You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

uwa taki dan dan ta to ba dawowa dake akayi ba kinzo ne ki gane mu ki koma.
Mutane ba abinda suka aje a ransu sai bakin sheri da gulman tsiya du kuma tsuliyan su tab da kashi.
Wan yar gurin lami har ciki tayo na banza ban san ya sukayi suka barar dashi ba a gidan nan bayan ciki ya girma kowa ya gama gani ta dashi a gari.
Tasha wahala kamar zata mutu Allah dai yayi da sauran shan ruwan ta bayan taji sauki sai gashi kuma ta koma harkan banzan yanzu ai baki ga tun shigowan ki garin nan bata gidan nan ba.
Wani irin ba dadi naji har cikin raina dan dan uwanka dai dan uwankane ko yaya wani abu mara kyau ya samay shi dole kaji daci.
Mikewa nayi ina daukan ledan naman zan fita manjo tace ina kuma zaki dashi nace su umma saude zankaiwa kada ya lalace tace ban abina nan gobe ke dumama min inci ko ki muna miyan shi.
Manjo ki bari a basu don Allah goben sai a sayo maki maikyau in maki miya da akwai kudi sosai a wurina ai.
Ba dan taso ba haka ta kyale ni na fita tana mita kansu naje kofan dakin najiyo muryan saratu din ta dawo tana fadin a ruwa fa mama saude.
Tace ita kuwa saratu girman dan mutum baida wuya wallahi kinga yadda yarinya ta goge ta zama wata yar birni da ita haka ?
Tayi kyau kamar a waje take zaune ba a cikin kasan nan ba ni canzawa yarinyar ya ban mamaki sosai.
Umma lami tace kai saude tun dazun fa kike dada yarinyar nan wa yasan tsiyan da take shukawa a can.
Sallama na yasa su dakatawa da maganan na shigo falon sai wani warin da gahi ya doki hanci na nace ina mikawa mama saude leda ga wanan manjo na sayowa ta kasa ci kada ya lalace.
Da sauri ta karba tana fafin a, a kuma dai babba yanzu sai a hankali muryan saratu ne ke fadin wai a ruwa kece nan da gaske ?
Murmushi nayi nace nice anty saratu mun samay ku lafiya ai tun dazun nake tambayan ki akace bakya nan.
Ina kokarin juyawa tace don Allah tsaya in kara ganin ki wai kece a ruwa haka ?
Murmushi nayi tare da fadin anty saratu bari da safe ma hade zan gyarawa manjo wurun kwanci ne.
Ina fita naji mama na fadin may ye a cikin wanan leda din ta bude tace may nama ne mai tarin yawa fa.
Ai gaba daya sukayo ruuu wa nan nan aka fara gardaman yadda zasu raba ba tare da saura diyan sun gani ba daga ciki anty kubuta tace ina jinku wallahi a rabashi kowa ya samu ehee.
Tare muka kwanta da manjo saman katifan nata na ragga sai dai nayi dabaran gyara wuri ta bakin katifan idan tayi barci in sulale in koma sama hakan akayi.
Don ina jin tayi barci na dawo kasa ina ta tunanen labatin da manjo ta bani yau wanda ban taba sanin shi ba.
Washe gari kiran sallah masalacin unguwar ne ya tayar damu tunda nayi sallah na zauna ina karatun kur,ani na wajen do yanzu na sauka sai dai tulawan da nakeyi din.
Sai da rana ya dan haska na mike na fito gidan babu motsin kowa don ba zance sun tashi suyi sallah ba ma lokacin daga dakin manjo na fara na share ko ina.
Sai na fito tsakar gidan shima na gyara ko ina jin motsina yasa mama saude fitowa tana fadin fatu har kin tashi a raina nace ni yasu nikan naci suna kala kala a duniya.
Amma a fili dan dariyan yake na sakar mata tare da rusunnawa ina gaida ita da kwana ta amsa a washe tana fadin baki gaji da gajiyan hanya ba kika hau aiki da wanan safiyan haka ?
Mama wurin ne yai min ba dadin gani shine nake gyarawa na bata amsa tace kin san gidan namu ne ai sai a hankali.
Bayan na gama na shiga hura wuta ruwa wanka na fara kaiwa manjo kafin in dawo na dora na shayi don nayi niyar yau a gidan sai kowa yasan nazo garin.
Bayan na dora na fita na sayo bread mai yawa leda biyu yadda zai ishi kowa da kayan tea ban samu a shagon isah ba kamar yadda nayi tunane sai dana dan taka zuwa gaba na samo abinda nake son saya.
Na dawo na samu manjo ta fito ina shiga take tambayana ina naje nace na sayo abin karyawa ne waje.
Tace da kin bar naman jiya da bamu karya dashi din ba dariya nayi mata nace manjo kefa kikace ya isheki naba masu ci yanzun kuma zancen naman bai fita ranki ba har yanzu ?.
Ba kunya ranan har fada suke wurin rabon bread din dana kai masu da ruwan shayin dana hada mai yawa kowa yasha.
Na dawo na zauna na mulke jikin manjo da mai tun tana fadan hakan har ta kyale ni nace ko may yasa ku tsufin nan baku son mai haka nake fama da Amma idan tafito wanka sai na mulke ta da mai itama .
Sai lokacin na tuna da zancen tsaraban da Amma ta ban in kawowa manjo mikewa nayi na dauko da kyat ina mamakjn may ye a cikin kayan haka mai nauyi ajewa nayi gabanta ina fadin wanan sako ne daga Amma tace a kawo maki.
Kallon kayan tayi kafin tace ikon Allah wanan duk may ye a cikin sa haka ?
Ban sani ba na bata amsa tare da fadin ga dai abin da nauyi sosai tace bude muga abin arziki nikan wa yan nan mutane suna kashe ni da farin ciki a duniya.
Bayan na bude na fara zaro kayan a hankali abune a cikin leda baka an nade sai wani buhu wanda na bude semo ne ciki irin na leda leda din nan su tumatur da galon din mai sai shimkafa irin wanda diyanta ke kawo mata ko wani lokaci bata ci sai mama hadiye da yaran ta ke amfani dashi.
Shine ta bayar a kawo wa manjo din yanzu ikon Allah wanan matar ta kashe ni da kunya na zauna ina bude ledan turmin zani ne a ciki guda biyu suma dai irin da ake bata din nan ne kyauta ta hadowa manjo dasu.
Naja kayan gefe na dauko nawa tsaraban na fara fitarwa ina nuna mata harda abinda ban sani ba mamu ta hado min irin sabulu dasu omo clean man shafi masu yawa don rabo.
Manjo tace yar nan wanan uban tsaraban haka mai yawa mutanen nan basu gajiya haka da dawainiya.
Duniya ke nan baka san inda zakaci arzikin wani ba rabonki yasa muna ci daga tsagon wanan mutumin yanzu a ruwa.
Allah baibar maki mahaifin ki duniya ba gashi ya baki uban goyon da ko mahaifin ki na raye sai hakan gare ki.
Manjo ke nan nace ina zama don bude jakkar da na shako da kaya wanda duk rabi na kyautane a cikin su ga wani ghana most go dana shake daban don ni ko yaushe cikin yi min kaya mamu take shiyasa na iya kwaliya kamar may yanzu.
Duk wanan kayan da kike fitarwa na maynene manjo ta tambaye ni nace bayarwa zanyi amma sai Atika tazo ta zaba ikon Allah yau A ruwa kece mai ba da kaya hakan ga wasu.
Ta kara jijiga kai tana fadin abin Allah wuya gare shi yau ina lami mai maki gori da sallah ta fito taga ikon Allah tunda farar safiyan nan haka ?
Nace kai haba manjo ki barsu kawai Allah yafi su akaina ko yanzu ai hakan dadin kine manjo koba haka ba na fadi ina kallonta don kawai in hanata wani katobara don nasan abu nacin ran tsohuwar sosai.
Atika ta shigo na baje mata kayan ta zabi wanda ranta yake so a ciki don ba zan manta halarcin su a gare ni ba ni da kaina na tayata zabe na kwashi kayan nakai wasu kubura sauran.
Ban samay su wurin ba sai na bawa mama saude dake aiki kamar jaka a tsakar gidan ita kadai na basu nasu tsaraban danazo masu dashi.
Fita mukayi da Atika zuwa gidan su acan na aika akayo mun chafane na dawo na hadawa manjo abinci mairai da lafiya har da ganye na hada mata.
Naba kowa na gidan rana har da godiya akai min hakan da umma lami taga inayi sai hassada ya shiga cikin zuciyar ta da yamma sai gata ta yafa wai zata unguwa.
Ta dan jima da fita na sharo dakinn na fito ina share waje mama saude ta dan fita ta leka waje sai gata ta dawo naji tace nikan fatu ina son yin wata magana dake idan zaki rufani.
Da sauri nace mama may ke faruwa ne kuma tace tau zan dai fada maki gaskiya kiyi hankali da yaya a gidan nan don ta fito fili ta fadi tana bakin ciki dake fatu.
Yanzu ma wanan fitan nasan wani sheri za,a tafi kulla maki don ki aka fita tace sai ta danbalaki kin koma kowa na kyamarki duniya.
Innalillahi nace tare da fadin may nayi mata mama saude na fada cikin tsshin hankali tayi saurin fadin rufa min asiti fatu kada babba taji zancen nan don Allah.
Kin san idan baba taji yau akwai tashin hankali a gidan nan sai a dauke ni munafaka kuma.
Nayi maki alkawarin fada maki duk wani mugun nufin da yaya ke yi a kanki ko ba yau ba don har nima bata barni ba.
Yanzu dai don ki yarda dani har in indan ta amsa wani sheri zakiga ta baki abin dadi tace wake kawai ta dafawa shi kada ki yarda kici wanan abin idan ma son samu ne kawai ki kiyayyeta ki saka mata ido na kwana biyu ki fahinci komai a kanta.
Nace mama na gode tace don Allah kada ki bari babba taji wanan zancen din ba zata iya rikeshi a ranta ba.
Naji mama na gode nace na juya na tafi zuciyata cike da fargaba zancen sai tunanen abinda naiwa umma lami nake a raina sai dai na rasa kamo amsa.
16/11/2021, 23:11 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHEEM

Haba yar uwa mayye ribanki cikin daukan alhaki ki saida imanin ki don kawai ki gyawa wasu rai bada abinda zan hada ki dashi sai daran Allah dana Annabin rahama sai darajan iyayyen ki.
Uhumm wai duk baki dubaba saboda son zuciya da da hassada kin gwammace mu abiki hakki gobe kiyama baki san ko kwayan zarra sai an futarwa mutum hakkinsa ba kina ganin kamar a nan duniya zamu tabbata ne.
To ki sani yanzu Allah baiba mutum bashi tun duniya zaka girbi abinka wallahi na biki hakki dake da kika fitar da wanda kika turawa ya yada Allah ya bi mu hakkina.
Ranan dai idan nace nayi barcin kirki a gidan nan karya nayi maku don tunane ya cika min zuciya na da firgice saboda na rasa gane mai nayiwa umma lami har take son ta illantani duniya.
Washe gari kamar kullu ina tashi bayan na idar da sallah karatun kur,ani nayi sai da gari ya haska na mike dan gyara wuri da wuri nayi ma manjo abinci nace unguwa zamu da Atika don haka nai mata abincin da zai isheta har wani lokaci.
Bayan na gama ne na dibar masu nasu kashi biyu na mikawa kowa nasa hikimar yin hankan gare ni umma lami ne da yaranta zasu cinye su kadai.
Ruwa na debo a bakin famfo na surka na shiga wanka na dade a zaune ina shiri duk da ba kwaliya nake yi ba amma ranan na bata lokaci ina kwalliya.
Wani yello less na saka a jikina mai dan flawer da zare bulle a jikin shi sai duwatsun dake shana shi idan ka gitta.
Takalama da jakka blue na dauka sai dan oud dana shafe jikina ya dauki kamshi don mamu ta saba min da shafa turare mai mai na arab a jikina ko tufafina banda hammata da chest dina kawai ban shafawa don gujewa cancer.
Manjo na tambaya ko tana son wani abu sai cewa tayi bana son komai yar nan dan dama wanan lemon kwalban mai sanyi.
Murmushi nayi ina fadin wann bakin dai naki manjo na gane kwadai yake so a cikin sa fita nayi zuwa waje inda shago yake na sayo mata multina da fanta guda hudu na kawo mata .
Yayin da idanuwan su kubara dake kwaliya a kofan shiga wurin su yayo caaa a kaina har saida na tsargu da kalln da suke min din.
Ban dade da manjo nayi mata sallama bayan na aje mata komai a kusa da zata bukata a wuni hatta ruwan sha na sayo mata mai sanyi nayi mata dibara sakawa a wani tsohon kulan dake dakin tana fadin kin ga maganin ajiyan tsofi gwaggon duk zuwa sai ta min korafin in yarda shi naki.
Ina fitowa duk suna waje nasan gulmana wa yanda ke waje suka kai harda umma sai da nagani a wurin na taka kamar tarwada zuwa wurin su tun kan inyi magana mama saude tace yau kan yar gidan babba ina za a haka da wannan kwaliyar ?
Muushi nayi ina fadin zamu nan gidan samirace yar ajin mu da tai aure na juya ina fadin umma zamu ziyar ne yau zan tafi.
Ba zaki dade ba ke nan ko ta tambaye ni cikin kallon fuskana kada plan din ta ya baci nasan nace zuwa sha daya insha Allahu zamu dawo.
Tace to a dawo lafiya ina bada baya taja tsuki tana fadin sai na kasaraki ai yanda ko kare bai sunsun naki don bakin jini mu za,a kawowa barkado a gida ?
Ke a dole uwarki ta fifitaki akan yayan mu wallahi karya ne baku isa ba daga ke har uwartaki da kike kuri da ita.
Haba umma ni ban son irin haka wallahi fatima fa yar uwan mu ne umma idan kin kasarata ai mun kara yawa ke nan muku a gida ?
Kubura wallahi ki fita min a idona tun ban saba maki ba wawiya daba tasan inda ke mata ciwo ba kinfi bukatan ta dinga kwaso tsumakara tana kawo maku kwance kuna jin dadi sakawa ba ku hakan zaima ku dadi ko hakazaifi maku dadi ?
Nidai don Allah da kin barta har sau nawa fati kr zuwa garin nan da zamu ganta harara ta watsa wa yar nata sai ta kasa karasa maganan don kallon da uwar tai mata.

Hjy jummai tayi mamakin ganin yayan nata data gani kamar daga sama washe gari ne suna zaune Umar ya shigo falon kamar an jefo masu shi sai mamakin ta ya karu sosai.
Abinci aka gabatar mai bayan yan gaishe gaishe tana fadin ku lafiya wanan tafiyan haka babu sanarwa zuwa ai maku tanadi.
Daddy bai fada maki komai bane mama Aliyu ke tambayanta hakan cikin tsure ta da idanuwan shi.
Alh kuma ni bai ce min komai ba ta fada slowly a cikin muryan mamaki da tunane a ranta.
Ko ma dai mainene ai zai fada muna tunda ya kiramu kuma gamu munzo inji habbib ya fada a miskile shiko umar baiko ta kansu don ko abin karyawan da aka aje mai bai taba ba.
Kodai wani abinne ya taso yake neman mu hakan cikin zolaya Aliyu yace zancen auren ku ba kila wani kallo habbib ya watsa mai tare da fadin kainan daban ne idan ma auren ne ?
Wani aure kuma hjy tace tana mere bakin ta tace aure kai ai yabi ruwa kowa yaje gaba ya neme nasa badai diyana da wanan gamin gambizan ba.
Mama ni fa har yau ban ko san yarinyar da daddy ya lika min ba don koda yace inje mu gana wani zuwa danayi banje ba har na wuce.
Ai gara ma yar wurin bros wancan zuwa naga ta girma sosai tayi clean gaba daya lokaci guda kodan ban ganta da katon hijjab din nan bane oho ?
Umar ya dago kai daga abinda yake a cikjn waya ya watsa mai wani kallo ya kama dariyan mumuke .
Yace Allah bros da abin mai yuyuwa ne akwai iri mai kyau fa gurin don ko ina zaka shiga da ita nan gaba.
Kai karabani da zancen haushi a gabana habbib ke wanan irin magana ko da itace autar mata ba zata taba shigowa ahali na ba mudfin ina raye.
Kyau dan maciji ko kunama may ake da irin da ko asalin su basu gama sani ba maimuna fa har yau bata san uwar ta ba a duniya.
Kai wai mama da gaske ne wanan zancen ni tun tasowana nake jin ana wanan maganan fa ashe gaskiya ne ?
Yo ina tasan ta dama irin yan cin ranin nan ne ai ubanta ya gani ya aura da iyayyen ta zasu koma kasar suna sudan suka matsa saida ya sakae masu ya suka tafi da abinsu har yau basu kara waiwayan ta ba.
Shegiya dama ta tafi da wanan annoban amma hajiya ta hana a wanan lokacin dole ta tafi tabar yar a nan ashe annoba zata zomowa mutane nan gaba.
Umar ya dago kai ya kalleta don jin zagin da ta aikawa mamu din tace na zagi kanwar uwar ka ko miskilin banza.
Maimunan nan kamar tayi ma wani asiri a kanta tun kuna yara nake rabaka da ita kuna leke da juna.
Dan murmyshi yayi yace kai mama zagin dai ne ba dadi maimuna kuma tare muka taso a gidan nan muna yara shine shakuwana da ita ba wani abu ba.
Koma dai may na hana wana hurdan a tsakanin kai baka ko kishina da alama mai kina kake shigewa jiki.
Shidai bai daga kai ya kalleta ba sai dakilan wayan hannun sa yakeyi can dai ya mike ta kalle shi tana fadin ina kuma zaka yanzu.
Zan leka Amma ne a wurin ta nasan yanzu tasan nazo don akwai yarinyar data ganni gidan nan nasan zata fada mata nazo.
Ko dai yar tsanarkace ta ganta hjy ta kalle shi tana tsuki tace wanan yar banzan yarinyar bana wai ta tafi garin su ganin gida nima jiya maryam ke fada min tafiyan su.
Shidai yasa kai ya fita ya barsu a gurin yana ficewa tace wata kila wani abin ne ya bata mashi rai da zuwan shi haka ?
Yana tunane iyalin shi daya barone ba shiri kila don kiran gagawan da akai mai ba shiri yazo.
Arniyar matar nan zan waiwayeta don har yanzu bata kwanta min a raiba na tsani ganin ta a rayuwana.
Babu wanda ke son ta a gidan nan idan ka dibe shi daya kwasota gidan nan kaf in maka na mahaukaci kyamarta suke.
Ba wani abin kyama halin merry dai na rashin son yayi hurda da yan uwanshi shine matsala ranan fa munje gidan ta hana muna ruwa common ruwan sha fa mama.
Ta gyara zama tana fadin ita din da kanta lale arniyar nan ta samu guri da yawa zafin ran babawo na banza ne.
Shiyasa nake kara kyamatan wanan bakin hadin da Alh ke son yi maku don maimuna na iya kwace min da da kilibibin nan nata.
Shiru sukayi suna sauraren ta ba tare da sun furata komai ba ga kalaman ta da takeyi akan maimuna din.
Sallama yayi kofan falon tace lale marhabin da mutanen turai sadauki kaine yau ka leko mu kasan nan ai ka kyauta duk da dai kadade baka zo din ba ko yar nan da aka haifama bamu santa ba.
Zaku santa Amma idan sunzo don zuwan merry kasan nan ba yanzu ba don yarta sai kila idan ta girma zamu shigo dasu wani lokacin yana zama yake wana magana wa Amma din da take tambayan shi.
Sadauki irin dadewan nan haka ba a leko gida ba baida dadi wallahi an san aiki yana yawa amma mutum ya share gida har wani lokaci.
Ai hakkuri Amma nima hakan bada son raina nake dadewa ba don aikina ne da yaimin yawa ko wani lokaci.
Ina mai dakin naka take da yarta ina suna lafiya ya kuma jama,an wurin naku suke ?
Dan bata rai yayi yana fadin suna lafiya Amma baki san dalilin kiran mu da daddy yayi ba haka a cikin gagawa ?
Shiya kiraku kasa nan ashe tayi mai tambayan malam bahaushe mai ban haushi.
Mayar da kanshi yayi saman kujeran da yake zaune a kai ba tare daya iya bata amsa ba ga nata tambayan.
Itace tace wata kila dai akan wani maganan siri ne ya aika kuzo haka sai dai ni bai sanar dani komai ba gaskiya.
Shidai baiyi magana ba sai faman tunane yakeyi a ranshi ko dai maganan mama gaskiya ne idan haka ne mai zaisa daddy ya lakantani da zancen dukiyan shi bayan yasan ina da nikin baninkin din su a hannu na koma dai may nene zamu ji ai yace.

Ta shiga ta fito daki hankalin ta a tashe tana jan tsuki tana magana ita kadai kamar mahaukaciya mama saude ne da abin ya dama tace wai yaya lafiya yau kuwa ?
Tace uhumm bari saude abubuwa ne suke son yi min yawa a kaina yau ta fadi tare da shigewa dakin mama saude ta bita da kada kai tana fadi a ranta mugun nufi yabi mai shi.
Daga gidan su samira mun shiga wurin gida biyar muka dawo gidan su Atika muka yada dandali bayan karfe hudu.
Hankalina yana gida wurin manjo saidai kamar an kashe min jiki da zuwa gidan bayan muyi sallah na kwanta a gurin ina dakilan wayan Atika shiya dauke min hankali na manta da komai dake gabana a lokacin.
Bayan sallah magariba dana isha, kuma na dasa wani kallo ina kallon ci gaban shi hakan ya jani har goma da rabi ban shiga gida ba.
Saida umma ta leko dakin tana fadin nikan yau a gidan nan zaki kwanane dare fa ya somayi sosai take fada min na zabura da sauri ina kallon lokaci a wayan na mike ina fadin yau nasan zan sha fada wurin manjo kan don nace ba zan dade ba da zan fita.
Har cikin gidan mu Atika ta rakoni muka shiga dakin manjo da muka samu har ta kwanta a lokacin sai dai batayi barci ba.
Tana ji mu ta daga tana fadin yaran nan ina kuka shiga haka tun safe kuka fita nace wallahi manjo ina nan gida su Atika muna kallo ne ya dauke mi hankali.
Jin hayaniyar mu ne ya sanarwa umma mun dawo sai gata kofan tana fadin yau ina kuka shige haka yarnan tun

Please Login or Register in order to submit comment