You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mata dan murmushi tayi tare da fadin.
Koma ki zauna na kusa kammala ba abinda zaki iya min yanzu kan nace nafa iya girki don nike girka muna abinci a dakin mu kuma manjo na cewa yayi dadi.
Tace eh lalai manjo kan tace yayi dadi tunda girkin mu ba iri daya bane ki bari sai nan gaba kyayi ai ban dai fita ba na kama dauraye kayan da nagani tayi aiki dasu kafin in fito kitchen din.
Ban yi wani hiran dare ba tunda ban saba kai wani lokaci a falke ba da anyi magariba nake shigewa barci don hakane muna gama cin abinci nayi masu sai da safe.
Washe gari tunda na tashi ban kwanta ba a zatona tare da yaran zamu fita amma sai naga har sun fice batace min komai ba.
Haka yasa na kara shigewa na kwanta ban sani ba ashe barci ta dauke ni a can cikin barci na nake jin ana tasheni a hankali na bude idona mamu tana tsaye a kaina tace ki tashi ki shirya ga mai kaiki school nan zuwa .
Tana fadin haka ta fita ta barni a dakin na shirya wani dogon rigar na saka na tamfa sai hijjab dina dana dauko.
Na dawo falo na zauna ita kadaice duk yaran sun wuce makaranta a lokacin don haka dags ni sai ita a lokacin muryanta na tsinkayo tana fadin.
Don Allah ki natsu idan kunje don a san ajin da zasu ajeki a nan din don karatun na yasha bamban dana can sosai nna gyada mata kai kawai bata kai ga ci gaba da maganan ta ba mukaji sallama daga kofan part din ta.
Ta amsa tare da fadin Ahmed shigo mana ka tsaya kuma can ya shigo yana dan gyara natsuwan shi a natse suna gaisa wa ta kalloni tana fadin ga yayan ku na nan nace ina kwana ya amsa a dan sake da lafiya.
Anzo lafiya ko yaya mutanen gida ?
Nace suna lafiya ba tare da ya karasa shigowa ba yace idan kin shirya sai ki fito mu tafi don Alh najirana zamu fita dashi.
Hjy tace a shirya take zuwan ka take jira kawai a dauki hijjab dina dake gefe ina kokatin sakawa a jikina tace ubangiji Allah ya bada sa,a na amsa da amin tare da fadin sai mun dawo.
Ta kara fadi Allah ya tsare ya bada sa, a muka fice mun fito daga part din tane naga hjy Jummai a karon farko tun shigowa na gidan mace ce kamar basamudiya ga tsawo ga kiba sai dai bakace sosai amma tana da dan kyau fuska gaskiya.
Kallo daya tai muna ta kawar da kanta gare mu daga itama fita zatayi a lokacin don makulin motar da take kadawa a hannun ta ya nuna alama.
Kamar yadda naji ya gaida ita nima haka na gaishe ta sai dai banji alaman ta amsa mako dayan mu ba.
Muka fice itama ta fito a daidai lokacin ta shiga nata motan tare da wata mata daga cikin motar mu ina kallonta sun zuba muna ido musanman mani din suna magana.
Tunda muka fara tafiya ya kunna kira,a a motan na shek Abdullahi Abba zaria a hankali nima nake dan kama inda na iya a cikin karatun.
Mun danyi nisa da tafiya naji yace fatima kike ko na amsa a sanyaye da eh amma wasu suna kirana da sayadi wasu kuma suce min A ruwa, sai dai kakanina kawai ke kirana da a ruwan nan.
Yace Fatiman dai yafi dashi zamuyi maki amfani a school din ke nan na gyada mai kai yakara cewa, kina zuwa islamiya a can nace eh sai dai ba ko yaushe ba don ni ban iya karya ba.
Subbahanallahi naji yace har sai dana firgita ina kallon titi ko wani abu ya gani ya firgita shi ashe wai magana tace yake wa tasbihi.
Don may baki zuwa kullun yace baki san shine zai cece kiba gobe kiyama wanan ai yafi na bokon da kikaga an mayar da hankali gare shi ma,ana sosai.
Ko baki san da haka ba ya kara tambayana yana mai juya tare da dan kallo na nace naji ana fadin hakan .
Sai naga ta dan saki murmushi kadan tare da fadin ji ma kikayi baki tabbatar ba nace hakana ne gaskiya yace to kin gane ina son kiyi min alkawari daya don Allah daga nan idan mun fito zan biya islamiya dake kusa da layin ku in maki register a nan.
Don Allah ki mayar da hankali sosai ga karatun duka biyu wataran zasu amfane ki sosai jin nayi shiru yace kinji ?
Nace eh cikin gyada mashi kai kawai yace alkawari fa kika dauka zakiyi tsakani da Allah kada in kai ki kwana biyu kuma kice kin daina.
Nace a sanyaye zanyi don ko mamu naji tana maganan islamiya din gare ni yace dakyau shiyasa nake kara son halin hjy maimuna wallahi akwai sanin Allah ga al,amarinta .
To yanzu kin gani tunda itama tana so kinga hakan zai mata dadi ni kuma nayi maku alkawarin zuwa in kaiku kullun kuma in dauko ku kin yarda da hakan ?
Nace na yarda, banji kince in sha Allahu ba yace cikin dan kallo na nace insha Allahu din.
Dan dariya yayi mai sauti yace bari mu gama da nan din sai mu wuce can ganin yana shiga wani gida mai kyau yasa na mayar da hankalina ina tunanen ina zai kaini kuma ?
Sai da muka shiga naga ashe babban makaranta ne haddade mai kyau ga yan makaranta nan birjit dasu maza da matan su kowa harkan gaban shi yakeyi a gurin.
Wani wuri muka tsaya da motar yace bissimilah muje na fito bayan ya bude min motar don ban iya budewa ba.
Office din shugaban makarantar muka nufa namiji mutumin sai dai ba wani mai shekaru ba sosai muna zuwa suka gaisa da alama sun san juna sosai dashi don sai da suka dan taba hiran yaushe rabo dashi kafin su dawo zance na.
Niko ina zaune sai raraba idanuwa nake a office din sai can naji yace wanan ne yarinyar yace eh itace kanwar tawa.
Ya juyo gareni yana fadin maye sunan ki nayi saurin Fatima Abubakar Azare kallon Ahmed din yayi yana fadin na dauka ai yar garin ku ce ?
Yace a, a diyar Alh nane a azare ake tayar da ita yace masha Allah fatima wani aji kike a can nace to a can ina jss 3 muyi exam din zuwa ss1 ne .
Yace kai ya akayi karama dake karatun ki yai sauri haka amma ba matsala bari mu gwada ki mu gani.
Waya ya daga ya kira wani layi ba a dade ba sai ga wata malama ta shigo suka gaisa ya nuno mata ni yace ina son ki gwada min wanan yarinyar ko zata iya wucewa ss.
Tace yes sir tashi muje ko ta fada tana kallona na mike na bita ashe da ace ina zuwa makaranta dani gifted ce har ga Allah don Allah ya taimaka na amsa duka tambayan da tai min sai wurin lissafine na fadi daya.
Muka dawo fuskanta dauke da murmushi har suna hada baki wurin tambayan ta to yaya tayi making ?
Tace ba matsalan komai wallahi nan gaba ma zamuyi alfahari da samun ta a school din nan in Allah ya yarda.
Ahmed yaji dadi tare da washe baki mutumin yace ta biyo ka ke nan wurin kokari unlike sauran yaran da ka kawo muna gaskiya sai a hankali lamarin su.
Bamu fito ba sai da yabiya kudin komai da aka bukata har uniform sai da aka bani kafin mu bar wurin zuwa islamiyan nan ma sai da akai min gwaji akasan ajin da za a ajeni suma har uniform suka bani kafin mu dawo gida.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:42 - 🤐🤐🤐: HASBUNALLAHU WANI,IMAL WAKEEL, , , , , , ,

Ke mai kikai mata salma ta tambaya cikin wani murya ba tare da na juyo daga inda nake zaune ba nace ai gata nan ki tambaye ta .
Cikin kuka take magana tana fadin wallahi dukana tayi fa anty sallama tace what ke kika duke ta fa ??
Ashe akwai tsiya yau a cikin motar nan nace ayi tsiyan mana wake jin tsoron ku wallahi kaf din ku ina iyawa daku na fada ina zare idanuwana gare su.
Ganin hakan yasa Aisha ta dan duka tana mata magana a kunne ashe fadi take kinga yarinyar nan salma akwai abinda ta taka tunda kikaji tana fadin hakan.
A cikin daga murya tace may ko ta taka a rayuwan ta Aisha yau sai na koyawa yarinyar nan hankali gobe ba zaki kara rashin kunya ba haka.
Driver daga inda yake yana tsawata muna amma baisa mun bari ba idan sun fada mi in fada masu mai zafin da yafi nawa daci.
Har motar ya tsaya muka fito tana kaimin dangwara a kaina a zikin zafi na rike hannun na murde ta ba tashin mu daya ba dasu suda sukai tashin gata daga falo sai mota ba wani abincin kwarai ake ci ba kuma.
Sai gata tana batun faduwa nan sauran yan uwan sukayo kaina da duka nima na haukace masu ina kai masu duka iya karfina sai duk suka dare.
Wani malami da abin ya faru a gaban shi ne ya kiramu mun fara mai bayani sai ya gane rikicin gidane muka kawo har school don haka ya kwashe mu sai wurin pc.
Sai da ya gama sauraren bayanin kowa yace mahaifin ku zan kira don wanan abin ba za a kawo muna shi nan ba ku lalata muna sauran dalibai da rigima.
Nan wurin ya daga waya bayan ya nemi layin Alh a addimition book ya kirashi sun gaisa ya fara mai bayanin komai yace ya bari gasu nan zuwa.
Ba,afi awa daya ba muna rusunne a cikin rana duka yan gidan sai ga Alh tare da Ahmed sun iso hankali tashe yake kallon mu.
Nan pc yayi mai bayanin komai ranshi ya bace ya juya wurin salma yace salma yaya akayi haka ya faru da girman ki bayan kece babba a cikin ku.
Salma a ina kika koyi wanan halin banzan na rashin tausayi da zage zage a bakin da har kike iya budan baki ki zaki uwar mutum a gaban shi.
Yana fadin a cikin yanayin bacin rai a fuskan shi karara kukan da salma keyi ne ya taba min zuciya naji ba dadi a raina nace don Alh a yafe muna mun yi kuskure Salma kiyi hakkuri.
Jin hakan yasa kowa na office din kallo na da mamaki har abokan fadan nawa saida na basu mamaki.
Nan dai akai muna fada sosai kada mu kara irin hakan nace a fada masu su bar zagan min uwa a gabana don ko gobe aka zagi uwata ba zan kyale ba Abba.
Yace ba ma za a sake ba sayadi insha Allahu na amsa da to Abba nan dai muka shige zuwa azuzuwan mu har munyi nisa na cin ma salma da sauri nace kiyi hakkuri sherin shedan ne .
Batayi magana ba sai kallona da tayi kasa da sama ta wuce abinta sai dai kafin mu bar school din har labari fadan ya karade school din ko.
Inda yan ajin su salma da yake siniors ne su suna gaba damu da shekara biyu don tana matakin karshe ne ita inda su Aisha su uku muke classmate class din mu daya da Aisha.
Haka seniors sukai ta shigowa suna ba punishement iri iri ranan sai dai duk ban dauke shi wahala ba a gurina nida na saba da wahalan samarin gidan baffa na .
Don duka da zagi ba wanda basu koya min wahalan shi wasu senior har zagina suke wai don ina da kyau nake son daukan kai wa mutane.
Nan dai yan matan ss suka kewayeni kowa na fadin albarkancin bakin shi a kaina wai ni da nazo gidan su salma cin arziki nake son in kawo masu rainin wayau wai sai inba salma hakkuri a gabanta in durkusa in taba takalman ta.
Muna cikin haka sai can naji wani na fadin kai ga dan rainin wayau nan ya tunkaro ajin nan kila wani dan gulma ya kai mai tsegumin muna nan.
Da sauri suka juya don ganin wa take fadi ganin mai zuwa tare da tawagan shi ajin sai naga sun fara natsuwa ni na dauka wani malami zangani sai naga ashe dan makaranta ne shima wanda ke sasu natsuwan.
Yana gaba makaraban shi suna biye a bayan shi su biyar har yan class din naga sun shiga natsuwa a lokacin.
Tsayawa yayi daga kofa yana kare masu kallo a raina nace shi kuma waye wanan din daya shigo suka wani kamay lokaci daya.
Idon shi ya sauke a kaina lokaci daya tare dan tsura min ido sai kuma ya juya gare su yana fadin may tayi maku haka ?
Da sauri wata ta juya tana fadin zagin Salma sani tayi don tana ta, , , , ke tashi don Allah yace dani sai dana tsaya kamar ba zan tashi ba ya sake fadin baki ji bane ya sauke min kallon shi dake girgiza yanmata a kaina.
A hankali na mike ina karkarde buje daya dan kwashi kuran wurin a hankali daga haka ya juya mutanen shi suka mara mai baya da sauri naga yan matan suna ficewa class din.
Suna fita yan aji sukayo kaina suna fadin ke kan kina da sa,a don yau sai sun dandana kudan su suma a wurin shi.
Ko a mota da zamu dawo gida inajin suna magana ta kasa kasa banda salma da har lokacin tana a cikin fushi sosai da kowa.
A ka,ida idan mun dawo da mun gaida mamu sai in kwabewa kanne na kayan school muje bayi in masu wanka daga nan sai in wanke uniform din mu.
A daidai lokacin ne Nafisa take fadawa hjy jummai abinda ya faru ai yarinyar bata karasa ba uwar ta mike tsaye zubur tace wace Fatima kuke magana dai ?
Wanan dai yar ta mamu data zo zataci gaba da bata labarin yadda abin ya faru uwar ta daka mata tsawa da fadin dallah rufa min baki .
Ta juya ta fita sai part din mamu ta shigo babu ko sallama mamu na zaune tana sakawa yara tufafi a jikin su sai ganin ta tayi ta shigo tana huci.
Da sauri take fadin hjy lafiya nagan ki a hakan shiya kawo hakan don yar agolan ki ta dakar min yarinya don tsaban rainin wayau.
Ashe dama da biyu da uku kika dauko ta gidan nan don tazo ta tayaki kishi akan yayan mu .
Hjy wanan wani irin magana zaki shigo min dashi haka ban san hawa ba ban san sauka ba asali ma wanan yarinyar tunda ta shigo bata fada min wani abu ya faru a tsakanin su ba yau.
A daidai lokacin na fito zanje inshanya kayan dana wake a kofan baya wanda ake bi ta kitchen din su a fita a lokacin na tsinkayi abinda hjy jummai ke fadi.
Tana gani na tace ehhe gata ma ke may ya hada ki da yaran gidan nan har kika iya daga hannun ki kika mari Nafisa.
Mari hjy har abin yayi muni haka dama bashi kika sata tayi ba zaki wani nuna baki san komai ba yanzu akai.
Ta sake juyowa inda nake tsaye tace tambayan ki nake samun aurin yar angola har yakai ta daki yaran gida kina tunanen ki zauna lafiya.
Nace cikin dan tsiwa uwa ta take zagi niko nasan zafin uwata shine na kwabe ta na bata amsa da hakan.
Eyye ke gaki mai uwa ko to an zagi uwartaki ko ita tai abin zagi ai zaginta za a yi balle ke agolan gida.
Hjy wanan maganan bai kamata yana fitowa a bakin ki haka ba naga dai yar nan kema dai yar ki ce idan ga kara ko.
Kin bari an kara maki ne da kika shigo da fankama da isa a cikin mu suna cikin hakane sai ga hjy maryam dan gara ita ta shigo da sallama falon saida ta bimu da kallo tace.
Yanzu ran nan ke fada min abinda ya faru dazu da safe ai naje can ban samay ki ba sukace min kina nan.
Ai dole inzo gutin wanan gitsaran yarinyar da aka jajibo muna a gida da sunan agola dama nasan shigowan yarinyar nan cikin zurian mu ba alheri bane gare mu gidan nan.
Hjy maryam tace nima abin ya bani mamaki wallahi wai ace kamar wanan yarinyar ta daga hannu ta mari nafisa habadai.
Yo ba zata mare ta ba an sakata rashin mutunci don tana yar ido to bari kiji idan ma daurin gindi kika samu nayin hakan zamu zuba a gidan nan muda ke a gani.
Wanan marin sai ya zamo maki fitina da bala,i a cikin gidan nan don ba kyale ki zanyi ba ki daki banza .
Hjy wanan maganan ga yarinyar nan bai dace ba gare ki don fadan yara babba bai shigan sa don kunya zaiji daga baya don haka a tsawata mazu dukkan su kada su kara nan gaba.
Kyace haka mana tunda kin kawo muna jangwagwan a gida idan dai har sayadi jangwagwan ne a gidan nan ke nan sauran yaran suma sun zama jangwagwan a gare ku data mareta may yasa bata rama ba.
Kinga da abin wata kila baikai haka ba a ranki tunda kinji zafin marin da akai mata amma bakiji zafin zahin datayi ba.
Ranan dai sunyi nasifa sosai akan maganan inda da kyat mama hadiye da Amma suka shiga tsakanin su.
Kowa abu daya yake fada mata akan fadan yara bai kamata kuna shiga ba haka inji mama hadiye.
Kiran fatima da agola kuma fatima ta wuce a kirata da agola a cikkn gidan nan yanzu don itama gida tazo ba agolanci tazo yi ba a nan koda kuwa maimuna baga gidan nan fatima mai zuwa ne ta zauna daku.
Mama hadiye bata kai kafshen maganan ta ba tayo cikin ta tana fadin dama nasan ku da daurewa karya gindi sai dai dadin abin sunan ta dai agolan gidan nan .
Har mai gidan ya dawo gida daga kasuwa ya samu ana fitina a gidan tu a get maigadi ke fada mai yau gidan ba lafiya tunda rana ake abu daya a cikin gidan.
Wucewa yayi ba tare da yayi magana ba yana jin muryan matan ya shige part din shi don rage kayan jikin shi ranan su salma basu leka islamiya ba suna daki suna zuga uwar su wai mahaufin nasu ya goyi bayana a school daya je.
Sai bayan isha,i ya bukaci kowa ya hallara a part din shi ko wace ta shigo tana takama yana aiki shi bai kula da su ba sai bayan wani lokaci ya dago yana gyaran murya
Yace hjy mai ke faruwa a gidan nan har na dawo ina jin muryoyin ku abinda naki jini da gani a gidana abin bakin ciki ace gidana ake wanan abin.
Shiru falon yayi sai daya kara maimaita tambayan shi gare su ne hjy jummai tace Alh a gaskiya bakai muna adalci ba daga mu har yaranka yau.
Yace ni din nan danayi maku mai kuma Alh yanzu ace daidai ne ka goyi bayan yar nan yar gurin maimuna don kawai tazo agolanci sai ta taka muna yara kuma ka dauki laifi ka basu.
Jummai kin san abinda kike fadi kuwa ?
Tace ai dama yanzu kullun magana ta ba daidai bane gare ka a daki mutum kuma a hana shi kuka.
Yace su yaran suka fada maki hakan naje school din su kan fitinan da sukayi yau na basu laifi tace kwarai kuwa a to ka basu laifi mana tunda su kaiwa fada.
Mikewa yayi zuwa waje ko anan ma daya barsu sai da suka dan taba don wanan karon hjy maimuna bakin ta bai mutu ba gare su.
Karshe tace ko an sake ni na bar auren Alh dole dai ku gan mu cikin gidan nan don ba inda zamu tafi daga ni har su.
Hjy tacr ina ko zaku tafi tunda ba a iya komawa gidan tsohu aci tuwo da kuka yanzu.
Saukin abindai anan mata ta samay ni ba kuka kuma gidan kowa ana cin shi don ba abin raina wabane inji hjy maimuna din.
Kada ki sake kice zaki zagan min iyayyena ban iya wanan ba don nasan darajan mahaifana sai ga Alh ya shigo damu falon buuuu a bayan shi.
Wuri ya nuna muna mu zauna kowa ta nemi guri ta natsu ya fara tambayan karaman yar gurin hjy maryam ta koro magana tiryan tifyan ta fada mashi.
Kallon gurin da take yayj yana fafin ki fada min goyon bayan da nayi a nan don Allah ta wani tabd baki tana fadin koma maynene aikai kaja muna shidai a gidan nan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:43 - 🤐🤐🤐: SUBBAHANALLAHI WABI HAMDIHI, SUBBAHANALLAHI AZEEMUN, , , , , , ,


Mamu tayi murnan ganin har islamiya akai mun register da kuma yabona da yayi kan an gwadani na samu nasaran wucewa gaba.
Tayi farin ciki sosai da har ta kasa boye mai hakan a fili sai godiya take zuba mai tare da fatan alheri gare shi.
Bai jima ba yana gama mata bayani tare da kara ja min kunne ya bar gidan namu a daidai lokacin da nake kokarin shigewa dakin mu don rage kayan dake jikina don ban saba da hakan ba sosai mamu kanta duke tana karanta takardan da aka ban admision a makarantar .
Nakai kofa naji muryan ta tana fadin ashe makaranta daya kuke da sauran yaran gidan nan har kananin duk a can suke karatun su ai .
Banji komai ba ga zancen ta illa faman tunanen yadda zan saka dan kayan da naga yan makarantar dashi a jikin su wanda dan buje ne sai guntun hijjabin da baikai ko ina ba a kawunan su.
Har takalma da sock duk an bani a scchool din da littatafai masu yawa na karatu dans rubutu school bag kawai za a saya min a gida.
Ina tsaka da cire tufafi jikina Mamu ta shigo dakin tana fadin idan kin gama sai ki fito na kwance maki wanan kan a gyara su nan kin san duk sati

Please Login or Register in order to submit comment