You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

baya a duniya ya fifita dan wani.
Shiru tayi badon ta yarda da zancen yar nata ba taci gaba da kada kafa Allah kadai yasan irin tunanen da takeyi a ranta.
Wayan ta dake gefe ne yayi kara ta kasa kallon wayan balle ta daga sai sadiyace tace mama wayan ki na kira fa ta juya ta kalli wayan a lalace tana duban sunan dake kiran wayan.
Gani hjy babba a screen din wayan ta fisgi wayan da sauri hannun sadiya tana receiving.
Tana dauka hjy jummai tace maryam kin ban mamaki koda yake ba abin mamaki bane don kishiya tayi farin cikin barin kishiya gidan miji.
Ace wai maryam baki kirani ba tun da nazo nan ke nan kins farin ciki da barina gidan kema dama nasan zakuyi murna na matsa na baku wuri kuyi yadda kuke so a gidan.
Haba yaya wanan abin fa bulalan hanyane fyadi yaro fyedi babba Alh yai muna bake kadai ke cikin wanan hali ba don kowa a gidan nan an fyede shi.
Haka dai nake ji daga baya wai har Ikilima ashe a cikin auren ita kuma wani dan kaddaran ya ba ita don duk wanda ya karbi auren yaran mu akan ganganci ne sai ya sako muna diyan mu.
Daga kai tayi ta kalli yarta dake tsaye suna kallon ta tace uhumm sadiq dai na shagon kware da kika sani.
Hjy tace sadiq sadiq dai wanan miskilin yaron da bai damu da mutane wanan yaron dan jin kai da fadi rai ?
Wallahi shi kuwa yaya shi ya hadata dashi yayi son ranshi ga yaran mu kamar bashi ya haifi abinshi ba.
Amma ita yar son agolan shi ya hadata da danshi inda yasan zata huta yanzun haka mun dawo daga rakiyan sune sun tafi kin san yau suka bar kasan ai.
Wa ya bar kasan kike nufi tace su umar da yar nake nufi mana .
Wai kina nufin dai babawo nawa kowa hjy maryam tace wai baki san da tafiyan su bane ko may cab ai sukan yanzu hakama jirgin su ya daga yabar kasan nan watakila.
Dif taji ta kashe waya bata kara kallon wayan ba ta wurga gefen kujera tana cewa yannen ta ashe uwar ma bata san da tafiyan su yau ba ke nan ?
Ni dai ina horon ki da kikama bakin ki mijin ku kin san yayi kokarin kan yaran nan don ba duka maza zasu tsare maka haka ba maryam.
In kinyi duba mutumin nan fa gata yayiwa yaran shi a fakaice a yanzu baku gane hakan gare ku sai nan gaba halin dattakone iri na mutanen da kega maigidan ku wanda mutanen yanzu ke ganin shi wani abu na daban.
Uba ko ince iyayye sukeda hakkin zabawa diyan su abokan rayuwa na gari amma boko da zamani ya sauya muna al,adan hakan.
Inda ada can baya ne ko kaka yana iyayiwa jikokin shi hakan ko wani daga cikin yan uwan shi yai bugun gaba ya aiwatar da hakan kuma a zauna lafiya babu mai korafi kan hakan.
Amma yanzu shida abinshi kuna son nuna mai ba isa da kayan shi ba shi kuma ya nuna maku ya isa da gidan shi.
Kuma yayi dacen samun diya na gari daga mazan har matan ba wanda ya musa mai kan hakan.
Har ita agolan nashi da kuke ganin yaiwa gata kunsan yanayin da uwarta take ji ne kan hakan babu wata uwa a zamanin nan da za ai mata haka da yarta taso a ranta.
Amma da yake tanada wayau bata nuna hakan yai mata zafi ba ta dake ta daure rabar abin a ranta kinga kenan darajanta saiya hauhafa a gare shi.
Shine kema nake nuna maki hakan don ba karamin daraja zakuyi a idon shi ba ya sakaku kun bi umurnin shi.
Yanzu ita hjy data bijire masa mai hakan ya haifar gareta gashi anyi din kuma bata gidan ita da kanta ta dabama cikin ta yuka duniya sukaji ta.
Da tabishi a sannu sai ayi abin salin alim ba wanda yasan abinda dake gudana a tsakanin su amma yanzu mai hakan ya haifar a gareta ?
Danka har yabar kasa da matarshi ke uwa baki da labarin hakan yanzu ai duk inda take wanan labarin tafiyan da taji tana can hankali a tashe.
Don haka ki natsu kiwa kanki fada tun baki barar da darajan ki da yake gani a idon shi ba har wani dadi kikaji wurinta da zata wani neme shiri dake don kawai ta dinga jin sirin gidan a bakin ki.
Idan magana ya fito kiji kunya ya dauka kina ha,intar shine da iyalin shi kece ke kawo rashin zaman lafiya gidan tunda keke tsegunta mata komai.
Sauran sukace wallahi hakan ne zai faru shiru tayi tana nazarin maganan da suke fada mata.

Hjy jummai tana jin abinda hjy maryam tace ta kashe wayan zabura tayi zuwa falo suka hadu da yayan ta yake fadin lafiya dai maryam tace yaya ni yaran nan zasuyiwa haka ?
Sai ta fashe da kuka ta kasa magana hakan yayi daidai da shigowan su hjy rabi a lokacin don nasu iya zama a gidajen su saboda abinda suke kullawa a tsakanin su na ala dole sai sin raba aurarakin nan don manufan su ya cika.
Da mamaki suka karaso falon suna tambayan abinda ke faruwa ta kasa fada sai kuka take tana aikawa umar zagi da kyat ta iya buda baki tana labarta masu abindake faruwa.
Murya sukaji daga bayan su ana fadin kwarai nine nan na tursasa ma yaron wucewa a yau don wanan irin shiririta naki da hauka da kikeyi.
In banda lalace da maida kai baya kin taba jin wanan haukan da kukayi jiya uwa ta dauki kafanta zuwa gidan auren yayanta tace wai sai an sakar mata diyanta ko sarakuwanta ?
Jummai na rasa inda hankalin ki da wayauki ya shiga a yanzu yara suna iya kokarin su suga kun zauna lafiya da mahaifin su amma ke kina kokarin kara bata abu.
Yaran nan don farin cikin ki a gidan uban su suke wanan abin don sharudan da mahaifin su ya kindaya maki.
Amma ke tunanen ki da hankalin ki ya kasa gano hakan jiya suna gidana da dare ni nan da yayan ki gashi nan muka tilas ta mai ya dauki matarshi su bar kasan nan suje nesa dake inda ba zakiji duriyan su ba har zuwa lokacin da hankalin ki zai dawo gareki.
Umar dane na gari don a daren jiya yayi niyar sakin yar nan idan haka kike so shiya saba da ubansh.
Mu muka hana su yin hakan don barin su aikata hakan abinda zai haifar yafi wanan haukan da kikeyi yanzu karshenta ma ku rasa Alh ga baki daya kinga waya kashe shi bakin cikin ki dake da yaran ki ya kashe masu uba.
Kina ganin yaya zasu daukeki daga baya idan haka ya faru dasu bafa zasu yafe maki ba jummai don diya ma suna da hakki akan iyayyen su suma.
Don haka nina tilasta mai dole a yau ya bar kasan nan tunda dama komai na yarinyar a kammale yake mahaifin shi ya gama shirin tafiyan su kafin ya aiwatar da komai.
Don haka ina rokon ki jummai ki bi abin nan a sannu kada rabo ya kashe ki idan ya rantse don idan kin matsa da wanan fitinan Allah na iya daukanki cikin wanan halin kowa ya huta.
Dago kai tayi ta kalle shi tun lokacin daya fara magana a falon yace kwarai kuwa rabo yana kashewa yana rayawa idan ya ratse.
Allah ana mashi dolene kamar fa kina jayaya da hukuncin ubangiji ne hakan da kikeyi.
Kince baza ayi ba anyi din da ranki da lafiyan ki kin gani kuma ba yadda zakiyi.
Kawu tana da yadda zatayi kan tunda ita ta haifi diyan ta ba shi kadai keda iko da su ba ai hjy rabi tace mai.
Rufa min baki mara kunya dama zan dawo gareku ai duk wanan abin dake faruwa da jummai da zugin ku takeyin shi.
Yar uwarku na cikin wani hali mara kyau maimakon ku bata shawaran kwarai a zauna lafiya sai ku buge da zugata ta bar dakinta ku kuna zaune naku dakunan kalau.
Ashe wanan zumuncin munafuncin zamu samay shi a cikin zurianmu kawu kamar yaya munafunci ya dakatar da ita cikin daka mata tsawa yana fadin ke rabi ki fice min daga ido har yanzu ina nan ga Adon da kika sannin a baya.
In ba munafunci ba da wani manufa naki zakiga yar uwarki na aikata ba daidai ba ki kara zugata yanzu da tazo ta zauna nan gidan dan uwanku shima so kuke ku kashe mashi nashi auran.
Tun wuri jummai kiwa kanki fada ki koma dakin ki kibar biyewa rabi da wanan mai kamar sunlobiya suna kara rikitaki don kyashi da hassada da ta dora a zuciyar ta.
Don haka yau din nan zamu je mu zauna da Alh sani yayi hakkuri ki koma dakin ki zuwa dare kuma kada naji kin muda mashi kan wanan zancen kuma.
Yaran ki sun san abinda sukeyi kuma suna da biyayya kwarai don sun zabi farin cikin ki sama da nasu ke kinfi kowa sani badon sharadin Alh ba gareki ba babu yadda za,ayi su karbi auren da basu shirya ba.
Yayan musa yace kwarai kuwa kawu don kawai suga iyayyen su a tare kowan su ya hakkure ya rugumi kadda ke kanki kin sa da ba haka ba umar da habbin ba akai masu can ba don taurin kan su ke baki la,akari da hakan.
Shine har zaki zauna kina shirin yiwa diyan ki baki akan sun zabi farin cikin ki a zauna lafiya su da mahaifi su ?
Kiyiwa kanki adalci da yaran ki idan kin masu baki suka lalace kanki kika zalunta jummai ba wani ba don kowa albarka yake sakawa nasa kullun da fatan gamawa da duniya lafiya.
Kawu yace fada mata dai dan albarka yayan yace ku kuma kada kuce ko bamu gane manufan ku bane kallon ku mukeyi sarai.
Munki magana ne muna kallon ko zaki gano manufarsu a kan diyan ki ki barsu sai dai kassh baki da niyar gano hakan har yanzu.
Nikan yaya kun tsaneni akan zancen nan wani manufa nake dashi akan antyn mu yace ki cusa yarki ga umar ko habbib dasu basu san kina yi ba har uwarsu din.
Kukan munafunci ta fashe dashi tana fadin an mata kage indai haka suke dauka tabar zancen koma tayi hakan ai ba laifin bane ta karasa fadi tana mikewa tabar falon.
Kawun yayi murmushi yace kingani rabi bata da gaskiya harke Rakiya kin san komai amma kika kasa haskawa yar uwarki hanya.
Shin in kun rabata da dakinta ko iyalinta ta zauna muna haka a gida riban mai zakuci in yar ku ta kaso auren ta da girmanta ta dawo gida ta zauna muna.
Hjy rakiya tace kawu ba haka bane ni naga ai duk gidane wa zanki wazan bari a cikin su amma Rakiya baku kyauta min ba hjy tace.
Ku barni inji da abinda ke damuna mana yake gabana mana na fada maku hakan bamai yuyuwa bane tun farko da kuka nuna min hakan ai.
Yanzu dai kyawa kanki fada Asma,u karamace a cikin ku amma ta fiku wayau da sanin ya kamata.
Don da ita muke komai a tsanake tun tasowan wanan magana itace tsaye ta bangaren ki ita taje ta zauna da yaran nan a madadin ki gidan.
Hawaye ta soma tana fadin da wani zanji yanzu da yaran da na kasa fahintar su ko da Alh da ya nuna min dani da babu duk dayane a gidan sa ko da abinda ku yan uwana kukai min ?
Yanzun dai a bar wanan zancen mu samu ki koma dakin ki ki zauna cikin iyalin ki shine mafita a garemu yanzu.
Ita gurin ta yanzu bai wuce taga ta koma dakin ta ba kamar yadda kawun nasu ya fada in yaso daga baya sai ta san inda ta bulowa zancen.
Don har yanzu bawai ta yarda da auren umar da salma bane a cikin ranta don ba zata yarda ta hada zuri,a da fakirai ba tana ji tana gani.
In ma auren zaiwa salma ai bata rasa masu sonta ba da aure amma ace wai yau almajirin su shine a matsayin surukin ta haba dai damay duniya yai kama ?
Hakama ba zata taba yarda da saka fatima a cikin dakinta ba nan gaba ta zamo mata annoba kamar yadda uwarta ta zamo masu yanzu.
Yadda kawun nasu yace haka ya faru sun samu Alh da sun bashi hakkuri yace shi baida matsala fa indai ta amince da bukatan shi a zauna lafiya.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:13 - 🤐🤐🤐: INA WA YAN UWA DA ABOKAN ARZIKI MURNA SALLAH UBANGIJI YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA ALLAH YASA MU DACE AMIN HAPPY EID MUBARAK TO ALL MUSLIMS UMMAH 👏👏👏


Tun fitan su hjy ban daina kukan da nakeyi ba sai manjo itama ta dauka tana fadin yau yar marainiyar Allah akewa haka ?
Idan sun san ba zasu rike muna ita amana ba su bamu ita mu tafi da abin mu don mu bamu gazawa da ita.
Su umma suna bata hakkuri ganin haka yasa Addah yi mun fada na daina wanan kukan da nake kada injawa kaina ciwo kokuma so nake manjo ciwon ta ya tashi ne ?
Sai kuma ta koma fadin kina wanan kukan haka anya kuwa fatima zaki iya kwatarwa kanki yanci a gidan miji da wanan shegen kukan da kike yi haka.
Rarashina suka dinga yi har na lafe na daina kuka suka koma hiran hjy da yan uwanta da suka zo suka kare haukan su sai da suka gaji.
Mama saude tace godiya ga Allah yau da bada yaya akazo garin nan ba da munji zance a gurin ta yadda take hassada kan wanan zancen.
Umma tace saidai ta mutu don da yardan Allah fatima taci gaba ke nan a rayuwan ta manjo tace Allah yasa, Allah yasa umman Atika.
Daga nesa ya tsaya ya kira Murja dax muke tare don itada Atika sune a wurina bata ko leka gidan Aisha ba tunda aka kaimu.
A falo ta samay shi tsaye yana jiran fitowan ta, yace kira mun wanan yarinyar da wani babba nata tace fatima yace mata eh a dake kice ina jiran su a falo ya fada fuska a daure.
Gabana ya fadi dam da murja ta shigo tana fadin sakon nan dai Addah ta shiruani muka fito tare daga dakin.
Yana zaune ya hade hanayen shi guri daya ya dora saman cinyoyin shi tare da dan zakudowa gaban kujeran kadan .
Da ganin sa kasan yana cikin damuwan a rayuwan shi ba sai ka tambaya ba ya fada sosao don tashin hankali da yake fuskanta.
Yana ganin yace mama sannun ku da kokari ku zauna magana nake son yi daku nace a kiraku samun wuri mukayi muka zauna ina a takure naji yana gaida Addah a mutunce yace bayan sun gama gaisawa.
Mama dama nace ai mun magana daku ne don ina son zuwa gobe karfe takwas na safe zamu bar garin nan don gujewa fitutunun da suke tasowa a tsakankanin iyayyen mu.
Zan koma bakin aiki na a can inda nake zamu tafi a gobe idan Allah ya yarda don haka a hada mata duk wani abinda take bukata a tare da ita musanman takardun ta na karatu.
Sai dai bayan shi ba zamu tafi da komai ba duk a nan zamu barshi idan akwai abinda take bukata za a iya aje mata nan gidan idan watarana mu shigo tayi amfani dashi.
Addah tace amma dai za a hada mata tufafinta ko yace har su mama idan munje can zan saya mata wasu sai dai tana iya diban kadan ta tafi dasu din .
Gobe karfe takwasa na safe jirgin mu zai daga daga kano zuwa can don haka sai ayi duk wani abinda ya dace don Allah da wuri.
Sai in akwai wani abinda kuke bukata a yanzu sai a sanar min a sawo don amfanin ku ko ya fada karshe.
Da sauri Addah tace wallahi babu komai sam barka mun gode kwarai a dai rike muna yar marainiyar Allah amana idan kuje can ita kadai muke gani mu tuna da mahaifin ta a yanzu.
Insha Allahu kada kuji komai kudai yi muna addu,a don shi muke bukata a gare ku tace insha Allahu.
Ya kara mata godiya yana mikewa ya fita a nan ya barmu saida ya fice daga falon muka koma daki mun samu suna jiran dawowan mu suji abinda ke faruwa don hankalin kowa a tashe yake da farko.
Bayan mun zauna ne take labarta masu yadda sukayi sai murja tace wai ana nufin har kayan ki a nan zaki barsu ba zakije da komai ba ?
Addah tace harsu yace a diba kadan don Allah kada a dauki masu yawa idan sunje can zasu saya sai umma Atika tace a dai saka mata hijjab da zani don sallah a can .
A cikin daren nan suka kira mamu suna sheda mata don haka ta shirya mun duk wani abinda zan bukata na tafiya a cikin daren nan.
Mamu ta nuna bata san da zancen ba sai dai batayi sanyi a gwiwa ba wurin daukan duk abin da tasa zan bukata a can ta cusa mun su a dan karamin jakkan trolley .
Karfe hudu suka tashi kafin a tayar da sallah duk anyi wanka an shirya yana fitowa sallah sukace ya kaimu cikin gida don inyi sallama da mahaifiyana.
Wani yasa ya kaimu sai ganin mu akayi mun shigo ashe mamu bata fadawa kowa ba nan dai muka samu kebewa da mamu tace to sayadi zaki shiga sabon rayuwan mai kama da incin kai kamar kuma bauta.
Kiji tsoron Allah a duk inda kika samu kanki ki sani aure bautane na ubangiji don Allah sayadi kibi mijin ki sauda kafa ki girmamashi ki bashi hakkin ki daya rataya a kanki a duk lokacin daya bukaci hakan.
Ki kula da ibada kada ki sakaci da rikon ibandan ki komai ritsi komai wahala ki rike ibadan ki kada naji wani abu akasin haka daga gare ki .
Sauran magana zamuyi a waya idan kun isa don nasan ba zai barki ki zauna haka ba waya ba ubangiji Allah yai maki albarka ya baki zuria masu albarka.
Kuka na fashe dashi duk da muryana daya dakushe don kukan dana sha kaina kamar zai tsage gida biyu Addah ce ta shigo dakin ta samay mu har mamu kuka mukeyi tace haba maimuna maimakon ki bata karfin gwiwa sai kuma kema ki zauna kinawa yarinya kuka haka ?
Nan ta tsaya tana fadin ai da alama yaron arziki ne don jiya yadda ya nunawa mahaifiyar shi cewa amana yar nan take wirin shi ya isa a gamsu dashi mu dai fatan mu Allah yasa muce gwamma da akayi .
Yanzu taje ta sallami wanan tsohuwar idan ta dawo taci wani abu kada tabar gida bataci komai ba ita ta riko hannu na zuwa part din Amma da mamaki muke kallon shi don ba wanda yasan yazo gidan .
Kasa na zube kamar bani ba gaban Amma ina hawaye tau A ruwa Allah yayi yau umar zai rabamu dake.
Kije kiyi hakkuri kinji a zauna lafiya yi nayi bari na bari manya sukace dashi ake kama miji kada inji ko in gani kin canza ga tarbiyan da muka sanki dashi.
Shi dai yana zaune yana shan tea din dake hannu shi ta juya gurin shi tana fadin sadsuki Allah ya baka ikon rikon Amana kaji .
A kwatanta adalci ya mike ba tare da yati magana ba yana aje cup din tea din data hada mai a gaban ta yace zamuje mu sallami daddy lokaci yana kurewa.
Ya fara fita ya barni a gaban Amma saida Amma taga fitan shi tace ke ki zage kada ki zama raguwa komai ya saki kiyi yadda ya dace idan ya haneki da abu kada ki yarda kiyi shi .
Idan kinyi haka kin gama samun kan mijin ki sadauki mutum ne mai saukin kai ga wanda ya fahince shi.
Ta miko mi cup din tea din da take sha tace karbi nan ki kurbe duka ki bani kofin shima haka nai masa yanzu don da haka yayi niyar tafiya baici komai ba kada ki yarda kina barin sa da yunwa kinji ko ?
Karban cup din nayi na sha ruwan tea din na mika mata kofin ta karrba mikewa tati muka fito tare a kofan falon muka hangoshi yana jiran isowan mu.
Tare dashi muka shiga yana gaba ina binsa a baya kawu yana ganin mu ya fadada fara,an shi yana fadin.
Har kun fito na gode ma Allah daya nuna min wanan ranan ko yanzu burina ya cika a kanku sadauki ka rike amana kamar yadda kaimun alkawarin rikewa.
Yace insha Allahu daddy zan rike ta dauki takardun ta kawu ya tambaya ?
Kallona ya danyi nace cikin muryan daya dushe mamu ta hada min duka to Allah yaba da sa,a yasa a dace mukace amin sai ga waya an kirashi ya dauka yana fadin gani tafe Nasir.
Nan muka fito sai Amma tace mu sallami hjy maryam haka yasa muka je kofan nata ni kadai na shiga suna zaune da wasu mata da basu tafi ba da gani a nan suka kwana matan.
Tana ganina tace fatima lafiya na ganki da sassafen nan haka tare da kashe ni da idanuwan ta duka..
Cikin wani irin murya nace nazo muyi sallama ne maman ikilima zamu tafi tace ina cikin kara fito da idanuwan ta waje don mamaki.
Zamu tafi tare da yaya can inda yake aiki gabanta ne yai wani mugun faduwa tace england Fatima kina nufin dake zai tafi ko mai ?
Muryan Amma ne daga kofa tana fadin ki fito yarnan jiransa akeyi da kyat hjy maryam ta iya controling din kanta ta fito daga part din ta sai ganin mutane tayi sun cika an rakomu dole ta wayance a furin har bakin mota aka raka mu ina kallo muka shiga baya har kawu yana wurin da kowa na gidan.
Ban san Aliyu yana cikin motan ba sai muryan shi naji yana fadin kai amarya kukan ya isa haka mana kamar mun dauko amaryan kwace.
Kada tayi shiru mana tayi tayi ta gaji ta kyale a can wa zatayiwa kukan munafunci a nan habbib ne yake fadin haka daga gaban mota inda yake ja.
A,a a bros kana

Please Login or Register in order to submit comment