You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

muryan shi daga kofan kitchen din yana fadin watau haka kike zama da yunwa don lalaci ba zaki dafa abinda zakici ba ?
Sallon daddy yace na kawo ki garin mutane na bar mashi ke da yunwa ko ?
Idon daya kashe ni dashi lokacin yasani saurin dukar da kaina kasa har lokacin ban iya koda gaida shi ba.
Ganin banda niyar magana ya juya ya fita na dauka ya tafi ke nan don ni fanin shi bayan mamaki sai tsoran shi ya kamani don ina mamaki yaya yashigo min gida bada masaniyata ba haka ?
Na dora ruwa ina kokarin ciro nodles in bare sai naji shigowan shi gidan again leda ya aje min tare da fadin ki fito ki zuba min nawa don yunwa nake ji kada ki bata min lokaci.
Nazo a hankali na dauki ledan na koma kitchen dashi na bude bread din alkama ne irin wanda ake ci da source a kasan.
Na dan dade tsaye ina kallon bread din don ban taba kokarin cinshi ba asalima nafi bukatan in dafa da kaina inci saboda tsaron addini na kada inzo inci abinda ba halal ba.
Na dauko plate masu kyau na shirya masa nasa na nufo falon dashi yana zaune hankalin shi a sytem din shi kamar wani mayen na,ura.
Naso in share shi in aje kawai in wuce sai dai dana aje na dan tsugunna daga gefe nace ya sannu da zuwa ina kwana.
Da kai kawai ya amsa min da uhumm na juya zan shige inda na fito naji muryan shi yana fadin wani yaro ne kike yawan tsayawa dashi a school din ku wani lokaci ?
Cikin mamaki na dago kai da sauri na dan kalleshi ganin niya tsurawa ido yasa na dukar da kaina da sauri ba tare dana bashi amsa ba.
Ya sake fadin bakiji bane na tambaye ki sai da na tsaya nadan yi dan tunane don ni na manta da zancen yusuf a raina sam.
Ya fadi a tsawace nace wani yaro ne wanan ya zubo min idanu sai kace wani tsohon zaki can dashi.
Nace ni ban san wani wanda nake kulawa ba a school din mu sai dai idan sheri za ai min yace sheri cikin mamaki sheri fa ?
Wa zai maki sheri ni ko wa zai maki sheri zaki fada mi ko sai na bata maki rai a gurin nan ?
Innalillahi nace a fili wallahi yaya ban san wanda kake magana a kanshi ba asalima niko kawa mace banda ita a makarantan balle wani na miji can .
Wa ya baki coffee da kika fito sallah ranan gabana yai mugun faduwa na dago kai da sauri nace yusuf ne .
Dan makarantar mu ne tun a Nigeria shine muka hadu dashi a nan yana daukana tankar kanwar ce a nan ko magana bama yi dashi.
Asalima ranan na samu sun sayane sai gani ya miko min sai nayi shiru yace da yake ke mabukaciyace lalaci ya hanaki ki girka a gida kika fita da yunwa ko ?
Nace a cikin laushin murya idan hakan ya bata ma rai kayi hakkuri ba zan sake ba in sha Allahu.
Kasa magana yayi duk wani fadan daya kulla zai mun sai kuma na bashi tausayi don bai tsamaci karaya haka da sauri a gurina ba a yadda ya sanni fitsarariya.
Bread din da baici ba ke nan ya mike cikin fushi ya bar falon ina jin tayar da motar shi ya bar gidan ban damu ba tunda nasan banyi komai da yake zargina ba akai.
Zama nayi inda ya tashi na fara cin bread da source din daya bari gurin rana banci abinci ba sai ruwa danayi ta sha ranan sai yamma na girka abinci naci.
Tun wanan ranan na gane wanan bread na alkama ban yarda in rabu dashi a gidan dama na gane masuyi din musulmai ne yan pakistan sai na kara mayar da hankali gutin cin sa sosai sai ya kosar dani har yamma.
Ranan na dauka zai dawo sai dai ban sake sa shi a ido ba nima hakan bai damay ni ba ko kadan.
Kwance yake mike saman dogon kujeran dake karamin falon su yana nazarin wasu jirage da suke so gyarawa a kasan Dubai.
Sai dai yanayin kwanciyar nasa yana nuna akwai damuwa sosai a tare dashi ya mika hannu ya dauki wayan shi dake gefe a je ya sake dialing din nomban merry din karo na barkatai ke nan tun dawowan shi london din.
Kamar yadda computer ta saba mai babatu wanan karon ma itace ta soma zancen cikin sanar dashi layin baya shiga.
Karan kararawan shigowa falon kamar ba zai dago kai ya duba ba yadan share don ya dauka cikin yan aikin gidan nasa ne ke masa sallama.
Merry tace ta shigo falon cikin shigar wani dogon riga da cinyan shi yake bude har kasa rigar mai hannu kamar dan shimin mata sai yarta dake dauke hannun mai aikin su ta daukota tana barci.
Dan peck takai mai daga inda yake kwance din hakan yasa shi mikewa zaune tare da rike mata hannun yana fadin yanzu ya gama trying din layinta yana rufe.
Merry bata amsa ba illa amsar yarta datayi a hannun mai aikin tana kokarin kwatar da ita saman kujeran daya tashi akai.
Itama taka zaune tana kokarin cire takalman kafanta masu tsinin gaske kafin ta juyo gurin shi tana sauke ajiyan zuciya.
Mai aikin cikin gidan su ce ta shigo dauke da abinsha tana kokatin ajewa a gaban ta kallon kayan yayi yace Greco na hana a kawo min wanan abin a gidana kin sani.
Yaya akayi ya shigo min gida ya fada tare da hade fuskan shi a lokaci guda yana kalli merry din rai bace kamar bashi bane ya gama fara,a yanzu ba.
Tace commo dear cikin dan marairaice murya tana fadin iam testing let me have some please you know we are in long joining.
Ya kalleta da idanuwan shi da suka kada sukai ja a lokaci guda sun sauya kala ya nunawa Greco hanyar fita da kayan da sauri ta dauke kwalban giyan zuwa waje.
Hakan yasa merry din tashi ta barshi a gurin tana fada a fili ya bita da kallo mai kama da harara kafin ya juyo ya mayar da kallon shi zuwa ga yarsu dake barci hankali kwance.
Wani irin tausayin yarinyar yaji ya darsu mashi a ranshi ya kai zaune a hankali yana dan shafan kan yarinyar tare da runtse idanuwan shi.
Lalai duk abinda babba ya hango yaro baya hango shi don sai yanzu bayan auren su ne yake sanin wasu munanan halaya na merry data boye mai a baya daya dauka ba dabi,un ta bane.
Ta boye mashi wasu abubuwa da dama daga cikin dabiun nata da sai yanzu ne yake gano hakan bayan haihuwan yarsu mm a farko ta fitar fili.
Wani irin ajiyan zuciya ya sauke tsoro da nadama auren merry ya darsu mashi a zuciyar shi.
Tsoron ingancin addinin shi da abinda addini ya shari,anta yana zo mai a rai take tsoron kada Allah ya kamashi da laifin daba nasa ba yazo mai a rai.
Take tunanen yar mutane da ya kawo kasan ya rabota da kowa nata ya darsu a zuciyar shi lokaci guda.
Idan wani abu ya samu yar mutane a inda ya watsar da ita da sunan karatu mai zace ma iyayyen su a gida ya samay ta ko basu tambaya ba ai Allah yana ganin shi.
Shine mafarin zuwa ranan ya dubani dayayi bayan ya saka wanda zai dinga kulla da duk wani movement dina a school din ba tare dana sani ba ya fara zuwa guri shi ya tambaye shi yace mai ina nan lafiya sai dai yana ganin ina yawan tsayawa da wani yaro dan Africa ne shima.
Tun wanan ranan idan ya dauki fushi da merrey yake zuwa nan ya huta ba tare da na sani ba idan ya gama abinda yakeyi ya wuce abinshi tunda dai yasan ina lafiya.
Ranan bayan ya bar gidana ya koma gida ya samu itama bata kwana a gida ba sai yarsu kawai ya samu a wurin Greco tana rainon ta .
Bayan ya gama duba yar ya shige dakin kwanan su a hankali yake bin dakin da kallo ido ya lumshe take mahaifin shi ya fado mai a rai lokaci guda.
A hankali ya kai kwance saman gadon dakin ya rasa abinda ke mai dadi a rayuwan shi wanan wani al,amarine da bai taba zaton zai iya faruwa dashi ba yake cin ranshi.
Duk wani tunane nasa yau ya dunkule a wuri daya yana hango zancen daddy su a lokaci guda tun farkom ganin shi da merry da daddy ke fadin su din basu da tabbas domin munafukai ne.
Bai taba tunane merry zata iya sauyawa daga irin sharudan da suka sakawa junan su tun kafin suyi aure da yake gani a nasa tunanen ta rike don son da take mashi din bayi zaton zata iya karya alkawari ba hakan
Can a cikin barcin gajiyan da yakeyi don idan ya dawo aiki yakan zauna a gida ya sauke gajiyan shi na yan kwanaki kafin a nemay su kuma .
Jin dararakun nasu harda kamar maza a cikin su yasa shi saukowa kasa bai shiya ba a hankali yake takowa daga steps din tsayawa yayi yana kare masu kallo su hudu ne mata uku sai namiji daya dake ta shafan macen guda a falon.
Wani tsawa ya daka masu tun daga saman inda yake tsaye duk suka juyo a firgice suna kallon shi da mamaki.
Ya tako inda suke ba tare da yayi magana ba ya nuna masu hanyar fita daga gidanshi kallon mamaki suke mai har lokacin rai bace yace merry may kike so mayar mun da gidane wai ?
Tace no no bamuyi haka dakai ba dear kada ka fara korar min abokai a gidan nan don ni ban kori naka ko daya ba.
Wani kallo yai mata ya juya ya shiga daki sai gashi ya fito rike da key di motar shi ya wuce su ya bar gidan.
Ina gidan zaune a cikin kadaicin da yanzu ya zama min jiki saye a cikin doguwar rigar kirar Oman baka a jikina naji ana lwankwasa kofa da farko naji tsoron hakan sai daga baya na daure ina tambayan waye ?
Yace ki bude nine gabana ya fadi na bude a hankali naja baya don in bashi hanya.
Ya shigo rike da ledodi da da jakkar laptop din shi a hannu bai tsaya min magana ba ya haye saman benen na bishi da kallo kafin in rufo kofan.
Tun da ya shige dayan dakin ya rufo ban kara jin duriyan shi ba har safe na dauka ko baya gidan ma don har lokacin muna hutu ban fita ko ina.
Har na gaji da kwanci na taso in sama ma cikina abinda zanci a lokacin naji karan budan kofan shi.
Daga kofan kitchen din ya tsaya yana fadin daddy ina kusa da ita yanzun hakan ko a bata ku gaisa ne.
Da sauri na juyo don jin abinda ya fadi ina kallon shi miko min wayan yayi da sauri na karaso inda yake na karbi wayan .
Sai dana share hawayen daya gangaro min a fuska a lokacin na iya cewa naam kawu yace hasbunallahu wani,imal wakeel yata nake ji haka radau a waya ?
Sai da na hade wani abu daya tokaro min zuciya na amsa mai da lafiya lau muke kawu yaya su Amma da mamu da sauran mutanen gida?
Yana tsaye ya tsare ni da ido yana sauraren yadda muke wayan da kawu a lokacin hakan ya hanani yin wani motsi mai karfi.
Bayan min gama gaisawa ya miko min hannu ya karbi wayan shi ya fara tafiya ina jin yana fadin tana karatu sosai daddy.
Lokaci guda hankalina ya tashi a wurin daya barni na rushe da wani itin kuka mai tsuma rai sosai bai kara shigowa gidan ba haka ya barni cikin kewan gida don jin muryan kawu danayi ranan.


Kuyi manaji dashi don Allah da kyat na iya rubuta makushi wallahi ban ma san abinda nake rubutawa ba karshe.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:16 - 🤐🤐🤐: DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAIIII,

A gida Nigeria kawu yana gama waya da dan shi cikin murmushi ya dago kai ya kalli Amma data matsa sai an kiramu anji lafiyan mu.
Za ace yara tun tafiyan su ba,a kirasu anji lafiyan su ba ai hakan bai dace ba.
Itama Amman murmushi ta sauke cikin jin dadi da kwanciyan hankali tana sauke ajiyan zuciya don ko ba komau yanzu hankalin su zai kara kwantawa tunda sun tabbatar da muna lafiya.
Karewama gashi ana tambayana ya mika min waya mu gaisa lalai hakan ya nina muna zaune lafiya ke nan.
Nan Amma ta shiga bada labari ga duk wanda yazo ta bangaren ta tana fadin ita kan wanan hadin yayi mata dadi sosai umar ya rike amana yar marainiyar Allah da aka dora mai a kai.

Sai dai ni a nawa ban garen ranan ban yi barcin kirki ba ina tuno mutanen gida da kewan su a rains harma da wa yanda ban shiri dasu ranan naji kewan su sosai a raina.
Ance inda kake nan aka sanka gani a garin mutane ba fada ba girma da arziki da kowa a garin ba zancen wance na sona wance bata sona duka dai gashi na rasa hakan yanzu a tare dani.
Na juya ina mamakin irin karyan da yaya umar yayi a gabana kan wai muna tare ko wani lokaci su barima ya bani waya mu gaisa ai.
Tabe baki nayi na sake juyawa tunanen mamu da hjy jummai na fara ina anyana ko wani hali suke ciki bayan mu barsu a can ?
Ko yanzu hjy su yaya umar ta saduda tabar zancen raba auren da tace muddin tana raye sai taga bayan wanan bakin auren namu.
Da za acema zataci nasaran rabawan a yanzu da sai nafi kowa farin cikin hakan matsala ta daya shine karatuna da zai iya samun cikas.
Wani shawara ne yazo min in jure in kara hakkuri akan wanda nake na zaman kadaici ni kadai a katon gidan nan har lokacin da burina dana iyayyena zai cika gareni na kammala karatuna.
Don yanzu komai ina fahinta ga kayan koyan komai a wadace banda matsala ta ko ina indai kan karatuna ne.
Tausayin mahaifiya ta dana baro a cikin wani hali duk da bata nunawa tana kokarin boyewa nasan wanan abin ba karamin taba mata rayuwa yayi ba.
Don na fahinci mamu na tausaya min tana matukan son ganin rayuwana ya inganta a duniyan nan.

Ban san yadda akayi ba ana saura sati mu koma karatun mu ne ranan ya shigo gidan kamar an jefo shi ina zaune ina kallon wani shiri na musulunci a tv mai suna women in hijjab.
Kafana suna mike saman dan center table ina tauna dan porncorn din daya zama min dabi,an ci koda yaushe.
Ganin shigowan shi yasa na dan rude na mike tsaye ina mashi sannu da zuwa ya amsa min kamar dai kullun ya nufi hanyar sama har ya fara hawa ya juyo yana fadin ki shirya nan da minti talatin kafin in fito.
Haka kawai ya fadi yasa kai ya haye saman abinshi binshi nayi da kallo ina tnane wani irin shiri yake magana ke nan ?
Hakana na mike na shiga daki sai kuma na rasa wani irin shiri zanyi a dakin lokacin ba wasu kaya sai dogayen riguna dole daya na zaba har kasa wani mai adon ja da bakin jan maron colour da adon baki gaban rigan gyalen da zai shiga da kayan na yafa na rufe daga kaina zuwa wuya duk da haka ina jin kaina kamar a tsirara ne duk da rigan ya rufe min ko ina.
Wai baki gama shitin bane ya fada a dan hasale da sauri na dauko dan jakkana na fito daga daki ina fadin na gama.
Kallona yayi daga samana har kasa ya kawar da kai ga kallona tare da fara tafiys na biyo bayan shi daga can cikin motan yace wa zai kulle maki gidan ?
Jikina na rawa na koma na dauko key inda nake ajewa nazo na kulle gidan na nufo wurin motan don tsoron shi da nake ji na takure a wuri daya zan shiga bayan motan.
Wani harara da tsawa yai min sai ganina nayi a gaban motan zaune ya bar gidan sosai yake gudu da motan .
Ni dai ban san inda muka nufa ba don ba garin na sani ba kaina a duke don nagaji da kalle kallen abin mamaki a idona ga tafiyan mai nisa sosai da alama.
Don tun da rana har wani lokaci muka isa gurin
Jin hayaniyan mutane yasani dago kai a hankali wani signboard na gani anyi rubutu manya a cikin style welcome to CUMBRIA PICNICK LAKE WINDERMERRE, , , ,
Bayan motar ya bude ya miko min wani bakin coat na mata kallon rigan nayi yace ki saka in ba haka ba sanyi ya illanta ki a nan.
Da sauri na karba na saka sai ga rigan yazo min har iya gwiwa na sai dogon rigan dake jikina ya koma kamar buje .
Waya yayi banji may akace ba naji yace muje don Allah bin bayan shi nayi ina fadin mutum haka komai a hasale yakeyin shi ?
Zaune suke duk da duhun dake gurin sun saka wuta a tsakiya wasu na kwallo wasuna shaye shaye wasu a kwance .
Hi Omar we are here muryan merry naji sun sauka a kunnuwa na lokaci guda da sauri na dan kalli wurin na karasa ta hanyan bin bayan shi zuwa inda suke zaune a cikin yashin teko da wasu mutanen da kusan rabin jikin su duk tsirara ne.
Unbelieveble wa nake gani nan kamar fatema ta fada tana kokarin tasowa daga inda take zaune din .
Haka yasa wa yanda suke tare a zaune suka juyo suna kallon mu tasowa tayi sukai dan wani musayan gaisuwa na gefen mumuke.
Nidai ina tsaye ina kallon ikon Allah ta barshi zuwa wurina taimin irin wanan gaisuwa hannunta yana rike a cikin nawa take tambayana yaya karatu ?
Nace da ita Alhamdullahi dan bubuga min baya tayi tare da jan hannu na zuwa wurin mutanen da ke zaune tare da ita tana fadin.
Meet Omar sister Fatema tana karatu ne a nan kasa tazo daga nigeria ne itama suka kara kallona suna fadin she is so beutiful.
Tare da tambayan merry din yaushe nazo basu sani ba tana fada masune hankalina yaje gurin yaya umar dake rungumay da yarshi zaune a cikin kasa suna hira cikin kwantar da murya yana rungumar yarinyar .
Cewan da merry tayi ga abokanta mu gaisa ya dawo da hankalina inda suke hannu suke kokarin miko min nayi saurin masu jam,i ga baki daya na gaida su.
Don nasan ko mazan zasuyi kokarin miko min hannunnsu hakan gareni wanda nasan sai dai in ba merry din kunya don bazan karba masu ba.
Merry tayi saurin cewa halan ba al,adan mu bane mun rike addinin mu sama ga komai don haka mijin ta yake shima.
Sai suka sa dariya a tare lokaci guda kamar yasan may sukeyi yace kezo nan zakace badani yake magana ba.
Ganin ni kadai ke jin hausa a gurin nasan dani yake magana na juya a hankali zuwa inda suke dashi da yar shi din ya rungumay ta wanan karon.
Ki zauna yace dani da yana nuna min wurin zama da hannun shi haka yasa da sauri nayi abinda yace din .
Na kai zaune saman yashin a kusa dasu na zauna tare da dan takurewa a guri daya.
Fuskokin mu yana facing din ruwan sake iska keta kadawa a lokacin mutane wuri ba adadi kowa da abinda yakeyi a furin ba wanda ya damu da wani.
Ina can ina kalle kalle naji muryan shi yana fadin ke yar nan nake son ki rike min kada ki bari tana bin wa yancan ya nuna su ba tare daya daga hannu ko kai ba.
Da dan mamaki na dan kalle shi yace eh nasan yarinyar tana da sabo zata saba dake idan kin nuna mata kulawa daya dace.
Yana fadin hakan ya mike ya barmu da yarinyar zaune tare dan hannu na mika mata sai ko tazo gurina yayin da hankalina yake gare shi ina kallon inda zai tafi.
Muryan yar yarinyar ya dawo da hankalina gare ta kallonta nayi naga ta bata rai tana fadin i want to sleep now.
Yanayin maganan ta ya ban sha,awa ganin tayi karanta sosai da zuwa irin gurararen nan haka.
Fuskana take kallo take maganan na dan sakar mata murmushi kadan ce tazo ta kwanta a jikina bata ki ba sai ta matsa inda nake zaune.
Zaune muke kafafuwan mu a cikin ruwan lake din na rugumay ta sai lokaxin tunanen kanne na yadda nakeyi dasu a hankali nakai hannuna saman kanta dake da kitso hudu na kalaba yaji dauri da ribon masu kyau.
Ina dan bin zanen kitson da hannuna naji yadda take sauke ajiyan zuciya a hankali alama barci na zuwa mata a lokacin.
Tace my mum sing for me idan ina jin barci duk dare na dan kalle ta ikin kamilaliyan fuska nace ban iya irin wankan da maman ki ke yi ba ni ai.
Tace kiyi ko wani iri kika iya na dan yi tunane kadan sai na fara karanto mata fatiha har zuwa karshen shi.
Nakai aya nayi shiru don na dauka tayi barci saboda yadda ta lafe a jikin nawa lokacin sai kawai naga ta dago kai ta kalle ni tana fadin may yasa na bari kuma taji dadin wankan sosai ci gaba nayi da maimaita mata karatun ina dan taba mata kai a hankali.
Yanayin da nake ciki yasa na zarce da karatuna a cikin zazzakan murya ba tare da nasan ina daga murya sosai ba a lokacin.
Sannu a hankali suke taruwa suna kallon yadda nake karatun su basu raina abin kallo a wurin su hakan ya jawo hankalin su merry gare mu ta tako har zuwa inda muke zaune din .
Hannu ta mika tana fadin tana baki wahala ko fatema a daidai lokacin da take mika hannu don daukan yarinyar a jikina tana fadin ina Dad din ta ne ya barki da ita haka ?
Abin mamaki ga yarunyar da tayi nisa a barci sama jikina uwar na tabata da niyar ta dauke ta saman jikina di don ta fahinci abinda nake karantawa yarinyar nata a lokacin.
Uwar na daga yarinyar

Please Login or Register in order to submit comment