You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gashi ko ya jawo din.
Kai ni wanan abu ya isheni wallahi yau dai ku sheda na dakatar da jimmai da maryam girki a gidan nan abar mutum daya yai jinya ta har lokacin da Allah yaban lafiya.
Ina wuta su sakashi a lokacin har mamun fada take ita bata yarda ba a lokacin saresarin a sakata gaba da wani kullin ya fadi a tsawace yana mikewa tsaye wanan dokanane haka kuma na yanke a raina da kyat yabi bango zuwa ciki cike da bacin rai a tare dashi.
Amma ce tabi kawu ciki ita da mama hadiye mama hadiye na fadin hakanma yafi wallahi mutum a cikin lalura za a ce sai lokacin da akaga dama za a kula dashi wanan wani rashin imanine haka don Allah.
Wanan abin zaijawa maimuna bakin jini a gurin su kuma shi nake son ku kula maimuna mutum ce mai ruwan ciki sosai.
Hajiya don Allah ku barni dasu idan ba ta baya na fito masu ba nagane so suke su karasani da raina.
Tau gidan kane iyalin kane abindaka yanke daidaine amma a sasauta don Allah Amma ta fada tana fita daga dakin.
Ranan kan zagin tonon asiri da gori mun shashi sosai ga bangaren biyu kowa ya koma sashen shi zuciyar shi cike da bacin rai abinda ya faru.
Hjy maryam da tayi waya tana shedawa yar uwarta abinda ya faru sai yar uwan nata tace daidai ke nan yayi min daidai tunda ana rabaki da shiga sharo ba shanu kinki dainawa ta kashe wayan kawai ta barta dashi a hannu.
Ita gaiyyan aikin yaranta ta shiga kira tana labarta masu saidai tayi neman layin umar ta sheda mai halin da ake ciki saidai bata samu layin shi ba ya manta tunda ya dawo ya canza layi saboda busy da yai mai yawa.
Amma ce tayi wa mamu magana don da ta bijire akan ba zatayi ba saida daddy yakai karanta ta yarda akan zatayi din.

Mun kashi rikici sosai da yaya da farko bai gane abinda nake nufi ba sai daga baya ya fahinci manufata din.
Kai ya girgiza tare da fadin baki da wayau yarinya karamace ke shiya har kikai tunanen hakan.
Banji kyamar merry da idan ta gama ba wankan tsariki takeyi ba sai ke da nasan kina wanka kina kula dashi yadda addini ya tsara zan kyamata ?
Ni lokaci ne banda shi kawai na zama gida saboda course din da mukayo a chaina muke gabatarwa a nan don karuwan na baya mu shiyasa nake kai wani lokaci a waje hakan.
Kunya ya rufeni gabadaya don yana fadi ya bar dakin ya tafi dakin shi abinshi.
Yanzu mai nayi haka na tambayi kaina waini nasan dadin namiji a kusa dani ko may ke nan nayi din.
Tunane nayi sai kawai na danna layin anty Farida a cikin daren nan na kirata kaf na kwashe abinda ya faru na fada mata tare da tambayanta abinda zanyi ?
Tace tawa kice min komai yai daidaita ke nan yanzu tsakanin ku har kin fara kishin mijin ki kuma.
Ba haka bane anty saukowan shi gareni da kuma matsin mahaifiyata daku yasa na yarda makaman yakina dariya ta tuntsure dashi tana fadin yanzu dai ki tashi ki shirya ki samu mijin ki a daki ki san kinyi gyaran da ba zai iya kawar da idon shi a kanki ba.
Godiya nayi mata bayan ta gama min bayanin komai na mike sai bandaki banda wani abin da ta lissafa min inyi don haka na dan zauna a ruwan zafi ina zaune ba a dauki wani lokaci ba naji na kara hadewa kamar ba wanda ya taba shigana.
Na zauna nayi komai kamar yadda ta umurce ni in yi manyatacen rigar baci na saka daga cikin wanda ya dawo min dashi da farko har ina zagin rigar dana dagashi naga harahara din shi yayi yawa sosai.
Zaune na samay shi a dakin shi ya harde kafa kamar mai tunane a lokacin sallamana yasa ya juyo ya kalleni.
Bai iya kawar da fuskan shi gareni ba har na karoso inda yake a hankali na tatare rigan cikin sallo na hauwo gadon jikin shi na dan fada ina fadin yaya har yanzu bakai barci ba ashe ?
Dan ajiyan zuciya ya sauke kafin ya kai hannin shi ya rungumoni da kyau yana fadin mamaki maganan ki nakeyi zarah kayi hakkuri nace ina kai kaina saman kafadan shi na kwanta da kyau.
Wani iska ya furzo daga bakin shi duk cikin sauke ajiyan zuciya ne hakan yace ban san yaya zan maki bayani ki gamsu dani ba.
Hakkuri na sake bashi na hana bayanin da yake son min din a lokacin ta hanyan hura iska a hankali zuwa cikin kunnuwan shi wanan abinda nayi ya jagula muna lissafin komai.
Sai da komai ya lafa a tsakanin mu na yunkura da niyar shiga bandaki da sauri naji ya rikeni sai da gaba ya sake faduwa a zatona wani abin zai sake min da wanan katon kan ihu sosai zan masa.
Amma sai naji yace dani not now ki bari sai dan anjima ka dan zaki iya kewayawa ba a wanan lokaci ba dan kallon shi nayi sai naga ya kawar da fuskan shi kamar bashi yai magana yanzu ba.
Kewayan da banyi ba ke nan sai a cikin dare na falka na samu yayi wanka ya gama sallah yana zaune yana karatu.
Nima wanka nayi daga gurin kewayawan na fito sai dai da yake ban zo da shirin sallah ba don haka na sake kwantawa da alwala a jikina kawai.
Sai asuba ya tayar dani sallah dakina nanufa na sake wanka tare da dauro alwala na fito na dade zaune ban daga ba ina addu,oi wani barci mai dadi ya dinga fisgana daga inda nake zaune dan kwance nakai a kasa gurin da nake zaune.
Shikuma samun kanshi da yayi da rage aiyukan dake gabanshi ya tuno wayan shi akashe yake duk wanan lokacin ya mayar da sim din nashi ya kunna waya.
Ya Umar zaman turaine kawai amma bai yarda ya yarda addinin shi da al,adun malam bahaushe ba don idan ya tashi ya tashi kenan sai kuma wani daren zai zauna bayan ya gama addua ya duba sakoni a laptop din na mayarwa ya mayar wanda baida bukatan amsa ya barshi.
Ranan baisan ya akayi ba sai barci ya dan fisgeshi har yai mafalkin da hajiyan su ina gudu tana bina da sharbeben yuka ga yara ina ja acikin galabaita.
Innalillahi yace lokacin daya mike zaune daga ringinginen da yake kwance din yana mamakin yadda akai barci ya dauke shi da kuma tuna abinda ya gani a mafalkin nasa.
Addua yayi kafin ya mike ya shiga yai wanka ya shirya daya fito saukowa yayi sai jini gidan tsit kamar babu kowa a gidan lokacin .
Haka yasa ya gane banfitoba kamar yadda na saba fitowa inyi aikina da safe dakina ya juya ya kalla yana rufe ya nufi dakin ya tura a hankali ina kwace ina dan juye juye cikin wahala ina dan magana irin na mai mafalki takawa yayi yana kiran sunana ban amsa ba sai ya saurara da kyau yaji ina fadin salma mai nayi maki zaki kashe ni ?
Gaban shi ne ya fadi jin abinda nake fadi da sauri ya bugi filon da kaina ke sama ina kwance a kasa yadda na kwanta a wurin danayi sallah.
Mikewa nayi a wahalce na sauke idona a kanshi yana tsugene daidai saitin fuskana kamar yana min addua a lokacin.
Ki tashi yace yana mikewa tsaye kwanci a wanan lokacin baida kyau kin sani yana toshewa mutum hanyan alherin sa ne.
Dan mika nayi tare da salati ina fadin bansan nayi barci ba a nan saidaya juya yace wanan dabi,ar kine nasani ya kamata ki daina.
Ban fito daga dakin ba sai dana shirya na fito yana zaune a falo na gaida shi da kwana zan nufi kitchen naji yace ga abin karyawa nan na amso muna yana nuna min kwalin daya sayo din.
Dan jakkan kwalin na dauka na nufi danin dashi ina fitarwa a hankali pakege ne a ciki guda uku plates na dauko a kitchen na juye a ciki ina mamakin ko a ina ya sayo shi da wanan safiyan haka ?
Chip's ne sai ganye da sauran tarkace irin abincin su na turawa na juyo ina fadin yaya ga abincin ya mike kamar dama ni yake jira in hada lokacin.
Har muka kareci ba wanda yai magana a cikin mu saidai ina kula da yadda yake tura abincin kamar yana da damuwa a ranshi lokacin.
Yana gamawa ya mike ya barni a gurin na dan dauki lokaci nima cikin damuwan ko may ya samai shi ya canza haka lokaci guda oho ?
Yana zama yaji sako ya shigo mai a waya kamar ya share sai yadai ya dauko wayan yana dubawa Aliyu ne yayo mai text.
Bros ina komai lafiya a wajenka mama tana neman layin ka bata samu akwai matsala a gida daya faru sai dai kabi hukuncin ta a sannu don Allah don ta dau zafi dayawa.
Iya abinda ya rubuta kenan ya dade yana maimaita sakon bai fahinci komai da sakon ke nufi ba iya abinda dai ya fahinta shine .
Akwai abinda ya faru a gidan wanda mahaifiyar su ke son daukan fansa a kaina kila kodai wani abin.
To ko shiyasa yayi wanan mafalkin dayayi da safe yasan dai shi ba gwwnin yin mafalki bane sosai hakan.
Idon shi a lumshe koda na fito yana tunane a ranshi rabuwa da zarah matsala ne gare shi yanzu kamar yadda mama ke nufi abin ya wuce nan yanzu.
Na nufi dayan kujeran zan zauna duk da idon shi suna rufe naji yace zo nan ki zauna yana nuna min gefen shi.
Sai lokacin ya bude idanuwan shi yana kallona na mike a hankali zuwa inda ya nuna min cikin kunya don munyi kusanci sosai da inda ya nuna min in zauna din.
Ta tako a cikin tafiyana kamar na tarwada na zauna a hankali ajiyan zuciya naji ya sauke lokacin dana zauna din hannun shi ya dora sama kafada ya dan karyo kanshi zuwa wuyana yace zarah fada min mafalkin dana samu kina yi dazun dana shiga dakin ki ?
Dagowa nayi na dan kalleshi babu wasa a fuskanshi nace mafalkine kawai dai ba kuma yau ne farkon yin shi duk na kwanta kusan kullun ina wanan mafalkin ko yaushe .
Fada min akan mainene kike mafalkin nace sai nayi shiru na kasa magana yace fada min mana ke nake saurare inji ?
Dama dama sai na kasa fadi yace umhumm dama anty salma ce dai nakan gani tana son wai kasheni.
Tun yaushe kika fara wanan mafalkin ya tambaya kunya naji na kasa magana yace kinga fada min in akwai addu,an da zakiyi sai ki dinga yi don yanayin dama samay ki dazun ya daga min hankali sosai yau.
Dama dai ba wani abu bane sherin mafalkine kawai yaya ganin ta nake wai zata kasheni sai kuma wani lokaci zata jefani a rami.
Nace tun yaushe kika fara tambayan danayi maki ke nan yanzu ai ko ?
Ya fadi yana dagowa daga kafadana tare da tsura min idanuwan shi akaina nace tun lokacin daka fara saduwa dani na karasa a hankali.
Sai naga ya koma ya kwanta a makarin kujera ya dora kanshi yana lumshe idanun shi a hankali .
Bai faye yarda da mafalki gaskiya bane amma wanan din yana da bambamci tunda shima yayi kusan irin wanda nayi din ai to mai hakan ke nufi ke nan ?
Ganin yadda ya kwanta yasa na kai kaina a jikinshi na dan mike kafafuwana ga makaran kujeran ta gefe na lushe idanuwa hannunshi naji ya dora a kaina yana wasa da gashina a hankali.
Wayan shi ne ya dauki kara ya dauka muna a hakka yadda muke da kusanci da juna din naji yace mama barka da asuba.
Jin hakan yasa na mike da sauri zanbar wurin naji ya rikeni gami da yimin alama in kwanta abina.
Barkan mu tace mai yace lafiya mama da safen nan haka kallon lokacin da yake kira safe nayi lokacin sha dayan rana yana batun yi a London.
Babawo akwai matsala a gidan nan nayi neman layinka in sanar dakai halin da muke ciki ban samu ba.
Naji yace may ke faruwane mama a gidan wai kamanni Alh zaice ya dakatar da girki a gidan nan kan wanan shedaniyar matar kaddaran da ya aura maimuna harda hjy maryam laifin ya shafeta don bai son gaskiya .
Abinda nake so dakai yanzu shine ka rubutawa yarta takarda ka turota jirgi ta dawo masu gida tasan munfi karfin ta ta ko ina don hakan kawai za kaimun ka wanke min bakin cikina.
Shiru kawai yaya yayi bai tanka ba a lokacin ita kuma mama taci gaba da aibantani da uwana ina jin ta kaf don ina saman jikin shi lokacin komai na shiga kunnena.
Can ko taji haushin shirun da yayi mata din ne bai bata amsa ba tace wai kanajina kuwa babawo ina magana kayi shiru ko kana nufin bukatana ba zai yuyu bane na sani.
Na fadama ban yarda da karatun da kace in bari ta karasa ba yanzun nake son ayita ta kare ba kare bin damo inhar ta kare karatun ai taci riba damu ke nan daga ita har uwarta din don yarta ta samu madogara ta dalilin mu don haka ina duban hanyar ta zuwa jibi ta kashe wayan don baida niyar bata amsa a lokacin.
Yana jin ta kashe wayan ta naji ya sauke ajiyan zuciya yana fadin mamake nan laifin wani ya taba shafuwan wani ne ashe ?.
Ya dago daga yadda yake kushingide ya zauna da kyau nima mikewa nayi zaune gaba daya yanayina ya canza ga baki daya lokacin.
Sai addua nakeyi a bakina don abin ya firgitani sosai Allah kadai yasan tsawon lokacin da hjy ke binshi akan ya sakoni don maganan ta ya nuna ba yau bane farko.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:25 - 🤐🤐🤐: BISSMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AMINN YA ALLAH,

GA MASU BUKATAN LAYINA ZASU IYA KIRA TA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 08036959257 DON TURA KUDI KUMA ZAKU IYA SAKA KATIN KIRA KO TA ACC NOBA KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU.

Ki sani shi hakki kona haramun ne kamar yadda wasu ke fadi hakki daine, don Allah mu kula yan uwa .

Tunda na samu naja kafata zuwa daki da kyat ban kara fitowa falon ba ina kwance ina faman tunane ga ba wanda zan iya fadawa wanan halin da muke ciki.
Wani bangare na zuciyana yana bani in sulale kafin sakin ya biyo baya in koma gida da kaina inyaso ya kawo min takardan nawa a gida.
Ba irin shawaran da banyi ba a lokacin har rana tayi lokacin sallah yayi nayi sallah ina kwance ina abu daya a da(kina har lokacin bancin ma manufa ba saidai ina ga shawaran in gudu in koma gida har lokacin.
Tambayan kaina nayi ta yaya zan iya guduwa bayan banga visa dina ba tun lokacin da muka sauka a kasan ya karba daga hannuna.
Sai bayan sallah la,asar ya shigo dakin ina kwance rub da ciki saidai ba barci nakeyi ba a lokacin.
A hankali ya karasa shigowa dakin yana kallona don jin shigowan shi dakin baisa na dago daga yadda nake kwamce ba a lokacin.
Zarah kinyi sallah kuwa ko kina nan kwance kina tunanen banza tun dazun idona da ya cika da kwalla na dago kai ina kallon shi dasu nace ciki ciki nayi dazun.
Zama yayi bakin gadon yana kallona cikin yanayin tausayi daya san maganan da mama zatai mashi ke da yabarni natashi kamar yadda nayi niyaryi da farko da banji abinda zai daga mim hakalina ba yace a zuciyar shi.
Ki tashi muje falo kayana da na sayo danaje china sun iso akwai kayan dana sayo maki a ciki ko zasuyi maki kyau ban sani ba.
Bandago na kalleshi ba ina daga inda nake kwance a raina nace shike nan ta faru ta kare har ya soma min shirin zuwa gida ke nan ashe ?
Ganin ban motsaba yace zarah ke nan badai maganan mama ce ya tayar maki da hankalin ki haka ?
Zarah kin fara sona har hakane yanzu baki son kiji ance za a rabamu ko mai da har kika shiga tashin hankali hakan.
Da sauri don ya fahince ni nace dole ne yaya ya sake kallona a cikin yanayin tausayawa a gareni yace mama bata sani bane ai komawan ki gida yana daidai da komawan ta nasu gidan itama.
Bayan hakan ku zarah sai naga yadan girgiza kai kafin yace idan nace maki yanzu babu mai iya rabani dake zaki gamsu da magana ta kuwa ?
Da sauri don in kwantar mai da hankali kamar yadda naga yana kokarin yi shima nace mai zai hana yaya in yarda da kai tunda ban gaka da mugun hali ko kadan a rayuwan ka da zaka iya cutana sai naga yayi dan murmushi ya sake kalloni ya gyada kanshi da alama ya gamsu da maganata.
Ke nan zaki daure da duk wani halin da mahaifiyata zata nuna maki na kiyayya nan gaba ?
Nace nima ai mama mahaifiyatace koda ban aure ka ba yaya yanzun ma zafin kishin mamune ya shafeni ai har take jin bata sona a tare dakai.
Naga ya saki wani laulausan murmushi a fuskanshi yayin da hannayen shi ke dunkule a wuri daya yana dan buga kafan shi daya a kasa.
Zarah ke nan kin dai iya magana kamar wata babban mace to wai in tambayeki zarah shin kinsan taba noticing mai kalman aure yake nufi a wurin ma aurata ?
A daidai lokacin na mike zaune daga kwancen da nake ina bashi amsan duk wani magana da mukeyi sai da nadan yi murmushi nace .
Nace yaya ke na indai zaman auren kowa wace mace zatayi dace da namiji kamar ka to ina ganin kaman mata sun gama dace maza da jin dadin aure.
Don baka rageni da komai ba na rayuwa yaya kana ban cida sha ga sutura maikyau sai wanda na zaba zan saka uwa uba ga karatu inayi babu matsala ko kadan a cikin sa babu kyashi ko hattara a zaman mu.
Sai nake ganin indai auren namiji ne kamar ka babu wace tafini dace da aure wanan zamanin kaf a duniyan nan.
Dadin zancena ya kamashi ya jawoni zuwa jikin shi tare da dan bubuga min baya yana fadin nima ina alfahari dake zarah taso muje falo kiga kayan dana sayo maki idan zasuyi maki in basuyi ba sai in sayo maki wasu a nan don kinsan wani sati zaku fara shiga school.

KANO NIGERIA.
Murjanatu ce tsaye a bakin famfon waje na kofan part din su tana wanki don ko wani part akwai famfon a kofan wurin do laluran waje.
Ganin yadda hjy maryam ke dan waige waige zata shiga part din yasa tasan ba alheri zata kullawa ba a lokacin.
Samun kanta tayi da bin bayan ta ta window gefen dakin hjy jummai dake bude ta labe tana sauraren su.
A daidai lokacin da hjy jummai ke fadin ai na fada maki yadda suka kona muna mai a gidan nan sai na konawa ko wanin kaf rai agidan nan fiye da nasu.
Nayi waya da babawo da safen nace ya sako masu yar iskan diyan su yasata jirgi da takardan ta ya turo ta gida karatun da yake fadi tanayi ban yarda koshi ta karasa ba.
Da sauri murja ta dafe kirji tana fadin na shiga uku A ruwa kena za,a sako kowa da sauri tabar wurin jin yadda suke faman aiban tani da mamu.
Kayan ta tataro ta nufi part din su Amma da mama hadiye dake zaune suka kalleta bayan ganin ta da himin kayan da ta fita dashi don wankewa ta dawo dashi kuma.
Ke dai malalaciyace kin kuma kasa wanke kayan ki dawo dashine hakana sai kinjera kina sawa sun kare, daga baya ki dawo ki damay mu da korafi kuma.
Murja batai magana ba sai da ta mayar kayan daki su ta dawo ta zauna jiki ba karfi tayi shiru tana tunane haka yasa uwar ta farga da halin da take ciki a lokacin.
Kasa daurewa mama tayi abin da da mahaifi tace wai yana ganki kin dawo haka jiki ba kwari kuma kamar wace tayi gamo kuma data fita.
Kallon Amma tayi tana fadin Amma Allah yayi gaskiya daya hana lebe a rayuwan bawan shi don mutum zai iya jiwo kanshi ranan mutuwa shi a bakin wani.
Labe kika fara yar nan wallahi amma labe nayi na jiyowa kaina abi tashin hankalin da ban taba jiba yau.
Aiko baki kyautawa kanki ba ga maryam nan har girmanta ya zama mata cuta har yaran ta komai mutum yace sai yaji ko sai ya gani ya hana zuciyar shakat dagangan da gangan.
Wai ma may ki jiyo kinzo muna hankali a tashe haka kamar wani ya aikeki yin mugun abu ?
Wallahi mama ruwan famfon mu nai fita da sauri nace barin tafi shiyan hjy intara sai in kawo inda nake wanki din.
Sai ga hjy maryam da saurin ta zata shiga part din hjyn su salma har tana tuntube wurin sauri shine naji zuciyana bata yarda da ita ba lokacin sai na matsa bakin windon ina sauraren su mama kinsan abinda najikuwa ta fada tana kallin mama.
Sai kin fada uwar labe mu ina zamu sani tunda bamu aikeki ba kiyi labe.
Umhumm mama labena kila yai rana Allah dai ya yafe mun wallahi ji nayi suna fadin wai hjy su salma tasa ya Umar ya sako A ruwa ya turo jirgi da takardan tana saki kada ya hado ta da komai yadda sukaji zafin abinda kawo yai mata suma nan suji shi kamar su.
Taci gaba da fada masu sauran maganganun da taji suna fadi a kaina da mahaifiyata a lokacin.
Abu ga tsufa hankalin Amma in yai dubu ya tashi nan ta shiga sake salalami sai da mama hadiye ta taushe ta.
Kada su bari a san an gane wanan magana zata kira mamu yanzu ta tambaye ta layina nacan akan zasu kirani suji lafiyata daga nan sai suji mai ke gudana a tsakanin mu.
Amma kafin nan murja karbi kudi ki sayo mun kati don kiran kasar waje saida kudi mai yawa a layi.
Ta cire dubu daya ta mikawa murja ta fice da sauri a daidai lokacin hjy maryam ta fito daga part din hjyn su salma a cikin fara,an ta.
Murja tace munafuka mun daiji shirin ku bake

Please Login or Register in order to submit comment