You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na kawo karanki akan may zanyi karan ki gun daddy kuma mama ?
Da kyat ta samu ta daidaita natsuwanta kafin tace nasan zaka iya tunda na hanaka tafiya da ita ?
Mama ina mun gama wanan magana dake ko akan may kuma zan tayar da maganan yanzu kuma ?
Kara kallo shi tayi irin duba na tuhuma duk sai yabi ya tsargu don bai san abinda zai biyo baya ba kuma yanzu yadda yaga ta hau din nan.
Tace bawai ya fada min kakai karana bane tuhumar hakan dai nakeyi dama babawo wai may yasa baku gudun bacin zuciyana ne ?
Yace mama idan ni na fadawa daddy ai zan fada maki gaskiya ko cewa nina fada mai din.
Tayi shiru bata tanka ba na dan wani lokaci kafin tace yanzu dai burin ka ya cika amma ka tabbatar da sanin duk wani abin al,ada da akeyi idan mace ta haihu zaka barmuna muma nan ayi kamar yadda al,ada yake.
Dago kai yayi ya dan kalle ta tace eh haka nace babawo don ba zaka maishe mu dakarkarun iyayye ba.
Naka tsarin kaje can ka kashewa kafiran banza kudade munan ko oho kenan mun haifar masu da daga sama.
Ayi hakkuri mama insha Allahu za ayi yadda kikace din sai a lissafo min duk wani abinda zaku bukata a nan din ayi yadda aka saba din.
Tace dama hakan za ayi don ba zan haifawa wata da ba saida lokacin cin moriyan ku yazo wata can daman ta amshe min ku.
Ga mata nan kasan yan asali amma duk basuyi maka ba saida ka tsalaka kaje inda zaka jawo min abin gori ga jamma,a.
Tana fadan haka ta mike zata shiga dakin ta ya bude baki da kyat yana fadin mama don Allah kiyi hakkuri idan ranki ya baci ne ?
Sai ta juyo jin yadda yai maganan kuma sai ya bata matukar tausayi sai dai babu yadda ta iya don hakan da takeyi tana son dasa masu tsorontane a zukatan su.
Ta maida kanta ta juya ta shige umar yaji kamar ya dora hannu akai ya kurma ihu dan tsaban takaici saidai koba komai daddy ya kwatoshi daga tafiyan tunda alama ya nuna ta yarda.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:08 - 🤐🤐🤐: BISSIMILAHI RAHAMANIN RAHEEM


Ban shiga school ba sai ranan monday kamar yadda Amma tace mun kuma har lokacin a gurin ta nake kwana sai dai danaji sauki ina dan zuwa part din mu in kai wani lokaci a can.
Haka sai yasa Amma bata son inyi nisa da gurin ta ko kadan ko yaushe idan ina gida ina wurin ta zaune idan kuma nazo part din mu zakaji ta aiko wai in zo.
Koda nazo din kuma ba wai wani abin zan mata ba zakaji tace kin je can kin zauna ta dinga matsa maki kawai.
Kawu ko da ya dawo da dan tsaraban Amma kullun wanda muke taruwa dani dasu Aisha mu cinye abin mu sai yan kanne na dakan biyo ni nan part din ta din su zauna tare dani saboda sabon da mukayi.
Wanda hakan yana a kunnuwan mutanen gidan da suke ganin kamar an kaini can gun Amma ne don wani abinda muke kullawa tsakanin mu.
Salma ne ta shigo muna tare da Amma a falon wanda a yanzu zamana a cikin sa yana samun gyara sosai kai da kai ina tsabtace shi.
Wuri ta samu ta zauna ba tare da taiwa kowa magana ba sai Amma ta kalleta tana fadin gaki kamar a jefo ki kinzo kin zaunawa mutane kimkam a kai ?
Cikin wani murya na shagwaba tace yanzu Amma don na shigo gurin ki shine kuma zakiwani ce min na zauna maku kimkam a kai ?
Amma tace kinga sakona nane kizo naki dai ya kawo ki dama ta mike zuwa wurin fridge din Amma tana fadin akwai fura a fridge din ko baki dama ba ?
Aiko ina dashi bazan baki ba son ba don ki nake ajewa ba ta juyo tana fadin Amma ai kin ba A ruwa tasha ko ?
A ruwa ai bake bace don A ruwa ta fiku sanin zafi na da darajana a gidan nan yaushe rabon da na sakaki a idona gidan nan ?
Dama ai hakane sai bare ya zo ya fika daraja kai da gidan uban ka ko baki furta ba mu san da hakan a wuri ki Amma.
Amma tace A ruwa tafi karfin zama bakuwa a gidan nan ko bare don duk daya kuke a gurina tunda suka fara magana ban kulata ba tun shigowanta falon sai yanzu da tayi wanan maganan.
Dadin abindai da ubana ba shegiya aka haifeni ba gida kuma gidan kawuna nazo salma ko anty salman da tasa muke kiranta ban kira ba lokacin.
Tace dama wani yace baki da ubane ko kinji na fadi hakan sallon kuma ki koma kice ga abinda nai maki yanzu daddy ya samay ni da fada.
Allah sarki ai bagware ba bobawa bane kowa yayi jifa a kasuwa yasan wanda ya jefe balle ma kin fito fili kin kira sunana kai tsaye abinda kuke dauka ba shi nake a nan ba.
Kada ki soma ki fada min maganan banza a gidan nan don kina ganin wuyan ki ya isa yanka ke a gidan nan kowa zaki iya fadawa magana kai tsaye.
Cikin bacin rai Amma tace salma ki fice mun daga shiya tunda ba alheri ya kawo ki nan ba yarinyar nan ko lafiya bata da amma saboda bakin halin ku kuda iyayyen ku ba wanda ya iya budan baki ya tambayi jikin ta.
Yanzu kuma kinzo zaki tayar mata da hankali haka muna zaunen mu kalau a nan wanan wani bakin hali ne shin inda uban yar nan yaje ko yau ko gobe iyayyen ku kuma tafe suke sai ko idan zasu tsaya gadin duniya ne in sani.
Mutane a kullun baku da magana sai gori a kan mutuwa to iyayyen naku da suka dauki duniya da fadi su zauna jiran duniya.
Juyawa tayi tana fadin shigowa nan yasa har za a fada min magana kan iyayyena saboda wanan yae sadakan da ake neman likawa mutane.
Kikai kuwa nace mata dama a kwance nake ina magana na mike zaune ina fadin duk mune yan sadakan idan sadaka illace ashe .
Gara wake da kowan wake don a sarafa waken a nau,i nau,i wani ko a kowan yake tsayawa tace may kike nufi nace kije wanda ya turo ki yai maki bayani ni yar sadakace .
Daga hakan ta wuce fuuu ta bar falon nan tabar Amma na sababi da ita bayan fitan ta na dauka zasu dawo da hjyn ta sai naji shiru kuma.
Sai washe gari kawu ya shigo yana tambayan Amma abinda ya faru Amma ke fada mai yadda akayi ta kare da fadin wa yan nan mutane ba mutanen arziki bane.
Ni ba don ka rigada kayi wanan alkawarin ba da an fasa wanan hadin abu tun yanzu yakici yaki karewa haka tun ba,aje ko ina ba.
Hajiya dama ai shine bukatan jummai ta dagawa mutane hankali ba gaira ba dalili ni amsan da fatima ta ba salma yai min dadi.
Da yake basu da tsoron Allah ni ba haka uwarta ta mayar min ba don cewa tayi Fatima tana zaginta ta hanyar diyar tane.
Lalai wa yan nan mutane basu tsoron Allah a rayuwa su yar nan ta shigo muna kamar an jefo ta tazo muna da tashin hankali haka ?
Hajiya nasan halin kowa a gidan nan fa ba sai kin tsaya kina bata ranki ba a kansu ina daga ciki ina jin su ban fito falon ba tunda baji ya dauko zancen namu da salma.
Ya fice tare da yi mata sallama saida takai kofa yake tambayana tace ina ciki na kwanta ne tun dazun yai mata saida safe ya fice .
Umar da merry wace yanzu cikin ta yayi girma sosai suka shigo gidan don yin sallama da iyayyen nasa wanda daga sama sauran mutanen gidan sukaji tafiyan nasu.
Sun dan jima gurin kawu kafin su fito su shiga dakin mahaifiyar shi a nan ma sun jima a dakin merry data kagu su tafi tace zata fara shiga wurin mamu kagin ya iso ta mike da kyat zuwa gun mamun.
Zaki gane kuren ki idan kin san sheri da macuciyar suke kulla maki sai kare ya fiki daraja gidan nan ta fada kasa kasa ba tare da daga murya ba.
Sai kuma ta juya gurin dan nata tana fadin ka sai dai ban yarde maka zuwa gurin maimuna ba yace na sani mama.
Daga haka yai shiru yana latsa wayan shi dake hannun shi ba tare daya sake magana ba sai can dataji shirun nasa yai yawa tace ke nan goben zaku wuce kai sai yaushe zaka dawo idan kun tafi ?
Ina ganin sai ta haihu zan shigo kasan nan ya bata amsa tace aikin dakake a nan fa tunda kace baka kare ba.
Na barshi a hannun wa yanda ke aikin ya bata amsa mata a yanayin rashin son magana don yadda yake ji din a lokacin.
Kasan zaka bar komai da za ayi a nan kamar yadda na fadama ina son ayi ta sake fadi ya dago kai yace amma mama cewa kikayi ai sai idan ta haihu zan turo maku ko ?
Ban yarda da hakan ba yanzu na canza shara kabar komai daya dace a gurina yadda zai ishe mu yace ba matsala mama.
Yana mikewa tace zaka tafi ke nan tunda matar ka ta kasa zama nan din ko ?
Yace gurin Amma zan shiga muyi sallama da ita yana kallon fuskanta yaji may zatace mai sai tayi wani iri da fuska kawai ba tare da tayi magana ba.
Yana ganin haka ya fita kiran layin merry yayi don baida halin shiga part din mamu a yanzu saboda bin umurnin uwarshi.
Merry ta fito suka shiga gurin Amma don yi mata sallama sun dan zauna bayan gaisawa yace Amma mun zo mu sallame kine gobe zamu koma England insha Allahu.
Ta kalle shi tana fadin goben nan dan nan ni na dauka wasa kake min ai da ka fada min ranan hankalin shi yana ga wayan hannun shi da yake tura sako yace.
Ina fatan kin shirya tafiyan ta dan tabe baki tana fadin rabani da shirmay yanzu in ka tafi sai yaushe zaka dawo ke nan ?
Yace gaskiya Amma ba maza ba don zan dan dauki lokaci a can sosai kafin inzo kasan nan.
Amma tace idan ka tafi zancen yarinyar nan fa da sauri ya dago kai yana fadin wace yarinya ke nan Amma ?
A ruwa nake nufi don naji mahaifin ku na fadin karshen shekaran nan zai aurar dasu duka.
Ya dauri fuska kafin yace Amma yaran nan kanana ne fa may daddy kewa sauri ga auren su haka yanzu da wuri ?
Ka tambayi uban nakama shida yake son hakan yarinya ko kallon arziki bata samu gare ka yaushe ka tsaya ma kai mata kallon tsab,
Amma may yasa kika damu zancen auren nan ne haka wanan yarinyar ma fa bata kai wani shekarun aure ba.
Nifa Amma kin sani auren biyayya ne zan maku don haka duk lokacin da kaga ya dacd sai a fada min.
Kallon kai a suwa Amma tayi mai taja tsuki tare da fadin banga laifin ka ba tunda idon ka ya bude yanzu da masu dan bujen nan.
Ban san da su a falon ba dawowa na ke nan daga unguwa nida su Aisha ina saye da les dinkin buje da riga yau anyi sa,a na saka mayafi a jikina .
Sai kitson da ke kaina daya dan fito don daurin dan kwalin danayi sai kamshin da jikina ke fitarwa don daga wurin bukin kawar Aisha muke don tare suka kare karatun su dasu salma akai mata aure.
Yana hangoni yaji gaban shi yayi mumunan faduwa saboda saboda shigata ra yau ya fitar min da surana na asali a fili.
A hankali ya lumshe ido daga inda yake zaune merry ko tana ganin mu ta shiga washe baki gare mu tana fara,a tace dama tana tunanen ta tambaye mu kada ta tafi bamu gana ba.
Kallon inda yake sukayi suna fadin yaya ina wuni kunzo lafiya ?
Ya amsa ba tare daya dago kai ba da lafiya nikan wurin Amma na nufa ina fadin Amma yau duk na gaji wallahi a cikin muryan da ban san inayi ba wanda mai saurare zan dauka shagwane.
Merry ta tace in zo kusa da ita tana son muyi sallama gobe zata koma kasar england maiyuyuwa ba zata dawo kasan nan maza ba idan ta haihu.
Jin haka na yasa Aisha ta ce ba zaki tsaya ki haihu a nan ba mu dauki baby tayi murmushi tace gaskiya ba zata iya zama nan kasa ta haihu ba .
Ban san ya akayi bakina ya furta amma uban babyn naki ai a nan aka haife shi kuma kema ai yar kasan nan ce.
Ba tasan may nake fadi ba sai kallona ina magana tayi tana fadin nayi fushi da kika zo gun grany kika nufa bayan kin gani a falon.
Dan rage murya nayi ina fadin ban kula ku bane a falon sai yanzu.
Idanuwan shi da suka sani saurin dukar dakaina ya dago ya watso min na jin nace ban farga sune a falin ba.
Nayi saurin dukar da kaina kasa tare da juya gurin Amma ina fadin Amma yunwa nake ji wallahi.
Ke yar nan yanzu kika dawo gidan buki zaki kira min yunwa a nan yanzun kuma?
Amma kin san Fatima kamar tsoron mutane take yi taki sake jiki taci komai da aka bamu a gurin .
Shine filancin ta nuna maku asalinta na kwarai ne ai macen kwarai bata zubar da mutuncin ta a duk inda take.
Amma mu zamu tafi sai kuma idan Allah ya kara sadamu da alheri don jirgin mu da safe zai bar kano zuwa lagos insha Allahu.
Yaya tafiya zakuyi ne da gaske Aisha ta tambaya bai bata amsa ba sai mikewan da yayi tsaye daga zaune.
Amma tace miskilin zai koma inda yafi wayau nan kunsan cizon shi akeyi komai tsiyan ka dai daga kauye kakani ka suke.
Ya dan murmusa yana fadin gara sai da kika tsaya akan kakanina da sai ince wani uban nawa kika gani ba kauye ?
Nikan dadi naji har cikin raina sosai jin zasu bar kasan gaba daya ina Allah yasa ma kun tafi ke nan namamajon kawai.
Jin kamshin shi kusa dani yasa na dago kaina shine kuwa ya matso kusa da Amma yana mika mata kudi tare da fadin ga wanan kiyi hakkuri sai idan na yo maki sako kuma.
Ya dan lakuci kumatun ta yana fadin Amma ki kula muna da kanki kin san muna ji dake sosai daga haka ya juya ya fara tafiya merry ma ta mike tana fadin zasu tafi tana kallon Amma din.
Hannu amma ta daga mata tana mata na bebaye alaman a sauka lafiya.
Wanan tafiyan nasu ni ji nayi kamar an min albushir da aljanna don ina ganin ya samu ya kurce masu ke nan ba zai dawo ba kuma nan maza.
Don ko hjy maryam sai daga baya take jin wai sun tafi basuyi sallama dasu ba dan gara ma mamu don shigan merry ta san zasu koma amma batai tsanmanin zai tafi bai sallame su ba ai.
Bata dauki wanan komai ba a gurin ta don ba bakon abu bane haka a wurin ta sai bayan sun tafi ne sai ga Aliyu da sako a boye ya kawo masu yana mai basu hakkurin rashin yin sallama dasu da bai sami daman yi ba.
Hjy maryam.tace ita kan ko ba sallaman baki ai ya gama mata komai ko Allah dai ya kaisu lafiya dashi da arniyar shi.
Sai dai mamu bata ji dadin hakan ba don taso suyi magana dashi a kan merry sai gashi kawai tafiyan shi taji daga sama babu sallama .


Ayi manege yau ban samu natsuwan typing ba yan uwa sai kun jini kuma zuwa gobe insha Allahu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:09 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHEEM YA FATTAHU YA SALAM, , ,


Sun isa lafiya inda ya samu abokan arzikin shi suna kewan shi sunyi missing din shi sosai musanman a gurin aikin shi mutane da yawa sunyi missing din shi gurin.
Tunda suka kaishi gida suka dire ya shige sallah ya gabatar da ake binshi yana gamawa yadan ci abinci don shigan dare sukayi .
Ya kwanta bai fito daga dakin ba saida hayaniyan su merry da akazo yiwa adduan kore mata evils sprit din da ta kwaso a Nigeria ita da baby ta da maigidan.
Pastor mahaifinta ya dauko masu dungurun gun don yin addua gare su don ma a ciki dare suka sauka da abin yafi nan don da church za a kaita ai mata wanan adduan.
Saukowa yayi yana saye da wando three quarter a jikin shi sai riga fara daya saka a jikin shidon shan iska.
Tunda yake saukowa yake kallon merry da take tsugun ne ta rufe ido hannaye ta na sama alaman roko take yi kenan.
Pastor da mahaifin merry sukai mai alama da yazo gurin adduan shi ma ya kalle su da mamaki ya kara tsare gida a fuskan shi don haka yake masu idan zasu tursasa shi yin wani abu na addinin su .
Pastor din yace ya kamata kaima kazo a kore maka evils din da suka biyo ku a tafiyan ku yace cikin kada kai banda matsala ni yana tafiya yake fadin hakan ys nufi hanyan fita daga wajen gidan wurin wani dan shan iska na gidan ya tsaya yana karewa dogayen gine gine garin kallo daga inda yake ya sauke ajiyan zuciya a hankali.
Dafa dan karfen dake gaban shi yayi yana lumshe idon shi a hankali babu abinda ke zuciyar shi sai tunanen abubuwan da suka faru zuwan shi nigeria suke dawo mai a rai.
Ya sauke ajiyan zuciya yana kara lumshe ido tare da dan damke karfe da karfi yana hadiyan zuciya.
Daidai lokacin mahafin merry ya fito yana bin kusurwan gidan yana wasu sambatu irin nasu na kiristoci da sukeyi wai ana koran shedanu a gidan .
Bai kula shi ba don idan da sabo ya saba amma shi ko a jikin shi duk wana abubuwan da sukayi yakan nuna takar bai san dunayi ba.
Inda har yakan basu mamaki irin taurin kan shi akan riko da addinin shi don basu san zai iya riko haka da addinin shi ba sai zuwan nan da sukayi nigeria ne merry ta tabbatar da idan tushen rikon addinin shi duk yan gidan su tana ganin kamar malamai ne don irin shigar su da suke .
Ita babu abinda ke bata mamaki kamar yadda har da kananun yara suke saka zunbulelen hijab da nikaf a fuskan shi tunda wanan yar ta step mum din don tun a waya ta labarta wa iyayyen ta wanan akidan na yan gidan.
Muryan maman merry ne ta zo inda yake tana fadin my inlaw ya hanya ya mutanen ka can ya dan lumshe ido cikin rasgin son nagana yace suna lafiya ta sake fadin .
Munzo kana kwance tu safe don yiwa merry addua ta samu kariya daga evils ayes ta haihu lafiya ita da baby ta su samu kariya.
Yana da kyau ya bata amsa da fadan hakan yana juyawa don barin gurin matar tana kokarin ganin ta jawo shi a jiki kamar yadda suke da dan cikin su.
Wanda daga hakan zasu yi amfani da daman wurin samun jawo ra,ayin shi gare shi na addinin su sai dai kuma yaron tauri ne dashi da rashin sabo sam baida yarda da kowa ko sakin jiki wanan halin yana matukar damun su a rai.
Tsoron su shine kada watarana yaja ra,ayin yarsu tace zata juye ta koma tasa a kidar wanda wanan babban kalubali ne gare su don su din suna da wani mataki a cikin church din su na shugabanci.
Haka zai zama abin kunya sosai a wurin su shine dalilin su na kin yin fushi da halayan yaron garesu na rashin yarda da amincewa dasu da baiyi ko wani lokaci.

NIGERIA
Tafiyan ya umar da sati aiyukan yan uwan uwanshi ya fito yana daya daga cikin wanda sukai hanya aka samu aikin don mahaifin su yayi iya kokarin shi a samun aikin abu ya faskara .
Gashi bai son zancen komawan su waje yanzu koshi umar din akwai dalilan da yasa ya barshi ya koma din don ya koma ya karasa.
Habbib yafi kowa korafin wanan tsayar dasu da akayi din wanda ba haka yaso ba yaso ya koma kamar yanda yayan nasu ya koma can.
Kawune ya fadawa sauran mutanen gidan inda suka dinga layi zuwa yin murna wa hjy jummai yar mulkin tana amsawa da kyat don bata so haka ba ita a nata ganin ai sirin su ne hakan ba dole sai kowa yasan da maganan ba a saka masu baki.
Itako abinda bata so ke nan kowa ya kama fada ana nanata magana ta dauki hakan da yawan saka ido ga mutum.
Wata rana kuma sai gashi umar ya bugo waya yana sheda masu haihuwan merry din wace ta haifi diya mace wai har anyi sati uku a lokacin da ya bugo wayan yace ya radawa diya sunan mahaifiyar su Aminatu.
Gida sunyi mamaki kwarai da jin hakan kowa na tofa albarkacin bakin sa ga irin halin umar din wanda shi bai damu ya fadawa yan uwa wani abin shi ba idan ba yaso hakan ba sai dai daga baya suji.
Hjy su tayi fada sosai kan rashin fada mata da baiyi ba da wuri lokacin da aka haihu din yace mama ni dai a nawa bangaren nayi wa yarinya huduba da sauran abin da ya dace ayiwa yaro idan an haife shi.
Amma ta bangaren merry ita har yanzu basuyi nasu bukin sunan ba tukun tace yau ga hauka ?
Kace sati uku da haihuwa zakace basuyi bukin suna ba har yanzu yace eh mama ga nasu al,adan ai yarinya zata iya kaiwa har wajen shekara ba ai bukin suna ba sai idan an shirya akeyi.
Tsuki hjy taja tare da fadin wanan bakin kwashe kwashen naka babawa mukan bai karamu da komai ba sai dadin ta kaici ni a ina na taba jin wanan shirmay haka ?.
Yace haka sukeyi ga al,adan yahudawa da suke koyo yasa na barta da akidar su hakana idan sun tashi sai suyi sai hjy tace sai dai kuyi ku tafi church ke nan har kai ana faman raye raye ko a can ?
Shi

Please Login or Register in order to submit comment