You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta koma kansu ta fita batu na sai haushi ya kara kamani lokaci.
Ina jin suna fadin mamu kuka takeyi ita macen ke tambayan ta tace she is not well.
Sai naga yarinyar ta bata fuska suna
Zaune sunyi sai ni suke kallo yadda nake kukan yarinyar ta mike ta fita daga falon can sai gata da goran ruwa ta kawo min tana bani tare da fadin sorry anty ki sha ruwa.
Ban karbi ruwan ba na mike zuwa dakin da ta nuna min a matsayin nawa na fada saman gado naci gaba da kukan ni kadai a dakin.

Sallama tayi ta shigo falon kamar yadda tayi tsamani haka din ne ya faru don hjy Jummai na zaune suna cin abinci da yaran da dawowan su ke nan daga school.
Salma ce sai kannen ta biyu mace da namiji ta saba da irin karba sallaman su wanan kuma yanzu ya bar damun ta ko kadan.
Yaran ta fara magana don tasan shi kawai zatayi ta samu kafan yin abinda ya shigo da ita shiyan tace a, a yan makaranta sai yanzu kuke cin abinci ne.
Hjy jummai ta dan ya mutsa tace kin san su da shiriri ta ai ko cin ma ai sai na matsa masu suke zama har da wanan babban banzan.
Babu wanda ya dago kai daga cikin yaran ya kalle ta tace hjy ashe kuma mun samu bakuwa ne a gidan jiya ?
Bakuwa daga ina kuma ina take a, a yarinyar nan mana wa take da suna yar wurin maimuna da ta haifa can bauchi mana ashe jiya tare da ita suka zo.
Wani irin kibiya ya soki zuciyar hju jummai ta dago da mamaki tana fadin ke nan an kawo muna agola a cikin gidan nan ke nan ?
Masuyi iya magana sukace wai sani in fika ba wai agola da rabon gida lallai kan tana nan tazo kin ga yadda yarinyar ta girma kuwa ?
Ba zaki ce , , , , , don Alh hjy maryam rabani da wanan zancen kazantan wai may ke damuwan Alh ne haka yanzu ?
Lalai kan a bincike shi don abin ba lafiya ba wanan ma na gidan ya muka kare dasu balle an dauko agola an jefa a cikin namu kuma .
Hmmm, cabdijam ashe ko akwaita a gidan nan ke nan don ba zata sabu ba bindiga a ruwa samun wurin na maimuna har yakai ta dauko yar ta ta kado muna ita gidan nan .
Hjy maryam tace sai dai inda sunan hutu tazo nan amma kuma ai yanzu karatu akeyi ko ina shi yasa abin ya bani mamaki .
Ke yaba mamaki ko ni maryam zamu gani idan zai fada muna ko zaiyi shiru inko har yai gigin fada min zai ko ji amsa a wurina wallahi.
Hjy maryam da ta samu abinda take so ta hau zuga hjyn har da fadin wana karon akan maganan yar nan ba kyale shi zamiyu ba bore zamuyi masa wallahi.
Ko bakiyi ba aini zanyi don ni ake cutata fiye da kowa ni mai yaya da yawa a gidan nan abin bai tsaya ga wa yan nan shegun data tara muna ba har ya kai a dauko wata a dada muna kuma.
Duk da kalamin ya bata wa hjy maryam rai sai ta shaye da yake munafunci ne tace.
Duk fa abinda akeyi da sanin wanan tsohuwar mai glass tana zaune take bada umurni komai nina dade dagano su ai hjy maryam ke fadin haka.
Ta san komai mana, idan ma ance maki da shirin ta ne wanan ba za a yj musu ba don kuma kawai ta kuntata muna tayi haka amma maimuna bata farawa tace yar ta tazo ta zauna damu wane ita.
Wai a gidan an ake nufin yarinyar ta zauna sallama da tun shigowan hjy maryam ta hade rai sai yanzu tayi magana .
Maryam tace niyar su ke nan Allah, salma kun samu karuwa don wallahi yar ta kusa kama kafan ki wurin tsayi da komai nagani.
Kai haba maryam ko da na haifi salma ai fatima bata koyi aure ba sannan kuma da tai auren ta dade Allah bai bata yar ba sosai.
Hjy maryam ta nisa tana mikewa tare da fadin tana nan naganta dazun zasu sashen hajiya da cewa Amma tace munafuka ke nan inji hjy jummai.
Haba mama stop saying that to her ko banza she is Dad mum kinga bai dace and beside idan maganan ya fita ace kece mara kunya kina zaginta.
Hjy maryam ta gane nufin yarinyar saboda shayin uwar yar da takeyi ya hana tayi mata magana a lokacin.
Batai wani dadewa ba ta fito daga part din da zuman itama idan Alh ya dawo zasuyi mai maganan basu yarda da zaman yarinyar a gidan ba dukkan su.
Tana fita salma taja tsuki tare da fadin amaybo olo popo ita wanan aikin ta ke nan ta gani ta kwaso ta fada Allah mama yaci ki gane wanan matar haka.
Laifi tayi don taga abinda bai dace a gidan ba ta fada min idan an kyale wataran sai abin yafi haka girma take bani yanzun da take ban girman watau baki sun hakan kuma ?
Tabe baki tayi salis ya shigo yana fadin mama dad ya kara sayen motane naga mota har biyu sabbi a waje .
Da sauri tace wajen gidan nan ko ko dai kafin yaron ya bata amsa wayan ta yai kara ta dauka habbib ne a layin da sauri ta daga wayan ta kara a kunnen ta tare da yin sallama.
Sama sama suka gaisa da dan nata yace mama kin san da zancen motar da Dad yasa ya umar ya sayawa matan shi kuwa.
Cikin wani murya tace what tare da dagowa daga kujeran tana fadin umar ko na da hankali yaya akayi hakan ya faru ?
Ta mikw tana fadin hold on barin leka inga abinda ke gudana yace ai har motocin sun karaso gidan ko yanzu umar din ya kirani yake fada min wai ai ma Ahmed magana ya yi masu takardu.
Kai habbib yaushe umar ya canza hakane yace wallahi bai camza ba mama yana nan dai umar din da ko koka san shi miskili sai ma abinda ya karu.
Wai kana nufin matan nan za a ba motar yace kwarai kuwa nima yanzu yake fada min ashe tun lokacin da aka saya maki naki Dad yai mashi maganan nasu.
Ashe akwai bura uba a gidan nan don ba zai yuyu ba lokacin da nayj wahala daku su ina da yanzu zasu ce komai alai min sai an masu shi a gidan nan.
Mama wani abin ba amma ina zasu hada kanki dasu da dai kin kyale kowa ai don ki akayi hakan sun ci albarkacin ki.
Kin san shi bros wani bahagon mutum ne shiyasa ban masa magana a kan hakan ba sai ya nuna min nafishi sanin abinda zaiyi ne.
Kwai dai ki saka masu ido nasan ai Dad din zai maki bayanin ko ma may nene so ki basar kawai mama.
Ai bai fufe baki ba ta kashe wayan tare da mikewa zuwa hanyar wajen gidan inda ake aje motocin gida wuri ne mai girman gaske ko wacen su zata aje nata dana mai gidan guda biyu.
Turus taja ta tsaya tana karewa motocin kallo duk da nata ya na gaba sosai ga wa yan nan amma sai kyashi ya tartsu a zuciyar ta a lokaci daya take ganin nasu ya cunawa nata.
Ranan ina wuta ta jefa kanta idan da tasan ba zai kone ta ba ranta yayi bala,in baci da wani zataji a gidan da zancen dauko masu agola a gida ko kuwa zancen motocin da aka tillastawa dan ta ya saya wa kishiyoyin ta
Salma ne da kanwar ta suke tausan uwar tabi a hankali har ta gane komai don kila Alhajin ne ya bada kudi a saya mashi aiko a hasale ta juyo gare su tana fadin idan ya bada kudi sai akace an fitar dani a ciki ko ?
Ranan sai dare Alh sani ya dawo gida don haka bata samu zaunawa dashi ba don ko dan kewaya sun da yakeyi ranan bai samu yayi masu ba.
Sai washe gari suka samu ganawa da maidan wanda ta samu yana shirin shi na fita kasuwa a lokacin .
Tana shigowa dakin tace fita zakayi ne yace yau har na makara don jiya na gaji da yawa sai ta samu wuri ta zauna a bakin gado tare da fadin.
Dama nazo magana akan motocin da aka shigo dasu jiya ne gidan nan don banji kayi bayanin komai ba akansu.
Wani irin mamakin ta ne ya kama shi lokaci daya tare da takaicin ta ba ko gaisuwa zata fito mai da wanan zancen gatsau.
Sai kuma tace gaba da fadin bayan nan sai zancen yar wirin maimuna da hjy maryam tace min ta gani a gidan nan jiya da safe wani abin tazo yi garin nan halan ?
Lalai yau yasan Jummai sakariyace girman kawai Allah ya bata a gidan mutum mai yara irin jummai zai zauna yana kishin ba gaira ba dalili haka.
Jin yayi shiru yaci gaba da saka tufafin shi ta sake fadin Alh bayani fa nazo kai min kana jina kuma kayi shiru.
Wani irin kallo ya watsa mata daga inda yake kafin ya hade abinda ya taso mai azuciyar shi yace.
Jummai nike auren ki ko ke ke aure na dani dake wa ya,aje wani a gidan nan ne, jummai wai wanan wani irin rayuwa kike neman jefa kanki a cikine wai ?
Kada fa ki manta a karshina kike gidan nan dake da duk wani wanda ke zaune a gidan nan kada fa ki mata kamar yadda na auro ki haka na auro kowace ku a gidan nan.
Ina son ki sani na auro kune a gidan nan baki dayan ku kamar yadda kowan ku keda hakkoki a kaina.
Amma ke kin kasa tuna wanan hakin da nauyin da ya rataya a kanki kina kokarin shigo min da wanj akida na daban a gidana.
Aje ni kikayi da zaki zo min da wanan maganan ba ko gaisuwa ko wani da, a gaba daya kina kokarin cusa min wani ra,ayi naki a cikin gidana.
Kafin ki zo nan duk yan uwan ki sun shigo mun gaisa dasu da kwana amma banji wata wace ta tambayeni komai ba.
Amma ke kin taso zakal zakal don kin raina ni zaki sani a gaba kina tambayana kamar kin aje ni.
Zancen yarinya ai uwarta na gidan sai ki tura wace tace ta ganta taje ta tambayo maki abinda tazo yi maku gida.
Mota kuma ki manta ki tambayi wanda ya kawo su ya aje kafin ya tafi yai maki bayani kada fa ki manta ke matar aure ce kamar kowa a gidan nan.
Abinda ya kamata ace kin tsaya kin yi kin koyar bashine a gaban ki ba sai shirmay banza kin watsar da cina da sha na balle gyaran muhalina uwa uba hakkina don wani dalili naki na banza.
Yarana da iyalina a kullun sai kokarin watsa min tarbiyan su kikeyi don baki da tunane da lissafi zaki taso ki sani a gaba kina tambayana yar wurin maimuna
Shin kin mata da nima ya tace tana da daman zuwa gidan nan duk lokacin da taso koda kuwa ba maimuna a gidan nan..



ZAINAN IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:42 - 🤐🤐🤐: RABBANA ATINA FIDDINIYE HASSANATAN WA FIL A FIRANTAN HASSANATAN WA, KIN,NA AZZABAN NAR


Wani kallo take mai ba don taso ba ta kyale shi don ya fito mata a namijin sak ranan babu hanyar ko daman da zata fada mai wani magana kuma akan wanda ya fada mata don duk abinda ya fada tasan gaskiya ne.
Lalai tana da rauni a zamantakewan su to amma ai duk da yan aiki keyi komai kamar yadda yace bata gaza wurin basu umurnin komai ba.
Ganin bai kulata ba sai harkan gaban shi yakeyi ya barta zaune a dakin kamar ba mutum wurin yasa ta tashi fu fu fu ta fice zuciyar ta cike da bacin ran shi.
Tana gani bai mata adalcin ba akan komai kokarin yake ya fifita wasu yanzu a kanta abinda ko ba zata taba bari ya yuyu ba ke nan a gidan.
A hanyar ta na fita ne suka hade da hjy maryam zata shigo ko kallon arziki bata samu ba a wurin ta, ta wuce ta fuuuu ta dan kalleta tare da sauke murmushin keta a gefen fuskanta.
Da sallama ta shigo dakin ya dago ya bita da kallo ranshi a bace har lokacin ta dan dade a tsaye bai dago kai ya kalle ta ba sai da tayi gyaran murya ya juyo a fusace yana fadin.
Kin zo hada wani sheri ne a nan kuma ke may yasa baki barin halin ki na sarika noke ne a gidan nan nasha sanin kina wanan halin ina zuba maki ido ko zaki canza sai dai abin naki ya fara kureni a yanzu.
A marairaice tace may kuma nayi kake fada min haka Alh da shigowana ban san matsalan ku da matar ka ba zaka aza min laifi irin haka na zargi ?
Ba zargin ki nakeyi ba don Jummai ta fada min kece kika kai mata tsegumin yarinyar nan Fatima yar wirin maimuna.
Wiki wiki tayi da ido tana dukar da kai kasa tana cewa ni bada wani manufa na fada mata ba don dai naga yarinyar ta girma ne shine nake magana amma in hakan ya bata ma rai kayi hakkuri.
Yace wanan abin ya isheni kun dauki tsana kun sakawa yar mutane may ye laifin maimunaa wurin ku har make ita jummai din wa ta bari a cikin ku tunda tun akan auro kine bamu da kwanciyar hankali da ita a gidan nan.
Abinda baku sani ba shine hadin kan ku yanzu na dauko hanyar gyaran shi tunda ba na Allah da Annabi bane sai kuje can ku hade kan ku ni kuma zan hade maimuna din mu gani.
Yarinya kuma tazo ke nan da zama a gidan nan babu idan zata sai ku dafata kuci idan kuna iyawa ku zauna lafiya
Yana fadin haka ya juya yana kokarin saka babban rigarsa nan ya barta ya fita batunta tana tsaye kanta a sunkuye ta kasa koda furta wani abin kuma balle ko ta motsa don bata taba tunanen mijin nasu yasan sari ka noken da takeyi tsakanin shi da matar shi ba uwargidan su.
Sai gashi yau daga sama yana fada mata halayen ta a natse gashi ta kasa fadin abinda ya kawo ta dakin don nauyi da kunyar abinda ya gama fada mata.
Yana gamawa zai fita ya kara fadin ku baku ko tunanen kaddara da mutuwa ya kawo maimu da yar ta cikin mu yanzu kun manta kaddara tana iya fadawa a kan kowanen ku don Allah babu inda baya ikon shi a duk lokacin da yaso.
Wani irin yanayin nadama yazowa hjy maryam sai dai kafin tayi magana ya gwauta ta yai ficewan shi daga dakin ya barta tsaye tana sauke ajiyan zuciya.

Ina zaune a falo babu kowa sai tv dake ta faman aiki shi kadai babu abinda nake sai faman tunanen makoma a gidan Alh sani da akace zama a yanzu ya dawo nan din din din.
Hjy maimuna ta fito daga daki ta tsurawa diyar nata ido na wani lokaci haka yasa ta fahinci yarinyar tayi nisa a tunane wanda tasan ba na komai bane sai na kakarta.
Ke sayadi shiru sai data fada sau biyu firgigit Fatima ta dawo cikin hankalin ta tare da dago kai tana kallon mahaifiyar nata sai kuma tayi kasa da kan ta don kawar da idonuwan ta da suka tara hawaye a lokacin.
Take tausayi da soyayya yar ya tarsu a zuciyan ta wuri ta samu gefen yar nata takai zaune sai data sauke ajiyan zuciya kafin tace.
Kiyi hakkuri sayadi ki dauka wanan wani abu ne kaddarare ya hau kan mu dani dake duka nasan akwai zafi a yanzu raba ki da kakar ki danayi a lokacin da kuke bukatan junan ku.
Amma ba yadda zanyi ne yin hakan ya zama dole a gare ni don samun ci gaban ku baki daya nan gaba .
Munyi maki alkawarin duk hutu idan kina son zuwa wurin ta za a kaiki ko ita tazo nan tunda naji Alh na maganan taimaka muna ma ta hanyar dauko zuwa asibiti nan.
Kin san kuma don ke ce zaiyi hakan daba haka ba sai dai a barta can ta halaka kina ji kina gani tunda babu abinda zakiyi.
Tun zaman ta data fara magana sai yanzu naji sanyi ya ratsa min zuciyata jin za a dauko min manjo kusa dani da gaskiya.
Tace amma fa hakan bai faruwa har sai kin sake ranki a gudan nan ya gani haka zai sa yaji karfin dauko manjo din kusa dake.
A hankali nasa hannu na share hawayen da ya bata min fuska da farko na sauke ajiyan zuciya tare da dago kaina na kalle ta a karo na farko data zauna a gurin .
Tace kwarai amma fa sai kin daina wanan tunanen yaga kina walwala a cikin mu kin sake jiki da kowa a gida nan kin rugumi yan kannen ki kin saka su a jikin ki.
Kin mayar da hankali a wurin karatun ki na boko dana mahamdiya hakan zai sa ya ji dadin tallafa muna amma idan kina cikin wanan halin karshen shi ma yace a mayar dake can din kin ga ke nan ke kika cuci kakan ki mai neman taimako a yanzu da kanki.
Da sauri na kara kallon ta tace eh ke kika cuce ta mana tunda kin ki ki kwantar da hankalin ki mukai ga manufan na son ya taimaka maku tunda ba halin in fito baro baro ince ga yadda nake son aiwa mahaifiyar tsohon mijina daya mutu.
Da kyat na bude bakina da yai min nauyi nace mamu na daina insha Allah zanyi kamar yadda kika ce inyi insha Allahu.
Tace da kin kyautawa kanki tana mikewa take fadin hakan daga haka ta fice a dakin ta barni ci gaba nayi da tunane can dai na dan gano abinda take kokarin fahintar dani din da sauri na mike na tsiri gyaran falon dole har zuwa dakunan kwanan mu duk dako a gyare suke a lokacin.
Ta dan dauki lokaci sai gata ta shigo tsayawa tayi tana bin falon da kallon aikin danayi har zuwa bedroom din ta sai dai bata tarar dani a falon ba lokacin na shiga wanka.
Na fito daidai lokacin ta leko dakin nawa tana fadin yanzu Alh ya bugo min wai gobe za a kaiki makaranta ai maki inter view.
Sai dai ina ganin kamar makaranta daya zaku dinga zuwa da sauran yaran gidan nan don haka nake son ki koyi kawar da ido a kansu domin su din ma kamar sunfi iyayyen su kishi dani a gidan nan.
A Cikin rashin kuzari na amsa mata da to kawai babu abinda zancen bayan wanan amsan don yanzu ba zance ga diyan gidan ba tunda ban san ko dayan su ba har lokacin.
Takai kofa ta juyo tana fadin kina iya yin sallah yanzu don azahar ya yi nake gani idan kin idar sai kije gun Gwago tana tambayan ki wai kwana biyu baki shiga ba gurin ta ba.
Duk a sanyaye nake jarbawa do har lokacin ban gama walwalewa daga damuwn da nake ciki ba.
Ban gama shiryawa da wuri ba don haka na bata lokaci zuwa sashe Amma din har lojacin da kanne na suka dawo gida daga school.
Wanka nayi masu ba tare da umurtan mamu ba don gani dama na kawai cikin kokarin ganin na sake kamar yadda mamu ta bukaci inyi.
Sai dana shiryasu muka zauna cin abinci wanda na gani ga fuskan mamu hakan yai mata dadi ba kadan ba saidai bata fito fili ta fada min hakan ba.
Mun samu amma zaune da yan matan mama hadiye da suka dawo makaranta basu ko cire uniform din jikin su ba suna zaune dashi muka shigo part din da sallaman mu.
Amma tace wa nike gani nan kamar yar bauchi wai nikan aruwa uwarki rowan ki takewa mutane ne a gidan nan.
Ace muna gida daya tun shekaran jiya rabon da in saki a idona ko da yake takawo min uzurin baki da lafiya ne.
A raina nace Allah sarki uwa ke nan ta boye halin da nake ciki ashe bata fada masu gaskiyan abinda nake mata a part din ba don in na shige ban fitowa ina ciki zaune ko kwance ga matsin da nakewa yaranta koda yaushe.
Har kasa nakai ina gaida ita yayin da yan matan biyu dake zaune ban ko ishesu kallo ba a gurin tana min ba,a tace ke ni kawar ki ce ki daina tsugunna min.
Ga kujera can ki zauna yarinyar albarka kin samu tarbiya irin wanda ya dace diya mace tayi ba irin wa yan nan marasa hankalin yaran gidan nan ba tana magana tana nuna jikokin nata dake zaune.
Sai kuma ta sake juyawa wurin su tana fadin ga yar uwarku nan nasan baku santa ba diyar maimuna nane tadawo nan gurin mu da zama ke nan ita ma.
Kara sako min idanuwa sukayi suna kallona dayan tace a nan gidan itama zata zauna ke nan ?
Amma tace gashiko kin ji na fada maku dama ai itama yar gidan nan ce ba bare ba a binda yayiku shiyayi ta itama don haka ina son a zauna lafiya a tsakanin ku.
Suna wani ya mutsan baki tare da fadin mu may ye namu a ciki sai dai idan wa yancan dake kurin gidan su ne kullun.
Amma tace rabani da zancen su daku dai nan nake magana idan kanku yana hade wane su su kawo maku wanan iskancin.
Dayan ta koma ta kwanta ba tare da ta furta komai ba sai mu ke fira da Amman jefi jefi wanda ba wani hira bace ita dai ce mai tambayana labarin kakata ina dan bara amsa daya dace.
Mun dan dauki lokaci a gurin ta na kado kan yaran muka dawo part din mamu inda muka samay ta tana girki.
Ban zauna ba na nufi kitchen din gurin ta tare da tambayanta abinda zan kama

Please Login or Register in order to submit comment