You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yana fadin wanan ai cin zalin ne maimakon abi yarinya da lalama sai kuma ki hada mata da duka haka.
Ko kene da girman naki za ai maki haka ai ba zaki ji dadi ba lokaci daya wanan wani irin haline haka maimuna ?
Mamu tace yaya don may yarinyar nan zata daga muna hankali haka tazo ta saka gwaggo a gaba tana fadin wai mahaifin ta ya dawo ya dauketa hannun makiyanta.
Kawu yaja tsuki yana fadin banji dadin haka ba wallahi ba abakin yara yan uwanta ya kamata yarinyar na taji magana nan ba taji kuma sai a hanata shiga wani hali.
Zaki samu yarinya da duka kamar jaka dawani kike son taji dukan ko wanan magana kawu yayi fada sosai kafin ja hannu zuwa wurin kujera ya zaunar dani a kusa dashi yana kiran sunana da Fatima.
Share hawayen ki kinji ki saurare ni mu nan da kike gani kaf ba makiyan ki bane mu illar masayon ki kina ganin ni zan cuce ki ko mahaifiyar ki koko hajiya zata hada baki damu ta cuce ki na girgiza kaina alaman a, a gare shi.
Fatima kin taba ganin inda uba yaki yarsa yayi abinda zai halakata ko baki dauke ni mahaifi bane a gare ki cikin kuka nace kawu na dauka Amma don Allah kada ka hadani aure da mijin arniyar nan koma waye ka bani ba wanan da bai sallah ba yana auren kafira.
Kawu yadan runtse ido yace naji to ki kwantar da hankalin ki yanzu zamu san abunyi amma fa sai kin kwantar da hankalin ki haka zai faru ko kina son gani bacin raina ne dana mahaifiyar ki.
Na girgiza mai kai ya kama min magana a cikin nasiha da lalashi har ya samu na rage kukan da nakeyi din sai kuma ya lura da rawan darin dana soma a lokaci guda haka yasa yakai hannu shi a goshina yaji jikina ya gashe gaba daya.
Da sauri ya mike yana fadin ina zuwa ya fita daga dakin sai can gashi ya dawo da goran ruwa da serchers din panadol a hannun shi ya bare ya bani biyu yace in sha.
Nasha yace in samu wuri in kwanta na mike ya tambaya ina zani nace part din mu yace dawo ki zauna nan guri hajiya ban yarda ki koma wurinta tunda bata san ta rarashe ki ba.
Ban zauna ba nace a wahalce sallah zanyi ya gyada min kai na shige dakin Amma na barsu a falon suna ma mamu fada a kaina.
Na dade a ban dakin ina kuka kafin mama hadiye ta kwala min kira na fitoda kumburarun idanuna ina neman hijab.
Aisha mama ta kwalawa kira tazo tace kawo ma Fatima hijab ta saka sallah zatayi ta koma da sauri ta shigo dakin Amma ta kawo min .
Rana dai a dakin Amma na kwana har dare barci yaki zuwa min sai tunanen banza nake barkatai a raina ina jin Amma ta tashi zata je alwala tana magana ita kadai.
Wanan rayuwan damay yai kama ace ta ko ina babu dadi duk jummai ta rikita min rayuwan gida wanda ma bakayi zaton zai iya abu ba halinta ya koya mashi.
Mata kamar ibilishiya kun hana min farin ciki a rayuwana dana iyalina baki daya wanan yaron dake kokarin ganin ya gyara tarbiyan gidan shine kuma yazamo makiyin su a yanzu.
Taja wani uba tsuki ta dan dade a ban dakin koda ta fito ta samay ni a zaune bakin gado ta kalleni tana fadin tashi kikayi nace banyi barci ba dama Amma.
Ido ta zaro waje tana kallona yar nan ai gara ki ba kanki lafiya ki runtsa shima wanda ake rikicin kanshi nacen bai san abinda akeyi ba yanzu.
Wuce ta nayi ba tare danayi magana ba na shige ban dakin nima alwala na dora na fito na tayar da sallah koda na sallamay na dade a gurin zaune na hade kaina da gwiwana ina hawaye.
Ban san lokacin da kukan nawa ya tsananta ba har ya fito fili daga inda Amma take tace Allah buwayi gagara musali yar nan har yanzu kukan nan bai kare ba.
Ina kunyi magana da kawun ki yace zai duba a kai kodai makiyin ki za a daura maki ai kyaba kanki hakkuri ko ?
Nace cikin kuka Amma ki taimakeni ki ceci rayuwa ta kada ki bari a aurani ga wanan mutumin don Allah wallahi Amma tsoron sa na nake ji wallahi.
Ki kwantar da hankalin ki yar nan ai tunda na fahinci bakya so ba maiyi maki dole idan kuma sun matsa sai anyi ni da kaina zan warware auren idan naga yana maki ba daidai ba.
Nace Amma baki faga iskancin da sukeyi da matar sa ba ko a gaban kowa ne baida kunyar rungumar ta Amma haka Allah yace ayi don Allah?
Tace ina fa yar nan nima yanzu ai na gano ki sosai ba so hadin nake son ayi ba amma fa kinga sai idan kin kwatar da hankalin ki.
Don kada su dauka kece baki da tarbiya tunda shi namiji yayi shiru ke mace mai zai hana kema kiyi kamar yadda yayi .
Kin san mutane a ruwa sai a dauka baki da kunya da har kika tsaya kina fito na fito da iyayyen ki a kan auren ki gashi kinji har kawun ki ya fara fadin ko baki daukeshi a matsayin mahaifi ba.
Wanda hakan nasan ranshi ya baci sosai ne ga irin abinda yaga kina nunawa akan dan cikin sa kamar kin nuna shi bai haifiki ba ke nan tunda shi yayi biyayya ga mahaifin shi bai musa masa ba tunda ya tunkare shi da zancen.
Jin haka da sauri nace Amma nima in sha Allahu zan dauki shawaran naki kamar yadda kikace.
Tace to kiyi shiru duk abinda sukace kice masu to kamar yadda suke so kinji ko nace to Amma na gode.
Tace nasan manufar mahaifin ku kan wanan hadin shine yaga rayuwan ki dama ya inganta ne kamar yadda yake tausayin ki ke kadaice gun mahaifin ki kuma gashi ba wani mai karfi a gidan ku .
Haka yasa yai wanan hikimar ki samu suma yan uwanki su samu ta karkashin ki suci arzikin da Allah yai maki.
Shiru nayi ina sauraron ta tace ai da farko itama uwar taki tayi wanan haukan sai dana zauna muka fahintar da ita manufan yin hakan ta kafin ta sauko ta yarda da auren .
Don ba wanda ya zaci haka daga gurin ki tunda ai kina da ilimin ki yanzu kin san abinda ya dace mai kyau da marakyau ashe abin ba haka yake ba ke a gurin ki.
Jikina ya fara sanyi don tulamin kasan da Amma keyi don dai kawai taga hankalina ya kwanta a lokacin.
Na nisa kafin ince Amma nifa duk wanda kawu zai ban ya bani amma dai ba wanan dan hjy ba tunda ta nuna bata so na shima nasan ba zaisoni ba Amma.
Tace kwantar dai da hankalin ki yanzu abinda nake so dake shine ki samu iyayyen ki da safe ki basu hakkuri akan abunda kikai masu su yafe maki.
Sanan da kike fadan wau ba zai soki ba ai halin su ba daya ba da mahaifiyar sa kuma ke mace ce A ruwa zaki iya jan hankalin duk wani da namiji komai shekarun shi ko mukamin sa balle umar da yake mai saukin kai wani lokaci.
A hannun mu fa yake har yanzu ko da kike wanan maganan da uwarsa zata iya raba sa da abinda yake so da nine mutum na farko da jummai zata rabashi dani a duniya.
Sai dai ba yadda zatayi jinina ne shi din ko taki ko taso dole ne diyan ta su bini don nice dai kakar tasu balle ke da zaki zama matar shi nan gaba tasan lokacin da zaki kama abinki ga hannu ne.
Kai na dago na kalli Amma don jin furicin ta na karshe a gare ni sai dai ban iya furta komai ba don yadda nake jin bakina yayi nauyi ga magana yanzu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:07 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAMANIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAIJIN KAI, , , , ,

Saida akai sallah mun dade zaune kafin nakai kwace a gurin in faras barci barci mai nauyi ya dan dauke ni har Amma ta fita daga uwar dakin nata zuwa office din ta inda a nan zata wuni har dare watau falon ta.
Bai fi minti talatin ba na tashi zubur ina dube dube a dakin sai kuma na mike na nufo falo inda na samu Amma ita kadai tana dube dube cikin kayan ta tana ganina tace da sauri badai har kin falka ba yar nan nace Amma zanje wurin mamu ne.
Tace ki bari gari ya iddasa wayewa mana na dan tsaya kamar mai tunane nace Amma barin je kawai na nufi part din mamu din yayin da Amma ta bini da kallon tausayi tana gyada kai kawai.
Na samu part din a rufe haka yasa saida na tsaya na kwankwasa kafin ta bude tare da tambayan waye ?
Da muryana da bai fita nace sayadice ta bude tare da jayewa hanya na kutsa kai ciki ina shiga falon naja na tsaya guri daya yayin da ta mayar da kofan falon ta rufe kamar yadda na samay shi.
Ta tako a hankali zata shige dakinta nayi saurin kaiwa kasa cikin sheshekan kuka ina fadin mamu ki yafe min don Allah sai kuma kuka yaci karfina a lokacin.
Kamar zata wuce sai kuma taja ta tsaya guri daya ba tare da tayi magana ba ita kuma bata wuce ba.
Samun wuri naga tayi ta kai zaune kafin ta fara magana sayadi kiyi hakkuri da hukuncin da yaya ya yake akanki dani dake duk a karkashin ikon sa muke.
Haka Allah ya kaddara a kanmu sayadi kin san idan ta nawa ce bazan taba yarda da wanan auren ba don kamar yadda hjyn umar bata son auren nan kusan nina fita rashin son shi a raina sai dai ba yadda zanyi ne tunda ina karkashi ikon iyayyena da mijina.
Don haka kamar yadda nayi iyawa yina wurin ganin na hana yiyuwan wanan aure bai samu hannuwa ba na barwa Allah zabin sa haka kema nake son kiyi hakkuri kada ki yarda ki rsgin kunyan da za a tsane ki gidan nan har ai Allah waddai da halin ki.
Addua bai bar komai ga dan adam adduan mumumini bai taba faduwa kasa banza kin sani don haka don Allah sayadi ina rokon ki Allah kiyiwa Allah ki sakawa zuciyar ki salama kamar yadda na sakawa nawa na barwa Allah alamarin shi.
Ki koma ga Allah kamar yadda muka saba mika alamari a gare shi idan babu alheri cikin auren nan ubangiji ya wargaza shi tun kan a yishi.
Ki nunawa mara kunya cewa ke din diyace mai tarbiya da biyayya ga iyayyen ki kamar yadda shima yake kokarin nuna biiyayya gun mahaifin shi din.
Kema ina son ki taushi zuciyar ki duk abinda zakiji ko ki gani sayadi ki toshe kunnuwan ki da idanun ki a gidan nan.
Sai yanzu na fara gane manufan yaya akan wanan hadin da yayi wanan bin kuma bake kadai yaiwa shi ba dake da Aisha ce da Rukaiyyan gida yaya balarabe.
Babu wanda ya nuna tshin hankali daga bangaren su don haka sayadi mu may zaisa mu kasa hakkurin haka mu nunawa mutum mai adalci da mutunci a gare mu gazawan mu a cikin jinin shi.
Kukana ne ya yawaita alokacin ta yadda ba zan iya tsayar da shiba itama mamun kukanne ya kwace mata lokaci guda sai da mukayi mai isar mu ba mai ba wani hakkuri a cikin mu.
Itace ta fara tashi tabar falon na dade a wurin bata fito ba sai can gata tafito ta shiga kitchen bata wani jima a ciki ba tafito dauke da cup cike da tea a cikin sa yana tururi ta miko min tare da fadin ki karba ki sha.
Nasan rabon ki da abinci tun jiya da rana kafin kuje islamiya ko na dago kaina da idanuwana da suka kadai sukai jajir kamar gauta don kukan dana kwana inayi har fuskana ya dan kunbura.
Zama tayi gefena bayan na karba tana fadi a cikin wani murya mai nuna rauni a zuciyar tace sayadi ba zaki daina kukan nan haka ba.
Sayadi ya kike son in yi nima fa al,amarin nan yafi karfin tunanena yanzu sai naga kamar dama haka Allah ya tsara abinsa a kanki.
Don dolene ni kaina nabi umarnin iyayyena don su manyane sun fimu hagen nesa nasan idan da babu alheri gwaggo ba zata taba yarda da wanan hadin ba sam.
Sayadi kiyi hakkuri badon bana son ki bane kikaga na kyale a, a sai don ban san abinda Allah ya shiryawa al,amarin ba .
Ba don wanan tunanen danayi a raina ba wallahi yadda kika nuna din nan baki so zan iya tsayin daka inga cewa an fasa wanan auren sai dai duk abinda zai faru ya faru.
To amma idan nayi hakan kamar nayiwa Allah shishigine ga al,amarin shi yanzu idan nace zan hana.
Sayadi baki san halin da nake ciki ba a yanzu don a halin nan badon nakai zuciyata nisa ba ko auren nan zan iya kashewa na huta idan hakan zai maki dadi a rayuwan ki.
Da sauri na dago kai ina kallon ta don mamakin furcin ta nace a razane mamu kada ki kashe auren ki sabodani kodon su fauziya mamu kina gidan nan ma yaya yaran nan suke fama a gidan nan.
Mamu ta daga kai ta kalleni naga idanuwanta sun canza alaman itama tasha kuka a daren jiyan sosai ke nan yanzu kuma ga furcin da tayi min koda nake yarinya ba zanso ace auren uwana ya mutu a sanadin aurena ba .
Haka yasa naji wani tausayin uwata ya kamani na karfafa hakuri da juriya akan komai gamay da auren nan har in ya tabbata a zuciyana.
Tea data miko min na fara kurba a hankali don hankalinta ya kwanta dani sai naji ta sauke wani irin ajiyan zuciya mai karfi tana mikewa ta shige daki.
Haka na daure nayi ta kurba tea din a hankali har ya saura kadan na mike nakai cup din kitchen ban fito ba don ganin yanayin kitchen din danayi alaman tun jiya rabon shi da samun gyara haka na daure na wanke kayan ciki na sharo na goge ko ina.
Falo na dawo na gyara na kakkabe kujerun na fara moping sai ga ta tafito don jin motsina da takeyi tace aiki kuma kika kama yi nace a kunyace eh mamu.
Na gama na shiga nayi wanka tun wurin shafa mai naji wani irin zazzabi mai karfi ya rufe ni a dadafe na karasa na zura digon riga kawai a jikina na haye gado na kwanta ranan dai a takaice ban shiga school ba.
Ban dade da kwantawa ba zazzabi mai karfi ya kara rufeni ni kadai a daki ina makyartan sanyi jikina ya gashe sosai saboda zafin jiki.
Shirun da mamu taji ta dauka ina part din Amma ne sai ta shiga kitchen ta dora girki har lokacin zuciyar ta ba dadi gareta.
Kayan yara da suka cire ta shiga daukowa sai hangoni tayi saman gado dunkule a cikin bargo ina kaduwa.
Mamaki ya cikata ta nufo inda nake tana yaye bargon irin yanayin da nake ciki ne ya bata tsoro da sauri takai hannunta saman jikina tana tabawa hakan ya sani bude iddanuwa na ina kallon ta cikin wahala.
Sai kuma na lumshe idon ina hawaye tare da kokarin fadin mamu banda lafiya ne a kidimay take fadin may ke damun ki ne sayadi nace nima ban sani ba.
Innalillahi tace tana kokarin fita daga dakin namu jima kadan sai ga su tare da Amma sun shigo Amma na fadin.
Dama abinda nakewa gudun ya faru ke nan, amma yan banzan yaran nan masu gadon uwarsu suka fadawa yarinyar nan maganan nan yanzu.
Takai hannun ta saman jikina da sauri tacire hannun tana fadin wanan sai asibiti kiramun sani yanzun nan akai yarinyar nan asibiti.
Ta juya gare ni tana fadin sannu uwata sannu kinji da jiki yaran nan basu kyauta muna ba gaskiya har uwar su naso koda zakiji zancen nan sai nan gaba.
Waya mamu ta dauko tana kiran layin kawu kira biyu ya daga kiran yana fadin maimuna yaya akayi tace yaya barka da kasuwa dama jikin yarinyar nan ne yayi zafi gwaggo tace a kiraka a sheda maka.
Yace subbahanallahi ga Ahmed nan zan turo ya kaita asibiti yanzun nan ni ina nan nazo unguwa ne daga haka ya kashe wayan.
An dan jima sai ga Ahmed ya iso gidan kofan mamu yaje yana sallama aka amsa mashi kamar kullun daga kofa ya tsaya suna gaisawa sai ga Amma ta fito daga dakin tana fadin ka iso ba dan albarka.
Fito muna da ita mu tafi takecewa mamu tana fada tare da Amma muka tafi asibitin Ahmed tun fitowana yake faman yi min sannu yadda nake tafiya ban ganin wuri yaji kamar ya kamani a cikin ransa sai dai ba halin yin hakan gare shi.
Privet Asibitin da suke zuwa gidan mukaje inda ya fara shiga ya samu hanyar ganin likita da sauri ya dawo ya taimakawa Amma ta kamani zuwa ciki.
Likita ya dubani yace zai ban gado in dan kwata tare da allurai a gani zuwa yamma yadda jikin zai sauka min.
A take Ahmed ya sawo maganin dayace basu dashi a lokacin sauran treatment za a saka a bill din Alh.
Bayan ya dawo ne Amma ta gaida shi da kokari ta fara korafin fadin ban taba ganin yan banza yara irin yaran nan ba ace kada wanda ya fadawa yarinyar nan zancen auren nan a yanzu amma don bakin tsegumi irin nasu sai da suka fada taji.
Da sauri Ahmed yace zancen wani aure tana gyara zama take fadin auren ta da yaron nan umar mana sanin bai fada ma bane.
Ai hadin gida yake son yi da yaran wurin su uku yabawa yaranan dasuka dawo da wasu dabi,un kasan turawa sai yanzu yake fadin har sauran ya bada su a tare rana daya zai wanke su duka.
Da Amma ta daga kai taga yanayin da Ahmed ke ciki a lokacin da bata karasa zancen ta ba gaba daya hankalin shi ya tashi da jin wanan zancen da tsohuwar ke rabtaba mashi.
Taja tsuki tana fadin ko ma ina umarun yake yanzu yasan halin da yarinyar nan take ciki oho ta dago kai tana kallon Ahmed din da bai san inda yake ba lokacin.
Ina kake ne tace tambayan ka nake layin wayan umaru idan kana dashi mu kira in sheda mai halin da ake ciki.
Ahmed da gaba daya hankali shi bai tare dashi yaji maganan ta kamar daga sama ta sake maimaita abinda tace din .
Ya sauke ajiyan zuciya yake fadin banda layin kowa a cikin su hajiya daga haka ya fara kokarin ficewa dakin zuciyar shi cukushe da bakin ciki yana fadin .
Shike nan nauyin bakina ya jamin hasaran abindana dade ina mararin sa a raina yanzu shike nan yarinyar nan ta subuce min ke nan mafalkina a kanta ba zai zamo gaskiya ba.
Wuri motar shi ya nufa ya shiga yai mata key ba tare da sanin ina ya dosa ba a lokacin hankalin shi gaba daya ya tashi da zancen tsohuwar da yasan bata karya.
Innalillahi ya ambata yana shafo kanshi tare da fadi a fili shike na an min sakiyar daba ruwa fatima ta subbace mani kenan .
Ashe yarinyar nan ba rabona bace sai kuma yace kai yana bugun sitiyarin motar da hannun shi mema ya hana in fito tun wuri in nuna ra,ayina gurin Alh nasa dana fadi da baiyi wanan shawaran ba gidan shi ya yanke shawaran zuwa a karshe.
Gaba daya lokaci guda ya fita hayacin sa ga zufa na karyo mai duk ilahirin jiki shi zama yayi a falon shi yana nanata innalillahi a fili kafin yaji dan natsuwa nazo mai a hankali.
Daga haka yakai kwance ya dafe kanshi dake sarawa da hannu shi daya yana sauke numfashi a hankali har barcin natsuwa yazo mai bai sani ba.
Mamu da taji shiru bamu dawo ba kuma ba wanda ya kirata tasan halin da ake ciki ta daga waya ta kira maigidan su hankali tashe tana tambayan shi halin da muke ciki.
Yace suna tare da Ahmed na shigo gona in zagaya ni tare da malam mudi amma barin kirasu inji halin da ake ciki.
Kiran Ahmed yai tayi wayan na rigin ba a dauka ba sai hankalin Alh ya kara tashi asibitin ya nufa daga gona shida malam mudi.
Yazo ya samu ina barci ga Amma a zaune ko abin sallah da abinci ba a kawo mata ba da mamaki yake tambayan Amma yaya akai haka inashi Ahmed din Amma tace tun dazun ya fita ina magana dashi naga ya juya ya fita daga dakin.
Kawu yace to lafiya don na kirasa wayan na shiga bai dauka ba ya sake gwada layin sa har ya katse ba a daga ba.
Yace to yaya haka don dai Ahmed bai taba yi min haka ba gaskiya gida ya nufa sai gasu sun dawo tare da mamu da mama hadiye.
Tare da abinci da duk wani abinda za a bukata a zaman asibiti har lokacin hankalin kawu bai kwanta ba na rashin daukan wayan Ahmed din.
Shiko Ahmed da kyat ya tashi yai sallah daga gurin da yake ya jawo wayan shi ganin misscalled ratata a wayan yayi saurin dubawa Alh ne da wasu yaran shagon su ke kiran shi kamar hadin baki sai ga Alh ya sake jefo mai kira da sauri ya daga yana sallama da kyat Alh yace lafiya kake kuwa Ahmed waya nata ringin baka daga ba haka kana ina ne yanzu.
Ahmed yace Alh banjin dadin jikinane ina gidana kwance da sauri Alh yace subbahanallahi gida kana may dabaka zo asibiti ba ?
Yace ciwon ba sosai bane Alh nasha magani ai na kwata ne yasa banga kiranka ba.
Allah ya sauwaka indai ciwon ya matsa ma kayi maza ka kawo kanka asibiti kaji ko yace naji Alh ya kashe wayan .
Su mamu dake jin yana subbahanallahi suke tambaya yace wai ashe baida lafiya ne yasa bai daga wayan ba.
Amma tace ikon Allah lafiya fa ya kawo mu asibitin nan ya danyi zirga zairga ya shigo har ina fada mai abinda ya jawowa yarnan ciwon ta nace dashi ya kira min layi umar din tun lokacin ashe baida lafiya shima dan mutum ba a bakin komai yake ba wallahi.
Ai ikon Allah

Please Login or Register in order to submit comment