You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin fara,a kamar yadda tayi min fara,a itama.
Ki zauna ga wuri sannun ku da zuwa tana ta jin dadin zuwan mu gidan nasu sai na samu kaina nima da jin dadi a raina sosai ba kamar yadda naji a gidan merry ba.
Sai gasu sun shigo falon shida maigidan matar ta kawo muna abinsha da ci ta aje a gaban mu aka kara sabon gaisuwa tsakani mu dasu .
Mijin ne ya kalli matar tashi yace ai sai ku shiga ciki kuyi halin ku na mata ko da kuka saba idan an hadu.
Tana dariya ta jani tana fadin taso kanwata mu basu guri sun kore mu da wayau ne kawai dai.
Wani dan karamin falo na kara gani ta nuna min kujera tace in zauna a kawo maki abinsha ne naga baki sha wancan dana kai maku ba matar tace.
No nagode na bata amsa dashi haba ki saki jikin nan kamar gida kika zo ai ban san dai yaya kuke da enginer ba amma ai aminin maigidanane sosai duk da kasan nan suka hadu amma suna amintaka sosai da junan su.
Yayanane na ba amsa dashi tace ikon Allah yayan ki na jini ko may nace eh gidan mu daya dashi karatu nazo yi nan ni.
Au wallahi har na fara muna ina zaton ko yayi aure ne ai ya rabu da wanan arniyar matar tasa daya aura nan.
In fada maki maigidana baiso auren su ba amma saboda nacewan wanan arniyar saida tasan yadda ta auri dan uwan nan naki.
Abu kamar aikin asiri tun wanan lokacin zumuncin su da maigidana yayi rauni suka rage arkalla da juna kamar farko.
Don matar bata son kowa ya mami mijinta daga ita sai yan uwan shi Allahne ma ya kwato shi har ya waiwaiyi gida daga bayan nan nasan karfin adduan iyayyene yai aiki a kasa.
Murmushi nayi kawai don jin abinda ta fada nace ai mu duk da muka taso bamu san yaya umar ba sai zuwan shi daya yan shekarun da suka wuce muna dai jin labarin sa kawai a gidan mu.
Gaskiya ba zaku sanshi ba kan don ina ga ai ko ashrin baki rufe bama ko ta fada tana kallona nidai dariyan kawai nayi mata ban bata amsa ba.
Hiran yanayin garin ta dauki min da al,adun su sai kewan gida da mutum kanji farkon zuwan shi idan bai ganin na gida a kusa dashi.
Har ta kai ga tambayana a gidan shi nake zaune nace a,a ina wani gidane dake kusa da school din mu don yafi mun kusa.
Tace sau daya nasa wancan gidan nasa muntafi ganin amarya a lokacin akace bata nan tana America ne da zama.
Naji dadin kasancewa a gidan Yusuf baba yola do matar tana da dadin hira sosai ban dai yarda na buga komai a gidan ba sai dare yaya yace in fito mu tafi.
Haka muka rabu da sunan watarana zan sake kawo masu ziyara a gidan da zan tafi taimin kyauta na bajinta da ba zan manta da shi ba don har da kayan abincin mu na gargaji ta bani da turare da sauran tarkace.
A waje muka samay su sai maigidan nata ke fadin to amarya munyi murna sosai da wanan auren ubangiji yasa wa aure albarka.
Kallon juna mukayi nida halima danace wa shi yayanane da farko tace wai kana nufin matarshi ce ita din yace wallahi ai Umar baya da kirki ashe aure ya kara har kusan shekara biyu ke nan bai fadawa kowa ba.
Sai yau yake fada min nima na sani tace amma yanzu take fada min shi din yayantane gidan su daya karatu tazo yi nan London.
Mungun yace ta fadi hakan ga kowa daya tambaye ta yaya suke umar ai yakai mugu wallahi.
Amma ko dana sani ai daba hakan ba dana baki tsaraban ma,aurata don ni ina samun su koda yaushe ana kawo mun.
Nifa ba mijina bane na fada ina daure fuska a matsayin yayana yake kuma kawuna na fada na bata rai.
Dariya naga miji da matar sun kwashe dashi tace ba laifi zamu kara haduwa da yardan Allah nan bada dadewa ba tunda har kunzo gidan mu muma muna nan kawo maku ziyara watarana.
Mukai sallama suna tsaye har motar mu ya daga ba wanda yai magana daga cikin mu har tsawon wani lokaci.
Na cika nayi fam har muka kai gida ba wanda yayi magana a cikin mu ina ganin street din mu na sauke ajiyan zuciya sai lokacin ya dan kalloni kadan ya kawar da kanshi.
Ban tsaya ya zagaya ya bude min ba nayi wuf na fito daga motar ina sauke ajiyan zuciya a fili na nufi hanyar shiga gidan sai dai key din gidan yana hannun shi dole na jira ya gama rufe motar ya nufo ya bude gidan zuwa lokacin kankara ya fara sauka a ginin gidaje da motoci yana rufewa .
Ban tsaya kallon wanan ba Allah Allah nake ya bude in shiga gidan don zuwa lokacin a matse nake sosai don fashin sallah da nakeyi lokacin.
Yana budewa har ina bugeshi wurin shiga na haura sama da sauri tare da bude dakina jakata na wurgar saman gado na nufi bandaki don kintsa kaina .
Ruwa na hada masu zafi da zasu isheni na dade a bayin ina gasa jikina kafin in fito rigar barci kawai na saka naje na rufe kofa na haye gadona.
Washegarima ban fito da wuriba don ban falka da wuri ba dana tashi kuma sai dana tsaya na kintsa jikina kafin in fito.
Abinda ban sani ba shine zuwan mu gidan abokin shi ba ziyara mukakai na Allah da Annabi ba shawara abinda zai fitar shi yaje nema gurin Yusuf yola din kamar yadda yake kiranshi.
Bayan sun sallame mu zuwa ciki ya dubi Umar din yace abokina lafiya kuwa na ganka haka ?
Umar yace ina cikin matsala abokina Yusuf yace subbahanallahi may ke faruwane haka duk yanayin ka ya nuna kana da matsala.
Nan ya kwashe yanayin zaman su da merry sauyawan ta gaba daya da komai yana fada mashi.
Yusuf din yace kaga abinda nake hango maka tun farko mutumina wa yan nan mutane ba abin yarda bane sam.
Yaya mazon SAW zai magana a kansu maganan ya tashi daga baya tun farko na fada maka auren wanan matar matsalane gare ka kana dan bahaushe musulmin asali kajawa kanka wanan nauyin.
Ansan idan mace tayi jahadi tsakani da Allah har ta yarda zata musulunta wanan baida illan komai kasan son tsakani da Allah take maka.
Amma ni yadda iyayyenta suka kafa sharudan su kai kuma ka yarda dashi kana ganin zaka iya juyata daga baya ne ?
Ba yau irin hakan ya fara faruwa ba muna gani wasu ma da farko zasu yarda su musulunta sai daga baya su koma akidarsu ta kiristanci don yaudara.
Wasu ko har bayan rai suna cikin islama ba zasu canza ba irin merry yana da wuya ta canza farat daya idan ka tsaya tun farko kayi nazarin waye ita din.
Yana da wuya merry ta iya canza addinin ta farat daya idan kayi la,akari da irin kungiyan su datake bi tun muna karatu.
Godiyana ga Allah shine da Allah ya kwato muna kai hankalin ka har ya koma gida tun lokacin nasan kana da rabo mai karfi.
Ai yadda ta biyo maka ta baya ta cuce ka haka kaima zakayi ka nuna mata namjin duniya kake na gaske.
Fita batun da yar insha Allahu yarinyar tana girma ita da kanta zata neme ka ai ya katse a bokin nashi da fadin Yusuf ina tsoron queen ta taso cikin addinin uwarta mai zurfi.
Don tun yanzu duk akidar yarinyar irin dabu,un su ne takeyi don merry bata yarda sam yarinyar ta mamay ni ko wani nawa takima fada mata komai a gamay dani.
Umar wai ka manta da rijejeniyar kune danasa ka saka cewa zaka iya kara aure aduk sanda ta sauya wani al,ada daga rijejeniyar ku.
Ban manta ba umar din ya bashi amsa sai dai ina tunanen sheri irin nasu do hakane kaga yanzu komai nawa yana zuwa gida ina kokarin ganin komai nawa ya koma gida ga baki daya.
Merry tasa da wanan shirin naka ya girgizawa Yusuf din kai yace bata san komai nawa ba tun farko don ban yarda da hakan ba ban shi harka sana,anta itama haka bata shiga nawa.
Kayi dabara Yusuf yace, yadan kada kafafuwan shi na dan lokaci yace da umar din da yai shiru yana tunane.
Umar ka tuna shekarun ka suna korawa fa a yanzu girma yana dada shigan mu ga al,adan mu da iyayyen mu suka koyar damu iyali shine alfari mutum koda yabar duniyar nan muddin kana da diya masu albarka tankar baka barta bane.
Sai nake ganin idan ka tsaya ka dogara da merry da yarta tankar kaida kanka ka dabawa cikin ka yukane ka kashe kanka.
Kowa yana alfarin zama waje ne na dan lokaci idan ka gama tara abinda kazo nema sai a koma gida ayi rayuwa cikin yan uwa da abokan arziki.
Yau idan haka ya kasance dakai umar damay zakai alfahari baka da mata bakaga yarka ko ta canza ra,ayi zata kara haihuwane yanzu.
Umar yace ba alaman hakan a tare da ita don kullun ikirarin ta queen ta ishe mu rayuwa do haihuwa akwai wahala ba zata yarda ta sake ba.
You see abinda nake hango maka ke nan tun farko abokina nu sai nake ganin ka kara aure kawai shine mafita gare ka hakan zai sa merry ta shiga hankakin ka in har tana son ka.
Aure kan ai na dade da karashi yacewa abikin nasa da sauri Yusuf ya dago kai yana kallon shi yace yes almost to two years ke nan ina da aure Yusuf.
Sai dai ban ba auren nawa wani muhinmanci ba sosai don aure da iyayye suka daura a bisa kaddara don karamar yarinyar nan daka gani yanzu matatace ita.
Saidai muna zuwa nan na canza akalan zancen ta koma yar uwata yanzu haka karatu takeyi a nan tun bayan zuwan mu na sakata a makaranta.
Tunda ya dauko chapter dina Yusuf din ya kura mai idanu yana kallon shi da mamaki sosai a fuskan shi sai da yaji yakai aya yace.
How comes Umar bansan wanan zancen ba yace laifinane abokina nan dai ya kwashe duk yadda auren ya kullu har irin zaman da yakeyi dani ya fada mai.
Yusuf yace lalai Umar kakai namijin gaske kana sa kamar wanan yarinyar a gida may zakayi da wata merry can data dade da shan ruwa tun baka aure ta ga daya sharrr.
Wai dakata umar kai baka tsoron Allah ya kamaka da wanan hakkin yarinya karama da kake tauyewa ?
Baka tsoron alhakin mahaifin ka yabika ko da akan yayan ka ko wani kaddaran ka ?
Umar ka tuba kaji tsoron Allah wanan alhakin yayi yawa ina zaka dashi shawarata ka rungumi matar ka hannu bibiyu kaida kanka zaka dawo ka bani labari.
Yusuf na fada ma matsalan da auren yarinyar nan ya jawo min nida mahaifiyata fa sunna ka raya fa umar ba zina kayo ba.
Yarinyar nan watarana abin alfahari ne a gare ka ta bangare da dama ka godewa Allah daya baka mahaifi mai hangen nesa.
Shiru umar yayi tun lokacin da yusuf ambaci tauye hakki gare shi don shi tausayina yake ji sai yake ganin ban isa aure va sai zuwa lokacin daya kare tsare tsaren shi kafin yasa mafita dani.
Sun dade suna tataunawa da abokin nasa mumuna ciki bamu sam anyi hakan ba muna can muna tamu hiran a ciki.

ZAINAB IDRIS MAKAAW
16/11/2021, 23:23 - 🤐🤐🤐: ASSALAMU ALAIKUM WARAHA MATULLAH YAN UWA MUSULMAI, , , , , ,

Idan nace Allah ya isa in kin karata baki biya ace akan novel ina jan Allah ya isa to yar uwa dake da kika fitar mun da novel da ke da kika karanta baki biya alkalin mu Allah na barki gare shi yar uwa.
Kuna raina kalman hada mutun da Allah alhali kun san Allah zai iya yafe maka laifin dake tsakanin ka dashi amma ba zaii yafe na tsakaninka da wani bawan sa ba mai hankali da imani kadai zaigane inda maganata yadosa nagode .
Koda na sauko karfe sha daya saura ba rana don haka banyi tsamanin yana gidan ba a lokacin tunda yarshi da matar suna asibiti nasan hankalin shi yana gurin su a nawa tunane ya tafi tunda safe baya gidan.
Kallon yadda gidan ya danyi mun kura na kwana biyu da bai samu gyara ba don tun kan in kwanta ciwon marin dana sha wanda yai min rabon da na tsaya na gyara gidan.
Na sauko ina bin gidan da kallo aikin gyaran gida na fara saida naga komai yayi yadda nake so na feshe ko ina da kamshi.
Sai na koma kitchen nan ma gyara na fara kafin in dora girki sai da na kusa gamawa naji kamshin turaren shi ya daki hancina hakan ya sanar da zuciyana yana gidan.
Don in tabbatar da zargina a kanshi na dan juya da zuman lekawa koshi din ne ya fito sai mukai arba dashi tsaye kofan kitchen din.
Ina kwana nace mai daga inda nake tsaye lafiya yace ya karaso cikin kitchen din zuwa wurin fridge ya dauki goran ruwa ya fita.
Sai a lokacin na dan sake zuciyana can naji shi yana bugun kofa da kankara ya taushe shi ta baya.
Ya samu kofan ya bude ya fita lokacin na fito kitchen da abinci na aje a saman dining naga ya kara shigowa bai ko kalli inda nake ba ya dauki wani abu naga ya fita.
Ashe kankarane ya rufe motar daga dare zuwa wanan lokaci shine ya dauki abin kawar da kankara da ake fesawa ya fita ya fesawa motar.
Zuwa lokacin na fahinci kamar fushi yake dani don haka nima na fita batun shi dama ba shiga nake ba sai idan ya sakani ciki.
Ya dan dade a wajen har na karya na koma dakina bai shigo ba naso inga ko harda abinci yake fushin da ban san dalilin shi ba tun barowa gidan Yusuf yola da mukayi.
Ko daya shigo ban falon hakan ya bashi daman zama yaci abincin daya gani aje saman dining din sai da yaji ya koshi.
Ranan dai motar da bai shiga ba ke nan sai jirgi yabi zuwa wurin queen ya dubata bai shiga wurin merry ba.
Ya fito ne a daidai lokacin da wasu kawayen merry suka shigo don duba jikin yarinyar dakuma yi mata addu,a.
Yafito ya barsu a dakin a zaton su gurin merry ya nufa saida suka gama da da yarinyar suka nufo dakin da merry take .
Bayan sun gama abinda sukeyi ne suke tambayan ina mijin ta tace baishigo ba yau itama shi take jira don likita yana son ya sallamay ta yace sai sunga mijin ta.
Da mamaki suke kallon juna su kafin guda yayi karfin halin fadin yanzu yabar dakin da Faith take kwance mun dauka yana nan ne gurin ki muyi maku addua a tare.
Fuska ta bata don bataji dadin jin hakan ba daga gare su don suna cikin masu adawan auren ta dashi don dai church din su dayane an kuma taso tare yasa bata rabu dasu ba suma dai black American ne a can aka haifesu sai dai su suna ban addinin su sosai irin sisters din nan ne su.
Ya tafi gurin likitane ina gani ta basu amsa da hakan don kawai kada su zargi komai a zuciyar su.
Fitan su ta mike zaune don dama taji sauki sallama kawai take jira don sai ya saka hannu za a yarda a sallamay ta saboda case din su har yanzu ba akare ba.
Ga iyayyenta basu zo ba don yau sun makara saboda matsalan snow da aka tashi dashi sosai a kasan mutame basu faye wani zirga zirga ba.
Amma wa yan nan yan tsaurin addinin haka suke bi cikin wanan yanayin suna wa mutane addua don kada a sake hanya abi wani addini na daban.
Karshe dai dole saida merry ta jira zuwan iyayyenta don su sukai komai har saka hannu akan zata kai kanta police station.
Sai dai ita Faith har lokacin ba,a bata sallama ba don yarinyar tafi jin rauni a jikin ta saboda koda abin ya faru tana gaban mota ita da uwar a lokacin.
Matsala shine don suna a cikin maye sukai tukin ganganci wanda hakan doka ne na kasan London din.
Sai dai duk abinda ake ita merry hankalinta yana ga mijin ta da bata san dalilin rashin zuwan ta ba sai dai ko maynene yana da nasaba da dan matsalan da suka samu ranan a asibiti dashi harda iyayyen ta da suka so saka baki a cikin case din lokacin.
Wanan abin yayi matukar bata mamaki da haushin yadda ya share su din saidai abin mamakin dataji gun yarsu shine kullun uban na zuwa ya duba yarshi asibiti haduwa ne kawai basuyi dashi.
Gashi tayi neman layin shi har ta gaji ance baya shiga duk lokacin da ta kira layin nasa din.
Haka yasa ta kulle shi a rai sosai tasan duk zai gama fushin ne ya dawo ya nemay ta ko ya samy ta a can garin da take aikin ta din.
A nawa bangaren kuwa zaman doya da manja muke a gidan daga gaisu sai kuma gobe in mun gaisa din sai dai bai fasa cin abincin da nake sakawa dashi ba ko yaushe .
Watara sai dare yake fita ban sanin dawowan shi watarana kuma tun safe idan ya fita sai yamma yake dawowa gida.
Gashi zaman shi a nan ya bala,in takurawa rayuta sosai don banda halin leka ko waje kamar yadda nayi mai alkawarin yi din kafin in dawo gidan.
Har Allah ya nuna mun koma makaranta muna cikin wanan halin dashi hakan ba karamin dadi yai min ba don ina haduwa da abokai a can ina dan rage miyau na.
Ranan na dawo na samu takarda saman dining ya aje min cewa zaiyi tafiya sai ya dawo bai fada min inda zai tafi ba nima kuma ban damu da in sani ba.
Zaune yake a cikin jirgin da zai kaisu kasan Malaysia a hankali ya runtse idanuwan shi ba abinda ke yawan fado mai a rai sai irin karfin halin wanan yarinyar da yakewa daukan yar kankanuwar yarinyar amma sai wayau da hali irin na manyan mata a tare da ita.
Zarah ya furta a hankali shi kadai yake magana kamar zarare ya dan sake murmushi a fili tare da mayar da kanshi saman kujera ya lumshe idanun shi.
Taso yin kamanni da uwarta maimuna sai dai ta dara uwar da abubuwa da dama yanzu ko ta halaiyan su yasha bamban.
Yasan zarah yarinya ce mai hazaka da kokari don yawan bibiyan karatun na da yakeyi ba tare dana sani ba.
Ga komai tanayin shi a bisa gaskiya da koyi da addini da abinda iyayye suka koyar da ita a gida.
Ya kula yarinyar batada kyashi ko hassada a rayuwan ta don da watace da yanzu ya fara gani ko ji akan irin zaman da sukeyi zata iya samun shi makale da merry a jikin shi amma bata taba nuna bacin ranta ba.
Yasan da ace merry ce da wani fitina ya afku yanzu don da kowa ya gama jinsu ko.
Zarah tana da kunya da kamun kai don bai taba ganin wani shiga a wurinta na asha ba tun zuwan su nan ko a gida ya kulatafi saura kula da kama jiki a gidan su.
Ya kula yarinyar bata da yawan magana amma akwai bakar magana da manyan magana a bakin ta batare da kiyas tawa ba.
Ya lumshe ido tare da fadin yarinya karama da halin manya nisan tunane da sanin ya kamata ga babba saboda irin biyayyan dokan daya sa kuma tabi.
Ya kara mayar da kai yana fadi a ranshi yarinyar tana da saukin kai da saurin shiga mutane ko shine yasa take saurin samun sabbin abokai a nan wanda ya hana mata hakan.
Tana da saurin shiga zuciya duk wanda ya ganta don ladabin ta ga gaisuwa dole jama,a su so zarah don ita din kyakyawace mai kyawon hali.
Ido a lumshe yace zarah kedin kyakyawace kina da duk wani abinda da namiji yake bukata gun mace musanman wanan idanun irin na uwarki har sunfi na uwarki dara dara ga yawan lumshesun da takeyi musanman idan tana cikin hushi hakan yana kara burgeshi da shiga ranshi.
Kai ya girgiza yace ke komai kin iya karamar alhaki dake zarah tafiya kamar wace take tsoron kasa a cikin natsuwa komai sauri take takon ta.
Raban da bata da lafiya yaga gashin kanta ya dauka kari tayi amma daya fahinci nata ne saida yaji tsoron yawan gashin kan nata saidai baya samun gyara yadda ya dace shiyasa
Wanan kuma yasan laifin shine da bsya bata kulawan daya dace ta samu daga guri shi.
Astangafurullah ya furta da sauri tare da fadin Umar may kakeyi hakan wani nauyi ka daukanwa kanka haka ?
Ka kawo yar mutane nan bisa amana ka watsarda ita tana rayuwa a cikin kunci da kadai duk ta dalilin shi.
Saboda tsoron ya lalatawa yarinyar mutane rayuwa ya keyin hakan don kawai shida ita su kaucewa furcin mahaifiyar shi ya dannewa yarinyar mutane hakkin ta haka.
Gaskiyan Aliyu dayace dashi ranan da mahaifin su ya fahinci hakan da wani ido zai kalli mahaifin nasu dashi.
Zaiji kunya matuka yasani don ko Amma fushi sosai zatayi dashi yan gidan su dama wasu mutanen zasu dauka tsoron matar shi merry ne a zuciyar shi.
Wani irin daci da bacin rai ya ziyarci zuciyar shi lokaci guda bai sake bude idanun shi ba sai lokacin da yaji mai sanarwan jirgin na fadin sun iso kasar malasia jirgi zai sauka kowa ya shirya.
Washe gari ya kama weekend ban fita ko ina ba sai zagewa sosai danayi na gyara gida na tsabba na wanke kayana da duk wani abindake bukatan wanki a gidan.
Har dakin yaya ban barshi hakana ba dukda fushin da yakeyi dani kafi ya tafi tafiyan dayayi.
Na gama nayi wanka na dawo falo dauke da littafin kawa,idina ina karantawa.
Bell din gidan yayi kara ina mamaki waye zaizo min da wanan ranan anty farida ne da dukkan yan gidan su akofan da murna na tare su ina fadin kushigo babana sannun ku da zuwa.
Tace yau dai gaki ga baban

Please Login or Register in order to submit comment