You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nuna min ya juya da sauri ya bar asibitin saida na tsaya yin shawara kafin in tura kofan da sallama na shiga.
Idona akan manjo wace ke kwance kamar gawa sai na,urorin dake zagaye da ita a ko ina bata san wanda ke akanta ba a lokacin.
Dea sauri na karasa wurin gadon ban farga da wace ke sallah ba a dakin lokacin sai muryan Addah na naji tana fadin wacece wanan ?
Na juyo da sauri zuwa gareta na fada jikin ta sai kuka mai karfi ya zo min da sauri mamu data kagu ta sallamay sallah ta sallama.
Tace ke ke waya kawo ki nan may kika zo nema ko kinzo ki tayar mata da hankali ne kuma ?
Maza ki fice daga dakin nan tun ban saba maki rai ba yanzun nan maza ki fice ki bamu wuri tace a cikin wata murya mai karfi ba shiri na bar dakin dafe da bakina daya cika da sautin kuka.
Sai bayan na fita Addah ke fafin maimuna may yasa kika koreta haba dai kin san fa irin kaunar dake tsakanin su da babba.
Yanzu da kika koreta ina zata tafi mamu tace damay tazo dama ta nan ban san wanda ya kawo min ita nan ba wallahi shegen naci ne da ita.
Ina fitowa a tsorace hankalina tashe ban san inda zan dosa ba a lokacin na dade tsaye bakin get din ina sake sake a raina kafin in yanke shawaran bin kafa in koma inda na fito.
Do zan iya gane hanya don yanzu na dan san garin sai dai akwai tazara da gidan kadan da asibitin.
Ga garin sai walkiya ake alamun hadari zai taso a garin banyi nisa da tafiya ba aka fara iska a hankali na kara sauri don kada ruwa ya fado.
Tafiya nake don da kyat nake ganin gabana don iskan dake mayar dani baya duk kura ya cika min ido sai dai hakan bai hanani rike wayan mamu a hannu na ba gam.
Tasowan hadarin yasa abin hawa suka rage gudu a titin sai jefi jefi suke gilmawa .
Haka nake dan hadawa da gudu don in isa gida da wuri ina cikin tafiya mai kama da sarsarfa har ban san na hau titi ba a lokacin.
Karan taka burki danaji da karfi gaf dani yasa na rufe idanuna sai na jini a kasa tim na cikin motar ya leko daga tagan motar daidai lokacin da nake kokarin tashi tsaye yace ke wata irun mahaukaciya ce kamar dabba baki kallon hanya zaki wani hayewa mutane tsakiyan titi kamar na gidan ku.
Muryan yayi min kama da na yan gidan mu ina dan dangesawa na mike don jayewa a saman hanyan.
Ya sake fadin kauce dan Allah kina bata min lokaci har ruwa ya sauko ko na latse ki a wurin in take banza ke har da watan azumin kike fita yawon banza ki ?
Da sauri na matsa daga wurin da sauri ina kaucewa saman titi ina kallo ya ja motar shi ya barni a gurin sai lokacin naji kafana yayi min tsami na fara tunane naji ciwo a kafan.
Sai kuma na fara tunanen waye a cikin su da sauri na tuna shine habbib a cikin su nace lalai wanan yakai mara imani da rashin tausayi .
Ka buge ni kuma bai tsaya bani hakkuri ba ya hauni da fada da zagi lalai ba karya yaran hjy jummai basu da imani a zukatan su ko kadan.
Nasan duk ya gane ni amma ya nuna kamar bai san daga inda na fito ba har yake zargina da yawon banza haka dan iska kaci arzikin manjo yau don ba fada ne a gabana ba yanzu lafiyan kakata na damu dashi yanzu.
Da tunane kala kala har na karaso gida lokacin an fara dan ruwa da karfi ina zuwa na tura get naji a rufe na shiga duka.
Abin mamaki mamu na gani a tsaye ta kauce a hanya na shiga ba tare da tai min magana ba har muka shiga part din mu ina dan dangyasawa.
Mamu bata nuna min tausayawa ba ga abinda ya samay ni sai dai ko ba a fada na hango damuwa a fuskanta karara.
Ruwan sama mai karfi akayi ranan tun shigewa na daki nake jin dan zazzabi na son kamani ajikina wasa wasa kafin asuba sai ya rufe ni lif.
Gani ban fito ba yasa mamu duba dakina a cikin fada sai ta ganni dunkule a cikin bargo tundaga kaina har kafa.
Abinda yasa ta karaso inda nake ke nan tana fadin ai kinga na wanda baijin maganan iyayyen shi yanzu hankalin ki ya kwanta kin gano ma idon ki tashin hankali.
Dama kwancin kike son yi ke ma saj kije asibitin ku kwanta da kakar taki tunda haka yafi maki yarinya bajin magana .
Ta fita daga dakin can abin da da mahaifi sai gata ta dawo dauke da cup da magani a hannun ta tace oya tashi ki sha magani mara jin magana.
Banda wani katabus a jikina kamar ma na zautu a ranan komai sai ido nake bi dashi kawai ban iya yin maganan komai da kowa.
Ina kubawa naji tea ne mai zafi ashe na dan hade maganin ina miko mata kofin tace cikin tsawa kurbe shi maza ki shanye.
Haka na daure na sha fiye da rabi nayi kokarin aje kofi zan sauko daga kan gado tace ina zaki kuma nace zan shiga ban daki ne mamu.
Ta kauce tana bina da kallo sai lokacin ta kula ban tafiya daidai tace da sauri ke may ya samu kafan ki kuma ?
Nace mota ta buge ni a hanya ta tsura min ido kamar mai nazari kafin tace kin tabbatar nace wallahi mamu ina tafiya ban san na hau titi ba ashe mota na tafe ban sani ba.
Tace a ina ta buge ki na dan daga rigan dake jikina ina nuna mata wurin abinka ga farar mace wurin yayi wani irin ja da sauri mamu tace amma yar nan kikaki fadan wanan rauni irin haka ?
Nan dai na barta a tsaye na ja kafana a hankali zuwa bayin da kyat na iya dukawa da kafan na gabatar da uzurina lokacin.
Har na fito na samu mamu a dakin sai na nufi hanyar falo tace ina kuma zaki nace ruwa zan sha mamu.
Dawo ki zauna in dauko maki tana fadin haka ta juya ta fita sai gata da goran ruwa mai dan sanyi kadan ta miko min na karba ba kurba kadan na mika mata ta fita.
Sai gata ta dawo da man tiger tace in bude wurin ta shafa min tana tsaye na koma na kwanta ta sake fita.
Ban falkaba sai takwasa ranan na iya mikewa zuwa sallah fada ma Amma abinda ya faru dani mamu tayi sai gata ta shigo gaida ni tana ta faman tsinewa wanda ya kade ni da mota.
Nan dai na daure cikin karfin hali nace mamu dan gidan nan ne fa ya kadeni da mota kuma ya zageni da yar iska mahaukaciya wai na fito yawon banza.
Nan ta saka salati tana fadin yaran nan ko suna da imani wani irin bakin ciki suke son sauke muna a gidan nan ne wai.
Dama wanda yabar akidar shi ba wani imani ne da shiba ance yaren ka addinin ka kowa yabar gida gada ta barshi babu alherin da yarab nan suka koyo ga wanan tafiyan nasu sai bakin ciki da takaici idan kwai ya tashi fashewa a gidan nan tsiyan abin ba kan uwarsu zai tsaya kadai ba bakin cikin har mu zai shafa duka.
Mamu bata gane may Amma ke nufi da zancen ta ba sai tace ai basu dawo da wani matsala ba sai dai daukan kai da rashin ganin darajan mutane.
Uhhummm kawai Amma tace tare da fadin Allah dai ya kyauta yar nan ta juyo gareni tana fadin wanne daga cikin su yai maki wanan karen aikin haka ?
Gwago da ki barsu ai itama bata jin magana saj da na cewa yarinyar nan kada ta fita ban san yadda akayi yarinyar nan tasan vurin nan ba don bakin bin kwakwafin ta na tsiya ai sune maganin ta.
Amma gwago don Allah a bar zancen sai gaba idan sun kara don irin kawaicin da dan uwansu yayi muna kan kakarta kinga ina ganin har yanzu mahaifiyar tasu bata da wanan labarin.
Amma tace toh shike nan daba don haka ba wallahi da yau mai shi ya jini a gidan nan wanan an kashe ta yaso yin don haushin ta da suke ji.
Ta dade tana fada a kaina har zuwa lokacin da suka fita daga part din lokacin zazzabin ya kara taso min na kwata barci mm ai nauyi a dunkule.
Ban garen Umar yana jiran yaji kiran mahaifin su kan maganan su da Amma kamar yadda yai tsammani kira daga gare su tun bayan maganan su da Amma.
Sai dai har gashi ana ta faman shirin sallah har lokacin baiji wani abu ya taso akan zancen ba ko canjin fuska a gurin iyayyen shi.
Sai Amma din daya rasa gane ma inda ta dosa tun ranan da sukai maganan ta canza mashi kwata kwata bata bashi fuska yanzu ko kadan.
Yanzu ma yana son zuwa ya gaida ita sai dai yanayi daure fuskan da take mashine baya so ko kadan haka dai zai daure yaje su gaisa din.
Don Amma din wani babban makami ne a gare shi nan gaba a abubuwan dake shirin tasowa tsakanin shi da iyayyen shi nan gaba.
Da sallama a bakin shi ya shigo falon tana zaune tayi tagumi ta zuba ma wuri daya ido jin sallaman shi yasa ta dago tana kallon shi.
A sanyaye ta amsa mai sallaman ya shigo yana fadin dazun zan shigo naga ficewan ki nan sai na fasa shigowan .
Tace cikin dan bata rai wallahi naje duba wanan yar ne kuma yace wata ya ke kullu sai kin tafi duban ta ne kuna shagabata tana kara narkewa.
Kai ma ba haka nai maka duk cikin jikokina kaf ku fi tsaya min a rai ku biyun ban don naku yafi zuwa daya da nawa ko yanzun ma wani mara imani ya kade da mota a cikin gidan nan jiya da dare.
Amma mota fa kika ce tace zan ma wasa ne kafa yana nan ya hau sosai kuma uwarta da kawaici ta hana a fadawa mahaifin ku don gudun fita da halarcin da kai masu.
Amma Amma wanan aiba abin kyalewa bane don ba karamin magana bane idan tsotsayi ya kaishi ga kashe ta fa ?
Ganan min hanya kadai dan nan nima abinda na hango ke nan zan bincika in san ko waye don gaba tace shine daidai don bai kamata a kyale zancen ba don wani dalili can rayuwa ne fa .
Can dan shiru ya biyu baya saj Amma take fadin dama ina neman ka akan zancen kayan nan gasu aje har yau baka ce komai ba kuma har gobe jajibur.
Kaya Amma ya kallo ta yana tambaya yana rike da haban shi da hannu daya yayin da kafan shi daya ke tankwafe saman kujeran da yake zaune a kai.
Tace kayan da kasa aka shigo dasu nan mana tayi mai bayani yadda zai gane may take nufi da maganan ta.
Yace kai Amma suna aje ashe naki tsaraban ke nan ai da zaki rabawa mutane su dan jikan ki ya dawo kibawa yan uwa gaba daya mama ma na bata na bangare su ai ita da yan uwanta.
Kai dan nan Allah yayi maka albarka ai ban san manufarka ba ke nan ya mike yana fadin zai fita nan Amma ta shiga kasafa kayan ita da mama hadiye mukan yan gaban goshi ne na samu tsaraba masu yawa sosai wanan lokacin don ammace mai rabon.
Wanan labarin yaje kunnen hjy jummai ta kulu da danta sosai sai dai saukin abin akwai da shakku da shayi tsakanin ta da dan don shi kaifi daya ne idan ya furta abu.
Tayi ta dakon shigowan shi bai shigo ba sai kuma ga su Aliyu sun shigo lokacin shan ruwa suna fushi yayi masu fada kan buge ni da mota da habbib ya tashi yi.
Suna shigowa uwar ta tare su tana fadin yaya na ganku haka Aliyu yana zama yace dan matsala suka samu da big bros a waje.
A gigice take fadin matsala kuma akan may kuka samu matsala kai da dan uwanka har haka sai Aliyu ne dai ke iya bata amsa da fadin.
Don kawai ya buge wanan yarinyar shine yake masa fada akan ya kula kin san hahbib shine yaso taso mashi ya dakatar dashi a cikin fada.
Kallon habbib tayi ranta na mata kuna tace wace yar ka tashi duka yace ba duka fa ba da mota ya kade ta lokacin da iskan nan ya taso jiya.
Habbib yace wallahi mama abinda bros keyi wani lokaci haka ya tursasa ni akan sai nayiwa wata tsohuwa can da Amma tayi magana aiki ashe kakan shegiyar yatinyar nan ne ma wa kuke kiranta yar agolan gidan nan taku.
Dam dam zuciyar hjy jummai ya harba take ranta ya fara baci idon ta ya rufe ta mike tsaye ta fara fada.
Lalai munafincin gidan nan yakai dama nasan yaron nan ba a banza aka barshi ba har abin yakai a hada min diyana fada a gidan nan.
Aliyu yace bafa fada sukayi ba mama ki kwantar da hankalin ki don Allah shi bros din ne yayi ma habbib fada a kan ya daina kada tsautsayi da kadara yasa ya kashe ta kinga ko gaskiya ne ai ya fada mai.
Suna tare uwaf amma ina tayi gaba ta fara da wurin mu na samu na dan tashi ina buda baki don mamu saboda ciwo na yau sau daya ta leka asibiti wurin manjo.
Daga sama mukaji sababin ta tana fada da tonon asiri kala kala wanda hakan ne ya jawo hhankalin sauran mutanen gidan suka fara fitowa daga part din su don gane ma idon su abinda ke faruwa dasu.
Alh sani shima ya fito hankali tashe yana tambayan mai ya faru a hasale ta juya inda yake tana fadin munafuncin gidan ga mana.
Diyana basu taba fada a tsakanin su ba sai a kan wanan bakar annoban yarinyar A ruwa ta kai muna ko ina a cikin gidan nan saboda samun wuri.
A ruwa fatima ke nan kike nufi munafuncin may akai maki keda diyan naki ?
Hjy jummai tace a munafunci mana tunda har aka iya boyen min abinda aka tursasa shi yayi wa dan uwanshi abinda rashin bai so ba.
Ke nifa ban fahince ki ba ki fito fili kiyi magana kin tsaya muna kwana kwana.
Sai ta boye zancen kade ni da mota ta fito da zancan asibitin kawai muryan Aliyu ne da tun dazu ne ya shigo ya tsaya yana sauraren ba tare da sunsan yana nan ba.
Yace mama yanzu fadan da nayi mai kan ya kula da kada tsautsayi ya gitta ya kashe ta iyakan fadan da nayj mai ke nan .
Mahaifin su yace wai shin wa aka kade Amma dake fitowa tace A ruwa ya kade ta fito asibiti duba kakarra jiya da dare.
Ranan sun ji nacin ran mahaifin su ya nuna ma uwar har diyan bacin ranshi akan abinda suke nuna min gidan yace shi amana ya dauko ni yana riko ba agola ba kamar yadda suke fadi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:52 - 🤐🤐🤐: BISSIMILLAHI RAHAMAIN RAHIM , ALHAMDULLILAHI RABBIL ALLAMIN, , , ,

Ranan haka mukai buda baki babu dadi a gidan kawuna mijin uwata wanda hjy jummai fadan ta duk akan taimakon da danta yayiwa kakanane take fadan.
Rayuka sun baci a ranan don kowa yana wurin har mamu ta kasa hakkuri take fadin ban taba zaton don Umar ya taimake ni a gidan zai zama laifi ba don ko yaya dai su din diyan dan uwana ne ko ba aure a tsakanin mu.
Tace alfaharin ki ke nan dake da ma su zuga ki to ban haifarwa duniya da ba idan kina so ki jira naki su aimaka maki daidai lokacin Umar ya juya yabar gurin don zai iya cewa bai taba zaton haka daga mahaifiyar su ba.
Ganin ya fita suma sauran suka juya suka nufi hanyar fita waje suna mai mara mai baya sai dai kafin su fito ya riga da ya shiga mota yabar unguwan gaba daya.
Zuciyar shi cike da kunan rai ga halin da mahaifiyar tasu ta nuna a gaban su ranan ya fahinci wani abu sosai a zama gidan da take yawan korafi akai.
Tsaye sukayi cirko cirko a kofan gidan mai karatu abinda kika sani ne a wanan zamanin mai hali koda shine karami shike juya kowa.
Balle shi da yake babban su a gidan kuma suna sane da abinda iyayyensu ba su sani ba a gamay dashi jiran dan wani lokaci yake kafin ya baiyana kanshi gare su.
Har goman dare bai shigo gidan ba wanda hakan mahaifiyar tashi bata ji dadin yin hakan ba don tasan a ranan ran kowa a bace yake a gidan.
Sai dai bata damu ba abinda ya damayta shine rashin walwalan diyan nata da tagani a tare dasu gaba dayan su sun kasa sake jiki har lokacin da suka dawo gidan.
Shiko yana barin gida wani katafaren hotel yaje ya kama a nan ya kwana tare da kashe wayoyin shi.
Haka yasa uwar ta kara shiga damuwa don kashe wayoyin da yayi a lokacin dan haka tun da safe ta samu mijin su da zancen .
Nan kuma sabon rikici ya kara barkewa a tsakanin su tun sunayi a daki har abin ya kaisu ga zancen ta bar mashi gida hakan ya jawo hankalin kowa a gidan.
Haka akayi jajibirin ranan rayuka a bace a gun kowa babba da yaro don hajiya ta hanawa mutane zaman lafiya dadin takaicin ts shine rabon tsaraban da Amma tayi na danta .
Halin da ake ciki bai hana tayi fadan haka ba sai da maigidan yace duk ta kara tankawa ranan sai ya sake ta ganin da gaske yake yi yasa ta ja bakinta tayi shiru akan maganan.
Ita ko Amma kamar da gaiya dan duk wa yanda batai tsamani ba sai da Amma ta tsakura mata tsaraban ana sa albarka sai bugo waya mutand keyi suna godiya gurin hjy jummai din.

Nikan ina fama da kafana daya hanani shakat a rayuwana don ko wajen ban iya lekawa ba tun dawowana dana shige sai dai ina samun kyakyawan kulawa don Alh yasa an duba min kafan an ban magani.
Sai na ke samun sauki sosai ga kafan washe garin sallah haka na tashi sumul kafan ya huce sai dai alaman a aurin don jan da yayi bai bace ba har wanan lokacin.
Rigan da Amma ta bani cikin tsaraba mai kwaliya sosai na duwatsu na saka tare da rolling din dan kwalin shi a kaina zuwa kafada na.
Ranan har kwalliya nayi sosai a fuskana tsurana ya fito tsab na mace yar matashiyar balaga.
Sai dai duk abin da nake a cikin dauriya nake yin sa don hankalina yana gurin manjo dake kwance sharkaf a asibiti.
Ina dakewa ne don in nunawa mamu yadda take so dani don hankalina ya daga akan korar da tayi min a saibiti ranan har na hadu da kaddara macuci ya buge ni da mota a hanya.
Badon komai nake dakewan da dauriya ba sai don mamu taga nayi hankali ta barni in je in duba kakata dake cikin wani haki lokacin.
Mun gama duk wani abinda zamuyi har abinci na danci tare da fauziya don dai mamu taga na sake kamar yadda take so din.
Ganin muna zaune sai kallo nace ma fauziya ta tashi mu leka Amma muyi mata barka da sallah a part din ta.
Muka fito zuwa wurin ta a daidai lokacin duk yan matan gidan suna waje suna daukan photo tare da yannen su.
Gaba dayan su kallon su ya dawo gare mu kowa da abinda ke a cikin zuciyar shi ba kamar Umar da yagano rigan da ya sayawa mahaifiyar shi a jikina abinda yasa shi kura min ido ke nan lokacin da muka tun karo wurin da suke don shiga wurin Amma din.
Bazai mata da rigan ba don kudi ya bayar mai yawa yace a zaba mai riga ta kece raini a cikin mata.
Mai shagon ya zabo mai to yaya akayi wana rigan yazo hannun wanan yarinyar sai ya tuna da marrry yabawa ta saka mai a cikin kayan hjy jummai ke nan surin Amma na samay shi ke nan.
A lokacin Aisha kece min dana karaso gurin da suke A ruwa zo kema mu dauki photo da su bros yau take sallah a tuna baya wata rana.
Ke Aisha wace A ruwa kuma can don kema kin samu an laba ki ciki shine zski muna kalar dangi a nan sai Ikilima yar wurin hjy maryam tace wanan namu yan gidane bada yan ci rani ba gaskiya iya mu jikokin Amma zamu dauka.
Ke mayar da yukan ki kube, don ni ina da tarbiya don ba zanyi photo da mazan da ba Ahalina ba nasan mutuncin kaina ku da kuke ganin hakan wayewa sai ku mayar da hinma ai na wuce abina zuwa cikin part din.
Na fadi haka ne a daidai lokacin da hankalin mazan yake gurin da suke kallon wani a waya suna dariya hankalin su baya gare mu.
Ashe duk sun jini wani kallo suka jefeni dashi a lokaci daya na mamakin abinda na fada Aliyu ne yace ke wanan yarinyar may take daukan kanta.
Kada kaga laifin ta don su suka fara takalan ta da basu fada mata irin maganan nan ba da bata basu amsa daidai da su ba Aisha ke fadi.
Ni har mamakin yariyar nan nake ji wai tana ganin kamar tafi kowane ko may Habbib ya tare shi da fadin haka.
Nan dai aka shiga aibantani inda umar yana jin su yayi shiru kamar baijin abinda ke faruwa a wurin tsakanin yaran ya mayar da hankalin shi ga wayan shi.
Sai lokacin ya dago kai yana fadin na lura kuna cikin bada gudun mawan tashin hankali a gidan nan yanzu da yarinyar nan ta biyo nan wa tayiwa magana a cikin ku ?
Sai kowan su yayi shiru ganin yadda ya ke magana don da kyat duka fsayar dashi ayi photo bukin sallah yaci gaba da fadin.
Yarinyar nan kun sata a gaba ku kwantata ku gani idan kune a matsayin ta yaya zakuji idan ana maku hakan dan magana kadan kunsan zai

Please Login or Register in order to submit comment