You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin bata rai.
Hjy tace look merry exchange words with you ki bar wanan kayan a nan daga haka ta juya wurin umar tana fadin ka fara ganin abinda nake fada maka ko ?
Mama ki bar wana zancen hakan bai dace ba wallahi irin dawainiyar maimuna gareta yasa ta sayowa yaranta chuculet.
Nan babu yara na datun farko damu ra saba zata san wata maimuna ne can ?
Mikewa meery tayi duk suka kalleta lokaci guda yana tambayanta ina zuwa tace the other part daga haka ta fice daga part din.
Ehyeh wanan kafirar dani take wasa zan sasaba mata a gidan nan ita wacece da har zatai bugun gaban kanta ka fada mata ta dawo nan yanzu ko in saba mata tasan halina.
Yacw haba mama hakan bai dace ba gaskiya bakuwace fa kuma su ba al,adan su bane hakan suna zamane da wanda zuciyan su ya kwanta ne.
Babawo kana son mu gama dakai lafiya to ka kiyayyeni a gidan nan wallahi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:05 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM WA, WA DADAKA A, ILAN FAHADDE, , , , ,


Mamu na zaune tana waya yayin da mu muna zaune mun fara cinn dan waken fulawa da dan wake kadan a ciki da mamu ta shirya muna as a lunch.
Ko wanan mu na son wanan cimar haka yasa muka bazu a falon mu mun mai dashi abin marmari don haka wasu mu naci da tsinke wasu suna ci da fork.
Sai ganin merry mukayi ta fado falon ranta a bace tana fadin i told you I don't want to go there that woman hate me at all she fight with out resing.
Mumu tai dan murmushi tace don't mind her is her habit, she can't talk polityly.
You have to bear it she is you mother inlaw so nerver mind with her habit.
Dan zaku dawo ku zama daya wata rana idan kun saba yanzu abin yana sabo ne a gare ki ta dan mede baki alaman abin ya ishe ta.
Dan wake mamu ta zuba mata a plate tana mika mata saida ta dan kalla ta girgiza kai don bata taba fani shi ba kuma bai burgeta ba.
Mamu tace test it will enjoy it , is made with bean and flower tadai karba a ya tsune tana dan kokarin dauka a kyamace daga inda nake zaune haushe da takaicin yadda mamu ke lalashin ta taci ya cika ni.
Yaji na dauko ina karawa nawa da mai ta bini da ido tana kallona sai gashi ta hade wanda ta saka a baki tana kara daukan wani takai baki.
Sai ga merry na batun tashi da plate din abincin gaba daya da aka zuba mata ko magana bata yi sai ruwa da mamu ta zuba mata mara sanyi don ta kula bata shan ruwa mai sanyi sosai.
Muna gab da gamawa ne ya fado falon da sallaman shi ya dan tsaya daga kofa yana fadin sorry nayi distubing din ku a yanzu.
Mamu tace ba komai dan wanke muke ci da mai da yaji dan murmushi ya kirkiro a fuskan shi yana fadin ta iyaci don an tsanmanin ta taba cin sa ba?
Aiko gashi sai ci take babu kakautawa mumu ta fada da dan murmushi ya danyi kamar zai zauna sai kuma ya ja ya tsaya yana fadin na gode kwarai maimuna da wanan karramawan sa kike mata sai dai ina ganin zuwa wani sati zamu koma don shirin haihuwan ta don ina ga ta kusa haihuwa yanzu ga lissafin mu.
Mamu tace da sauri haka zaku koma ai na dauka a nan zaku tsaya sai ta haihu kan ku tafi ?
Ya dan sosa kai yana fadin zanso hakan nima sai dai hakan ba mai yuyuwa bane don ba zata so hakan ba ita ga kuma wanan yawan fitinan datake fuskanta wanda ba sabawa da hakan tayi ba ita.
Kayi hakkuri umar wanan ba zai sa ku wuce a yanzu ba da zaku dan daure ku kara lokaci zaiyi kyau har ga iyayyen ku yanzu sai suga ai ba wani dadewa kukayi a kasan nan ba zaka koma kuma.
Kaga sai su dora laifin ga ita merry din datazo daga baya ya dan ja iska ya furzar tare da fadin nasan zasuyi wanan tunanen a ransu amma ba yadda zanyi ne don tun yanzu merry ta fara fuskantar matsala da hjy wanda ba zan so hakan ya faru ba gaskiya.
Hakkuri zakuyi don iyayye dama zama dasu sai hakkuri don kullun a yara suke kallon ku kadai ga yadda yake kasancewa ko ga mahaifan mu ai.
Dazun da ka ganni daga wurin baba nake yau min tas daga naje mai da shawara sai yake ganin na raina su.
Dan tsohon nan ai bashi da fada ko sosai sai dai yanzu da tsufa ya fara zomai dole ne ya fara fada kan dan magana kadan.
Muryan merry ne take fadin ta koshi da yawa bata dauka zataci sosai haka ba yace ta tashi su tafi wani kallo tayi mai tana fadin so soon ai na dauka kace sai dare zaka dawo ka dauke ni yace haka naso amma yanzu na fasa.
Tayi kokarin mikewa sai ta koma ta zauna dan murmushi yayi ya duka yana kokarin dagata da kanshi da sauri na kawar da kaina ina kokarin kara yaji sosai do ya dauke mi hankali daga kallon su.
Wai ke may ye haka kina ta zubuda yaji ga abincin ki tun dazu kina sane da bai baki lafiya kuma.
Mamu ina son sa da yaji ne na dan fada a shagwabe ina bata fuska lokacin har ya mikar da ita tsaye suka tsaya suna kallon plate din abincin nawa.
Prity ko zaki bimu zuwa masaukin mu yau ki debe muna kewa na dan lokaci kadan ina son zama dake mu danyi hiran yanayin ku na nan.
Merry ta fada tana kallo na da sauri na girgiza kai ina fadin No no no is time for my qur,anin school and want to miss it.
Ganin suna magana da mamu tana mata bayanin abinda nake nufin nayi saurin shigewa dakin mu na fara shirin barin gidan suna nan na fito a cikin zubulelen hijjab dina ina fadin fauziya ku dauko hijjab mu rafi kada mu makara.
Ranan da mamu ta karbi girki hakana ta daure zuciyar ta ba dadi har lokacin ta shirya zuwa sashen mai gidan don gabatar da hakkin shi daya rataya a kanta.
Kawu ya debe rai da zuwan mamu part din shi do har ya fara gabatarwa kanshi wasu al,amuran da sukeyi masa idan sun shigo.
Sai ga ta ta shigo fuskanta ya kalla wanda har lokacin ba walwala a tare da ita , sallaman da tayi ya karba ta aje abinda ta shigo dashi a hannun ta.
Sai da takai zaune ta fara gaida shi da dawowa shima ya karba kamar yadda ta gaida shi din a sanyaye,
Dan shiru ya biyo falon kafin kawu ya kawar da shirun da falon yayi da fadin kinki ki tuna min zancen kayan yaran nan don ni na manta da zancen shaf a raina..
Sai da na hadu da Fatima dazun suna dawowa na tuna dan kunya ne ya kama mamu tace abubuwan ne da yawa itama dai fitina ne da ita wallahi.
Yace kin san halin malaman da saka yara a gaba suna takura masu in bashi ba ai wanan da take amfani dashi ba laifi yana da tsawo nagani.
Ai ka santa da shegen son uztazanci dan maganan da akayi bai saukaba ya daga mata hankali.
Wanan ai yana da kyau yaran nan kaf din su ina hankalce ta fisu son addini shiyasa nake son zancen fatima akwaita da kokari wurin wurin riko da addini sosai.
Kai yaya sayadin da saida nayi da gaske take wanan halin yace to ai kinji tunda har zaki iya sakata abu tayi shi.
Jikin mamu ya kara sanyi tayi shiru sai can race shekaran jiya naje gida gun baba .
Ya katse ta da fadin kinje kai karan mu ni da hajiyan mu ko ba haka bane yaya ta fada a dan kunyace tare da fadin kun dai ki fahintana ne kan wanan zancen.
Amma ta yaya zanki umar da sayadi tunda ban san abinda kayi tunani kai wanan hadin ba ni abinda nake jawa yadda tun yanzu hjy ta nuna bata son hada komai dani a fili yasa nima na, , ,
Kema sai haukan kishin ya kwashe ki kuka kara bakanta min rai ko kawu ya karasa fadi kafin ta furta nata.
Kin ban mamaki maimuna da har kikayi zaton zan kai fatima gurin da zata sha wahala ko wani abu makamancin hakan nafasan abinda nake maimuna.
Yaya kayi hakkuri banayi hakan don in bata maka bane abinda nake hange cikin wanan auren duk kun kasa hangen shi ku a yanzu.
Matar da ta nuna wa bare ma halinta balle yar nan da tun yanzu ta nuna bata kaunan ta don may ni zan nuna ina kaunan wanan hadin kenan nida yar mun zama kwadayayo ke nan a wurin ta tana hattaran mu muna biye don kwadai wanan ba zaiyuyu ba.
A takaice dai baki yarda da hukunci na ba ke nan har yanzun ?
Tayi kasa da kai tana magana kasa kasa a cikin ladabi tace ni bance na ban yarda ba kai tsaye ai kadaiji hujjan da nake dashi.
Girki dai haka akayi shi ba wani dadin rai gare su dukkan su duk da mamu tayi kokarin danne zuciyar ta ga zancen kamar yadda shima kawu bai kara tayar da zancen ba a fili sai dai ba gudu ba ja da baya ga abinda ya zartan.
A cikin satin ne kuma kowa na gidan yasan da zancen gidan da umar ya gina dama wasu harkoki da yakeyi.
Hakan bai hana mumu wanke kafa taje har falin hjy jummai tai mata murna ba lokacin suna zaune da yaran ta ana hiran haduwan gidan daya gina din.
Tayi addua tare da fatan alheri daga haka ta juya ta fita ta barsu tana fita hjy jummai tace munafukan banza munafukan wofi.
Ta wanko kafa tazo don wani simi simi da ita tana fadin wai Allah sa kaza Allah sa kaza kamar yakai ciki munafuka watau a yarda da yar ta ko mai.
Mama ai tayi kokari don tazo habbib ya fada cikin rashin kulawa shiko Aliyu mikewa yayi yana fadin bros yanzun zaka fitane ?
Binsu tayi da kallo suna ficewa daga dakin Aliyu yace mama bata son zancen gaskiya may ye laifin matan nan datazo mata murna ko yan uwanta ai ta riga su zuwa.
Gidan umar sukaje sun samay shi a waje da wani abokin shi suna magana haka yasa basu tsaya ba suka shige ciki.
Merry dake kwance ta karde falon da kidan coci tana bi daga inda take kwance din ta dago ta kalle su ayatsune tana fadin wanan shigowa haka kamar wasu yan aike fa.
Sai da kowan su ya samu wuri ya zauna suke fadin gunki aka aiko mu inji Aliyu habbib ne ya kalle ta tace ba zaki bamu ko ruwa mu sha ba ai ki tare mu da wani zance.
Tace ruwa nine zan debo maka ruwa kasha ko wa tana fadi tana gyara kwanciyar ta amma kin san mu haka akidar mu yake maigida shi zai tari bako da abin sha ai .
Tace to hell with your culture at all no any respect in that culture baku san ku yadda ake girmama bakon ku ba ko kadan.
Sunyi galala suna kallon ta haka yasa habbib ya fara mikewa yana fadin kai mu tafi ta tabe baki tana kallon su a wullakace tace akan ku zan fara rama wullakancin da ake mun.
Umar dake shigowa falon yace har zaku tafi ke nan yanzu fa kuka zo bako zauna ba halan.
No bari mu tafi zamu dawo wani lokacin habbib yace yana tafiya Aliyu ya mara mashi baya.
Ciki ya shiga ya samu merry a yadda suka barta yace kinga su brothers sin shigo ko zama ina basuyi ba kuma sun wuce.
Tace eh da sanina suka wuce don raini suke son kawo min wai na basu ruwa su sha wani kallo yake mata kafin yace merry kin san mai kike fada ke kika kore su ke nan ko ?
Tace idan zasu zo su kawo min raini zan masu abinda yafi wanan ma a gidana don ba zasu zo suna takura mi ba.
Alamarin merry ya fara ba umar tsoro ga matsin da take mai kan tagaji da zaman Nigeria ita dai sai su koma taki yarda kuma ta koma ita kadai.
Ya dai samu ya dan rarashe ta kan ta yarda ya karasa abinda yasa a gaban shi ita babba damuwan merry shine ta samu ta raba umar da mahaifan shi da take ganin tsana daga idanuwan su.
Tunda ya samu ya rarashe ta tadan yarda zasu kara lokaci sai kuma dokokin data na ba zata sake zuwa guri mum din shi ba koda kuwa ta shiga gidan.
Gashi kuma zuwa lokacin ita hjy ta dan sauko ta fara nunawa merry ta fuska da baikai ciki ba tana son jan ta a jiki.
Hjy da kanta tayiwa merry korafin rashin zuwanta gidan su kwana biyu merry ta kama mata yawo da hankalin cewa ai suna tafe.
Sai dai har lokacin bata ga duriyan ta ba a gidan sai kuma ta fara zargin ko mamuce ta zuga merry din a kanta kada ta yarda da ita ko kuma ta zuwa gidan ita a boye.
Haka yasa hjy ta kasa hakkura ta tun kari dan da zancen a ciki waya yace yana lagos idan ya dawo zasu shigo ai .
Har kwana biyu bata ganshi ba ta kara kiranshi a waya yace insha Allahu yana tafe a gobe zasu dawo.
Washe gari da yamma sai gashi ya tun karo gidan lokacin baiko karasa gidan shi ba ya nufo gidan su don yawan kiran mahaifiyar tasu da take mai yake daukan wani abune ya faru.
Yayi sallama ya shigo gidan ranan saye yake da wando da rigan bakaken kayada farar riga a cikin kayan suit din.
Wuyan shi yana daure da nicktie sai kamshi turaren sa ke tashi mai dadi da kan gauraye wuri idan yana gurin.
Kayan suyi mashi matukar kyau a jikin shi kai kace don shi aka hada kayan ya karasa shigowa yana fadin mama na dawo don naga kamar kina bukatan gani na sosai.
Tace ai dole babawo kana kasan nan matar ka tana kokarin rabaka damu ina ga kun koma can yanzu dai maimuna takai ga bukatan ta fafir wanan yarinyar takini a kasan nan..
Haba mama merry har ta isa ta rabani daku kawai dai daurowane hakan tace wana dalili;yasa bana son ka auri wanan yarinyar yar gurin maimuna.
Kai mama har yanzu kina ga wanan zancen na dauka ai an bar wanan maganan tunda itama ta nuna bata son hadin .
Karya ne munafukane balle yanzu da take ganin ka samu ci gaba haka ai yanzu take da kwadan hakan sosai wai ranan don bata da kunya sai gata tazo min murna har nan part din.
Mama ni sam ban dauki wanan wani munafunci ba tunda kuna wuri daya tare haka kema watarana alheri zai samay ta kizo mata murna ina har hjy maryam duk sun zo.
Wani kallo tayi mai tace maryam ne zata zo min murna nan ta dai zo min gulman wai taji hajiya na fadin gidan ya tsaru ke nan suna zuwa gidan naku ke nan.
Kai mama ku dai baku rabuwa da wani zance zan karasa gida don ko gida ban samu zuwa ba na wuto nan mu gaisa do ki ganni.
Dadin haka hjy taji tamike ita ma tana fadin yaran nan sun min magana wai suna son su koma hakana sai dai nasan ba abune mai sauki ba Alh ya yarda da zancen komawan naku kuma.
Tsaye suke aharaban gida suke wanan maganan sankarewa yayi a tsaye tankar ruwa ya ci shi dama yasan wanan abin zai faru gun mahaifin nasu.
Motar da tashigo na mamu data kwaso su manjo da Adda daga tasha ne ya dauke mata hankali har bata san shock din da dan nata ya shiga ba a lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:05 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAMANIN RAHIM HASBUNALLAHI WANI, IMAL WAKEEL, , , ,


Kallon mamaki take yi masu ba don komai ba sai ganin bakin kamar da shirin kwana sukazo gidan abin yake bata mamaki a ranta.
Lalai maimuna ta kafu har wasu baki ta gaiyyato masu a gida gaba gadi wasu irin kauyawa can dasu .
Abinka da yan karkara ganin su a waje su Addah da basu san kan gidan ba suka dakata suna jefa masu gaisuwa hakan yaba mamu daman nufansu itama tana gaisawa dasu don ganin umar a tare da ita da tayi.
Bayan sun gaisa ta kalli hjy tana fadin kakar sayadi ce tazo da yarta yar marigayi din daya rasu tana nuna Addah.
Ummumm hjy jummai tace ba tare da furta komai ba a gare su sai umar din ne ya daure yace sannun ku da zuwa ya hanya?
Wani kallo hjy ta jefa mai da yasa ya dan kwantar da kan shi kasa ba tare da ya shirya ba sukan suka juya suka tafi.
A dakin mu ta sauke su basu zauna ba don gabatar da sallah dake a kansu sai da sukai sallah ta gabatar masu da abinci.
Suna zaune suna cin a bincin mukai sallama dawowan mu ke nan daga islamiya lokacin.
Na dan tsaya waje iba magana da Aisha kafin in tunkari part din namu kai tsaye tun a kofan na fahinci akwai baki a part din don takalman roban da na gani aje a kofan shiga part din.
Ban damu ba don na dauka ire iren yan uwan su ne dakan dan leko lokaci lokaci wurin mamu din.
Murya naji kamar na Addah tana fadin kun dawo ya makarantar ina ita A ruwa din tubarkallah masha Allah yara sai dada girma suke yi .
Da sauri na nufi dakin da nake jin muryan nata na daga labulen dakin da sauri wani ihu na yanka da mukai arba dasu ina fadin wayo ni manjo na.
Na nufeta da gudu na fada mata a jiki sai kuma na fashe da kuka a lokaci daya manjo sai fadi take ni daga min kada ki karasani kin wani girma haka kamar ke kadai ake kiwo a gidan nan.
May kuma kikewa kuka yanzu kuma na kasa magana sai kuka nake na makaleta sai manjon itama ta kama kukan .
Muryan mamu daga kofa take fadin yau ka tsiya zaki dagata ki fice nan wanan shegan takar banzan da kikeyi fa ?
Barta suyi Addah ta bata amsa tana fadin kin san tsakanin fatima da babba sai Allah.
To kuma sai akace tazo ta tasa ta a gaba tanawa mutane kukan banza haka ?
Wanan ai sai ki tayar mata da ciwon ta dan Allah daga ki ba mutane guri mara ta ido kawai cikin dan share hawaye manjo tace mata.
Maimuna barta tayi abinta Allah ya nufa ta kara sani a ido ne dana tafi dana barta da dawainiyar dakon kewata a zuciyar ta.
Kai babba ba gaki yanzu tana gani ba zata cikamu da kukan banza haka kawai ?
Da kyat na banbare a jikin manjo naje wajen kiran da mamu ta kwala min a kitchen na samay ta tana dora ruwan abinci tace in kin gama shagwaban naki sai ki zo mu hada masu abinci.
Ina dan goge fuskana nace may zanyi mamu tace ki debo kayan miya ki fara jajagawa a turmi miyar kubewa zanyi.
Haka na daure na kama aiki hankali yana daki wurin manjo na matsu in gama inje in samay su a dakin muyi hira.

Umar yana tsayawa kofan gidan shi wayan shi yana kara ya dauka ganin sunan mama yasa ya furta mama kuma da mamaki karara a fuskan shi don yaga yanzun suka rabu da ita ai.
Ya dauka yana fadin mama lafiya dai ko ?
Tace na kiraka ne in fada maka ba ruwan ka da wa yan nan yan kauyen bakin na maimuna kada inji kada in gani ka barta da mutanen ta don zuciyata ta kasa natsuwa a yadda naga kana wani gaidasu.
Yace mama kada ki manta bakin gidan mu ne fa dole muyi gaisuwa irin ta musulunci ga bakin mu ai.
To ubana fada min yadda akeyi kasan ban sani ba sai ka koya min yanzu yace mama Allah huci zuciyar ki nima ina zasu ganni kuma.
Ta sauke ajiyan zuciya tace yanzu naji magana don nasan wanan makiran tunda ta fara fadin wai kakar yarta ce wai tsigar makirncin ta kulla kuma.
Na gode mama ya fada a gagauce don hango merry da yayi a garden tana murnan dawowan shi.
Ya fito motan da sauri ya nufi girin ta tare da ware hannayen shi alaman tazo gare shi a lokacin cikin so da shaukin ta sosai.
A haka suka shige ciki suna makale da junan su kamar zasu cinye juna a lokacin zaka dauka yayi wata barkatai ne bai garin.

Mamu bata bari nabar kitchen din ba sai da muka kammala aikin mu gaba daya daidai ana kiran sallah na fito don inje inyi sallah .
Bayan na idar na fada dakin na samu manjo ta idar tana jan tasbaha a hannun ta hakan bai hanani zuwa i rabeta ba lokacin.
Ta shafa tana fadin ja,ira har yanzu kina nan da shegen son jikin nan naki haka ?
Adda ta dago tana fadin ke dagata kada ki tumurmushe ta don Allah kin ganki kuwa yanzu yadda kika koma cikkkan mace dake makerin halittan ki ya gama keraki tsab.
Na mike daga jikin manjo ina dan dariya tare da fadin kai Addah ni wani girma na kara a hakan ina kamo hannun manjo .
Nace cikin yanayin damuwa anya manjo kina ko cin abinci a can nasan mugayen ban ba wani kulaki zasuyi ba ai.
Adda ta kalleni tare da dan harara tace a, a da yunwa take kwana tun bayan zuwan ki nan .
Na danyi dariya nace ba haka bane Addah wallahi manjo duk ta zube min a idona wai ina Atika da umman ta na kawar da zancen don gudun maranbarama.
Addah tace ai kuwa har kofan yaya suke da zamu taso

Please Login or Register in order to submit comment