You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

falon ba na shiga kitchen din na samu ya rage min karfin gas din.
Sauri nayi na kammala na gyara gurin don kada ya dawo ya riskeni ciki ranan a dakina naci abinci nayi sallah ina gamawa hutu muke na danyi karatu na shiga nayi wanka don akidanane yin hakan ban iya kwanciya banyi wanka ba tun a gida na saba da wanan wankan daren.
Na fito har lokacin jikina bai sake ba a gidan tunda nasan yana gidan lokacin don ba inda zai tafi din yanayin sanyin da kasan ke ciki mutane in ha dole ba basu faye zirga zirga zuwa ko ina ba.
Bayan na kammala shirina na kwanta har barci ya fara zo min sai lokacin na tuna da ban rufe kofa ba don gujewa yaya ranan don a da haka nake barin kofan koda baya gidan ma.
Tashi nayi na fara tunanen ina key din kofan ya shiga duk iya neman da nayi mai ban iya ganin sa ba a dakin.
Haka na koma na kwanta jiki a sabule naja bargo na rufe jikina dashi har kai sannu a hankali barci ya fara daukata.
Banji shigowan shi dakin ba don barci ya fara daukana a lokacin ya shigo dakin ya tsaya yana kallon yanayin dana kwanta din a tsorace nake da alama.
Fitalan dakin ya kunna haske ya gauraye dakin ga baki daya zubur na bude idona daga barcin daya fara fisgata na bude idona na sauke a kanshi.
Yana tsaye ya harde hannayen shi ya zubamin idanu akaina ba wasa ko wani sayina fuskan shi yace ki tashi kiyi alwala sallah zamuyi.
Banga fuskan yin musu ba a lokacin na tashi kamar yadda ya umurceni ina tafiya kamar zan fadi don tsoro a lokacin.
Sai dana dan bata lokaci zuciyana cike da tsoron abinda zai faru a kaina wanda ban sani ban taba zaton haka zaizo min ba.
Har na fito na samay shi a tsaye a tsakar dakin nawa ya kurawa wuri daya ido kamar mai tunanen wani abu a ranshi jin karan budan kofana bai tsaya ba naga ya nufi saman sallayata.
Jiki ba kwari na fara neman abin sallahna na saka lokacin naji ya tayar da sallah ko.
Raka biyu mukayi saidai don dogon surar da yaja muna a lokacin yasa muka dan dauki lokaci muna sallah.
Mun idar ya tsaya addua a baiyyane godiya ga Allah da neman zaman lafiya da zuri, a masu albarka ya shafa nima na shafa.
Naji ya ambaci sunana a hankali haka yasa na dago kaina na dan kalleshi kafin yace zarah ki kwantar da hankalin ki ba ha,intarki zanyi ko wani abu ba idan nayi hakan na zalunci kaina na zalunceki riban mai zan samu a yin hakan.
Ki tashi mu kwanta ba komai zan maki ba kwanciya kawai nake son muyi tare har zuwa ranan da zaki bukaci ban hakkina da kanki.
Kuka na soma yi sosai a lokacin ya dago tare da dafa min kafadana ya kara matsowa gaf dani har ina juyo numfashin shi a lokacin.
Kidimaiwa nayi lokaci guda don gaba daya ya juye min daga yaya ya koma min wani abin tsoro yanzu s rayuwana.
Ban san lokacin dana kai kaina a kadan shiba ina kuka ya dade zaune yana sauraren kukan nawa bai hanani ba.
Harsai da yaji na sau#uta kukan ya mike ya dauke ni sai saman gado tare da kashe fitilan dakin yana sauke numfshi a hankali.


ZAINAB IDRIS MAKAWA

NOVEL DIN KUDINE DON ALLAH KI KIYAYI SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA
16/11/2021, 23:24 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM IYYAKA NA ABBUDDU WA IYYAKA NAS,TA,IN, , , ,


Tun lokacin daya fahinci barci ya dauki ni yayi ajiyan zuciya tare da kallon yadda nake sauke numfashina a wahalce har lokacin a tsorace nake da abinda ya faru tsakani dashi din a wanan daren.
Jin ajiyan zuciyana a cikin barci yasa ya dan rungumay ni zuwa jikinshi yana sauke ajiyan zuciya a hankali tare da fadi a cikin ranshi.
Zarah kin shayar dani mamaki a rayuwata dama hausawa sunce samun abin kwarai wahala gare shi.
Wahalan da yasha da zuciyar shi da tashin hankalin mutane da dama daga ahalin shi ma duk akan cikan wanan burine na mahaufin shi.
Lalai hausawa sunce abinda babba ya hango yaro yaro ko yahau tsauni ba zai taba hango shi ba tabbas daddy yayi gaskiya wurin dawo da rayuwan shi ta asali.
Tabbas ance kowa yabar gida gida ta barshi duk daba wai ya taba wani abin asha ba a rayuwan shi saita hanyar sunna.
Zai iya cewa matan hausawa daban suke ashe ko ta jinsin su yau sai yake ganin kamar farkon shiga jikin wata mace ya fara a rayuwan shi don irin ganima da ni,ima da natsuwan daya diba a jikin yarinyar daya raina da farko.
A fili ya furta Allah ka yafe min daddy na tuba nayi kuskure ka yafe min daddy naso in yaudari kaina in yaudare ka.
Ashe ba zabin banza kai muna ba daddy ka fimu sanin abinda bamu sani ba a rayuwan mu yau da nabi ra,ayin mama na bijirewa daddy da na yaudari kaina ashe.
Da kyat ya samu ya dan runtsa idon shi barci ya dan daukeshi kadan da asuba alarm din wayan shi ya tayar dashi don sallah.
Firgigi ya falka yana kallona har lokacin barci nake ina sauke ajiyan zuciya saboda kukan dana sha.
Ya mike yana tunane a ranshi kodai zalaman shi yasa yajinwa yar mutane ciwo bai sani ba in ma zalaman ne yasan yayi mata haka kanta daren jiya zai iya cewa matsuwan shice ta ja mai yin hakan don a matse yake a yan watannin nan yana bukace da bukatan shi.
Har yakai bandakin ya shiga don yin wanka yaga wurin a tsabtace kamar inda ba,a amfani dashi ko yaushe komai na gidan yana nan tsab dashi don tsabta zarah badai tsabta ba .
Duk tsaba da kulawan shi saida ya yabawa tsabta irin na zarah a rayuwan shi yarinyace zarah karama amma tarbiya data samu a gida yasa ya fara kwadaituwa da halaiyan ta.
Don irin yadda ta iya boye sirin su tsawon shekara biyu da rabi ba wanda yasan alakan auratayan dake tsakanin don dokan daya saka mata kawai.
Tasan idan yana gidanta ta ciyar dashi yadda ya kamata sai dan gyaran da yai mata kadan wanan kuma yasan karancin shekarunta ne ya hana ta gane hakan.
Har ya fito daga wankan bayan ya hada ruwa masu zafi a ciki har lokacin ina kwance ina batcin wahala.
Sallah ya tayar a kada ya makara yana idarwa ya nufo gadon ya ya dan kira sunana a hankali haka yasa na dan motsa ganin da yayi ban da niyar tashi yasa shi sukutana a cikin barcin na danyi kara ina fadin a wahalce don Allah yaya kayi hakkuri na dauka wani abin zai kara yi min kuma.
Saida ya tabbatar da na zaunu da kyau a cikin ruwan dumin ya bar ban dakin zuciyar shi cike da tausayina a lokacin don kawai baida zabi ne har hakan ya faru tsakanin mu.
Don saboda da shakuwan da mukayi a dan zaman tare sai yake jina wani bangare na zuciyar shi yanzu.
Sauka yayi zuwa kitchen ya hada min tea mai zafi da kauri tare da dauko magani a dakin shi ya nufo dakina har lokacin ina zaune na kasa anyanawa kaina komai a bandakin sai kukan da nake wanda ba sauti ciki.
Muryan shi naji yana fadin ba zaki fito hakana ba lokacin sallah yana shigewa ko sai nazo nayi maki da kaina.
Jin hakan nasan yanzu ba karamin aiki bane gare shi don zai iya yin hakan tunda ya furta hakan a fili.
Da sauri na dan cudanya jikina yadda addini ya koyar damuyi ji nayi ba zan iya kara sanya zanin dana kwanta dashi ba na dan leko kai daga ban dakin sai na ganshi a tsaye ya ban baya kafita in dauki zanina don Allah na iya fadi a lokacin.
Da sauri ya juyo don jin abindana fada yana fadin a ina zanin yake in miko maki nidai ka fita don Allah in dauka da kaina nace cikin dan muryan da bai fita.
Baiyi magana ba sai naji ya juya ya fita da sauri na fito na dauki zani na daura na saka hijjab din sallahta na tayar ina idar a lokacin kuma abinda ya faru tsakanin mu ya dawo min a raina tiryan tiryan wasu hawayene suka ziyarci idanuna bal,bal,bal lokaci guda.
Kuka sosai na zauna nayi ni kadai a dakin mai faruwa ya riga daya faru a daren jiyan saura in tsura ido inga sakamakon da zai biyo bayan abinda ya faru din tsakanina da yaya yanzu.
Tun da har mahaifiyata ta kasa ban zabin kaina na matakin dana dauka da nake ganin zai fitar damu daga manufan su maganan ta kullun nakira ko takira shine inbi umurnin mijina in mashi biyyaya ma,ana dai in mika kaina a gareshi a fakaice .
Nasan yanzu sunana karamar bazawace a gurin shi kai ba wurin shi bama a gutin kowa dana sani don ba yadda za ayi indai ba hjyn su ce ta janye maganan ta akan mu ba ya zauna dani har madi.
Tau yau dai na mika saura mamu da kawu dasu amma su saurari hukuncin abinda zai biyo bayan umurnin su yanzu gareni.
Haka na zauna ban iya tashi a gurin ba balle duk motsi sai na runtse idanuna don ciwo da nake ji a karkashina har a cikin raina nake jin shi lokacin.
Ina zaune ina ta sake sake a raina in kulla wanan in warware ni kadai a dakin na kudundune kaina da gwiwa na.
Muryan shi danaji yasani razana da sauri na dago kaina fuska shabe shabe da hawaye ido ya kurawa yanayina ido a hankali ya kai tdugunne a idana nake zaune.
Dan rungumoni zuwa jikin shi yana fadin oh sorry zarah don't cry again don wanan abin ya faru tsakanin mu kike zubar da hawaye haka ?
Makin ki godewa Allah da ya tsareki ya baki ikon sadaukawa dan uwan ki da wanan abin mafi daraja ga mace.
Don't cry again kukan nan naki yana taba min zuciya matuka ba sai kinyi kuka zan gane abinda nai maki bada sin ranki ba and kuma wanan kukan yana nuna min irin kiyayyan da kike mun a filine zarah.
Ban iya magana ba ban kuma dago kai na kalleshi ba jin nayi shiru ba amsa ya mike tsaye a hankali ya dagoni daga inda nake zaune a takure.
Bakin gadona ya kaini ya zaunar dani a hankali ya mika hannu ya dauko flask din shayin daya hado min ina kallo ya tsiyaya a cup ya miko mi yana fadin karbi kisha sai kisha magani don jikin ya rage maki tsami.
Da kyat na iya bude baki nace dashi na koshi cikin muryan kuka kin koshi damay yaci yana kallona .
Maza karbi nan ki shanye in baki magani ko kuma ranki yanzu ya baci a dakin nan jin yadda yake magana fuska a daure yasa na mika hannu da sauri na karbi kofin shayin na fara kurba kadan kadan saboda banjin dadin shi ko kadan a bakina.
Yana tsaye ya dora hannayen shi saman kunkurun shi ya rike da hannu biyu haka yasa corth din jikin shi fara dan dagawa daga baya ta yadda zaki iya hango zanzaron shi da farar rigar shi ta ciki.
May zakiyi yace yana kallo na fuska na yamutse nace nakoshi yace kina wasa da nine zarah ki shaye nace sai ki sha magani fuskan shi a daure.
Don dole na mayar da cup din a bakina ina kurban shayin a hankali yana tsaye ya kura mi idanu kadan na rage cikin cup din na aje saida ya kalla yace wanan fa na maiye kika rage.
Da kyat na iya budan baki nace mai wanda zan sha maganin dashine sai naga ya juya zuwa inda ya dauko flask din magani ya dauko yana barewa kwara uku buyu iri daya guda daya kalan shi daban ya miko min na amsa ina juya kafin in watsa baki ina bata fuska don dole na hade da kyat.
Ko ke fa yarinya da raki haka don't be lazy don mijin ki jarumi ne shi don haka ban son mata ragguwa daga dan tabaki kike wanan rakin haka.
Aini ba yar iska bace nace a hankali yace niko dan iskane amma fa da matana don haka saiki shirya koyon iskanci daga yau.
Zaki iya kwanta ki huta zan dan fita in samo muna abinda za a ci anjima yace ba tare da ya tsaya jin mai zance ba ya fice daga dakin.
Nabi bayan shi da kallo ina maida kaina ga filon dana jawo a kusa dani don ban son yin dogon motsi a lokaci.

Bayan ya fitane ya duba motar shi idan tana fita ganin kankaran ma kara rufe motar yayi lokacin yasa ya hakkuri ya tare taxi zuwa inda ya nufa.
Barci nayi sosai daga kwanciya na don haka bansan lokacin daya dauka bai gidan ba sai wajajen la,asar ya dawo har lokacin ina barci.
Tayar dani yayi inyi sallah lokaci ya kure ban koyi azahar ba haka na daure na tashi na shiga bandaki ruwa masu zafi kwarai na hada na kara shiga sai naji dadin jikin nawa a lokacin na dan dade zaune a ciki kafin in fita in daura alwala na fito naji dadin jikin nawa ba laifi don ya rage min yadda nake jin shi da farko.
Yana fita falo ya koma yaci abinci sai kuma ya zauna waya da wata kawar merry data kirashi tana tambayan dalilin daukewa merry da yarta kafa da yayi ?
Don merry taki kiranshi don tasan shi da kansa zai nemai ta idan yana da bukatanta duk zai kare fushin shine su dawo daidai don bai iya broke da ita.
Bai fada mata komai saicewa da yayi is a family issue don haka ba maganan su bane.
Yana gamawa ya aje wayan yana juyawa sai wayan ya dauki wani kiran kuma ya dauka itace sai ya dauko da zuman cewa ta barshi kada ta kara kiran layin shi.
Saidai baikai ga hade fushin shi ba mamaki ya kamashi ganin sunan mai kiran shi a fili ya furta mama ya dauki wayan.
Gaisawa sukayi a mutumce da farko kafin dan shiru ya biyo baya sai can hjyn ta kawar da shirun ta hanyar tambayan shi yaya iyali ya amsa da suna lafiya mama tace kadai ki kawo min takwarana har wanan lokacin in gane ta.
Yace zamu zo mama in Allah ya yarda har lokacin yana mamakin kiran mahaifiyar tasu a yau.
Baza kuzo ba don kada na tursasa ma ka saki wanan yar banzan yarinyar daka lakawa kanka na fadama ba zan hada zuria da wanan iri tsiya ba a jinina .
Haba mama kiyi hakkuri ki bar wanan maganan haka ki barwa Allah dalilin shi nayin haka a kan mu.
Rufa min baki mara kunyar banza duk bare baren da kakeyi na na sani bawai ban sani bane don magana bai biyuwa a gidan nan.
Uwarta ta mayar dakai saniyar tatsa yanzu sun samu wurin ci tunda na ubanku ya kare yanzu shi yasa tun farko naki wanan abin don nasan idan sun samu namiji ya zama bawan su.
Mama akan mai zanyi wani bare bare matar nan fa yarta na a hannuna akwai nauyi a tsakanin mu yanzu fiye da da can baya tunda ina auren yarta.
Yarta na gidana zaman matana ace kuma ko gausuwa ba zamuyi ba da ita ai abinda nauyi mama danne hakkin yayi yawa mama.
Babawo kasan mai wanan furcin nake yake sakani yanzu a gaba har zaka iya kiran wanan yar da wai matar ka ?
Da kasan yadda naji a yanzu da wanan kalamin naka haka da baka furta min ba har yaushe ta zama matar taka kuma ?
Ina kace min ba a gari daya kuke da ita ba ba ruwanka da ita rufa ido kawai kake ma mahaifin ku kadai sanyata karatune kawai.
Mama amma ai na baro gida da itane da sunan aure ko in banda ke ai ba wanda na fadawa gaskiyar zancen.
At list ko bata karu dani da komai ta karu dani da karatun da takeyi don fushin daddy ya rage a kaina sai ya dauka laifinsu ne.
Kai babawo kana jina ka turo masu yarsu gida nake bukata yadda suke bakanta min rai a nan da uwarta da duk wani dangin Alh suma suji a jikin su.
Yace mama ai saura dan lokaci kadan ta karasa karatun ta gaba daya kinga sai na tarkatota in turo ta gida zuwa lokacin.
Amma yanzu tunda bata kare karatun ta ba ai kinga dawo min da ita za ayi nan kuma zaune bai kare muna ba ke nan kuma.
Babawo bakan yadda na tsani wanan yar ba a rayuwata naki jinin wa yan nan mutane wallahi balle har in hada iri dasu kai ni wanan matar takama tafi soyo min a rai bisa ga yarinyar nan Fatima.
Mama na gane mai kike nufi ai ki dan ban lokaci kadan ya rage komai yazo daidai ai naji tace cikin isa tare da fasin matsiyata ai ko banza saida suka karu damu da wanan karatun daka sakata yi.
Ba komai mama kiyi hakkuri komai zaizo daidai a daidai lokacin ya dago kai mukai arba duk da fitowana ke nan daga dakin bai hana in fahunci da mahaifiyar shi suke magana ba lokacin don jin karashen maganan su.
Ya samu ya lalabata ta yadda ba zan iya fahintar komai ba lokacin sai bayan ya kashe waya ya dago yana fadin ki sauko mana kinja kin tsaya kuma nan.
Kamar in juya in koma saidai da ya riga da ya ganni a lokacin don haka banda zabi na tako a hankali ina saukowa daga saman benen.
Nazo na samu wuri na zauna dan nesa kadan dashi zuciya ta sai fadi nake shike nan ta faru ta kare dama hjyan su ce ta matsa ya lalatani ya sako ni ashe ?
Ya jikin naki maganar shi yasani dagowa firgigit daga tunanen da nakeyi a lokacin nace a hankali da sauki .
Zaki iya tashi ki zuba abinci ko na zubo maki zan iya nace mai ina kokarin tashi ina cije baki ya bini da kallo kafin yace ko mu tafi asibiti ne a dubaki ?
Naji sauki na bashi amsa ba tare da na juyo na kalleshi ba na nufi kitchen din kai tsaye.
Abincine lafiyayu masu tsada da bazasu lalace ba kwalaye da yawa kala kala ya sayo ya aje a kitchen din ma,ana zan kwana biyu ban girka muna abunci bake nan.
Dan tsankwaro abincin nayi na fito ban nufi dining inda na tashi na zauna ina cakulan abincin a hankali.
Ya sake dago kai ya kalleni yana fadin wanan abincine ko shirmay wanan din zai kosar dake ?
Kinsan yanzu abincun da zai gina maki jiki mai kyau ya kamata kitche shiyasa naje halal store na sayo maki wa yan nan din don sune daidai kici kwana biyu don ki helling.
Ban dai dago kai na kalleshi ba ko in tanka mai naci gaba da cakulan abincin ina kaiwa baki a hankali.
Wayana ya dauki ruri na dan kalla ga mamakina mamuce ta kirani naso share wayan sai naga ya dago ya kalleni yana fadi bakiji bane wai ?
Wayan na kalla ina ya mutse fuska na dauka tare da sallama ciki ciki babu sauti ina fadin mamu ina wuni yayi saurin dago kai ya kalleni.
Sai kuma ya dukar da kai yaci gaba da zanen shi a board ya maigidan naki sayadi ta tambaya nace lafiya.
Bata saurareni ba tana fadin yanzun muke kallo aka nuna yadda kankara ke ta,adi a garin ku shine nace bari kiraku inji idan da sauki wurin ku ?
Nace ai kuwa kawai da ganin yadda ya dago kamar baiji dadin yadda nake amsawa din ba sai ta tambayeni waiko lafiya kike sayadi ?
Lafiya,lau na karasa da kuka da sauri ya dago kai yana fadin mainene haka a hankali ta yadda ba zata jiyoshi ba.
Mamu a cikin fada take fadin ki godema Allah, Allah baki miji salihi sayadi don da wanine wanan iya shegen da kikeyi na shagwaba da bai daukan maki shi ba wallahi.
Nasan Umar sosai nasan halinsa sayadi Umar mutum ne mai hakkuri da sanin ya kamata mutanen da basu sanshi bane suke ganin shi shu,umi.
Kawun ki yasan da hakan kullun yana godiya ga Allah kasancewarki matar umar kibi mijin ki sauda kafa sosai zaki ji dadin shi sayadi.
Banda shakkan komai akan auren ki don zuciyata ta yarda da wanda kike aure sayadi don haka ban yafe daki sabawa mijin ki ba ta hanyar aurataiya kinji na fada maki.
Sunkuyar da kaina nayi kasa lokacin sai hawayeb dake min ambaliya har yana diga daga cikin idona lokacin don haka ki natsu kiyi biyayyan aure don shi kikaje yi ba wai ki raja,a akan karatu ba kawai.
Nasan yaya na jin mu don shirun da falin yayi lokacin koda baiji duka ba yana jin wani abinda take fadi ta kare da fadin ni zan kashe ki gaida mijin naki idan ya shigo ubangiji ya kara albarka kice ina masa godiya don Allah.
Kamar in ce tamai mamu saidai babu halin yin hakan a lokacin tayi sallama ta kashe wayan har lokacin hawaye bai daina fito min a idanuna ba don takaici da dacin da nake ji na kowa har mamun dake yabon sa yana ji.
Saidai ban san hakan karin daraja uwata bane a idon shi don dana dan dago na saci kallon shi yana zaune ya bar abinda yake idanuwan shi a lumshe da gani yana cikin yanayin tunane mai zurfi a lokacin.
A raina nace ji munafuki kamar gaske kai namiji dai muna fukine ashe da gaske yanzu fa na gama jin sunayi dani da mahaifiyar shi.
Niko ga nawa uwar tana yabon shi kamar ya biya mata makka shidai yaya tunane zancen su da mahaifiyar shi yake ta yaya mama ke son in wullakanta masu ya ta gama zagin su uwarta kuma ta kira tana yabona da sa yarta ga hanyan daidai.
Sam ba zai iyaba yanzu ma ya fara zama da yarinyar nan idan mama bata sani ba yanzu ya fara sanin wacece zarah a shirye yake da ya saudakar da duk wani fitina da zai biyo baya idan an koma gida shi yasan irin shawaran daya yake a zuciyar shi ya kuma barwa

Please Login or Register in order to submit comment