You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne mukaji ihu a cikin gidan wanda yasa mu fito ga baki dayan mu gidan waje.
Nafisa ce suka samu matsala da sauriyin da zai aure ta wanda murja tasha min korafi akan basu dace da juna ba nakan ce ina ruwan ta ba ita ke son shi ba hakana.
Sai gasu yau dan magana ya hadusu yayi mata dan karen duka a kofan gidan mahaifin ta kuma ya shigo har ta cikin get ya jefo mata zagi da tonon asiri a tsakanin su.
Wanda babu dadin ji kowa na gidan yana waje an kasa wanda zaiyi mai magana a gidan sai saurare akeyi abinda yake fadi din.
Kai amma dai baka da mutunci da kima aikai ka fita rashin tarbiya da zakazo har cikin gidan mahaifinta kanawa mutane rashin mutunci haka.
Ka koma gida a baka tarbiya zai fi don kai baka san darajan mace ba ko a gidan ku na fada a hasale.
Don raina ya baci da rainin wayau daya kawo muna har gida yana ciwa iyayyen mu mutunci.
Yace naji banda mutunci din ita tana da shine sau nawa ni kaina ina zubar mata da ciki shine yanzu zata koma bin wani dan iska kuma wai a haka akeson lakaka min ita in aura.
Salati aka dauka ga baki daya nace fita gidan nan mara mutunci da sanin yakamata har in kuyi hakan ai tare kuka aikata zunubin ku.
Asalima kaine wanda ka lalata har taji bata iya hakkuri dakai ta fara bin wasu mazan kajira kaga naka sakamakon dan iska kawai mara tarbiya.
Jin ina fada dashi yasa murja saka baki itama ta shiga tona mai asiri tana fadin kai waye baisan abinda kakeyi ba garin nan.
Kana sato kudin mahaifin ka kana rudin yan mata dashi har giya da karuwai kake kwasa kuma mun sani.
Yace ni kikewa kazafi babu kazafi a zance na don bakin da bai karya ya fada min daga gidan ku na samu labarin komai ka fita zakka a gidan uban ka kakaiwa mahaifin ka ko ina a duniya.
Ya nuna mu yana fadin you see karan ku zanyi don wanan sherin da kai muna Allah ya kaika dan iska kaji tonon asirin da baka taba zato ba na bashi amsa.
Ke Fatima ku kyaleshi yayi abinshi ga mara kunyar da ta ja min wanan abin har gidana ya juya wurin hjy data daskare a wuri daya yana fadin kin daiji halin yarki yau da kunnuwan ki.
Abinda take aikatawa a gidana sai kuma ya kasa karasa maganan ya juya ya koma part din shi.
Daya bayan daya muka dinga watsewa a gurin don maganan ya girmi kunnuwan mu da ji.
Dagani har mamu ba wanda yabi ta maganan balle mu zauna muyi zancen a dakin kowa yayi shirin kwanciya ya kwanta abinshi.
Washe gari ma da wani sabon rigiman muka tashi don iyayyen yaron ne suka zo gidan tunda safe wai anciwa dansu mutunci sun fasa auren a basu kaya su da suka kawo na aure.
Da lissafin kudi mai yawa da wai za a bashi wanda taci nasa tun anayi dasu da hjy a daki har suka fito waje suna cacan baki .
Hakan yasa aka fito don jin me kuma ya faru yau din ma daya daga cikin matan ke fadi munzo ne mu karbi kayan da aka kawo na auren dan mu yace ya fasa.
Ina tsaye daga kofan mu nace hjy ku koma kuce mai ba za,a bayar ba duk abinda yakeji a shirye muke dashi.
Shida bakin shi ai yace sau uku suna zbar da ciki shi shida ita don haka an rike kayan a matsayin kayan jegon ta na diyan da yake fitar mata.
Ban taba sanin akwai abinda zai girgiza hjy ba haka matan na fita get sai hjy ta sake wani irin kuka a wurin.
Gwanin ban tausayi tana fadin Nafisa kin gama dani kinja mun abin fade a gidan nan kin tozartani a idon jama,a.
Amma ta karbe da fadin kada kiga laifin yarki ita kadai kece mai babban laifi a gidan nan kowa yace ruwan wani bai tafasa nasa ko dumi baiyi.
Jummai kin cuceni kin bata min zuria ta ba zan taba yafe maki ba a rayuwa sai Amma ta fashe da wani irin kuka itama mai ban tausayi.
Da sauri su mamu da mama hadiye suka isa wurin ta suka kamata suna fadin tazo ta bar wanan maganan don Allah wanda ta fada ya isa.
Nikan kafana naja na koma cikin part din mu ina jin babu dadi a raina don abubuwan da suka faru babu wanda zaiso ace nasa ya sama yau.
Ko banza Nafisa yar uwatace kuma kaunar uban diyana bako zanso ace wani abu mai muni irin haka ya faru da ita ba.
Mamu ta dawo part din ta tana kitchen sai jin sallaman hjy maryam mukayi tashigo gaida ita nayi ina mamakin shigowan ta shiyan mu don ba kasafai take shigo muna ba sam na shafa da zancen daya faru ne yakawo ta.
Mamu ra fito tana fadin a,a hjy ce tace kedai nice maimuna magana ya isheni a zuciya nace bara na dan zo nan in rage.
Ke kinji mun yarinya da abin kunya haka ana cewa namu sune lalattu ana muna gori ya tayi goshi kaya har sait uku da sauran tarkace ashe ashe ba alheri suke aikatawa ba da yaron nan shiyasa dare da rana suna makale da junan su.
Hjy wanan magana ai ya shafi kowan mu nake gani ko kin mata da cewa Nafisa yar dan uwane ne wai ?
Kekuma ai diyar mijin kine idan sunan gidan nan ya baci ba Nafisa kawai za a zarga ba duk ya shafi yayan gidan nan ga baki daya.
Hakane kuma ta fada cikin wani yanayi sai kuma tace amma dai idan da dayan mu wanan magana ya shafa da yau munji hjy a gidan nan.
Ko itace ya shafe mu ai tasan gaskiya don babu musulmin kwarai da sheri zai samu dan uwan shi har yaji dadi a ranshi.
Bata dai gane komai ba haka yasa ta fita bayan ta gama yan surantanta a wurin nikan kamar bana falin zaune a lokacin don ko kallon ta banyi ba.
Tana fita nace mamu wanan matar har yanzu halinta yana nan ashe tace Allah dai ya rabata da wana halin yanzu ita har taga abin gulma a nan.
Can kuma ta juyo tana fadin wai nikan kunyi maganan da kikace da gwaggo ko bakuyi ba har yanzu.
Nace munyi mamu ta fada min komai har auren su duk ta ban labarin komai nace amma ai bata da laifin wucewa ta barki don su Amma su suka hana ta wuce dake a lokacin wanda a yanzu take da ta sanin yin hakan.
Haka dama Allah ya nufa damu haka ya tsaro min nawa rayuwan kuma nace hakane kuma.
Ina son zan kirata yanzu idan na gama abinda nakeyi sai muji ko za,a sameta muyi magana.
Ganin hankalin mamu ba zai kwanta ba yasa na dauko wayan na kira layin nayi sa,a ya shiga sai dai ba dauka ba har ya katse.
Kira biyu nayi ba a daga ba na fahinci mai wayan bata kusa da waya a lokacin.
Tana zaune ta tasani a gaba har na aje wayan ina fadin idan taga kiran zata kira kila daga baya.
Mamu ta sauke ajiyan zuciya tana fadin Allah yasa nace idan bata kiraba zan kara kira kafin dare yayi.
Har na aje wayan sai naga ya kamata in kira yaya inji lafiyan shi da yaran don yanzu ban san takamaiman ida suke ba dakai.
Kira biyu ya daga da sallama na amsa mai yana fadin yau kin tuna damu ke nan nace ai kullun ina tunawa daku.
Allah yasa yace nace baka yarda ba ke nan yace ina zan yarda tunda kina son dagwara min laifin da kinfi kowa sanin banawa bane.
Akan me zan dagwara ma laifi yaya Allah yasa hakan shine alheri a gare muna fada sai naji yace hakan kamar yaya ?.
Nayi saurin gyara zance na da fadin na zama ba kusa dakuba mana yanzu yace gara da kika gyara lafazin ki.
Ina sultana gata a hannun mamu tana jin ka bata wayan yace nace sultana din ko mamu yace sultana dai.
Na yunkura na kara ma yarinyar waya a kunnen ta magana yake mata tana dariya ba bakin da zata bashi amsa a lokacin.
Na cire wayan a kunnen yarinyar ina fadin bari in barka kayi aikin ka yace aiki yafi jinku a yanzu da nakeyi.
Yaushe zaku dawo ne ya tambayeni nace babu rana gaskiya kenan baki tausaya muna zahra dan murmushi nayi nace ina tausayin ku mana.
Saidai banda yadda zanyi ne a yanzu ka sani ina dai kwantar mai da hankali kada ya fusata in samu mu rabu lafiya dashi a lokacin.
Mun dauki lokaci muna wayan saida na tambaye shi queen fa yaya wajen su suna lafiya ko yace ban koma Europe ba har yanzu muna nan landin labawa tukun .
Mukai sallama na kashe wayan na zauna ina tunane a gurin yadda wanan al,amari zai kasance muna nan gaba.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:34 - 🤐🤐🤐: Ina zaune a inda nake ina tunane naji muryan mamu tana fadin kina son tayar da hankali kan auren da mijin ki zai kara ko ?
Na dago kai nace mamu auren shi bai damay ni ba sai dai nasan auren gaiyya ake son mashi a kaina.
Don murja ta gano ko wace yarinyar ce ashe diyar hjy sabuwace da sukai zama lagos ance idanun yarinyar a bude yake sosai zata girmi anty salma na a wurin haihuwa sosai.
Sayadi ba zaman lagos ba ko zaman turai tayi karewan bude ido mai zai dameki indai kin rike gaskiyar ki da amanan mijin ki a ranki kina kuma aiki da hankalin ki aiko tsakiyan faransa ta tashi karewan bude ido zata barki ne.
A yadda Murja ke fada min taji wai ashe zancen nasu ya dade sosai yarinyar taki da farko da hjy taso ayi hadin sai yanzune suka aminta da ayi suna bin hjy sauda kafa har ta yarda.
Mumu tace kamar nasan da zancen nan a baya saidai aikin mantuwa kawai ashe zancen nasu yana nan har yanzu ai da farko na dauka diyar Rakiya ce ko Ramatu dan suma suna son auren shi naji wurin hjy maryam.
Ashe yar wurin hjy sabuwa ce kuma yanzu idan wanan ce aiki barsu kawai zai fita a tsakanin su don bata da hakkuri ko kadan kowa yasani.
Ba mutunci ne da wanan matar ba su kansu suna tsoron masifan ta shine kuma yana zaune zaman zaman shi zasu dauko yarta su bashi kai hjy bata lissafi kafi ta aikata abu wallahi.
Mamu ai duk saboda nine nake gani zasuyi wanan hadin .
Tace a wurin hjyn gidan nan ba amma su wurin su aiba hakana bane mijin ki kamilin mutum ne da yasan kansa ga zati da kyau da cikkaken ilimi uwa uba arziki wanda ko wace mace yanzu take gurin samun mijin irin shi.
Haka ya tashi da farin jinin mata tun muna yara duk da koda yaushe fuskanshi shi a daure yake bai hana mata suce suna son shi ba harda wa yanda suka girmay shi lokacin.
Shiya banyi mamaki ba lokacin da yazo gidan nan da matarsa merry don nasan irin nacin da mata ke gwada mai ta gwada mashi har ya yarda da ita.
Ni dai abinda nakewa gudu da tsoro shine asiri tun dawowan hjy sabuwa garin nan da zama gaba daya hjy ta fada harkan bokaye da malamai inma da tanayi dai a boye take abinta amma yanzu a filin Allah take lamarin ta.
Saidai ni abinta bai faye damuna ba tunda ina bin dare ina fadawa Allah matsalolina ya kuma amsa min na gani.
Mamu nidai idan abin zai zama fitina gara in tsira da rayuwana kowa ya kama gaban sa .
Da sauri tace kina ko da hankali sayadi mai yasa kikaji manya na fadi anyi hakkuri da yanayin aure mai dadi ko mara dadi duk a kan yarane fa.
Kan yaro sai ke mace ki danne komai naki kiyu hakkuri ki barwa Allah al,amarin sa komai da zai faru da bawa Allah yasani.
Don yara wasu mata ke zaune gidan mazajen su suna cin boni gun kishiya da miji don sun kwamace da wata ta ba yaron su tarbiyan banza garasu suba abinsu mafi ingancin tarbiya tun zamaninda da ake da sauran imani balle yanzu da imani yai karanci ga zukatan mutane.
Idan kinyi hakkuri komai yazo mai wucene a gurin Allah sai a koma kamar ba,ayi ba daga baya.
Mamu amma aini nayi karanta da shanye irin wanan abinda kike lissafo min na fada ina kallon fuskanta.
Tace kaiyya sayadi hakkuri ga yaro da babba aka san shi balle ban sa a raina cewa don mijiki ya auri yar wurin hjy sabuwa zai juya maki baya yadda kike tsamanin zaiyi ba duk dako itama yar uwasa ce kuma iyayyen su zasu tsaya sosai a kan auren na sani.
Kedai ki kwantar da hankalin ki Allah ya saukeki lafiya ayi a zauna lafiya ba shike nan ballema shida baida ra,ayin aje mata a guri daya irin namun nan may zai damu mutum .
Ba zama wuri daya ke sakawa mata kyashi da hassadan junan su ba haka abu yakici yaki karewa ko yaushe.
Ranan mun dade da mahaifiyata muna hiran abu daya saida likacin sallah yayi muka tashi mukai sallah da cin abinci na shiga wurin Amma.
Washe gari na tashi da niyar zuwa gidan Anty salma da tazo tana min korafin naki zuwa wurin ta dama ina da niyar zuwa wanan matsalan yazo muna na dawo gida.
Sai ranan nayi waya da drivern gidan yaya akan ya kawo min motana zan fita dashi kwalliya sosai muka sha dagani har sultana fauziya da murja.
Rigan dake jikina basai an fadawa mutum an kashe naira a gurin sayen shi ba dayai wani tafiya Dubai ya sawo min shi ga sultana da ta kwaso farin mu kamar yar turawa kwaliyan dan riga pink da wando dogo har ribon da ta kalman kafatan adon pink ne da fari a jikin ta.
Daidai mun fito ke nan daga wurin Amma da muka shiga sallama aka turo get din cikin gida za,a shigo.
Ban damu da kula matan da nagani suna shigowa gidan ba a lokacin don hankalina yana ga wayan da nake da Aisha muna dariya ina tafiya salo salo kamar da kamar da gangan nakeyi banko san inayi ba.
Wani irin kallon kishi da tsana suke aika min daga inda suke suna kallon yanayin shiga na a cikin rudewa.
A hankali tacewa uwar wanan kuma a gidan nan take ne tana magana kasa kasa kamar rada ga uwar.
Wata kila bakuwa sukayi wanan motar da muka gani waje muna magana kai amma dai wanan ta hadu wallahi.
Taji ina ace haka ta samu haduwa koda rabin nawa ne aida tasan dole mijin da take muradi ya so ta.
Ga mace kamar balaraba sak da ganin ta yar wani ne ko matar wani a kasan nan irin yaran nan ne da suka taso a cikin hutu kinga fatarta wani irin luf luf dashi kamar wace bata shiga rana dan cikin jikina daya turo ta kalla tace ciki dai yanawa wasu mata kyau wallahi.
Ita kadai take zancen ta a zuciyan ta sai taji duk irin kwalliyan data fito dashi suna yauki daga ita har uwarta duk sun muzanta a gurin.
Ganin sun danzo kusa damu yasa na dan barwayan ina fadin sannun ku da zuwa ina wunin ku.
Mun saba da gaisuwa irin na tura da zaka hadu da mutum baka san shi ba ku gaisa.
Tana mamakin jin muryana daya dan girgizata sosai bamu kara kulasu ba mama hadiye ne ta fito tana fadin Fatima ku biya gidan saratu don Allah ku gaisheta na amsa da to mama da cewa gidan kanwar mama hadiye din.
Bari na dan riko abin da zamu kai mata nace ina sake hannun sultana zuwa part din mu da sauri.
Ba yar ba har uwan saids gaban ta ya fadi uwar tace kardai nace wanan ce matar yaron nan dama ?
Da wanan mamakin suka shiga wurin hjy da sukazo dubawa don tun maganan su Nafisa ta kwanta ciyo.
Shine suka zo dubata don yanzu zumuncin su ya taso sosai a tsakanin su idan ba a hadu ba ana makale da waya.
Hjy dake zaune tana ta dago tana dan murmushi tana masu sannu da zuwa.
Suka amsa da um kedai hjy muna shigowa muka hade da wata mace data dauke muna hankali yanzu gidan nan.
Hjy tace a gidan nan kuka ganta Nafisa dake gefen ta zaune tunda tayi masu sannu da zuwa ta kawar da kai gare su tace Fatima ne fa suke fadi yanzu da zan shigo na gansu zasu fita ita da murja.
Na,ima tace na shiga uku itace fatiman matar Umar dama anya kuwa kuwa Umar zai soni yana da wanan matar haka ?
Da sauri hjy jummai tace inkiji soma ai daya ke nan ai sai yayi maki so da kaunar da bai taba yiwa wata mace irin shi ba indai ina raye.
Mu zuba dani dasu zaki sha mamaki ke dai kawai mu samu yanzu mu shawo kanshi a samu ayi wana abin gida bai koshi balle in barwa daji ganima .
Iya gudun shi nake kallon nan gaba bausan sanda zai kawo kafan shiba gidan nan da kansa yana rokon gafaran mu.
Hjy sabuwa tayi dariya tace tun yaushe wasa yake damu ai don dai kawai ma ya zama namu ana daga masa kafa.
Mikewa Nafisa tayi ta bar falon zuwa daki waya ta dauko tana tsegun tawa salma zancen da sukeyi a falo tana jan tsuki.

Muna fita gidan muka shiga mota nida murjane a gaba fauziya da yarta suna baya zaune suna dan hiran yara.
Wai fatima kin san wa yan nan da suka shigo gida yanzu nace wasu mutane ke nan don ni har na manta dasu a raina.
Tace wa yanda kika gaiyar mana da zamu fito nace OK matan nan ai ina ga wurin hjyn su yaya suka zo ko ?
Itace fa Na,iman da ake fadi yaya zai aura din ta fada tana kallona wanan din da suka shigo yanzu fa murja na tambaya ina kallon ta.
Ita face da uwarta ina fada maki kaina girgiza ina runtse idona duk da ban masu kallon kyauba amma na danyi tunanen kamanin su.
Ban taba zaton zanji abinda naji a raina ba lokacin da sauri nace innalillahi ina kallon hanya.
Suma bakiga irin kallon kurullan da suke maki bane da suka shigo ba lokacin kila suma sun gane ki ne suke kallon ki.
Suka sani na bata amsa ina kallon ta tare da fadin sai fa kin mun kwatance don ban iya kai kaina gidan yanzu gaskiya.
Tana mun kwatance muka isa gidan tun a waje na gane salma na cikin wani yanayi don har yanzu gidan na a yadda na san shi a baya ba,a gyara komai ba daga gidan.
Nan dai muka shiga bayan nasa Fauziya ta riko abinda muka kawo mata sallama mukayi daga kofan shiga tana ciki ta amsa muna.
Tana fito da gani girki takeyi a lokacin mamakin ganin mu tayi wanan lokacin yau a gidan nan nace gidan ki kuwa yau dai gamun zo falo ta kaimu tana kame kame aiki yai yawa bata samu ko gyaran falon ba yau.
Muka zauna muna gaisai tana tambaya mu mutanen gida ranan mun sha hira tanayi tana duban girki har yayi ta zubo muna mukaci tare bayan azahar sai ga maigidan ya shigo cin abinci dama tace muna kila ya dawo don ba kullun yakan samu dawowa gida ba.
Allah ya taimaka sai gashi ranan ya dawo tundaga waje yake kallon bakon motar daya gani kofan gida haka ya daure ya shigo gida da sallama tare da zullumin wanda zai sama a gidan.
Kasa nake zaune na sake jikina muna hira dan kwalina yana saman kaina na rufa ya shigo da sallama.
Muka karba tare da mai sannu da dawowa da mamaki yake kallona tare da fadin wa nake gani haka kamar Fatima gidan yau nace nice yaya.
Duk cikin mu ni kadai ke masa wanan karan kiran shi da yaya tun farko kuma yana jin dadin hakan har cikin ran shi.
Gaisawa ya zauna mukayi sosai yana tambayana yara nace suna lafiya baban su ya tafi dasu suna gurin shi.
Kefa may kikeyi a garin nan har yanzu sai nayi mai dariya kawai anty salma tace kamanta na fadama tana gida yace amma na dauka laluran cikine ya tsayar da ita aiko ?
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya mike yana umurtan ta takai mai abunci a daki tunda muna gurin .
Nan ta barmu ta shiga hidiman mijin ta muna dan hira da murja sama sama a gurin na lura da akwai biyayyan aure sosai da salma take mai don yana shigowa gaba daya sai naga ta daburce min .
Sai da ya gama na mike ina tambayan ta ya kare cin abinci ne ina son magana dashi taje ta fada mai yace in shigo tashi yayi saman kujeran da yake zaune ya koma bakin gado ya zauna.
Na shigo da sallama muka kara gaisawa yace banji dadin jin kina gida haka zaune kuma ban sani ba don yanzu na rage shiga gidan tun bayan auren mu da salma bana shiga kamar yadda nake zuwa dacan.
Nace yaya dole na zauna gida abubuwa sunki canzawa ta bangaren hjyn su salma har yanzu dani nan dai na kora mai dan bayanai da suka faru.
Yace ni abin yana ban mamaki wanan hali na hajiya har kullun ita bata amfani da girman ta da shekarun ta.
Yanzu shi Alh dayace ki zauna gida yana ganin hakan shine mafita ga zancen ku ?
Nace yaya ni hakan yafi mun sauki gara kowa ya zauna a matsayin shi zai fi abinda ke daga min hankali shine kullun dan zance kadan tayiwa mamu gori da zagi da cin mutunci.
Zuciyata ta fara gajiya da wanan abin yaya don ba zan yarda ina ganin mahaifiya ta ko yaushe a cikin tashin hankali yaya meye laifin mamu a cikin barin ta da mahaifiyar ta tayi ?


Please Login or Register in order to submit comment