You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dauki cup din ya mika min tare da fadin karba ki sha .
Kaina girgiza mai yace No no no kinsan bana son musu ki karba kawai ki sha nace maza bude bakin ki na baki yace ba yadda na iya dole na bude baki ya fara bani a hankali tare da dan guntsura min bread din ina ci har na shanye sai zufa sai lokacin naji yayi ajiyan zuciya ya aje cup din.
Ya dauki nasa ya fara sha a hankali ina zaune sai zufa nakeyi ina kallon shi har ya shanye ya aje cup din yana fadin tun dazun ina tunanen ki ina gidan Yusuf nasan dama haka zaki zauna da yunwa kiba kanki wahala kan dan maganan da baikai ya kawo ba.
Da mamaki na kalleshi har lokacin warning din mamu yana nan tana min yawo a zuciyata bandai iya furta komai ba sai shi naji yace dani kin tuna da wanan matar abokina da muka hadu da ita ranan wurin shiga taron nan ?
Na gyada kai a hankali yace itace ta bugawa merry waya ta ganni da wata sai dai ga haukan merry har yanzu ta kasa kwantar da hankalin ta tayi nazarin yaya alakana dake yake ne wai.
Ko da ya juyo yana wanan bayanin sai ya samu ina gyangyadi a wurin murmushi yayi ya sauke a jiyan zuciya tare da tayar dani na gyara kwanciyana.
Shikan ranan bai iya barci ba don irin rikicin da sukayi da merry da ya fada mata cewa ni din matarshi ce a yanzu.
Kuma har ina shirin haifa mai diya da zai iya juyasu yadda yake so ya sa su hanyar addinin shi sai ta fadi kasa a somay.
Sun kwashe ta zuwa asibiti bata yarda ta zauna ba tana farfadowa ta juya zuwa America ranan shine ya tsaya gidan yusuf suka shirya irin nasu don sun san tana kasa tana dabo a tsakanin su yanzu.
Washe gari bai tayar min da maganan ba nima haka na shirya zuwa school abina dan ban yarda na saka zancen a raina ba ko kadan.
Munyi exam lafiya har lokacin tun ina sauraren zuwan merry naji shiru ranan ina zaune ya dawo yake ce min in shirya zan koma gidan Yusuf in zauna a can zaiyi tafiya har ya dawo.
Nadan so yin gardaman hakan sai dai ba fuska da zanyi hakan gurin shi .
Matar Yusuf din ita da mijin ta sukazo gidan suka daukan min duk wani abinda zan iya bukata a can dukda ba wani abu suka daukar min ba a gidan nidai na bar mamakin hakan a raina kawai.
Don na zargi akwai wani abinda suke boye min daga su har yaya din a lokacin wanda basu so in fahinta niko kwatar min da hankali da mahaifiya tayi dukda bata san halin da nake ciki ba yasa na fitar da komai a raina.
A kullun sai nayi in fadawa mamu zancen cikin dake jikina sai inyi tunanen yaya zan fada mata waini ina dauke da ciki a jikina wanan abin akwai kunya gaskiya.
Haka yasa naja bakina nayi shiru wanda shima yaya hakan yai mai dadi don har gashi ya kaini inda za a taimaka min in haihu batare da wani tashin hankali ba ko wani yasan da hakan don sun rigada sun gama shirin komai.
Nidai ba zance banji dadin zaman gidan yusuf ba ba don ko ba komai banda zaman kadaici ko kadan saidai kewan mijina da yakan damay ni don dan sabon da mukayi dashi a lokacin.
Ina sati daya da zuwa gidan ya dawo a wani safiyan nayi murnan dawowan shi kwarai da gaske har ban iya boye hakan a raina.
Ramla tana zolayana nidai sai murmushi nake mata kawai zuwa karbe biyu na idar da sallah ta shigo dakin tana fadin in shirya zamu fita inji mazan mu.
Ba wani shiri nayi ba dan hijjab dina kawai na dora a kaina karami muka fito baya muka zauna .
Tafiya mai dan nisa sosai da gidan mukayi zuwa wani unguwa sai dai unguwar yana da kama dana tallakawa a gaban wani gida yusuf ya tsaya da motar shi.
Saida yayi waya muka fito lokaci daya da wata mata da naji Ramla na kira da mummy tana kallona tace a masha Allah wanan ce yar tawa gaskiya sun dace sosai da maigidanta ta kamo hannuna zuwa ciki tana fadin yata sannun ku da zuwa.
Hausanta nakeji wani iri a raina nace oh nidai Allah ya kawo ni sun dan dade tare suna hira kafin su barmu gidan da sunan sai sun dawo daukan mu.
Hira sosai anty Ramla da dattijuwar matar suke keyi akan haihuwa har zuwa rainon yaya da sauran su ni dai ina sauraren su.
Tun ban kula da hiran su ba har yakai na mayar da hankalina gurin su kamar uwace ce ke koyar da yar ta abubuwa na fannin haihuwa.
Har ya kai ina masu tambayoyi suna ban amsa a tare cikin natsuwa nake fahintar su sai matar tace in miko hannayena ta gani na mika mata ta rike da hannunta bibiyu ta dade tana tsura masu idanu kafin tayi murmushi tace abubuwa ai zasu zo da sauki insha Allahu ke Ramla.
Wanan da kuke gani babu wani harin da zai samayta asalima ko sun jefota ba inda abin ke zuwa do itama ba a banza take ba gaskiya.
A kwata da yawan ibada ta fada tana murmushi sanan kuna kinganta nan tana tare da mutanen a kanta sosai.
Don haka mijin ta ya kwantar da hankalin shi insha Allahu cikin amincin Allah da yardan shi komai zaizo da sauki wanan mafalkin da sukeyi ba karya bane gaskiya.
Saidai duk abinda sukayi Allah bai yarda suyi nasara a kansu don makiya kan a kwaisu dana gida dana waje sai dai ta girgiza kai tace dasun sani dasun daina bata kudin su sukeyi ga banza wanan ta zama kainuwa dashen Allah a cikin zuri,an ta ko.
Tun ban fahintar ida maganan ta ya dosa har na gane inda Ramla da mijin ta suka kawo mu wanan dattijuwar matar malamace ko kuma wata mai magani irin namu na hausawa a gida.
A,uzubillahi nace har ya fito fili suka kalleni lokacin da nake bin gidan matar da kallo ina kara fahintar wani abu a gamay da ita.
Tayi murmushi tare da fadin bana shirka kamar yadda kike zato yar nan saidai Allah yaban mutane a kaina dake zama tare dani har yakai bana iya zama a cikin mutane dole na dawo nan bakin ruwa na zauna a kusa dasu.
Ba kowa nakewa haka ba sai wanda zuciyana ya aminta dashi matsalan ku babbane tun a gida yake faruwa har yanzu ba a daina bibiyan ku ba.
Da maishi zai gane hakan ya daina da zaifi sauki gareshi don abubuwan dake tare dake manyane sosai basu bari wani sheri ya samay ki.
Haka dai tayi ta surutun ta ina kallon su kawai ina murmushi don ni banji komai a raina ba kan abinda take fadi lokacin gamay damu.
Fita mukayi shan iska ta bayan ta sai lokacin ma kula da unguwar sosai ashe a bakin ruwa gidajen nasu yake sosai.
Tayi girki da wani irin kifi kato dan miya kamar miyar kasar hausa na danyen kifi tare da abinci mukaci.
Sai dare sosai suka dawo suka dauke mu bayan sun gama ganawa da ita tazo har inda nake tana min addu,an Allah ya saukeni lafiya.
Zuciyana cike da mamakin wanan matar ko maiye makasudin zuwa gidan ta da mukayi ban sani ba nu dai na dauki hakan da ziyara kawai muka kawo mata.
A zato na dauka zamu sauke su Ramla ne mu wuce gida sai naga sabanin hakan lokacin don har shi yaya din a gidan Yusuf din muka kwana ranan a dakin da aka ware mun gidan.
Sai lokacin da muka kebe ne naga irin raman da yayi sosai ya ramay yayi dan baki a lokacin da ya fito wanka.
Ya hawo gado inda nake lokacin ina fushin rashin maidani gidana da baiyi ba ina jin shi na kyaleshi .
Zarah na san idon ki biyu fushi kike danine haka komay ?
Sai lokacin na dan juya ina magana ciki ciki nace ban son zama a gidan nan da nakeyi yaya ka mayar dani gidana don Allah.
Sai naji ya sauke a jiyan zuciya tare da rugumeni a jikin shi kamar karamar yarinya yace nasan bakiso zarah amma hakan shine daidai dake a yanzu.
Don barin ki wancan gidan ke kadai hatsarine gare ki idan haihuwa yazo maki bana gidan ko wani yazo maki da tashin hankalin a wanan halin da kike ciki ban kusa kinga ai zaki shiga wani halin da ba a son mace mai ciki ta shiga.
Mutanen nan su suka bada shawaran in dawo dake nan kusa dasu don kina gab da haihuwa don sun san ni ba zama nake ko yaushe ba.
To ka maidani gida mana nace a dan shagwabe haba zarah in kin min haka baki min adalci ba baki fatan abinda zaki haifa ya taso cikakken dan kasan nan ne ?
Ko dai kina samun takurawane a nan din da sauri na girgiza kai alaman a,a kawai dai ni ban saba dasu bane har yanzu.
Ki daure ki saba dasu ya ban amsa nasan Ramla tana da hali mai kyau don hakanema na yarda da shawaran in bar ki nan din don hankalina zaifi kwanciya.
Shiru nayi ban bashi amsa ba yace da fatan kin daina yawan mafalkin ana binki da gudu yanzu jin tambayan da yai min yasa nayi magana a lokacin.
Na daina sai dai yanzu mata uku nake gani suna bina amma bada gudu ba kamar da kafin su cin mun wani abu yake dagani sama.
Bai kara magana a haka barci ya dauke mu washe gari tunda ya fita sallah bai shigo ba daga shi har mai gidan wurin matar gidan na samu labarin wai ashe suna case ne da merry matar shi ranan zasu zauna kotu.
Asalima wai wanan gidan da nake zaune a cikin sa an rufe sai bayan kare case din mu yanzu ba a san inda nake zaune bane da har dani zamu tafi wurin case din.
Basu dawo gida tare ba gashi ina son tambayan shi sai dai ba zan iya hakan ba saboda nauyi da kunya itin namu na matan hausawa.
Sai bayan kwana biyu sai gashi ya kara ramewa sosai yayi duhu da ganin sa yana cikin yanayin damuwa.
Ina dan karamin falon gidan zaune idanuwa suna lumshe ina faman tunanen yanayin da na tsunci kaina a ciki kamshin shi ya daki hancina na bude idanuwana da sauri na sauke a kan shi.
Yana tsaye yayin da corth dinshi yake rike a hannun shi daya, dayan hannun na cikin aljihun wandon shi ya zuba min idanuwa cikin yanayin tausayawa gareni.
Kokarin mikewa nayi zaune sai na kasa da sauri ya karaso inda nake zaune yana fadin zauna abinki zarah.
Mai ya same kike zaune nan ke kadai kina tunane ko an maki wani abune ko kuma cikin na damun ki ne ya jero min wanan tambayotin kusan lokaci guda a jere.
Ban san yadda akayi ba sai ganin hawaye nayi sun soma zubo min a idona tun suna zuba a hankali har na soma a cikin sheshekan kuka.
Lokaci daya ya Umar ya rikice yana fadin fada min abinda ke damun ki yanzu ko muje asibiti ne dake ?
Ko gidan ne bakya so na rabaki dasu yau ganin ya rude har baisan abinda yake fadi ba yasa na dan rage sautin kukan nawa a hankali na bude baki da kyat nace yaya ka maidani gida don Allah wurin iyayyen mu.
Wani irin kallo yai min yace haba zarah baki tausayinane matsalan dake akwai a gida yafi wanan sau dubu a wurina yanzu kin sani.
Koda yake ba lalai bane ki san da hakan ke amma ina rokon ki zarah ki daure ki taimakeni ki kwantar da hankalin ki har zuwa lokacin da Allah zai saukeki lafiya ki haihu .
Izuwa lokacin komai zai kai karshe insha Allahu koba zaki iya min alkawarin komai ba na rokeki ki min wanan don Allah zarah for d sake of our urborn baby.
Na dago kai na kalleshi da sauri ni din yake kallo yana jiran amsan da zan bashi yana ganin na dago kai ya gyada min kai alaman in yarda da bukatan shi.
Ban bada amsa zancen ba don ba zan iya cewa eh ko a,a alokacin ba don irin yadda nake jin kaina.
Ganin nayi shiru ya mikar dani tsaye yana fadin muje daki in ja maki kafa ki ko zai maki dadi badon naso ba dole na bishi ya zaunar dani saman gadon tare da aje rigar jikin nasagefe daya.
Ya shiga matsa min kafan a hankali ina dan lumshe ido don jin dadin hakan da yake min din a lokacin.
Sai dai har lokacin ba wani magana don zuciyar kowan mu ba dadi a cikin sa shi yana ganin ya cutamin da yawa ga ciki ga rikicin daya taso tsakanin shi da merry.
Allah ya taimakeshi a kasan London suke ba a America ba don haka abin ya danzo mai da sauki ba kamar yadda merry din ta dauko zancen ba.
Don sam ta manta da yarjejeniyar su da sukayi kafin aure a rubuce dashi bata taba daukan wanan da muhinmanci ba don kamar da wasa sukayi shi.
Sai gashi wanan yar takardan ya rusa mata duk wani plain da alwashin ganin bayan shi tare da yan uwanshi a kan kara wasu hallita a cikin family din ta dashi.
Yayi barazanan bar mata dukiyan da take fadi akan zai bata takarda ta tafi har da yar tasu ya yafe mata.
Jin hakan har yan uwanta da iyayyen ta sun yarda da hakan daga baya merry din ta tubure masu akan sai tayi shawara da zuciyar ta ita kadai shinr aka kara basu lokaci.
Lokacin da suka fito cikin couth din dasshi da Yusuf ko kallon inda take baiyi ba ga Faith na kiran daddy daddy ya wuce ya barta a wurin zuciyar shi na masa kuna.
Kowa dake wurin saida yai mamakin hakan har yan uwanta sun fara fadin kinga irin abinda muke fada maki ga wa yan nan mutanen ke nan.
Basu da tabbas akan addinin su zasu iyayin komai lokaci guda ki kyaleshi don dole ya dawo ko don yar shi gareku.
Ku rufa min baki gaba dayan ku banson jin maganan kowa daga cikin ku idan rayuwan aurena ya samu matsala kune silan hakan gareni da yata.
Don kun hanani bin abinda mijina keso dani kun hana mu zauna lafiya dashi ga baki daya kuna ganin zamu iya juyashi a lokaci guda.
Omar ya wuce hakan da kuke tunani don yana tsaye ga addinin shi sosai hakama iyayyensa basu zauna a kansa ba.
Nan ta barsu ta shiga mota ds yarta tabi bayan shi saidai bata samay su ba taje gidan data san Yusuf a da baya gidan yanzu.
Ta juya zuwa gidan da suka samay ni gidan yana rufe kamar yadda hukuma tace a rufe shi har lokacin zama tayi tana karewa gidan kallo.
Tana mamakin yadda Omar ya zauna wata mace macen ma yarinya karama kamar fatema da ta sani a matsayin matar auren shi.
May zai samu gun wanan yarinyar da bai samu a wurin ta ba har ya iya bin umurnin iyayyen shi kanta.
Ido ta runtse sai hawaye taja mota kamar an tsikareta ta nufi gidan su ko yana can sai dai tun a haraban gidan ta gane baya gidan a lokacin.
Duk wanan haukan da merry keyi har yan uwanta basu kai ga gane akwai ciki a jikina ba har wanan lokacin ita dai zafin ta shine cewa da yayi ya a zaman matarshi nake nima.
Duk wanan abinda suke ciki ni ban sani ba don bai zauna yai min bayani yadda zan gane ba har in fahince shi.
Ni dai zan iya cewa wanan hutun baizo min da dadi ba din ga laluran ciki gana wanan halin da muke ciki ina zaune a gidan mutane a takure duk kokarin da sukeyi dani sai ban gani don ina ganin da hadin bakin su komai ke faruwa.
Ga Anty Ramla bata kasa dani ba kullun zata shigo wurina mu zauna muyi hira ta kawo min wanan ta kawo wancan haka dai take dawai niya dani a gidan.
Ni da kaina na ba kaina shawaran in sake jiki da ita wanan fushin ba zai fishini ba don ba zan iya fahintar komai a haka ba.
Ranan tana kitchen da safe tana aiki na fito na samay ta kitchen din ta juyo tana fadin mai ciki kin fito na danyi murmushi zuwa inda take ina kokarin karban wanke plate din da takeyi.
Tace rufa min asiri kada mai gidan ki ya samu kina wanan yace zan halaka mar mata kin ko san yana can amma kunnuwan sa na nan zarah.
Ban taba zaton akwai wata mace da zatazo tayi tasiri haka a zuciyar umar ba sai gashi har naga abinda yafi ma tunanena.
Zarah ki godewa Allah mijin ki yana son ki sosai da ba haka ba duk wanan barazanar da matarsa keyi akanki ne zarah.
Kin san umar ya zabi ya sadaukar da dukiyan shi akanta da komai nasa ya zauna dake ?
Nace ni kuma anty ?
Tace ke kuwa zarah ko cikin nan naki a jikin sa yake ya tsaya hakan yanzu haka duk wani shiri ya kamala duk da wanan halin na barazana ga hukuma da yake ciki amma ya gama shiri akan komai na haihuwan ki da ya dawo daga wanan tafiyan zaki sha mamakin shi kwarai
Wanan maganan da mukayi yasa naji kunyan kaina da kaina na rashin kwantar da hankalina garesu bayan nasan suna cikin barazana duk kuma a kaina.
Sai na samu kaina da jin kunyan kaina da kaina don haka na yanke a raina yana dawowa kawai in bashi hakkuri sai wata zuciya tace min akan may zan bashi hakkuri din ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:29 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM ALHAMDU,LILLAHI RABIL ALAMIN, , , , , ,


LITAFIN KUDINE GA MAI BUKATA TA KIRA 08036959257 DON TURA KUDI TA BANK KUMA ZA,A IYA TURA DARI UKU KACAL TA WANAN ACC DIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KIBIYA KI KARANTA BA TARE DA DAUKAN NAUYI BA, , , , , ,


Na dade kwance a dakina ina tunanen hiran mu da anty Ramla da mukayi da safe.
A karshe dai na gano a kainane duk wani matsala yake tasowa a yanzu tsakanin yaya da matar shi.
Har yake kokarin sadaukar da kaddadarorin shi gareta don dai a zauna lafiya a tsakanin su.
To ni har wani mutunci ko halarci nayi mai da ya zabi hakan a kaina yanzu iya sani na ba wani so ko kauna irin na masoya a tsakanin mu.
Saidai yanzu abinda zance shine akwai shakuwa irin ta zama tare da mutuntawa irin na yan uwantaka da aurataya kawai a tsakanin mu.
Har dadin may yaji a gurina da zai sadaukar da komai a kaina har ina da wanan matsayin yanzu gare shi haka ban sani ba.
Idan hakane ya kamata in gyara halin zaman takewan dake tsakanina dashi a yanzu fiye da da can baya da nake daridari da zamana dashi.
Ta yaya zan gyara hakan kuma na tambayi kaina shawara da manya akace bai baci duk da nima macece yanzu saidai ilimina da wayo na ai baikai in gano hanyar mafita da kaina ba.
Mamu zan nema kowa da sauri nace no ba mamu ba sai wa na tambayi kaina a take amsa ya zo min anty farida ko anty Ramla.
To may zancewa anty Ramla din in naje gareta dan dama anty Farida akwai shakuwa sosai a tsakanin mu wanda har zan iya sakewa in nemo mafita a gurin ta.
Tunda dama har takan ban dan shawaran yadda zanyi in karkato kanshi zuwa gareni saida taga banda ra,ayin hakan ta daina bani shawara.
To amma ai da zan baro gida Amma tace min ni mace ce da kaina zan iya kama zuciyar mijina ba sai an koya min yadda zanyi hakan ba.
Sallaman da akayi daga kofan dakin ne ya katse min tunanena Anty Ramla ce dauke da dan madaidaicin ture a hannun ta ta shigo dakin .
Na amsa mata sallaman a hankali ina kokarin tashi zaune tare da kakaro murmushi a fuskana.
Tace ashe ba barci kikeyi ba, yau kinki fitowa waje ki dan sha iska yanzu maigidan ya dawo yake tambayan ki nace kina daki shine yace a dubaki ko lafiya kike.
Shine nace barin dan riko maki dan abinda mai ciki ke so ka zaki sha tana aje tire din a gefena take wanan magana.
Kawai dai anty na dan kwantane tace tana kaiwa zaune kodai maganan mu ta dazun ne ya daga maki hankali.
Dan dukar da kaina nayi kasa ina fadin bai daga min hankali ba anty sai dai maganan yasa na shiga wani halin tunane .
Da sauri tace tunanen may zahra ?
Sai danyi shiru sake tambaya tayi tana kallin fuskana tare da fadin wai kina mamakin abinda merry tayi ne ko may ?
Kin san ai ba tunane gare su ba dama kila da biyu ta aure shi ai da farko tana ganin zata iya juyashi zuwa akidar su.
Ko kuma wata kila don kwazon shi da himma data gani yasa ta leke may Allah kadai yasan niyar ta na auren shi tu farko.
Amma kowa yasan merry ai ba matar auren mijin ki ba abune dai kamar na rufa ido kin san halin maza abinda ka raina shi suke dauka da muhinmanci su a gare su.
Murmushi nayi tace mutum wanda keda mata haka kamarki danya shataf ga kyau ga kurciya in ba abin maza ba may zaiyi da wata merry arniya ma can.
Anty nace sai nayi shiru na kasa magana tace au kin dauka da wasa nake fadi nace ba hakabane anty sai na fara hawaye.
Subbahanallahi tace hankalin ta ya tashi a lokaci guda wanan maganan ai ban fadeshi don hankalin ki ya tashi ba zahra.
Kai na girgiza mata ta dafani tace ki bar kuka kin san kina cikin wani hali da ba,an son tashin hankali a gare ki yanzu.
Anty ba haka bane kawai dai ina kukane don zamana da yaya ban taba kyautata mashi ba a rayuwana a

Please Login or Register in order to submit comment