shakuwan ya lafa mai yake fadin habbib ko kasan merry ce ta saka ai min hakan dan yarta .
Wani kuka ne na sake sakewa mai sauti ga hannayen shi rike cikin nawa ya rikesu gam habbib yake fadin mun san da hakan bros don Zahra ta fara fadi.
Habbib i can't survive don haka komai ritsi kada ku bata queen ka hada ta da yan uwanta ku rike min su amana bazan rayuwaba habbib.
Bros ka daina fadan insha Allahu zaka warke habbib ke fadi innallilahi nake iya fada a lokacin sai kalman shahada da nakeyi a fili a cikin gigita.
Dago idanu yayi ya kalleni idon shi gaba daya sun canza kala irun yanan da ake jefawa bawa yayin barin shi duniya sun sauka a idanun shi a lokacin .
Hakan dana ganine ya kara rikitani sosai yaya habbib yake fadin in fita dakin kada in kara daga masu hankali.
Kaina girgiza naki fita dakin don koma nace zan fita din hannayen mu yana sarke da juna yana murmushi jin fadan da yaya ke min a fuskan shi na kara kai dubana gareshi a lokacin idanuwan shi sun kara canzawa ga baki daya.
Allah ya ban hikimar kara furta mai kalman shahada sai naji ya karba min daga haka naji hannayen shi sun sake lokaci guda a take na kira sunan shi da karfi.
Saidai ina Allah ya riga da yayi ikon shi ya karbi abinsa lokaci ya cika babu sauran magani ni din dai da hjy ta tarewa ganin shi take hana in shiga dakin.
Allah ya nufa yaya zai cika a hannuna ta faru ta kare sai mu yanzu tamu ta rage shikan ya tafi abinsa ubangiji ya bamu cikawa da kyau da imani idan tamu tazo.
Likitan ne yayi dan aune aune yaja zanin ya rufe yaya umar a gaban idon mu muna ganin abin kamar a mafalki mai rabawa ya raba tsakanin mu da yaya umar din.
Ban samu kukan ba lokaci daya idanuwana suka kankance ina gani dishi dishi likitan yace yaya habbib ya kamani.
Fitowan mu yasa kowa ya gane abindake faruwa gurin Amma yaya habbib ya kaini itama Amman kuka take sosai hhaka yasa yaya habbib kiran su kawu yana sheda masu abindake faruwa.
Kafin wani lokaci labarin ya zagaye yan uwa da abokan arziki yaya Ahmed ne ya kaimu gida shida salma da Amma gaba dayan mu kuka muke sosai a lokacin.
Dare yayi don haka aka bari sai safe a kawar da yaya zuwa makwancin sa gaba daya lokacin ban san a inda nake ba don rudewa.
Hankalin kowa yana a tashe da wanan mutuwan mai girgiza zukata dayazo muna lokaci guda ga zancen merry dake ta yawo har an fara neman ta a ko ina a cikin fadin kasan nan.
Ba karamin jama, a yaya umar ya samu ba da sukai masa sallah da rakiya zuwa gidan gaskiya ga sheda na alheri da sai a yanzu muke jin irin alheri da taimakon al,umma da makwabta da yaya yakeyi idan yazo Nigeria ashe.
Dama ba a fadin halin ka sai bayan ranka kowa ke fadin albarkacin bakin shi a kanka Allah ya bamu ikon cikawa da imani Amin.
Karfe goman safiyan jumma,a aka kawar da yaya zuwa makwancin sa nayi kuka kamar raina zai fita banci bansha sai idan an tsareni don dole zan dan kurba ruwan kunu a cikina.
Da akai kwana uku yaya habbib yazo akan in koma gidan mu in zauna kada a bar gidan babu kowa don masu zuwa gaisuwa haka yasa muka kwasa muka koma can dani da manjo da Amma da suke tare dani a kowani lokaci.
Iyakata da mutane shine idanu idan kaji maganata sai yara suna kusa dani tunane babu wanda banyi a lokacin ji nake dama mu duka aka harbe da zaifi da barin na da yaya yayi a duniya ni kadai.
Sannu a hankali har na dan fara sabawa da rashin yaya a tare damu inda abin yazo min da sauki har yaran da yake shi yaya mai yawan tafiyane a lokacin da yake a raye haka yasa ko yanzu sai nake ganin kamar tafiya yayi zai dawo.
Hakama yaran kan dameni da tambaya yaushe ne daddy su zai dawo kamar yadda suka saba tambayana idan yayi tafiya.
A wansn zaman makokin da akayine aka samu aka shawo kan kawu ya mayar da hjy dakinta tunda Allah ya raba akan wanda suke fitina a kanshi.
Da farko kawu ya kafe akan har abada bazata dawo gidan shi ba tunda har yanzu bata saduda ba ko bayan mutuwan yaya saida ta tafka wani tsiyan ma.
Don kawai na aiki driver da motar yaya din ba kuma aiken shi nayi haka kawai ba shine yazo min da maganan akwai wasu takardun yaya da zai tafi ya karbo nace ya dauki motar ya fita da ita don sheda.
Shine aka fada mata tunda safe tayi min tas a gidan tana fadin sai a bari a raba gadon yaya da muke kwadayi nida uwata da yan uwana.
Wanan maganan ne yakai kunnen kawu yazo gidan yaiwa hjy tas akan ta fita harkata ta barni inji da abinda ya dakeni na rashin mijina.
Wanan abinda tayine yasa kawu cewa ba zai mayar da ita gidan shi ba saida aka taru dattijan unguwa suka bashi hakkuri da kyar ya yarda da sharadin ba zata kawo mai wani tashin hankali ba a yanzu kuma.
Gidan ya rage dagani sai yarana sai yan aikin dake gidan yaya habbib da yaya umar dama Nasir babban abokin yaya suna tsaye a kan mu bamu nemi komai mun rasa ba a rayuwan mu tankar yaya yana raye.
Mun cika kwana arba,in cif da yake inada karamin ciki wanda hjy sai daga baya ne take jin zancen cikin jikina din tayi fadan hakan kamar tsiya .
Inda take fadin wai da gaiya nake zuba haihuwa haka a gidan yaya dan kawai gadon mijina ga gadin nan dukiyar ai anbar muna muci.
Ni dai tashin hankalin yai min yawa na hjy don kulun safiya da irin fitinan da zata fito dashi duk kashedin da kawu yai mata kafin ta koma bai hana hjy tsula halin ta ba garemu.
Kamar ba dan cikin ta ta rasaba a lokacin gaba daya abinda ya bari a duniya ya rufe mata idon ta sai tsakure tsakuren maganan da takeyi.
Nazo ma kawu da zancen komawa na school tunda yaya dai ya tafi ke nan ba zai taba dasowa gare mu ba kuma gara in nemi na kaina don in kula da yarana da suke kanana tun yanzu .
Don gaba daya ban gane mai ake ciki da dukiyan shi ba kodan ban sawa kaina damuwa da hakan bane a lokacin oho ?
Saida kawu ya tambaya aka fada mai mudfin zan kula da kaina in tsare mutuncina zan iya komawa can in kammala har zuwa lokacin da zan haihu don dama idda ya saura min kuma ga ciki a jikina.
Aiko hjy najin zan koma London da yara ta samu kawu da zancen bata san wanan maganan ba har idan zan koma ne ma sai dai idan za a hadani da wani muje tare don ita sam bata yarda in koma ni kadai ba saboda ba,a san abinda ya bari acan ba.
Kawu yace a kausashe jummai kina da hankali kuwa kin ko san abinda kike fada kuwa da alama dai kamar kin dan motsu.
Tace da hankalina sarai Alh yardane kawai banyi da ba da ko wace mace ba matarshi bace tayi sanafin barin shi duniyan nan don me yanzu zan yarda da wata kuma.
Kiran habbib yayi bayan ta fita don kawu bai kara kulata ba yace suzo yana neman su bayan sunzo ne yake fada masu bukatana.
Sai habbib din yace nima nayi tunanen hakan gareta tun farko sai dai ban sani ba ko tana da daman yin hakan ga addini tunda tayi nisa ga karatun nata.
Kawu yace to ba wanan ba dazun muka gama magana da mahaifiyar ku ta nuna bata yarda Fatima ta tafi ita kadai ba don ba,a san abinda ya tara a can ba kada ta tafi tayi rub da ciki dasu ita kadai.
Innalillahi suke maimaitawa tare da fadin kai haba mama koma mai yaya ya bari a can ai ko fatima taci abinsu ita da diyanta taci bana wani ba.
Ku kuka san

Please Login or Register in order to submit comment