You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mallake yan baza ga baki daya.
Haka dai uwar tayi ta zugata da mugayen shawara har taji wani karfin gwiwa yazo mata lokaci guda .
Suna gama waya da uwar ta mike cikin karfin gwiwa ta nufi hanyar fita daga part din ta suka hade da yarinyar data turo din.
Da sauri yarinyar ke fadin wallahi anty ins ganin maigidan ne don naga yan aikin gida suna ta shiga gaidashi.

Babu abinda nakeyi sai juyi nake a gado tsakiyan yarana dake kwance suna ta barcin su hankali kwance.
Kallon fauziya dake kasa kwance nayi don gadon bai isar mu ta kwanta a kasa ita.
Itama sai barcin ta takeyi hankalu kwance abinta gyara kwanciya nayi inaci gaba da tunane a raina.
Yanzu yaya yana can yana morewa rayuwan shi da amarya ni gani nan da yara ina jinyar jikina.
Wasu hawaye ne suka zo min lokaci guda masu zafi sai dan jaririna ya motsa ina jin yana kuka na kasa tashi in kamashi a lokacin .
Zubur naga Fauziya ta mike daga batcin da takeyi tana fadin anty yaro yana kuka bakiji bane.
A hankali nace ina jin sa Fauziya tashi ne ban iyawa kawai da sauri ta mike takai gareshi lokaci guda ta dauko shi tana dan jijigawa.
Yaron yaki shiru ta nufoni dashi tana mika min dole na gyara na karbe shi na fara bashi nono yana ja.
Zama Fauziya tayi a bakin gadon tana fadin naso in dauko littafina a daki sai dai ban son komawa dakin don lokacin Anty Nafisa batayi barci ba.
Wanan ai na rasa me take nufi daku haka a gidan nan na bata amsa tace dazun naji tana waya da maman su harda kukanta tana fadin mama ya sakeki fa ?
Fauziya karde ince kawu ne ya saki hjyn su don dama ya fadi haka idan ta matsa da zancen auren nan .
Ke nan hakan ya tabbata ke nan ko dama ai sheri karene maishi yake bi akace idan tayi don ni tun yanzu ta fara girban abinta ai.
Saidai duk abinda ya faru zamuji ne muna zaune ai maganan duniya baya boyuwa yanzu.
Mun dauki lokaci muna hira sosai da Fauziya yarinya mai wayau tana kwantar min da hankali a matsayina na yar uwanta.
Washe garine da safe bayan yara sun tafi makaranta mun karaya na koma dakina don ban son yawan hayani ga Nafisa ta sake volume din tv dake aiki ya karade falon da kara lokacin.
Nayi barci na tashi sai ga kiran yaya a wayata banyi saurin daga wayan ba har ya katse ba a jima ba saiga wani kiran ya kara shigowa shine kuma again.
Na dauka cikin basarwa ina kokarin nuna mashi ba komai a bangarena nace ina kwana yaya don nasan safiyace can a lokacin.
A daidai lokacin da Samira ke shigowa ke nan daga part din ta taji yana fadin Zahra ya kuka tashi ya yaran.
Ja tayi ta tsaya tana sauraren shi har lokaci bai dago kai ya kalle ta kamar baisan mutum yana gurin ba a lokacin.
Har muka gama waya tana tsaye a kanshi sai zafi takeji a zuciyar ta na yarda taga yana hira dani a cikin dadin rai duk da a waya muke maganan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:20 - 🤐🤐🤐: Yana gama waya dani ya dago kai a hankali yana duban wanda ke tsaye a kanshi lokaci ganin Samira da take tsayen cikin yanayin damuwa tana sauraren shi ta, sauke ajiyan zuciya tana fadin ashe ka iso garin bamu da labari.
Ke haka aka koya maki a gidan ku idan zaki shiga wuri kada kiyi sallama ko gaida mutane ya fadi yana kallon ta ido cikin ido na dan lokaci.
Kafin ya mike da zumar barin falon don hankalin shi yana gun nahaifin su tun daren jiya da yasamu labarin abinda ke faruwa tsakanin shi da mahaifiyar su wanda baiji dadin hakan ba.
Don yanzu abin kunyane a garesu ace da girmasa iyayyen su zasu kashe auren dake tsakanin su shekara da shekaru suna tare ana hakkuri da juna.
Balle yanzu data dalilin shi duk yake ganin wanan abin ya faru haka a tsakanin su don hjy ta kasa yiwa mahaifin shi biyaya kamar yadda akeson ko wace mace ta kasance da yiwa mijin ta biyaya koda ya kasance itace da gaskiya ga magana.
Dolene na miji ya kasance shine mai juya gidan sa da iyalin sa ba wai mace daya aje tace sai abinda ranta ke so dole za,ayi ba.
Ya rasa mai yasa hakan yake kasancewa a tsakanin iyayyen nasu ko wani lokaci irin hakan baka taba jin fitina tsakanin shi da hjy maryam ko maman twin's irin haka mai karfi saidai a tsakanin iyayyen nasu biyu kawai akeda wanan matsalan a gidan.
Ko dai sunayi dashi ba mai karfi irin hakan da yake yawan faruwa a tsakanin mahaifan nasu ba .
Dear bansan ka shigo ba sai yanzu shine abin ya bani mamaki har na manta da ban maka sallama ba ashe tana magana tana wani kashe mai idanu irin na goggagun mata yan bariki.
Zai bude baki ke nan yayi magana sukaji sallaman hjy daga kofa wace itama sai lokacin ta san da isowan shi garin ashe itama ?
Wani irin bacin rai ya saukama Samira a rai lokaci guda tana fadin me kuma ya kawo wanan matar nan yanzu a daidai lokacin da zan fara dana tarkona gunshi ?
Cikin kula da ladabi yake fadin mama yanzu nake shirin zuwa inda kike ai don jiya da dare Habbib ya kirani yana fada min matsalan da kuka samu da daddy.
Da sauri hjy tace amma shi habbib din ya kasa kirana muyi maganan sai kuma yake iya fadawa wani ko idan ka fito ina jiran ka a waje tace tana juyawa.
No mama ki zauna muyi magana wanan ai tasan nan din ba part din ta bane so zata iya fita ta bamu wuri mu gama.
A take Samira ta kwabe fuska tana mashi kallon mamaki tare da fadin zaka zo hannu sai ka rena kanka a wurina idan nice.
Ta juya da karfi ta bar falon alaman bata so hakan da yai mata a gaban hjyn ba ai wanan sallon har hjyn taga wallentane a gidan.
Tana fadi a ranta kaida kanka zaka sameni har dakina mu zuba ni dakai sai lokacin take jin bakin cikin rashin jan ajin da batayiwa kanta ba don ko wace amarya ai angone mai binta har dakin ta.
Samira na fita hjyn ta sauke ajiyan zuciyan tana kallon dan nata tare da fadin zanso kabi wanan yarinyar a sannu don Allah.
Baiyi magana ba sai cewa yayi mama me yakawo haka har daddy ya rufe maki kofa da girman ki aka tozarta ki a garin nan haka ?
Kaima ka sani ai zancen wanan auren naka danayi tsaye akayi shine mafarin zancen da sauri ya dago kai yana fadin aurena kuma mama garin ya har haka ya faru kuma ?
Dama ai ya fadi idan har na matsa aikai wanan auren in san da sanin na bar nawa dakin ke nan sai dai idan ka manta hakan daya fada a baya.
Mama kin san da wanan maganan kika yarda har akai wannan auren da yarinyar nan ?
Kin kwammace ki bar dakin ki saboda ki farauta ran su ko ki batawa wasu rai kawai ?
Wanan wani zance kakeyi haka idan badon kana auren yarinyar nan ba har Alh ya isa yace kada ka auri yar sabuwa a gidan nan.
Mama ya isa har ya wuce duk abinda kaji daddy yai magana a kasan sa wanan abin abin dubawane ga mutum.
Ba wai don ina auren Zahra daddy zaice kada na auri wanan yarinyar ba sai dai don abinda ya hango a auren.
Da zaice don ina auren zahra kada in kara matane ai da yace in rabu da merry don bata dace dani da addini na ba .
Nafika sanin halin mahaifin ku babawo banda wanan abin baida wani abinda yake da hujja dashi kan auren nan.
Tunda sun riga da sun gama dashi ko baida tacewa kan maimuna da diyan ta yanzu ga kowa.
Har da maimunan bata kasan nan tana da laifi kan wanan maganan naku ke nan don Allah mama ki daina wasu abubuwa yanzu don girma dada shigan ki yakeyi a kullun .
Bamu jin dadin irin wanan abinda ke faruwa a tsakanin ku da daddy ko da yaushe.
Zanje wurin daddy mu zauna dashi don girman Allah mama kibi wanan maganan a sannu a samu a sasanta wanan maganan hakana din ba zamu so har mutane sukai ga fahintar hanlin nan da kuke ciki ba keda shi.
Na dade da fahintar laifina kuke gani kan matsalan dake faruwa atsakanina da Alh a yanzu.
Shiyasa banjin zafi idan wani yaji zafina kan haka tunda ance ita mace ba zata kwaci yancin ta ba don tana mace.
Mama kiyi hakkuri ba hakan nake nufi ba nidai rokona shine ki don Allah ki kwanta kibi daddy a samu a sasantaku ki koma dakin ki ya janye sakin daya furta a tsakanin ku.
Don kinga ita kanta maman twins da suka samu matsala kan gidan da iyayyen ta suka sai mata zata zauna a ciki yace bai yarda ba.
Da sauri tace gida fa kace aka sayawa maimuna koka saya mata dai.
Da sauri yace subbahanallahi mama ko banson albarka ai zan so fita kunyan jama,a ban sai maki gida ba zanje sayawa uwar matana saboda neman me zanyi hakan mama ?
Na sanan maka din komai zaka iya kan wanan shu,umar yarinyar a yanzu da take ganin ta daure ka gaba daya.
Murmushi yayi yana girgiza kanshi a hankali yana fadin haka dai kike gani mama amma ni ban yarda mace ta shige min gaba ba ko kadan.
Ban dai yarda in tauye hakkin mutum da yake a kaina matukar ina tare da mace bana tauyeta ko shiga hakkin ta.
Hjy tace yanzu yaya zancen gidan ita maimuna ake ciki Alhn ya yarda da zancen ne ko yaya ?
Bai yarda ba ita kuma ta kafe akan ba zata yarda ta dawo wanan gidan ba kuma suma iyeyen nata suka biye mata.
Shine yar nata ta kirani tana fada min abinda ke faruwa a tsakanin su wallahi mama kira daya nayi masu na basu hakkuri suka amince min da hakan.
Yanzu babu zancen gidan ke nan ko yace gida na nan a matsayin nata za,a zuba mata yan haya a bangare daya don su dinga kula mata da gidan.
Wani irin bakin ciki da hassada ne a lokaci daya ya rufewa hjy zuciya tana kara jin tsanan mamu har kasan ranta sai anyanawa take a ranta idan ba tayi da gaske ba wanan matar zata bata mamaki nan gaba.
Muryan dantane ke fadin don haka mama kamar yadda taga darajana tabi abinda na roketa kema ina rokon ki da duk abinda daddy zai fada kiyi hakkuri dashi a zauna lafiya .
Bata samu furta mai komai sai hakkuri yake bata cikin kwantar da hankali da taushin murya yadda zata samu fahintar shi.

Zama nayi yau na dauki kwalliya mai daukan hankali don yau ina son kaiwa yan uwan mamu ziyara tunda na haihu ban fita daga gidan ba sai yau duk dako yaya bai hanani fita inda nakeson zuwa.
Nafisa na zaune muka fito falon tun ina saman steps take bina da wani irin kallo har na sauko kasan inda suke zaune.
Da sauri fauziya dake fitowa daga dakin su ta zo ta karbe Abbati a hannuna tana fadin wai anty yaron nan fa girma yake karawa a kullun.
Tana zama a gefena da yaron a hannun ta take fadin hakan lokacin duban yaron Nafisa tayi take fadin na rasa wa yaran nan ke kwasowa da kyau haka kamar diyan larabawa dasu.
Kallonta nayi ina fadin Nafisa ke nan gashi kin fada dole suyi kama da su tunda suna da jinin su a gauraye dasu.
A daidai lokacin ne maria ta fito da sauran a cikin shirin su tsab suma ta bisu da kallo tana fadin wallahi dole yaya yaji dake har ransa ko don wa yan nan yaran Fatima.
Yara haka sai daukan ido a duk inda suke shiyasa nake fadawa shiyasa nake fadawa hjy ta bar yaya da iyalin su a kullun ko wani ahali ba a son rasu sukan rabu ba indan kaddara ta gitta masu.
Yanzu gashi ke baku rabu da yaya a yadda take so ba yanzu gashi batayi nasaran rabaku din ba ita da shekarun ta daddy ya hasale mata auren shi a kanta.
Na dago kai ina fadin Nafisa kin san abinda kike fadi kuwa yaushe wanan magansn ya faru kike furta hakan yanzu.
Wallahi Fatima anty salma ta dade tana min nasiha kan mu bar biyewa halin mama don shi kanshi yayan mu ba zaiji dadin halin da mama take sa muna nuna maku ba tare da laifin komai a garemu ba.
Ita dai anty salma ai ta huta da bata tsaya bin halin mama yanzu kinko ga ta zauna a dakinta lafiya ba wani tsangwama a yanzu.
Ga yaya ya ttaimakawa rayuwanta yanzu idan nayi magana ko ina son yayi min wani abin sai yace dani inyi aure kamar yadda yan uwana sukayi.
Fatima yanzu ta ina zan fara neman wani mijin Manir ne mun bata dashi kin sani tun kuna can ya dawo mu shirya mama tace bata yarda ba don ba zata bari taji kunyan mutane ba tunda har ya iya bata min suna a gaban kowa.
Amma har idan kina son shi har yanzu Nafisa mai zai hana ki fadawa yayan ki don nasan yaya zai fahince ki idan kin fahintar dashi gaskiyar maganan.
Shine kawai zai iya shawo kan wanan maganan har kowa ya yarda da shawaran shi in Allah ya yarda don yaso ace an hada auren ki dana Murja a lokaci guda.
Tun wanan dan hiran da mukayi da Nafisa dana lura abin duniyane ranan ya dameta tana neman abokin shawara har ta dan sake layin hjyn su garebi.
Munje gida anty don gaida ita tunda ta dawo daga kasan su bamu samu zuwa ba sai itace ma tazo inda nake dana haihu ta duba jikina.
Ina tambayanta yaushe su mamu zasu koma Nigeria ne take fadin suna son sai sunyi aikin hajjin banan nan a tare da ita zasu mayar da ita gida.
Nafisa kan sai mamakin irin arzikin su takeyi ga gidan babba ko ina yan aiki ne birjit a gidan kamar suna zaune a kasan su .
Ni kaina lokacin dana fara ganin su haka nayi mamakin abinda yasa har ta bude saloon ake mata aiki.
Take ce min ai ba a son mace ta zauna ba dan inda kudi yake shigo mata ko yayane ya kamata ace mutum yana da dan sana,an rufin asirin shi don ba komai ne zaka roki namiji ba ka samu kai tsaye.
Yini mukayi sosai a gidan mun sake jiki don irin yadda matar gidan take jan mu a jiki gaba dayan mu har Nafisa.
Da yamma muka dawo gida bayan mun dan kebe da anty ta van sakon da dama nazo karba wanda kakata ta bayar a kawo min ta hannun su.
Baya nayi wanka na kwanta ne sai kuma tunane ya dameni don yau kusan kwana biyu ke nan banji kira daga yaya ba.
A take zuciya mai nashe nashe ta nasa min cewa ina zai kiramu yana can yana cin amarci da amaryan shi shike nan ya gama da mu nan ke nan .
Naji wani irin kishi ya rufe min zuciyana kamar yadda ko wace mace take jin wanan yayin da mijin ta yai aure.
Da kyat na samu na yaki zuciyana kan irin yadda nakeji din a raina na samu har barci ya dauke ni hakana.
Haka yasa washe gari na tashi da wani itin bakin rai a zuciyana kin ma fitowa nayi daga dakin ga baki daya ina kwance inata faman tunane a raina.
Ina kwance a hakana wayana ya dauki ringing ina kallo yai ringing har ka katse ban dauka kira kusan uku yai min naki daga wayana a lokacin.
Sai ga Nafisa na doka sallama a kofan dakin nawa wanda tun zuwan ta ban taba yarda ta shigo min dakin ba sai yau da dan uwanta yace a bani waya muyi magana dashi ta wayan ta tunda ya kira ban dauki wayan ba.
Bayan ta shigo da sallama na karba mata take fadin barci kikeyi ne dama nace ma yaya ina zaton hakan ai.
Tana magana take miko min waya idanuwan ta kuma yana yawo a kusurwan dakin da take bi da kallon mamaki sosai.
Dama tayi zaton hakan don ganin yadda aka tsara dakin yaran dana su maria tasan namu abin kallone shi.
Na duba wayan har lokacin yana kunne bai kashe ba nayi sallama a hankali ina sauraren shi.
Ina kike ne haka waya yana ta ringing baki daga ba nace ina daki kwance ya dan ja tsuki yana fadin wanan ai halin banzane ka bar waya anata kira baka daga ba.
Idan da dane cewa zanyi dashi yayi hakkuri sai dai yau baiji hakan ba don amsawan ma sanyaye nake amsa mashi magana.
Yace ya yaran da kowa da kowa a gidan nace lafiya a takaice yana jin hakan ya kashe wayan abin shi na mika ja tsuki don Nafisa tunda muka fara magana tabar dakin.
Runtse idanuwana nayi ina anyana yadda yake cikin annashuwa a can da amaryan shi muko muna nan.
Sai zuwa yamma na samu sa,ida a raina ina fadin wai me nakeyi haka zan bada kafan da Nafisa zata samu wani abin fadi a tare dani.
Mikewa nayi na shiga wanka na fito na shirya a daidai lokacin da yaran suka dawo gida suna zaune a falo suna cin abinci na fito.
Da murnan su suke gaidani ina masu sannu da dawowa na zauna a tare dasu muna hira sannu a hankali nake jin dan sauran abinda nake ji yana gushe min a raina har yakai na daina jin komai a yanzu.
Banda in ba yarana kullawan daya dace su samu tarbiya ingantattace a gurina na watsar da duk tunanen wata kishiya don tarbiyan yarana yanzu shine a gabana kawai na yanke shawara a raina.
Zaman mu da Nafisa a dan kwanakin ba laifi don mun gama fahintar halin ta muna binta dashi saidai ban yarda rainin wayau yana shiga tsakanin mu ba don kada taga kafan yi mu hakan.
Sam ban yarda wani rainin wayau yana shiga tsakanin mu ba don ba dogon irin wasan nan a tsakanin.
Ko zama wuri daya don bakuntar da tazoyi munane har muke dan dasawa saboda nasan bata da dadi salma ta fita dadin sha,ani.
Komai da aka ban ina amfani dashi kamar yadda sukace din nayi amfani dashi haka ya jawo min saukan wani ni,ima da kyau a jikina.
Wanda ni kaina na hango hasken sirin abin a yana haskani yana kara min wani irin dau kaka ga duk wanda ya ganni a lokacin.
Don ko zama nayi na bar wuri zan barwa wanda zai zauna bayana kamshi da tunanen sirin kamshin.
Ga yarana yanzu sai wani irin kula na musanman da suke samu suma sai baiwan su sannu a hankali ya fara haskawa din.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:20 - 🤐🤐🤐: Suna zaune su uku a falon mahaifinsu sai mahaifin nasu dake dan kishingide yana sauraren bayanin kowanin su daya bayan daya tundaga kan Umar har habbib da Aliyu.
Baiyi magana ba har zuwa wani lokaci saida ya fahinci sun gama fadin abinda ke zuciyar su yana gyara zama yace.
Da fatan dai har zuciyan ku kusan banda laifi a cikin wanan magana don nine na aje jummai a gidan nan ba ita ta ajeni ba kamar yadda take tunane.
Na fahinci abinda kowanku yake ji a ransa game da wanan maganan sai dai kule tunanen haka don ita a bangaren ta hakan bawai ya dame ta bane.
Yau ankai har jimmai tana tunanen zatayi jayayya dani a gidan nan kan naba dan dana haifa umarni yabi take ganin ban mata daidai a rayuwan ta.
Sai yaushe zata gane niba makiyin ta bane wai idan bamu taru mun rufawa kanmu asiri ba a yanzu sai yaushe ake tunanen zamuyi hakan.
Sam a yanzu banga laifin jimmai ba don nine da sakacin dan na bata dama har ya wuce yadda ya dace ace an sakewa mace shine ya haifar da illa a tsakanin mu yanzu har jimmai take daukan kanta a matsayin miji nina koma mata.
Daddy hakkuri zakayi itama mams tasan bata kyauta ba abinda tayi a yanzu don duk wanda yasan gaskiya yasan babu gaskiya a cikin maganan nan.
Daga baya ke nan Aliyu don yanzu bukatan ta ya biya idon ta ya bude ko tunda tayi yadda take so ta nunawa duniya ban isa da danta ba.
Allah sarki daddy kada kayi tunanen hakan garemu don mu bamu da wanda ya fika a gare mu sai ita mama.
To aikai malam umar abinda take tunane ke nan take ganin ban isa ba gareku ta matan a karshen ikona take zaune.
Daddy a daiyi hakkuri a yafe wanan magana tunda har abin ya rigada ya faru sai a hakkura hakana a yafe.
Ai habbib idan kaga na janye sakin dake tsakanina da jummai a gidan nan to ta bi umarni ne shine za,a zauna lafiya dani don bata isa tace ni ban isaba ga idon duniya.
Shiru gaba dayan su sukayi falon don sun san idan yai irin maganan nan har cikin zuciyar shi yake nufin abinda ya furta.
Don kawu mutum ne da zaka dade kana mashi abu bai tanka mutum ba amma ranan daya tanka sai ran kowa ya baci a gidan.
Daddy a dai kara hakkuri don Allah wanan abin bamu jin dadin shi wallahi gashi yanzu muma muna da iyalan da zamu koyi da wasu halaiya naku a yanzu.
Tabbas hakane habbibu shiyasa ma nake son nuna aini ba lusarin namiji bane kamar yadda ta dauke ni .
Har zance ga abinda nake so ga dana yau jimmai ta fito a gaban jamma, a tace ban isa da abin nan ba ai kaga haka ba dadi ko.
Kowan su ya kasa magana sai can Umar yace daddy zamu tafi don wanan maganan yana son fin karfin mu ba zamu iya sasanta tsakanin ku ba.
Umar meye laifin ku a cikin maganan nan jimmai

Please Login or Register in order to submit comment