You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a ciki ba shima ya shigo suna gaisawa tare da tambayan yadda take jin jikin nata yanzu.
Hjy bata kai ga bashi amsa ba muryan hjy sabuwa ya katsesu tana fadin ina mara kunyar yake yana ganin yanzu yafi karfin mutane don ya samu daurin gindi a wurin iyayyen shi yasa kake son taka kowa yadda kakeso.
Har kan wanan yarinyar kake kokarin wullakanta yar uwan ka ka fifita agaolan gidan ku da aka cinna maku da sunan mowan gidan ka komay ?
Hjy kin ban mamaki kina gidan nan har umar ya tsaya yana fadin wanan magana ga yar uwan shi baki kwabe shi ba tana fada ra sawo kai dakin sai taja ta tsaya don ganin mu da tayi a dakin don bata zaci hakan ba a lokacin.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:23 - 🤐🤐🤐: Shiru dakin yayi ana sauraron abinda hjy sabuwa da ta fado dakin babu ko sallama take fadin magana iya son ranta.
Babu wanda yai mata magana daga cikin wa yanda ta sama a dakin ita da kanta taji nauyi da kunyan kanta lokaci guda sai kuma ta fara dan kame kamen zancen.
Ina gida yanzu wanan yar ta kirani take sheda min wai umar ya ci mata mutunci tunda safen nan akan matar shi.
Shine ya mike tsam daga inda yake zaune ya nufi hanyar fita daga dakin ba tare da yama tsaya sun gaisa da ita ba.
Fita zakayi ne mama Asabe take tambayan shi bai juyo ba yake bata amsa da fadin ina da abin yi ne yanzu.
Amma kasan wurin ka nazo aiko don kaji abinda ya kawo ni gidan nan yanzu ai.
Juyowa yayi da mamaki a fuskanshi yake fadin wai dani kike magana hjy ?
Itama kallon mamaki take mai don babu alaman wasa ko girmamawa a gareta ko kadan a fuskan shi.
Eh matar kace takai karan ka gareni nazo jin dalilin faruwan hakan don zancen mata ba a san namiji da daukan bangare daya ba.
Har kana fadin wani zance dani kaina na kasa fahintar may hakan ke nufi a zuciyana.
Matata fa kika ce hjy ki dai ce yarki dake zama a gidan nan ko zaifi sauki matata kan ai ga daya nan a gaban ki yanzu kina ganin ta.
Ke zahra ko kece kika kai kara a wurin tane don ban fahinci zancen nata ba har yanzu gaskiya.
Eh lalai kana da gaskiyan ka don ba laifin ka bane idan kayi hakan a yanzu saboda alama ya nuna baka cikin hayacin ka gaskiya.
Zaki iya fadin hakan tunda yarki na son ta lalata min gida da fitina don kawai taga tana cin albarkacin wani a wurina.
Saidai ina son ki fada mata cewa zaman ta a gidan nan yana gab da karewa idan bata fita harkan iyalina ba.
Don ba zan lamunci a wullakanta min matana da yayana ba ko kadan a zauna lafiya ko yanzu taci albarkacin mahaifiyata ce da take zama gidan nan donta.
Koda yake ku din baku sanda hakan ba tunda ko ita sin bataci ragowa a wurin ku ba sai kokarin nakasa muna ita da kukeyi ba dan Allah ya gyara zancen ba.
Jummai kina jin abinda danki ke fada mi a gaban ki baki yi yunkurin hana shi fada min wanan maganganun da yake fada min ba.
Ashe taimako yana iya komawa tsiya kefa da kanki kika bukaci hada wanan alakan don a ceto maki danki daga hannun wanan matar tasa da kika tsana.
Sai haihuwan da take zubawa a gidan don ta mallake dukiyan shi ita da uwarta da wasu can daban da baki son hakan ya faru dashi.
Ashe kin san bakifi karfin daki bama tukun balle matar tashi da alama ya nuna duk ta gama dake da diyan nakima.
Ai ashe don ni kika dauko yarki kika kawo ta gidan nan ban sani ba don ni bansan ma da wata aba bacan dana nazo wai matar mijina don banga alaman hakan ba a gidan.
Ke fitsarara kada ki soma kawo min rashin kunyar ki da ake fadan kina dashi nan don gida kika sama na rashin mutunci.
Sabuwa dama kece daidai dani ba yarki ba don haka yanzu ki kauda yarki kizo ki share daki mu zauna dake sai mu kara ina ganin haka zai fi don kece daidai dani wurin daukan fansa ba lusarar yar nan da kika aje muna a gida ba kamar ba mace ba don ko gaba na mata bata dashi.
Kutumar uban nan har iskancin naki yakai ki kalli tsaba idona ki fada min haka kwarai kuwa tunda ke baki ji kunyar fada mi magana irin haka a gabana ba.
Aiko ta kara tasowa tana kokarin kaiwa gareni da sauri yaya yace hjy muddin hannun ki ya kai a jikin matana wallahi sai na daure ki a garin nan karyan masifa kikeyi ana kyaleki ne dama.
Muryan hjyn su yayane data fashe da wani irin kuka lokaci guda a dakin ya mayar da hankalun kowa a wurinta .
A daidai lokacin samira ta fado dakin tana fadin wallahi babu mai wullakanta min uwa ya zauna lafiya a cikin ku.
Don uwa bata fi uwa ba ehhe ki daina kukan munafunci ki tsaya a gyara zance zaki sakawa mutane kukan munafunci don zancen ya tsaya a, , , ,
Saukan mari da tajine a fuskanta har biyu lokaci guda ya hana ta karasa maganan da take son fada.
Yaya ne da take tsamanin ya bar dakin yaga shigan ta ya dawo a daidai lokacin da take wanan magana ga mahaifiyar su.
Hanyar fita ya nuna mata ita da uwar yace ku fice min daga gida yanzu nan ba sai an jima ba har hjy sabuwa zatai magana ya kara daka mata tsawa saida ta firgice don tsoro.
Mai hakkuri ance ranshi bai iya baci ba don yau kan ko mahaifiyar shi ta sheda hakan don bai ragawa hjy sabuwa ba ko kadan ranan tsaye yayi yana umartan yan aikin shi da su tabbatar basu kara shigo mai gida ba.
Sai kuma ga hjy sabuwa ta zube a kasa tana rokon shi ya rufa mata asiri ya dubi zumuncin su ya bar samira a dakin ta.
Zumunci zumunci fa kika ce hjy ko kin manta ke da bakin ki kika fada babu wani zumunci a tsakanin ku sai na zaman unguwa daya dasu mama.
Yanzu hat zaki kira min wani kalman zumunta a tsakanin mu dama talala na sake maku don inga iya gudun ku saboda albarkacin mahaifiyata da kukaci na bar yarki a gidana tana zama.
Yanzu ko kun kaini bango ta yadda ban kaunar kara ganin kowan ku a gidan nan .
Dama ance yar mace bata taba zama mace ta gari do gashi kin nuna min baki san darajan iyayyen wasu ba balle naki .
Kun duke ta kuna ganin kamar kun daki banza ba wani matakin da za, a iya dauka a kanku do kawai an maku dubaiyan da baku san ana maku ba sai gashi kuma har zaku maimaita hakan a gaba gun matana a yanzu.
Kin dauka idan idon mama ya rufe da abinda kuke dura mata nawa dana yan uwana zai rufene hjy.
Da har zaki dauko yar ki mai ciwo ki kawo min har gidana wai da sunan aure watau duk mu taru mu halaka bayan ta gama halakanta da taimakon ki.
Baki hjy ta bude tare da fadin sheri kuma zakai muna umar don kaga muna rokonka ko may ?
Habbib dake tsaye tare da iyalinshi dana Aliyu yace eh ai dole ki roke shi kan cuta azzaluman mata mun dade da sanin komai kyale ki mukayi muga iya gudun ki gidan nan ai.
Ko kin dauka idanuwan mu muma a rufe yake kamar yadda kuka rufewa mama gaskiyan abinda ke damun yarki taki aurowa a lagos din.
Shine do cuta zaki kwaso sheri ki haro dan uwan mu dashi har gida wai da sunan kin taimaki mahaifiyat mu da yarki.
Hjy dake wani kukan takaici da bakin ciki a zaune ta wani dafe kirji da karfi tana fadin na shiga uku dama yar nan bata da lafiya ashe sabuwa kika rufe min.
Abin nasu kamar hadin baki don sai jin muryan yan uwan haihuwan hjyn su yaya mukayi suna fadin dama ai saida muka fada maki bakiji ba hjy a lokacin .
Yanzu ba don Allah ya gyara ba da kin cuci zurian ki da kanki anty wanan maganan nake fada maki a kullun kuke gabin zafina a cikin mu.
Akan wani ra,ayi naki can na banza zaki cutar da rayuwan yaran nan ki halaka mashi zuria irin wanan ranan ake gudu dama ranan nadama ga bawa.
Godiya mu ga Allah a kullun da yake kawo muna dauki akan komai kafin wani abin ki yakai ga samun mu.
Yanzu gashi kin biyewa hjy sabuwa har auren ki na shekara da shekaru yakai ga samun tangarda wanan son zuciya dame yai kama haka don Allah ?
Gida duk ya kidime da yayan mutane shikan yaya yana gama magana da hjy sabuwa tun lokacin ya juya ya shiga part din shi ya rufo.
Haka nima naja kafa zuwa part din mu yarana na samu zaune a falon maria ta hadesu a guri daya suna kallo.
Zama nayi a cikin su a daidai lokacin da su Aisha da Rukkaiya suka karaso ina masu sannu da zuwa.
A cikin alaman mamaki suka karba min tare da fadin wanan abin mamakin dame yai kama hakane wai ?
Rukkaiya tace mu dai gamu muda ba,a so din dai mune na kwarai a yanzu ai don da bakin suke magana akan irin taimakon da kike mata a yanzu .
Koma dai meye ai naka sai naka ba don Allah ya gyara yaya yana da natsuwa ba da yanzu ya dade da kwasan wanan cutar ko tunda auren nasu ai yakai wata biyu ko uku yanzu tana gidan nan zaune.
Wana ma wani iri rashin zuciyane ace mutum ya nace kan abu idan ba yasan cutar da yake son yi ba a gurin.
Ni wanan zancen ma gaba daya duk ya kashe min jiki wallahi wai mutane mai yasa basu da imani ne yanzu Aisha ke fadi.
Sai yanzu nai magana tun zaman su wurin ina fadin rayuwa haka take zuwa da kalubali mai tarin yawa ga bawa sai idan Allah kareshi a cikin ikon shi sai ya kawo mashi komai da sauki .
Abinda hjy take nuna min da farko ne nake jin zafin hakan amma yanzu na daina rikon abin a raina ko kadan don dai jini ya riga da ya gauraye da ruwa.
Don ko yanzu na bar gidan nan sunana ba zai taba kankaruwa a cikin zurian dakin hjy ba dole sai ance nice uwar yaran nan jikokin ta.
Kwarai kuwa Rukaiya tace dole ne kan a fadi hakan dan ma hjy ta godewa Allah rabon yaran nan bai kasheta ba yara kusan nawa ta nuna bata kaunar auren iyayyen su da diyanta.
Allah ya riga daya tsago sai zurian dakin ta sun fito daga jikin mu ai dan ni kiri kiri hjy ta kira sunan uwana ta hada dana ubana ta zagesu tas a gabana wallahi.
Wanan idan ba kakai zuciya nesa ba kina ganin mai zai faru a wurin saukin abin ma yaran nata basu dauki wanan halin nata ba a ran su da ai zumunci ta dade da lalacewa ko a family mu.
Gulman me kuke yi haka kuka kashe murya haka don da gani zaman gulma kuke a nan muryan yaya habbib ne yake fada muna haka .
Juyowa mukayi muna kallon shi da dan murmushi a fuskan ko wacen mu sai matar shi ke fadin kai yaya mu hiran abinda ya faru mukeyi ba gulma ba.
Kun gaisa da hjy ne da kuka zo nan kuka zauna ya fada yana tsare mu da idanuwa ma,ana umurni yake basu a lokacin.
Dakin ne baida dadin shiga yanzu yaya ana cikin wanan tashin hankalin haka yasa bamu shiga ba sai dan zuwa anjima idan an rage yawa.
Yadda ya juya yasa ta fadin Aisha tashi mu dubata kada muma namu ya same mu yanzu a gurin shi.
Ni dai ina jin su suna mikewa na mike nabi bayan su zuwa dakin da hjyn ke ciki duk da muna jin hayaniyar yan uwanta a dakin.
Mun samu har su salma sun shigo don labarin abinda ya faru da safen ya isa kunnen yan uwa sai zuwa gidan suke don jin ba,asin zancen.
Sallaman mu ya dawo da hankalin su kofan dakin muka shigo mu uku muna gaida su mama Asabe take fadin au a tare kuke da maigidan ashe ?
Tare muke mama Rukaiya ta fada tana neman wurin da zata tsuguna a dakin don ba wani fili a dakin don tarkacen hjy dake dakin yanzu.
Sun gaida hjy tana amsa masi cikin yanayin rashin dadin zuciyan da take a lokacin take tambaya da ina yaran suka barsu ne ?
Aisha tace suna gida wurin mama muka barsu da zamu zo mun biya can suka ce zasu tsaya a nan da cewa gidan kawu ke nan.
A dan dakile ta amsa don jin abinda Aisha ta fada din da alaman hakan bai mata dadi ba kasan ranta.
Fatima sannu da kokari fa muna ta jin kokarin da kikeyi da jikin hjy wurin asabe Allah ya saka da alheri ya baku masu rama maku hakan.
Dakin ne ya amsa da amin ina fadin hjy dazun ko kin sha wanan maganin dana hada sai mama asabene tace .
Ina fa yan nan ta dauko ke nan zata sha wanan bala,in yazo muna tunda safen nan ai sabuwa batayi ba wallahi.
Don Allah Asabe ku daina ganin laifin su nifa har gobe inda gaskiya yake nake fada sam sabuwa wuri ta samu a nan .
Allah dai ya kare komai bai kai ga faruwa ba a tsakanin su amma mama komai gaskiya ai hjy sabuwa tafi mama laifin don ta boye mata gaskiyan halin da yarta ke ciki don cuta da zalunci kawai salma ke fada.
Magani na hada na kara bawa mama Asabe don taba hjy din a wanan lokacin na fita zuwa dakin yaya don na samu yaya habbib shi kadai a zaune falon shi bai fito ba.
Dakin na tura na shiga da sallama na hango shi kwance yana rigingine fuskan shi yana kallon saman dakin.
Dan juyowa yayi ya kalli kofan kafin ya kawar da kai ya koma a yadda yake da farko na karaso ina fadin yaya ka kwanta kabar yaya habbib a falon shi kadai zaune.
Yana gidan nan ne har yanzu ya tambaya har lokacin kamar bason mu hada idanuwa dashi ne.
Zama nayi a gefen shi ina fadin lafiya na gabka haka yaya ina tambaya tare da kallon shi a yadda yake din kwance.
Yace da kyat No ba komai sai yai shiru nima dai shirun nayi na dan lokacin kafin yace Zahra na amsa da na,am ina kallin shi.
Kada ki dauki wanan abin daya faru da zafi kice zaki rike shi a ranki don Allah .
Da sauri nace haba yaya a kan me zan dauki wanan zancen da zafi bayan Allah ya karemu daga sherin hjy da yarta.
Hannu ya daga min yana mikewa daga kwancen yake fadin nasan kalaman hjy sabuwa da mama ta fada a kanki suna da zafi sosai.
Don haka nake rokon ki kan kiyi hakkuri da duk abinda hjy tayi maki kada kice zaki dauki wanan abinda zafi a ranki.
Yanzu bada bane yaya hjy nasan uwatake a gareni kuma sarakuwata don haka don mahaifiya taiwa yarta abu saita dauki zafi da ita.
Ajiyan zuciya naji ya sauke mai dan sauti yana fadin idan kin min hakan kin kyauta min matuka kuma ina alfahari dake akoda yaushe don nasan daddy bai min zaben tumun dare ba.
Ko nace ina dan kallon shi ina murshi yace kinfi kowa sanin wanan hadin namu ai daga Allah yake kawun ki idda sunna yayi kawai .
Au goron da zaka ba kawu a yanzu ke nan yace gaskiya na fada yana kokari tashi tsaye ta hanyar dafani ya mike tsaye.
A tare muka fito dakin har lokacin yaya habbib yana gurin zaune wanan katon tare da yaran yake fira jin fitowan mu yasa ya dago kai yana kallon mu.
17/11/2021, 07:26 - 🤐🤐🤐: Sun dade tare a falon bansan may suke zance a kai ba don ina daki tare dasu Aisha muna hira inda suke ban hiran abubuwan da hjy take yi masu na rashin dacewa gare su.
Ban furta komai ba sai kara kwantar masu da hankali a kanta kamar yadda nima mamu take yawan yi min nasiha da kada na nuna abun yana damuna don dan ta bazai ji dadin hakan ba idan na nuna.
Rukkaiya kan cewa take ita kan gaskiya ba zata iya shanye wani abu a ranta ba don da gangan ake maka cin fuska don kawai danta yana auren ka sai ka zama abin ki ga mutum ?
Sai bayan la,asar yaya habbib ya bugo waya yana fadawa matar shi ga driver nan a waje yana jiran su don yaran sun fara damuwa lokacin.
Sai da suka shirya sun dadauki abinda suke so a dakin nawa ban hanasu don sun nuna ra,ayi akan abina nasan Allah zai musaya min da wanda ya fishi idan na basu da zuciya daya.
Muka fito zuwa dakin hjy don su sallameta a zaune take lokacin tana shan ferfesun kaysn cikin rago.
Nafisa tana tsaye a kanta da ruwa rike a hannun ta tana bata jin sallaman mu shigowa yasa suka mayar da hankalin su gare mu.
Mun mata yaya jiki yayinda take dan dago kai tans fadin ashe kuna gidan nan har yanzu eh yanzu zamu koma don yaran nacan su damu mu dawo.
Ke nan ba za,a kawo su su ganin basu ko don kuna gudana da yayan ko hjy ta fada tana kai cibin da take shan ruwan miyan a bakin ta.
Can muka fara zuwa gaida daddy shine suka lekawa mama don sun saba da ita yasa muka barsu can tare da ita don lokacin an bugo waya ana wanan fitinan da safe.
Na fahinci may Rukkaiya take nufi yasa nayi saurin fadin hjy Nafisa ashe kin shigo ban sani ba ?
Tace ummm ke dai fatima na shigo dazun bayan azahar da nake jin abinda wayan nan marasa mutuncin sukayi yau .
Don ni ina kuryan Amma ina barci banji me ke faruwa ba sai dana tashi Amma ke labarta min hakan.
Wallahi naso na shigo a lokacin da yau sun kara raina kansu wallahi don wana karon ba zan kyalesu ba Allah.
Umm tashi mu tafi Rukkaiya tace tana hararan gefen da Nafisa din take .
Jin hakan nace Nafisa ke nan wa yan nan ai sai irin su yan duniya don babu mutunci a tare dasu ko kadan.
Na fahinci babu shiri a tsakanun su da samira do haka nake kokarin a rabu lafiya a dakin don yanzu sam bansan me yasa bana son tashin hankali ba ni.
Ganin sun fara fita daga dakin yasa nace barin dawo Nafisa in baki labari ta amsa da ai ina nan don kilama a gidan nan zan kwana yau.
Nace kice dai yau mune da bakuwa a gidan nan ashe mara masu Aisha baya nayi ina fadin sai yaushe kuma zan ganku ?
Muna nan ai tunda an kawo mu jiya ne don haka sai kin gaji da ganin mu har bakin mota na raka su suka tafi ni kuma na koma ciki.
Dakin nayi niyar shiga zancen dana sama sunayi ya hanani shiga dakin Nafisa ce ke fadin ai nasha fada maki wallahi fatima tafi su kirki dan dama Aisha don ita bata fitowa fili ta tsulawa mutum tsiya kai tsaye.
Uhumm ni kaina canzawan yarinyar nan yana ban mamaki don da farko na dauka makircin sune take min don mijin nata ya gani.
Amma yanzu na fara sarewa da al,amarinta don yadda akai wanan maganan sabuwa ta tona min asirin duk abinda mukayi tare da ita amma bata canza min fuska ba saima goyon bayana da tayi a gurin.
Jin hakan yasa na fasa shiga dakin naja kafana nabar kofan dakin zuwa part din mu zuciyana cike da tunanen maganan nasu.
Lalai mamu tayi gaskiya da take fadin duk abinda zataiwa hjy bazata taba son mu a ranta ba don kiyayyan mu ya riga da ya shiga ranta ko mai kankare shi sai Allah.
Tunanen ba zai kare ba na tashi zuwa gun maria don ganin halin da suke ciki don yinin ranan na barta da yaran tana dawainiya dasu.
Na sameta tana goye da babana da yai barci a bayanta sai sultana da take shiryawa don fauziya tana bayi tanawa yaran wanka lokacin saboda yamma dayayi.
Har zuwa lokacin da yaya ya dawo gida baya cikin walwala tare dashi na fahunci hakan ne ta hanyan rashin cin abincin dare da baiyi ba sai ruwan shayin daya sha ya kwanta a lokacin.
Ban matsa da tambayan shi haka nazo na kwanta na tashi don da safe ma muryan shine a inda yake karatun kur,ani ya tayar dani .
Kallon shi nake da mamaki da bai tayar dani inyi sallah ba a ranan haka kuma banji lokacin da akai sallah asuba ba a ranan .
Ki tashi kiyi sallah lokaci yana kurewa sanyin ruwan sama ya hanaki tashi kiyi sallah akan lokaci.
Ban iya magana ba lokacin don raina da nake jin babu dadi saboda rasa sallah asuba danayi a ranan.
Ban tsaya dakin ba fita nayi zuwa dakina na shiga bandaki kodana idar da sallah ban daga ba wurin ina zaune sai faman tunanen rayuwa nake a raina.
Merry ce ta fado min a rai tausayin ta ya kamani don raba da da mahaifi sai Allah nasan kuma wucen merry ta bar queen a kasan nan bawai ta bar zancen bane.
Saidai matakin da zata dauka ne ban san yadda zasu kaya karshe ita da mijin nata ba a karshe.
Mikewa nayi don jin ruwa ya kara saukowa a lokacin hakan yasani fita daga dakin zuwa wurin maria don in duba halin da suke ciki.
A daki na same su bata yarda tabar yaran sun fito koda falo ba don ruwan da ake shekawa a safiyan .
Tana ganina

Please Login or Register in order to submit comment